You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nisa ba ya rubuta text message ya turama kowane member na ƙungiya. Shima ya kaɗa kansa ya tafi tashi sabgar sa........✍️

     

72


.........Gaba ɗaya gidan Mammah ya hargitse da farin cikin saukar Shariffa lafiya. Bakin Uncle J kam har kunne. Suka rungume juna shida Twinyn sa. Bilal da Ammar ma suka haɗasu suka rungume. Dole suyi farin ciki zuri'arsu nata ƙara yawa da faɗi. A take sukai kiran Mammah suka sanar mata, dan tana gida bata bisu asibiti ba, sai ma su Nimrah ne dake ta damunta suje-suje?.
      Da farko ta hana su ne, dan bata son su tafi su barta ita kaɗai a gidan, dan Dada da Imran sun fita. Su Kulu kuma yau juma'a sun tafi gida su gaisa da mutane kamar yanda sukeyi duk bayan sati biyu. Su Dayyan kam sai a hankali, dan zatace ma tun bayan dawowa massalaci ta sake ganinsu ba. Garama Hanoon uwar son kallo da tana maƙale da tv kafin ta tashi itama ta shige.
         Hankalin Nimrah a rabe yake, ga farin cikin samun ƙaruwa da sukai ga lamarin son haɗuwa da Dagger. Ta tabbatar idan su Ammyn suka dawo gida ba lallai ta samu wata dama ba kuma balle suna hutun tahfiz ma gobe babu, dan cikin satin sama za'ai bikin saukar ƴan ajin sauka su su maye gurbinsu. Duk da suma dai saura ƙiris ne fa. Kawai dan makarantar nada ƙa'idar bin komai daki daki ne.
    Ganin yanda suka dage Mammah tace su duba idan driver na nan, idan baya nan sai dai su haƙura kam, tunda yanzu suma zasu dawo kasancewar an haihu lafiya asibiti bazasu riƙesu ba.
     Nimrah tafi kowa zumuɗi, kasancewar tata fitar da manufa biyu ne. Koda Ruky taje ta duba sai gata ta dawo baki a sama. Wai Malam Buba ya fita. Kaɗan ya hana Nimrah ta saki kuka, ta dai daure dan kar Mammah ta fahimci halin da take ciki. Suna cikin hakan ma sai ga ƴan asibitin sun dawo da kyakkyawan Jariri mai kama da Uncle Ja'afar Masha ALLAH.
      Sam ba haka Nimrah taso ba, dan ba ƙaramin ƙwallafa rai tayi da son haɗuwa da mutumin nan tai ba a yau. Sai dai ta san wannan damar kuma ta suɓuce mata. Dole ta saki jiki aka cigaba da murnar jariri, dan tabi ta katantane ta hana kowa ɗauka saboda Nimrah akwai son yara matuƙa. Kusan ma ganin jinjirin ne ya kwashe kaso mafi yawa na damuwar tata ta ɓuya daga fuskar ta, duk da sai da Mammah ta tambayeta ganin idonta ya canja tace abu ne ya faɗa mata.....

================

       Hajiya Hasiba ta baro gidan Uncle Nasiru rai mace kiran Fomer First Lady ya sake harziƙa mata zuciya. Dan ko gaisuwa bata bari sunyi ba cikin bada umarni tace tazo tana nemanta duk inda take. Daga haka kuma ta yanke kiran batare data bari tayi magana ba. Tsabar takaici kamar zuciyarta zatai bindiga haka taji, kuma dole taje kasancewar da bazar First Lady ɗin take rawa. Akalar motar ta canja tana jan tagwayen tsaki. Mintuna kaɗan ya kawota gidan saboda gudu tai sosai.
     Securitys ɗin gidan sun riga sun san wacece ita a wajen masu gidan, tunma suna gidan gwamnati bata da shamaki. Dan haka kai tsaye suka buɗe mata gate ta shige. Tun a compound ta fara gamo da abin takaici, wasu matan ƴan siyasa dake zaman jiran son ganawa da First Lady ɗin sukai mata caaa. Sama-sama ta amsa su da cewar su jirata shiga tukunna, daga haka ta shige. Yanda bata tsaya falo na farko ba balle na biyu zai baka tabbacin lallai ita ɗin ƴar gida ce. Dan kaitsaye upstairs ta haura abinta. Ga masu aiki nata miƙa mata gaisuwa cike da girmamawa.
      A falon saman ta samu First Lady harda tsohon shugaban ƙasa, sai Zahir dake kwance a kujera zuru-zuru alamar baida isashen lafiya. Idonta akan Zahir ɗin ta gaida shugaban ƙasa da take kira Daddy, sannan ta gaida First Lady. Cikin ƙasa haƙuri ta furta, “Zahir lafiya kuwa?”.
       Kai tsaye First Lady ta amsa mata da, “Inafa lafiya Hasiba, wasu shegun yara ne a makaranta suka nema illatashi. Shiyyasa ma Excellency yace na kiraki, dan binciken mu ya nuna yaran nada alaƙa dake”.
       “Alaƙa dani kuma ranki ya daɗe? Nida yarana sun kammala har University su duka balle secondary. Sannan banda yaro namiji da har zai iya faɗa da Zahir”.
     “Ba alaƙar jini ake nufi ba. Sannan ba maza bane yaran mata ne”.
        “Mata fa! Suka masa wannan abun?. Amma ina fatan ba'a barsu ba ko Daddy?”.
       Daga First Lady har Fomer President cikin takaici sukai ƙwafa a tare. First Lady ta ce, “Yanzu ne dai zamu ɗau mataki, dan mun saka ƴan sanda sun kama su amma sun sake su wai basu cika shekara 18 ba. Sai dai sukai maganar kotu.”
        “Ai gwara aje kotun, kaji ƴan iskan yara kamar wasu ƴan daba. To wai ƴaƴan ma uban waye a ƙasar nan?”.
      “Wannan shine dalilin da yasa muka kira ki. Dan muna son musan ƴaƴan waye ɗin. Dan a bincike na naga abokin mijin Nabeeha ne yaje ya cire yaran daga station, ya kuma kai lawyer. Sannan sunje da wani gadararren mutum daya ɓoye fuskarsa shine ma yace aje kotun Saboda yaran sun faɗi wata magana. Yanzu haka sun shigar da makarantar ƙara gaba ɗaya. Shi kansa alƙalin Excellency ya kirashi kan ya kora ƙarar yace case ɗin yafi ƙarfinsa”.
        “Abokin Haysam! Imran kenan? Indai kuma haka ne zata kasance ƴaƴansa ne shi Imran ɗin. To amma waye suka je taren?”.
      “Wannan shine amsar da muke nema muma. Yaran kuma ɗaya tabbas ƴarsa ce, dan da sunan sa take amfani, suna ma kama. Ɗaya kuma Muhammad”.
         “Miye sunanta?”.
     “Naja'atu Muhammad”.
“Mom anfi kiranta da Nimrah, a register kawai ake kiranta da Naja'atu ”. Zahir yay magana da ƙyar a karo na farko.
         “Nimrah, eh lallai wannan yarinya sheɗaniyar yarinya ce. To ai itace nake gaya miki shi Haysam ɗin ya tsinto a ƙauye shekarun baya wai an kashe iyayenta. Nabeeha tace bata yarda ƴarsa bace shine ya aureta. Mafari kenna na samu Nabeeha ta baro gidan”. Salati First Lady ta fara, shiko tsohon shugaban ƙasa da bai fahimci zancen ba ya nema ƙarin bayani. Nan fa sukai masa. A kuma lokacin ne tunanin Hajiya Hasiba ya dawo baya. Ta ce, “To kodai zancen Ismat gaskiya ne. Kusan sati guda kenan muna Chaina ni dake ba Amima ta kirani ba take min bayanin.....”
      “Tabbas anyi haka”.
   Cewar First Lady.
Hajiya Hasiba ta ce, “To shine fa ni kuma na kullesu a ɗaki har yanzu na hana su fita, yanzu haka ma daga yima Uban nasu gargaɗi nake dan na zata shine ya shiryo makircin dan itama Nabeeha ya janye hankalinta. To lallai bana raba ɗayan biyu Haysam ne. Dan babu mai wannan ɗabi'ar gadarar irin tasa. To amma yaya haka? Duka yaushe shugaban ƙasa yace ya masa afuwa? Kodai makirci ne abun dama ba'a prison ɗin yake ba?”.
         Gaba ɗaya tsohon shugaban ƙasa ya ma kasa magana, sai first lady ce ta furta, “A lallai biri yayi kama da mutum. Kuma yanzu na yarda gargaɗi mai razani akama alƙalin nan. To ai inaga Hajiya Hasiba kawai ki bar Nabeeha ta koma gidan, ta haka ne zamu san gaskiya. Dan tabbas bazamu bar wannan abin ya tafi a banza ba, dole ne yaran nan sai sun ɗanɗan kuɗarsu. Bazasu illata min yaro a banza ba, dan yanzu haka likitoci sunce sai an fiddashi waje, in ba haka ba nan gaba ya samu matsala a privete part ɗin”.
       “Kai jama'a wann shaggun yara. Banƙi ta taki ba ranki ya daɗe, kanku komai kuma zan iya yi. Amma baƙya tsoron sharrin Adeel. Jiya jiyan nan nake ganin saƙonshi wai na shirya zai sake sauka a ƙasar nan, kuma wannan karon komai yake so ayi a gama”.
       “Karki wani damu, ki barmu dashi. Yanzu kawai kije ama Nabeeha gyara kona kwana uku ne ta koma a cikin satin nan. Zan tura miki kuɗi, zan kuma kira ƴar Kamaru ta sameku gida”.
          “An gama raki ya daɗe. ALLAH ya ƙara girma”.....

     
×==×===×==×===×==×

         Sai dare Dada ya dawo gidan, lokacin kusan tara. An kawo masa jinjiri domin ya gani. Nimrah dake maƙale da shi ce kuma ta kawo. Dan har faɗa sukai da Ruky babu jimawa da taƙi bata shi shine tai zuciya taje tai kwanciyarta. Itako ko alamar barci bata ji, ga yunwa na cinta taƙi cin abinci, Mammah da Ammie dake gidan sunyi faɗa har sun gaji.
      Tunda ta shigo falon ya zuba mata ido. Dan yanda ta rungume jaririn famm abinta sai tai masa ƙyau. Kai tsaye ta nufo inda yake tunda shi akace ta kawo mawa. Cikin tsokana Ammar yace, “To ALLAH yasa dai shi Dada a bashi kona minti biyar ne, dan mu minti bibbiyu aka bamu”.
     Dariya Mammah tayi, “Ai ku kun samu minti biyun ma, Mu'azz sai a hannunta ya gani. Ruƙayya kam yanzu ba jimawa ta shige tayi fushi”.
        Dariya Bilal da su Ma'aruff suka sanya, Mu'azz ya dalla mata harara da faɗin, “Ai wlhy sai na rama”.
        “Sai dai kuwa ka rame”.
   Cewar Nimrah tana murguɗa baki. Kasancewar Dada a falon kuma ya sa ta tsaya iya hakan. Takawa tai ta ƙarasa inda Dadan yake, dan shima Mu'azz ya mata shiru saboda Dadan na nan. Maimakon ta bashi sai ta durƙusa a gabansa tana faɗin, “Dada gashi ka gani a haka. Idan aka tattaɓashi da yawa zai yi ciwon jiki”...........✍️


🤣🤣ASHE Dadan ma bazai tsiraba Ninah😂🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️.



73


.......... “Bala'i”.
   Cewar Ammar suna fashewa da dariya shi da Bilal. Ja'afar ya ce, “Haba Ninah harda Dadan kuma?”.
     Baki ta tura cike da shagwaɓa ta ce, “To Uncle dan ALLAH kace masa minti uku kawai ya bani. Ko kuma na saka masa a ƙafafu daga hannuna ya gani.”
       Dariya Ja'afar da Ma'aruff suka gimtse suma, karo na farko Mammah ta ce, “Adai yi haƙuri a bashi Auta. Kinga kafin ya gama gani sai kije ki dafa Noodle kizo kici dan abinci ma ya huce yanzu, ni kuma bazan bari ki kwanta da yunwa ba”.
       Mammahn ta kalla kamar zatai kuka. “Mammah ALLAH bana jin yunwa nifa”.
    Kafin Mammah ta bata amsa kawai taji za'a ɗauke mata jaririnta. Ai firgigita ta juyo. Suka kuwa haɗa ido da mai shirin ɗaukar. Ba kowa bane kuma face Dada. Dan shi kam ya gaji da jan ran da ake masa. Kannewa kawai yake. Amma ya ƙagara shima jaririn yazo hannunsa. Rabonsa da ɗaukar jariri kamar haka har ya manta. Idanunta da suka tara ƙwalla ta risinar, dan bazata iya jurar kallon nasa ba. Sai dai fa tsabar ƙarfin hali taƙi sakin yaron, ƙarshe ma tashi tai akan gwiyawunta tai kneeling a haka ta saka masa jinjirin saman cinya, hannayenta nakan cinyar tasa itama, dan ita sam a wannan yanayin bafa ta gane ma dawa take tare balle abinda tayi.
      Babu wanda bai gimtse dariya ba a falon nan. Dan hatta Mammah kauda kai kawai tayi tana murmurshi.
        “Tashi min anan?”.
   Dada ya faɗa cikin law voice ta yanda ita kaɗai taji shi. Maimakon tashin sai ta saki hawaye sharr. A matuƙar shagwaɓe tace, “Dada dan ALLAH ka bani to, ai ka gani”.
       Shi kam yau yaga lukutar jaraba. Yarinyar nan bata san a ina suke ba ne.
         “Kina son duka?”.
    Ya sake faɗa ciki-ciki. Kafaɗa ta maƙe masa tana tura baki. Bai sake ce mata komai ba, yasa hannu ya zare hannayenta duk biyu. Zatai magana ya wulla mata kallon daya sakata duƙar dakai ƙasa. Babu alamar wasa ya sake furta, “Tashi ki wuce ki dafa Noodle ki dawo sai ki amsa”.
         “Dada kayi alƙawari?”.
    Yanda ya zuba mata ido ya kasa magana ma yasa kowa ɓoye fuska yana danne dariya. Dan duk sunji mita faɗa ɗin. Shi ko ganin yanda ta tsatstsare shi da idanu babu alamar tsoro balle shakka yasa shi jinjina mata kai kawai. Tashi tai da sauri ta nufi kitchen ɗin, sai dai tana tafiyar tana waigen babyn. Kaɗan ya rage taci karo da kujera. Mu'azz ya fashe da dariya. Sai dai hararar da Dada ya watso masa ta sashi saurin danne bakin. Nimrah data hararesa itama tai ƙwafa tana shigewa kicin ɗin.
        Bilal ya ce, “Kai jama'a, anya duk randa Ninah ta haihu zata bari a ɗauka ɗan kuwa?”.
     “Gaskiya kam da kamar wuya”.
   Ja'afar ya bashi amsa. Mammah dake murmurshi ta ce, “Hummm ina wannan tunanin nima kam, dan kwanaki fa da suka rakani barka tunda ta amshe yarinyar mutane ta hana, duk wanda yazo sai dai ya gani a hannunta. Babyn ta fara kuka akace ta bada ita maman ta shayar da ita taƙi, wai sai-dai maman ta saka nn a fida ita zata bata.”
      Dariya suka sanya sosai. Shi kansa Dada da hankalinsa ke kan Baby yana masa addu'a duk da yayi kamar baya jinsu sai da yay ɗan murmurshi. Mammah ta cigaba da basu labarin kicimillin da akasha ranar. Ta ce, “In dai fa akai haihuwa a gidan nan Nimrah da Ruƙayya basa ƙara shiri, kullum cikin faɗa suke saboda ƙarfa-ƙarfar Nimrah akan Baby. Shiyyasa yaran nan duk suka shaƙu da ita, dan rainon datai musu ko iyayen iyaka kenan”.
        Motsawar Babyn ya saka Dada cema Mu'azz yazo ya kaishi dare yayi a kwantar da shi haka nan kada sanyi ya kamashi. Tasowa Mu'azz ɗin yay ya amshesa. Ya fita kenan shima Dada ya miƙe zai haura sama dan hutawa ihun Nimrah ya ratsa kunnuwansu.
        “Wayyoooo yaji wayyo idona?”.
Gaba ɗaya suka kalla hanyar kitchen ɗin, Dada ya tsaya cak. Kafin wani ya miƙe Nimrah ta fito tana laluben hanya da faɗin, “Wayyo Mammah ki cire min zan haukace idona. Zafi-zafi na shiga uku Mammah zan mutu....”
      Mammah da duk ta rikice itama har zata miƙe dan kamo Nimrah ɗin, duk da ga Dada a kusa da inda take amma taga bashi da niyyar hakan sai kuma Nimrah ɗin data iso gab da Dada tana lalube ta taɓa shi. Ai tana jin mutum bama ta tsaya son sanin waye ba kawai ta damƙeshi tana cusa fuskarta a jikinsa, dan wani irin tashin hankali take ji da raɗaɗi har tsakiyar ƙwaƙwalwa, sakamakon yajin ya shiga mata sasai cikin idon. Gata dama koda hannu ta taɓa kayan miya sai su yini suna mata zogin yaji shiyyasa ta ƙara tsanar girki.
        Dada bashi da zaɓin daya wuce riƙeta, dan duk wanda ya kalleta yasan a gigice take, kuma dole ka tausaya mata. Gashi iyayen nata duk sun miƙe suma fuska cike da tashin hankali kamar zasu tayata kuka. Ya tabbatar yayi sake zasu iya cewa ma baya ƙaunar ƴar tasu ko ya mata mugunta.
         A nutsensa ya furta, “Ki nutsu”.
    Ina ita ba saurarensa take ba, dan ita tasan mitake ji. Shima ya fahimci hakan, dan haka ya kamata kawai yana komawa zaune a kujerar daya tashi, ita ko da yake tana a jikin nasa sai kawai ta zauna a cinyarsa. A nan ɗin ma Dada bashi da mafita, baiyi magana ba kawai ya hau ƙoƙarin buɗe mata idon, ita kuma ta ƙanƙame masa hannu tana faman tirje-tirjen da kuka da kiran Mammah-Mammah.
      Matsowa Mammah tayi ta kama hannun nata cike da lallashi tana faɗin, “Kinga ya isa nutsu a cire miki. Da ya fita zaki ji zafin ya daina.”
         “To Mammah dan ALLAH ki cire. Wlhy ji nake kamar zan haukace.”
       Bilal ya kawo tissue, riƙe mata hannun da Mammahn tayi yasa Dada samu ya buɗe idon nata. Sai ko ga ƙaton yaji a ciki harda ɗiya. Idon kuwa yayi wata masifar rinewa jazurr kamar garwashin wuta. Tissue ɗin hannun Bilal ya amsa, yana saka mata taji zafin yafi nada, sai kawai ta sake ƙanƙameshi tana son ƙwace kanta. Sai dai riƙon na manya ne, dan haka ya matseta da ƙyau sai da ya cire shi gaba ɗaya.
    Babu wanda baiji tausayinta ba da ganin yajin babba da shi. Ita ko ta kife kanta tana sauke numfashin wahala da sauran azabar da take ji akan ƙirjinsa. Dada da ya san wannan yanayin haɗari zai zama mai girma da shiga cakwakiya sai kawai ya miƙe a hankali da ita a jikin nasa ya nufi doguwar kujera ya kwantar da ita. Yana ɗagowa zai bar wajen suka haɗa ido da su Ma'aruff dake murmushi. Da sauri suka gimtse shi da Ja'afar. Shima sai ya ɗauke idanun nasa cike da basarwa kamar bai gansu ba ya bar falon gaba ɗaya. Sai da suka tabbatar ya gama haurawa staircase ɗin suka fashe da dariyar. Kallonsu Mammah tayi itama, da sauri suka sake gimtsewa.
     Ammar, Bilal da Mu'azz daya dawo yanzu basu fahimci inda dariyar Yaya Ma'aruff da Yaya Ja'afar ta nufa ba sam. Itama Mammah da farko ba fahimta tai ba, sai da taga suna satar kallon upstairs suna ƙus-ƙus sannan ya harbo jirgin su. Kanta kawai ta girgiza tana maida hankalinta ga Mu'azz tace yaje ya ƙarasa dafama Nimrah indomie ɗin taci taje ta kwanta.......

^^^^^^^^^^^^^^^^

           A wannan daren ƙungiyar duhu sukai meeting na sirri. Meeting ɗin da gaba ɗayansa ƙulle-ƙullen masifu ne na tashin hankali ga ƙasa dama shugabanta Janar. Dan abinda yay musu sun tabbatar da babu bashi sai sun hukuntashi. Sai Dada, gaba ɗaya shirinsu a kan Dada kuwa ya ta'allaƙa ne akan yin amfani da Nimrah. Sun fahimci dole su canja taku, takun da zasu haifar da rauni mai raɗaɗi da ƙuna a zuciyar sa. Wannan kuma raɗaɗi da ƙunar ba zasu iya samar da shi ba sai ta hanyar taɓa zuri'arsa. Ta ko ina kuma sun fahimci dole sai da wani na jikinsa zasu iya hakan, musamman da a yanzu tsaro yayi yawa a gidan, dan Mole ya zama mai kawo musu bayanai sosai akan gidan yanzu fiye da Dagger. Hatta haihuwar Shariffa ta yau ɗin nan tazo kunensu, shima Dagger ya sanar musu kiran da Nimrah tai masa da buƙatar su haɗu da tayi sai dai hakan bai faru ba sakamakon rashin fitowar ta. Ta haka ne ma suka sake samun tabbacin Zak-Shadow ɗin ne dai a gida Mole baiyi ƙarya ba.
        Sai da suka gama tsare-tsaren su iya su manyan Sannan aka sake wani sabon meeting da saura members duk a daren dai. Hukuncin da suka yanke da tsarin da suka kammala yi yasa shima Dagger suka buƙaci ganinsa zuwa safiya. Dan yanzu kam aiki ne zai tashi ba wasan yara ba. Sannan zasu bama Mole dama irin ta Dagger, sai dai ba'a kan Nimrah ba. Nimrah Dagger zai cigaba da aiki kanta kamar yanda ya fara tunda ta riga tasan fuskarsa. Canjawa zai saka ta iya zargin wani abu daban tunda sun fahimci tana da wayo............✍️


Idanunsa dake lumshe shima ya buɗe yana sauke ƙaramar ajiyar zuciya, kafin ya ɗagota a hankali zai maidata ya kwantar ta sake ƙanƙamesa cikin ƙunƙunan barci name magagi tace, “Uhmm-uhmm Mammah, ni zan kwanta ana....”
       Batare data ƙarasa ba ta cigaba da barcinta. Wani ɗan murmushi mai fidda sauti cikin ƙirji kawai ya saki. A ransa yace (Trouble maker, idan kin kwanta anan ni kuma twin ɗinki ta farka ta ganni fa?). A zahiri kam kwantar da ita ɗin yayi a hankali, sannan ya haska mata fuska da waya. Idon da gefensa har ya kumbura, yakai hannu ya ɗan shafa wajen kaɗan, sai kuma ya ɗan furzar da iska yana zame hannunsa data riƙe gam a ƙirjinta. Sake ƙoƙarin cafkowa tayi, kawai ya saka mata bargo a ciki. Sai ko ta damƙe tana juya kwanciya ta matse bargon har abin yaso bashi dariya ma, ya dai gimtse ya tashi abinsa da ledar maganin ya fita, dan yasan idan ya bari da safe sai sunta shelar neman waya ajiye a gidan, ba man kai ne da su ba.

               °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
       °°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

           Washe gari gidan Mammah ya cika da ƴan barka. Musamman sashen su Lailah. Danginsu sai zuwa sukeyi. Sai dai duk wanda ya shigo sai yazo ya gaida Mammah. Kuma duk wanda zai shigo securitys ɗin nan sai sun masa ƙwaƙwaf.
      Yanayin da Nimrah ta tashi akan idonta ya taƙaita al'amarin tana nanuƙe da Mammah. Ruƙayya kam duk ta damu kamar zatai kuka. Kaɗan-kaɗan saita ce, “Ninah ba zafi?”.
     Tun Nimrah nace mata eh, harta koma tsokanarta idan ta tambaya sai tace akwai, sai taga ta damu sai ta saka dariya. Mu'azz ya tasa su gaba da tsokana sai da Mammah ta Koresa a falon. Hakama Afeef ko sau ɗaya bai nuna tausayin Nimrah ba balle Hanoon. Biebah kam har ɗan gasa mata idon tayi da ruwan zafi dan fuskarta ya ɗanyi fushi, a haka ma dan Dada ya saka mata magani ne ai da ba'a san yanda zata tashi ba.
     Har kusan sha biyu Dada bai sakko ba. Dan haka Mammah tace Nimrah dake zaune Ruky tayi filo da ƙafarta tana barci ta tashi ta kai masa abincin breakfast. Saboda ta kirashi a waya yace aiki yake shiyyasa. Kuma yaga yau gidan nasu hayaniya tayi yawa. Mammah tace shike nan bari tasa a kawo masa. Shine ta yanke wayar tace Nimrah ɗin ta tashi.
        Cike da shagwaɓa Nimrah ta ce, “Mammah banda lafiya fa”.
            “Haba auta, to wa kike son ya kai? Bakiga Ruƙayya barci take ba? Mamanku kuma tana aiki a kitchen”.
    Caraf Hanoon ta ce, “Mammah kawo naje”.
    Kafin ma Mammah ta bata amsa Nimrah data watsa mata harara ta miƙe. Ta sake watsama Hanoon kallon banza tana nufar tray ɗin da kulu ta kawo da faɗin, “Dama mutum ya kama kanshi. Mu uban mu bazai auri finga-fiyau ba. Mace sai kace taɓaryar gwari ba sama ba ƙasa.” dariya kamar zata kashe Kulu, da ƙyar ta iya matsawa ta shige kitchen. Hanoon kam da kallo tabi Nimrah dan ba komai ta gama ganewa ba. Mammah ta girgiza kai tana murmushi, a zuciyarta addu'a take ALLAH ya shirya mata Nimrah da Ruƙayya ita kam. Yara baƙar magana a bakinsu kamar dangin mahauta. Muhammad ne yay tashen baƙar magana yana yaro, ba yawan surutu amma idan ya yaɓa maka mai zafi kamar ka mutu. To ga magada nan ya samu har suna neman zartashi.
        Koda Nimrah tazo kofar ɗakin sai abinda ya faru jiya ya shiga dawo mata. Bana tattaunawarta kawai da shi ba, harda na abinda ta gani, har yanzu take neman mafitar fita amma ta gagara samu. Tafi minti ɗaya a tsaye kafin tai sallama dan babu daman knocking hannunta da tray. Sarai ya jita amma yaƙi tasowa ya buɗe mata balle amsawa. Yau ƴan sarautar ne aka. Itama jin shiru babu motsin kowa tayi kuma har sau kusan huɗu sai kawai ta rungume tray ɗin da hannu ɗaya, cikin dabara ta saka ɗayan ta buɗe. Koda taci karo da shi a zaune sai da taji shock. Ta ɗanyi diri-diri sai kuma ta nutsu jin tana neman yin ɓari.
      Yi yay kamar baima jita ba. Nan ko ya gama kalleta ta gefen ido. Amma sai ka rantse hankalin nasa akan rubuce-rubucen da yake yi yake. Ƙananan kaya ne a jikinsa, yanda rigar ya kamashi sosai gashi ƙaramin hannu yasa kallo ɗaya datai masa bata sake gigin yin na biyu ba.
Sai kuma ta tafi tunani mara dalili daya sakata shagala a wajen ta kasa ƙarasawa ta ajiye abincin..
         “Idan kikai ɓarin abincin nan sai

Please Login or Register in order to submit comment