You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cigaba da musu sai addu'a da fatan suma ALLAH ya basu masu yi musu”.
Gwaggo Nanah dake jinjina kai ta ce, “Wlhy ki musu ki ƙara muma muyi musu, ga gidan Yaya Babba can su Haire su da surukai ba arziƙi. Jiya matar Haƙilu kamar zatai dambe da Haire akan ɗanta, ke bakiji wannan tujara ba abin kaico”.
Murmurshi Mammah tayi, saboda a saki zancen ta ce, “ALLAH ya ƙyauta to, ai zamanin ne ya zama abin tsoro sai addu'a kawai. Kunga kuyi wankan kuzo ku karya hirar tafi armashi”.
Godiya suka yi ta juya ta fita. Dukan su suna jin ƙaunarta a ransu, Badiyya kam kunyarta take ji sosai shiyyasa tunda suka gaisa tai shiru kanta a ƙasa. Sarai Mammah ta fahimceta, dan haka ta ƙuduri aniyar cire mata abinda ke ranta gaba ɗaya, dan ita babban fatanta ta haɗe kan zuri'ar Abdul-rasheed ba rabuwar kansu ba....

★ Sai sha biyu su Nimrah suka tashi da ƙyar, shima sai da Mammah tazo da kanta ta tashesu. Dan suna yin sallar asuba suka koma gado. Aiko sai shagwaɓa suke mata wai ta barsu sai ƙarfe ɗaya sannan.
“Shike nan kun fasa zuwa gidan sunan kenan? Ai da nasan haka ne sai na tadaku kun wuce Tahafiz. Ga ƴan Bauchi can tun sha ɗaya suka iso ku kuna nan kuna barci”.
Tuni duk suka watsakke, cike da farin cikin jin zuwan ƴan Bauchi. Zasu nufi ƙofa a guje Mammah ta dakatar da su. “Kai kuji min ƙazaman banza. Haka zakuje musu da kayan barci? Ba brush kamar wasu ƙazamai. Maza ku koma ku gyara jikinku, wata taje ɗakin Biebah yanda zakuyi sauri”.
Cike da farin ciki sukace to. Mammah ta fito tana murmurshi. Koda ta dawo falon wajen su Gwaggo Alawiyya ta samu su Ma'aruff sun iso gidan. Dan tun ɗazun ta sanar musu sukace zasu zo yanzu. Sai ko gasu da ledoji niƙi-niƙi na kayan ciye-ciye. Fuskokinsu washe da murmushin ganin gwagwgwannin nasu. Badiyya na sinƙe-sinƙen kai ganin yanda suma basu nuna mata komai ba kamar Mammah sai ta ware aka fara gaisuwa da tambayar yara. Yaya Ja'afar ya ce, “Haba Gwaggo, kwa taho ku kaɗai duk babu yara? Bayan kun san ba ganin juna ake ba tsahon lokaci sai irin haka ta faru”.
“Makaranta tasa haka Ja'afar, amma in sha ALLAHU idan anyi hutu sai su zo. Tunda kudai kun tattaramu kun watsar, yaushe rabonku da Bauchi balle Maiduguri?”.
“Dama idan sunje Bauchin ba ganinsu muke ba Adda Khadijah, iyakarsu gidan Yaya Jamilu da Adda Alawiyya. Dan nidai sau biyu suka taɓa zuwa min lokacin rasuwar Inno surukata, da ciwon Ahmadi”.
“Munyi laifi Gwaggo Nanah, amma kiyi haƙuri zamu gyara in sha ALLAHU. Wani lokacin abubuwan ne ke yawa. Mafi yawan lokuta kuma zuwa Bauchin kasuwa ke kaimu. Ki tambayi Aunty Badiyya sau da yawa shima Uncle Jamilu a kasuwa muke samunsa ba gida muke zuwa ba. Itama Gwaggo Alawiyya takan jima bata gammu ba. Maiduguri ne dai kam ma zamuce muna shiga dan ziyara kai tsaye”.
“To na gamsu, amma dan ALLAH a gyara, mun san mu masu kuskurene a gareku, amma kuyi mana afuwa kunji, Yaya Abdul-rasheed mutum ne mai son zumunci da Adda A'isha da Adda Yakura, na tabbatar kuma akwai wanan jinin alkairin nasu a tare daku, kar ku biyema aikin son zuciyar wasunmu ku watsar damu gaba ɗaya. Suma lokaci zai yi da zasu yi nadamar abinda suka shuka. Dan har ma wasu sun fara, Yaya Babba a tsakanin nan babu abinda yake sai tafka asarori kala-kala, ga yara cike da gida, mata har huɗu. Yaya Haruna ne ma za'ace da ɗan sauran damshi-damshi. Shi ko Yaya Garzali ma yaje ya tare saudia aikatau ƙiri-ƙiri ko takan matan baya bi sai ya gadama.”
Sosai zancen ya girgiza su. Sai dai basu ce komai ba face ALLAH ya ƙyauta. A haka Ammar ya shigo shima da Mu'azz. Nan fa falon ya sake lacamewa da farin ciki. Sai kuma gasu Nimrah na fitowa cikin kwalliya tsaff suna baza ƙamshin turaren da suka satarma Aunty Biebah na SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Cike da farin ciki suka rungume Gwaggo Alawiyya da Gwaggo Khadijah dan su suka sani sukam. Abin birgewa bazaka taɓa cewa ba jininsu bane su. Sun gaida su Gwaggo Nanah suma. Suka amsa musu da kulawa duk da basu san alaƙarsu da gidan ba. Garama Fiddo ƴar Aunty Mommy data kwana a gidan itama, tunda sun jajje Bauchin ita.
Gwaggo Khadijah ta ce, “Oh ni Dije Maman Ma'aruff ƴan matan nawa duk sun miƙe. Kaga yara kamar wasa sun ƙosa. A wannan sai aure”.
Caraf Mu'azz ya ce, “Tab ɗin wazai kwasa Granny? Wannan gayyar ciwon kan da basu iya komai ba sai dambe da neman masifa da ƴaƴan mutane”.
Baki duk suka tura gaba. Gwaggo Khadijah ta ce, “Kunga ƙyaleshi ƴan uku Ko nace ƴan huɗu dan banbu Bintu ne. Ai ana yin auren duk zaku daina ko. Kuma dai ai kowa da ƙuruciyarsa, shima idan za'a faɗi abinda yayi ai sai kowa ya gudu”.
Dariya suka shiga yima Mu'azz suna masa gwalo, shiko yana hararsu da musu alamar zai kama su. Su Yaya Ma'aruff dai na murmurshi ne, Yaya Ammar kam dining ya nufa yana faɗin shifa yunwa yake ji, mi aka dafa ne?. Miƙewa su Nimrah sukai suma suna faɗin yunwar suke ji. Daga haka suka koma kan dinning ɗin harda su Mu'azz aka bar su Yaya Ja'afar suna hira da su Gwaggo Khadijah.....

<<%>><<%>><<%>>

Da yamma shagalin suna aka sha sosai a gidan Aunty Mimi, duk da kuwa haihuwa ce ta huɗu tayi. Babu ƙarya su Nimrah sun cashe da rawa iya iyawarsu. Kasancewar hall aka kama iyakar kuma mata ne kawai a wajen dan ko su Mu'azz basu shiga ba sai abin ya ƙayatar. Ƙarfe shida aka tashi saboda sallar magriba. Nan fa motoci suka fara ɗibar mutane zuwa gidajensu. Su Nimrah dai yau a gidan Aunty Mimi zasu kwana. Dan haka sukabi ƙanin mijinta da yazo kwasar yaranta dana family ɗin mijinta.
Duk da dai da farko ca sukai su bazasu shiga cikin yaran ba, sai da Aunty Shariffa ta fara musu faɗa da tabbatar musu zako ta kaɗa kansu zuwa gida sannan suka nutsu saboda suna son zuwa can ɗin su ƙarasa weekend ɗin su. Ga Bintu kuma ta ƙaru sun zama su huɗu yanzu.
Haneef dake matuƙar son Ruƙayya na sharewa yana faman murmushi yace su jira shi ya kai yaran ya dawo to. Feedo ce ta amsa masa da “To Uncle”. Su Ruky kam aka wani ɗauke kai gefe. Murmurshin shaƙiyanci Nimrah tayi, tare da ɗagama Bintu gira ɗaya cike da gulma. Aiko suka kwashe da dariya. Ruky da tasan da ita suke ta balla musu harara da jan tsaki zata bar wajen Nimrah ta riƙota........✍️
KIƊA A RUWA 2

27

.........“Sorry Trouble Buddy na. ALLAH ke ɗin ce kin cika wulaƙanci, Uncle Haneef fa ya haɗu ALLAH. Amma kiyita wani shan ƙamshi. Dan ALLAH ko kaɗan ki dinga kulashi mana, ALLAH idan ya ganki zakiga duk bakinsa yaƙi rufuwa”.
“Ai shiyyasa bazan kulashin ba. Ni fa bana son susun namiji haba. Mutum babu wani jan aji. Kuma ni an faɗa masa za'a min aure ne yanzu mtsoww!!”.
Bintu dake dariya ta ce, “Baby ai kece zaki saita shi yanda kike so. Amma kina wani yayyarfashi, jifa da salla yanda ya mana siyayya”.
“Mayya dama ke ai kwaɗayi ne zai kashe ki ke da Ninah”.
“Ya kashe mu dai, tunda tare muke”. Cewar Nimrah tana hararta. Ramawa tai itama, sai dai dai-dai nan Haneef ke dawowa dan haka hirar tasu ta tsaya. Fitowa yay da kansa ya buɗema Ruky gaba, zata zille ta shiga baya inda su Nimrah ke shirin shiga suka turata suna ƙumshe dariya. Juyawa Haneef yay ya kallesu da musu jinjina yana murmurshi. Daga haka ya rufe mata ƙofar ya zagaya dan suma har sun rufe.
Yana fara tafiya a titi ya ɗan kalla Ruky, cike da son birgeta ya ce, “Muje shan Ice-cream ne Baby?”.
Kai ta girgiza masa alamar a'a. Sai ya ɗan marairaice fuska, tare da maida lallonsa kan su Nimrah dake baya ta mirror. “Yaran Uncle muje mu sha ice-cream ne?”.
Cike da iyayi Feedo ta ce, “Yes Uncle”.
Nimrah zatai magana Bintu ta rufe mata baki, dan sun san bakinta ɗaya da Ruky. Ganin zata fisge itama Feedo ta ɗaura nata hannun akan na Bintu suka haɗu suka danne Nimrah. Sai da ta sakar musu wasu shegun mintsini masu zafi suka saketa kowanne na sosa wajen. Badan Nimrah da Ruky sun so ba akaje wajen shan wannan ice-cream dai. Haka ya jasu har ciki kowacce ta zaɓi flavor ɗin da take so. Ya ƙara musu da snaks. Duk yanda suka so ya maida su gida ƙi yay, haka ya janye ra'ayinsu suka zauna a wajen. Sai dai rashin sabo ya sasu kasa sakin jiki su dukansu. Dan abu ne da su dukansu ba tarbiyyarsu bace. Shi ko yanata tsiyaya musu zance da ɗaukarsu hoto da wayarsa iPhone.
Ganin fa an fara sallar isha'i hankalin Nimrah ya tashi. Dan in har ka gansu a waje irin wannan lokacin tabbas da wani a cikin Uncles nasu ne ko Ya Mu'azz ko Aunty Biebah ko kuma sun raka su Aunty Lailah anguwa ko Ammie. Amma basu kaɗai ba balle wannan da saurayi ma wai.
“Nimrah ya naga kin miƙe?”.
Haneef ya faɗa yana kallonta.
“Uncle Haneef kayi haƙuri ka maidamu gida. Wlhy idan Mammah taji zatai mana faɗa, balle Daddy ko su Uncle's”.
“Haba-haba ai in sun san nine babu wani faɗa da zasuyi”.
Miƙewa itama Ruky tayi, hakan yasa suma su Feedo duk suka miƙe. Kafin ma Nimrah ta bashi amsa Feedo ta ce, “Wlhy Uncle koni Abbana ya sani ubana zai ci. Muje ɗin kawai ma ƙarasa a gida”.
Babu yanda ya iya dole ya miƙe, ya tayasu tattare kayan suka fito. Kamar ɗazu yanzu ma dole Ruky gaba ta shiga. Cikin ƙankanin lokaci ya iso gidan Aunty Mimi da su. Yay horn maigadi ya buɗe masa gate ya shige. Suna fitowa a motar maigadi ya iso inda suke. Kai tsaye gaban Nimrah ya isa yana miƙa mata ledar hannunsa da faɗin, “Hajiya gashi wani yace a baki. Yata jiran dawowar ku amma yaji shiru yanzu babu jimawa yabar wajen nan.”
Ba ita ba hatta su Ruƙayya da mamaki suke kallonsa. Cikin kasa daurewa Nimrah tace, “Kuma ni Nimrah yace a bamawa?”.
“Tabbas ke yace, yace sunansa Kamal malaminku na islamiyya”.
Ruky ce ta amshi ledar tana faɗin, “Wato shima Sayyadi Kamal ɗin nan ɗan naci ne fa na lura”. Daga haka tabar wajen fuuu. Tsaff su Nimrah sun fahimci fushin Haneef tai amfani da shi akan Kamal. Dan haka suka wayance da masa godiya suka shige cikin gida.
Sun sami sauran dangin mijin Aunty Mimi da basu kai ga wucewa ba. Suka gaishe su suka wuce ɗakin da suke sauka in har sunzo gidan. Dama can suka kai kayansu da daddare. Ƙaton gado ne da zai iya isarsu koda su shida ne a ɗakin, sai wadrobe da mirror, sai ƙofar bayi. Kayan hannunsu duk suka ajiye suna zubewa a gadon kowa na faɗin wash, dai-dai nan Ruky data rigasu shigowa ta fito daga bayin alamar har tayi alwysSuma duk miƙewa sukai, dan rashin yin sallar akan lokaci na tsaye a ran kowannensu. Bintu ce kawai ke period dan haka taja ledar snaks ɗinsu ta fara ci tana faɗin, “Bari muga mi Sayyadin ya aiko mana da shi shi kuma”.
Tsaki Nimrah tayi a karo na farko tana shigewa bayi abinta. Fiddo ta sanya dariya dan Ruky ma harta kabbara salla. Dariyar su Bintu data cika ɗakin ya saka Nimrah fitowa da sauri, itama Ruky dai-dai tana idar da sallar ta juyo tana kallonsu. Litattafai ne a ledar saƙon Sayyidi Kamal suka nuna musu. Feedo ta ce, “Wannan fa shine auren ustaz ɗin, kaga wata lukutar jaraba wai saƙon littafai. Ninah kina cikin yanayi gaskiya”.
Nan ma dariya suka sanya harda Ruky yanzu kam. Dan haka Nimrah ta watsa musu harara ta kabbar sallarta itama. Koda ta idar sun gama mata shaƙiyancin nasu, dan haka bata sake tada zancen ba ta haye gadon ta kwanta wai kanta ke ciwo. Da ƙyar suka lallaɓata ta zauna suka ƙarasa shan Ice-cream ɗinsu da snaks ɗin bayan Feedo ta idar da salla itama. Dan haka koda Aunty Mimi tai kiransu suzo su ɗeba abinci sukace mata sun ƙoshi. Bata takurasu ba dan taga abinda suka shigo da shi, ta kuma san aikin Haneef ne......

<<<<<<(⁠✷⁠‿⁠✷⁠)>>>>>
★CAMPAIGN★

Kwanaki 100 na campaign suna gab da cika, dan kuwa ana satin ƙarshe na kammala taron kowane kamfen. Dan haka amsa kuwwar cikar kwanakin tamburan siyasa na gab da cika, tako ina ƙasa ta kara hargitsewa dan kowa burinsa satin ƙarshen nan ya tumfayesa da zuciyar yan kasar. Baka iya jin komai sai sautinkan waƙoƙin da aka rairana ƴan siyasa. Yayinda hankalin matasa kacokan ya koma can. Wasu ma sun ajiye harkokinsu da sana'o'in su ne kacokam. Kamar dai yanda aka saba alƙawuran nasu guda huɗu ne ga al'ummar ƙasa a lokacin da suke kan munbarin campaign. Zamu gyara muku harkar karatun, zamu inganta wutar lantarki, zamu wadata ku da ruwa, zamu gyara asibitoci.
Cikin rashin lissafi da auna abubuwa a yanda ya dace, da taro da kwabon da ake raba mana mu talakawan ƙasa da ɗan sabulai da zannuwan ɗaurawa mai hoton ƴan siyasar a jiki sai kaji mun sallama muna bada kai bori ya hau. Babu ruwanmu da tantance wane shugaban ya dace damu? Mi muke so a ƙasar da kawunanmu bayan waɗan can lissafin huɗu da ko a karatu sukazo ya kamata ace mun haddace su tsaff zuwa yanzu daga daɗin bakinsu mu nemo cigabansu. Amma ina babu batun tantancewa, a wasu wajajan ma siyasar ta haɗa rigima ne tsakanin ƴan uwan juna saboda ni ina son wannan wane ɗan uwana yana son wancan ba jam'iyyar mu ɗaya ba. Wasu har gaba zakaga ta ƙullu mai girma a tsakaninsu. Yayinda su ƴan siyasar da sukeyi domin su suna can tare suke shan shayi, tare suke ƙulla mai fishshesu musamman akan abinda zasu ribantu da shi game da kuɗaɗen da suka kashe wajen jawo ra'ayinku idan sun haye. Wanda ma bai haye ba akwai hanyoyin da za'a bi dan maida masa wahalarsa ta bayan fage kune a ruwa...

Alhamdullahi duk da irin tasu tafiyar bata banbanta data Janar Yusuf ba a yau kasancewar a ƙarƙashin damarsu ya ke shima a siyasar kamar saura abinda shekarun baya suka zo da shi wajen campaign shima dai shine a yau yake zuwa da shi. Kuma Alhamdullah zamu ce akwai nasara a al'amarin dan yana da magoya baya sosai a cikin jam'iyya da al'ummar gari.
Abinka da soja, a kwanakin kai-kawon duk da wahala da jigatar rashin barci dana hutu zuciyar maza a tsaye take da ƙyaƙyƙyawan fata. Tun ana farkon satin nan da sukai zama da Imran ya kuma gana da Uncle Nasiru basu sake haɗuwa ba. Dan a zahiri Imran baida alaƙa da siyasar Janar. Gara-gara ma Uncle Nasiru har campaign ya rakashi sau biyu. Duk wani abinda ya dace su tattauna sun kammala sun ajiye kundin shirinsu gefe har sai ta ALLAH ta kasance. Wato aci zaɓe ko a faɗi...
Tsahon kwanaki sun cika cir, awanni 48 ya rage a fara jefa kuri'a, dan haka batun campaign komai ya lafa a koma jiran ranar jefa kuri'a da gwamnati ta riga ta fitar kuma kwanaki 2 ne kacal, dan yau alhamis....

★_______★
★RANA BATA ƘARYA
Yau safiyar asabar. Safiyar zaɓen shugaban ƙasa. Duk wani masoyi na yan takara a kowane ɓangare jikinsa na'a farce ne. Ba yan takara kaɗai ba da zuri'ar su yan kasa kansu kowa hankalinsa nakan fata ga wanda yake so. Dan haka kasar ta wayi gari a yanayin sai addu'a kawai. Wasu cike da fata, wasu cike da tsoro duk da tako ina jami'an tsaro na aikinsu ne.
A ka'ida daga shekara sha takwas ne za'a iya saɓe zuwa sama. Dan haka su Nimrah basa cikin masu jefa ƙuri'a. Amma ganin su Mu'azz zasu suka maƙale zasu je. Mammah kam Daddy Imran da kansa yazo ya ɗauketa ita da Hajjo ya kaisu suka jefa kuri'arsu da wuri sosai tare da Janar Yusuf Shu'aibu Tafida da iyalansa. Duk da dai ba kai tsaye Daddy Imran ya fito a tawagar janar din ba saboda bada ƙafa. Amma janar na jefawa da iyalansa suna a rukuni na biyu da suka jefa suma. Daga can Mammah tabi Hajjo suka wuce can gidan dan suma su Gwaggo Khadijah zasuje gaida Abba, amma su basuje jefa kuri'a ba daga gida za'a kaisu can tunda Mammah ce ta riƙesu tace sai an gama zaɓe zasu koma gida, kuma acan suke da mazaɓa.........✍️KIƊA A RUWA 2

28

..........A ƙafa zuri'ar Mammah suka fita domin zuwa jefa kuri'a dan anan cikin street ɗinsu ne mazaɓar tasu take, dan babu wanda aka bari a gidan har su Afrah. Kasancewar anguwa ce ta ƴan gayu babu hayaniyar mutane, wasu ma duk sun koma state ɗinsu jefa kuri'a a can yasa anan ɗin babu yawan jama'a babu hayaniya balle damuwa. A nutse su Uncle Ma'aruff da su Aunty Shariffa suka jefa har zuwa kan Mu'azz karamin gidan. Kuma alhamdullahi dukansu Janar Yusuf suka dangwalawa. Suna kammalawa suka juya zuwa gida abinsu. Nimrah da Ruky ne a gaba, suna tafiya da baya-baya Mu'azz na musu video dan Nimrah harda Teddy ɗinta ta fito. Dan haka su Abees keta binta dan suna son taɓa teddyn magen. Daga ita har Ruky abaya ce a jikinsu, su duka sun musu ƙyau, tare da fidda tsayinsu masha ALLAH...

★WASHE GARI aka tashi da batun sakamakon zaɓe. Hankalin su Nimrah ba'anan yake ba. Bama kuma su fahimci miye damuwar ƴan gidan da batun sakamakon zaɓen ba da suketa bibiya tun jiya. Dan kamar wasa ranar ma a gaban television suka yini. Har kuma akai sallar magriba babu wani bayani, sai da aka dawo sallar isha'i suna cikin cin abinci aka sanar.....

A wannan daren ba gidan Mammah kawai ba ake jiran jin sakamakon zaɓen shugaban ƙasa ba, kusan ƙasar gaba ɗaya a kowanne gida hakan take, dan yau Daddy Imran salla kawai ke sakashi matsawa a gaban television amma ko abinci sai Anmie ta matsa masa ma yake cinsa, shima laumomi ne kawai. Ga Asma'u da Khalifa nane da shi suma. Zuciyarsa kam cike take da tsoro da fargaba.
A wasu gidajen kuwa irin namu na talakawa an kunna fitilu ƴan uwa da abokai sun taru a gaban rediyoyi suna jiran murya ɗaya tak ta shugaban zaɓe, murya ce da zata faɗa musu ko tarihin ƙasar za’a sake rubutawa ko zai sake maimaita kansa ne da wanda ba zaɓinsu ba.

★★★

Ko'a gidan tsohon Janar Yusuf Tafida ya ɗauki wani irin shiru mai nauyi. Yana zaune a kan kujerarsa mai laushi, hannunsa riƙe da remote, television ɗin a kunne amma zuciyarsa na bugawa da ƙarfi. Matarshi, Hajiya Zainab, tana zaune a gefensa, hakama kaf yaransa har mazan dake da mata na a falon zaune zagaye dasu kowa zuciya na rawa da addu’a, dan sun san yanda mahaifinsu ya ƙwallafa rai akan shugabancin nan yana buƙatar sanda za'a sanar da wa ya samu ace suna kusa da shi. Hakan zai bashi ƙarfin gwiwar amsa daga abinda ƙaddara zatazo da shi.
Tunda shugaban zaɓe ya fara magana kusan a lokaci guda numfashin biliyoyin al'ammar ƙasar ya tsaya cak.
_“A bisa sakamakon da aka tattara, ɗan takarar AGS Party, Honourable Yusuf Shu’aibu Tafida… ya lashe zaɓen shugaban ƙasa.”_
“Ya arrahim!”.
Hajiya Zainab ta faɗa tana mai fashewa da kukan farin ciki tare da miƙewa ta rungume Janar da ke kusa da ita kamar yayi sumar zaune. Sai da ta sake furta, “Alhamdulillah Daddyn Deen! Alhamdullahi!. ALLAH ya baka, ALLAH ya cika maka burinka, ALLAH ya baka wannan ne don ka gyara gaskiya!”.
A hankali Janar ɗin ya lumshe ido, zuciyarsa cike da wani nauyi mai girman gaske, nauyin da yake jin tamkar ya ɗauka daga yanzu nan har zuwa shekaru da yawa. Lokacin da ya buɗe ido sai kawai ya zame yay sujida, ganin haka itama ta bishi, hakama yaran da gaba ɗaya suka kacame da ambaton Alhmdllh duk sai suka bisu....

★★★

A gidan Mammah ma lokaci guda falon yay wani irin shiru na sakan, kafin su Yaya Ma'aruff su kacame da ambaton kalmar Alhamdullah. Sai da suka ga Mammah ta tafi sujida sannan suma duk suka bita har su Ruky. Mammah ta jima bata ɗago ba saboda hawayen da suke zubar mata. Koba komai tana ji a ranta nesa tazo kusa in sha ALLAHU. Sai da ta goge hawayen tas sannan ta ɗago tana murmurshi. Su dai su Yaya Ja'afar na mamakin yanda Mammah ke son janar ya samu kujerar nan, amma basu taɓa tambaya ba, yanzu ma kuma basu tambayar ba. Kawai suna ganin da Yaya Imran na son shi ne dai. Kuma Dada ma sanda yana nan yana girmama al'amarinsa matsayin ogansa......

<<%>><★><<%>>
Shima dai a ɓangaren Daddy Imran tamkar Janar ana sanarwa yi yay tamkar ha suma a zaune. Duk ihun da Khalifa da Asma'u keyi baima jisu ba sai da Ammie data zuba masa ido tana murmushi ta kama hannunsa ta matsa a cikin nata. Wani nannauyan numfashi ya kawo hawaye na cika masa ido. Ya kalli Ammie dake lallonsa cikin ido tana murmushi, dan duk da bai taɓa fitowa ya sanar mata shirinsa tsakaninsa da Janar ba tana tsintar wasu abubuwan nasu ta waya idan suna yi. Yau kam ko kunyar yara baiji ba ya jawota jikinsa ya rungumeta, a haka cikin dabara ya share hawayen da suka cika masa ido. Kafin ya saketa ya tafi sujida shima. Sai suma duk suka bishi, yana ɗagowa yayma su Asma'u alamar suzo gareshi, suma su biyun ya haɗasu ya rungume dan auta barci yake.
Sai da ya sake su suna masa congratulations yana gyaɗa musu kai da ɗaukar waya dan bakinsa ma ji yay ya masa nauyi. Kai tsaye layin janar ya kira duk da baida tabbacin samu, dan yasan a yanzu duk wani masoyinsa abinda yake ƙoƙarin yi kenan...

Tabbas hasashen Daddy Imran akan Janar haka ne, dan

Please Login or Register in order to submit comment