You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
baiyi magana ba ta gane mai yake nufi da hakan yasa ta juya da sauri ta bar wurin donta fahinci ogan nasu yaba cikin bacin rai a lokacin.
Zama taju din yayi a kusa dashi tare da tsura mai ido don ganin yanayin daya ke zaune a ciki.
Don baya son yana ganin sa a wanan yanayin yafi son ganin sa a cikjn yanayin nishadi da kuzari a tare dashi ko yaushe.
Don haka bayi kasa a gwiwa ba ya soma fadin wai lafiya na ganka haka ka zauna jiki a mace ?
Bai bashi amsa ba sai mayar da kanshi da yayi saman kujera ya daga kai sama tankar yana tunanen wani abu mai muhinmanci a lokacin.
Taju din ya kai hannun shi saman kafadan shi yana fadin wai meke faruwane da kai my man ka fada min matsalan ka ko wanan yarinyar ne take son bata min ranka ?
Cikin yan dakiku taju din yake jerawa jafar din wanan tambayan cikin bacin rai tare da kulawa a gareshi.
Yayin da jafar din ya sauke wani yar gajeruwan ajiyan zuciya ya dago kai tare da sauke jajjayen idanuwan shi ga taju din .
Kai taju din ya gyada mai tare da fadin nasan itace damuwan ka a yanzu don tun da muka shigo gidan nan naga yadda ta koma lokaci guda nasan za a samu matsala dakai don canzawan yarinyar nima ya ban mamaki matuka.
Bai bashi amsa ba sai dan shiru da yayi ya kurawa carpet ido kamar yana nazarin abinda zai fito bakin shi lokacin.
Kafin yace dashi ba itace damuwana a yanzu ba kaine taju don me kuma waya baka izinin shiga harkan gidana haka kai tsaye har kayi kokarin wuce iyakarka dani.
Taju din ya dago kanshi a razane yana kallon shi tare da shan jinin jiki don jin abinda ya fada din.
Kasan al,adan kasan mu kasan komai don me zaka wuce iyakar ka dani ka shiga harkan matana waya baka wanan daman yaushe har ka samu wannan matsayin haka ?
Kai ya dago da sauri yana dan kallon sa kafin jafar din ya nuna shi da yatsa yana fadin daga yau ban son ka kara shigowa gidan nan matukar bani na nemaka da kashigo ba.
Duk da ran taju din ya baci amma a fili sai ya daure yana fadin yanzu don wanan shine har ka wani tashin hankalinka haka ?
Sai kace wanan wani babban matsalane ni kawai nayi warni dinta ne don ta kiyayye shiga dakin ka kai tsaye bada wani manufa na fada mata hakan ba ai.
Murmushi jafar din yayi cikin bacin rai kafin yace dashi kasan nasan ka nasan halinka duk abinda zakayi ina warnin din ka akan yarinyar nan a tare dani.
Taju din ya marairaice murya kamar zaiyi kuka cikin ban hakkuri da nuna yayi laifi a gareshi nayin hakan iam sorry hakan ba zai kara faruwa ba tsakanin mu.
Shiru sukayi a falon yayin da kowa da abinda yake tunane a ransa kafin taju din ya sake fadin cikin yanayin kyarmar murya kayi hakuri please.
Sai lokacin ya dago kai ranshi a bace yana fadin kasan da kayi babban kuskure na bata min shirina akan wanan yarinyar don bazan so na rasa wanan yarinyar ba a rayuwana don ina matukar jin tausayin ta a rayuwana zaman ta yana da ma,ana mai yawa a gidana.
Taju din ya kara fadin nayi kudkuren yin hakan zuciyanane ya kasa hakkuri da ganin tana yawan shige maka da take kokarin a yanzu.
Wani kallo jafar din ya watsa mai da yasa ya mike ba shiri yana fadin iam sorry hakan ba zai sake faruwa ba tsakanin mu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
🦅 ABU CIKIN DUHU 🦅
5️⃣3️⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ALLAH SARKI YABON GWANI YA ZAMA DOLE JINJINA GAREKU ADMINS DIN WANAN GROUPS DIN WATAU ZAURE BIEBI ISAH DA HUGUMA GROUP DA ZAINAB MAKAWA GROUP1
WA YANNAN GROUP DIN SUNCANCANCI YABO A KO INA WALLAHI DAMA SAURAN GROUP IRIN NASU DA BANSAN DASU BA A SHAFIN SADA ZUMUNTA NA WHAFFS,
DALILI KUWA SHINE DUK KYAU DA DADIN NOVEL IDAN NA KUDINE BASU YARDA A JAFASHI A WANAN GIDAN NASU.
WANAN YA NUNA SU DIN UWAYENE NA GARI MASU IYA BADA TARBIYA GA IYALAN SU DAMA AL,UMMA GA BAKI DAYA A DUNIYA SABODA KARE HAKKIN DAN ADAM YA ZAMA DOLE IN YABAWA WANAN ADMINS DIN GASKIYA IDA BAN FADA BA BAN MASU ADALCI BA A RAYUWA.
ALLAH YA KARA TSARE MUNA IMANIN MU DA ZUKATAN MU ALLAHUMA AMIN DON HAKA ZAN TURA WASU NOVEL DINA KYAUTA GA WANAN GROUP UKU AKYAUTA SABODA ALLAH DA ANNABINSA .
Tsaye yake a tsakiyan dakin yakai gwauro yakai mari ya kasa zama a dakin ya tuhuta babu abinda yake tunane sai abinda ya faru a tsakanin mu dashi din da yammacin ranan.
Ya akayi har wanan yarinyar ta samu courge din da zata iya duban tsaban idanun shi ta fada mai magana haka kai tsaye ba tare data jin tsoro ko kunyar idan shi ba.
Anya kuwa zai iya wanan yarinyar nan gaba a yadda yake tunane idan ta kara wani shekaru a hannun shi kuwa ?
Kai da sake ya fada a fili yana dafa gado ya kai zaune tare da hada hannayen shi wuri daya yana fadin yaushe ma ta zama hakan ne a gidan nan.
Wanan tana da banbaci da zainab din da ya sani a baya wanan kamar idanuwanta ya bude yake gani idan ba karya yakewa kansa ba.
Tun shigowan shi garin nan ya fahinci canjin rayuwa a tare da ita gaba daya ta canza mashi ta koma wata babban mace da bai taba zaton kawan ta hakan ba a yanzu.
Ya zama dole ya lalubo hanyar da zai kwantar mata da hankalita har ta iya manta da wani zargin da take dashi a yanzu akan tajudeen din dayayi mai katsalandar a rayuwan shi ya tashi rushe masa komai daya shirya a baya.
Kwance yakai saman gadon rigingine yana mai lumshe idanuwan shi a hankali kamar mai wani nazari a lokscin.
Kafin ya mike zubur yana kiran layin wani abokin shi ba,ajima ba ya dauki kiran suka fara gausawa dashi.
Bayan gausuwa daya biyo baya yake tambayan abokin nasa kai mota nake so na mata lates one wanda sai ya girgiza mutum idan an bashi shi.
Dariya abokin nasa ya kwashe dashi yana fadin mutumina kayi sabon kamu ke nan kuma ?
Dama nasan wanan zaben yar kauyen da kayi zai dawo ya bata ma rai daga baya dan irin diyan tallakawan nan ba ka taba samun su a yadda kake son su.
Balle kai mutum irin ka wayayye na gani na fada idan babu wata a kasa har zaka fada tarkon irin wa yan nan diyan kauyawan masu kame maza har gwiwa.
Dan murmushi ya sake dan ya gaji da sauraren maganganun shirmen da abokin nasa Amadi yake fada mai a lokacin kan zainab din da shi kadai yasan abinda ya tsara a tsakanin su.
Cikin karfin hali yake fadin ba abinda kake tunane bane Amadi wanan dai yar kauyen da kake fadi din itace zan sayawa motar da babu wace mace dake da ita a garin nan ko akwashi kuwa baifi mace daya ko biyu ba a cikin kasan nan.
Kai mutumina da gaske kakeyi wanan magana kace yar kauye tayi tasiri a rayuwan ka haka ban sani ba nafa sanka a baya da kyakyamin mata balle wanan data zama yar , , , , ,
Dakata Amadi banson jin haka ga iyalai na don Allah ya fada muryan shi na nuna warning ga abokin nasa lokaci guda.
Amadi din cikin sauri yake fadin Iam sorry mutumina nasanka da riko da wasa nake maka nima nasan ai kai baka harka da mata dama.
Idan an samu sai ka kirani ya fada yana kokarin kashe wayan da yake ji kamar ya yarda ita lokaci guda don haushin da abokin nasa ya basa a lokacin.
Ya rasa meyasa mutane suke shiga zancen abinda bai shafesu ba kodan irin haka yanzu ya zama dole yayi wasa da idan mutane akan wanan yatjnyar su sancewa ita din mata take agare shi kamar matan kowa.
Ya dade a kwance kafin ya mike tsaye ya shiga bandaki ya watso ruwa ya dawo ya tayar da sallah ya dade zaune a gurin shi ba addua yakeyi ba kuma shi bai daga ba sai faman tunanen daya addabi zuciyar shi a lokacin.
Yana jin ana kwankwasa kofan shi yaki tashi ya bude sai kallon lokacin da yayi ta hanyar daga kai ya kalli agogon bangon dake dakin nasa makale don gwajin lokaci.
Har kusan sati daya nikan bamu hadu ba dashi a gidan duk dako nasan yana gidan haduwane kawai bana yarda muyi dashi.
Dan nima da baya na danyi nadaman tsayawa in masa rashin kunya a gaban shi duk da hakan ba halina bane aro nayi na yafa a lokacin.
Saboda bacin rai da takaicin maganan da tajudeen ya fada min a ranan na kwata na juya na rasa gano dalilinsa na fada min wanan bakar maganan haka kodan yaga maigidan bai dauke ni a matsayin mace bane a gurin shi yasa hakan ban sani ba.
Bawai yadda yayan ya daukeni yake damuna naba a,a hakan ni bai taba damuna ba a rayuwa saidai yadda shi taju din yai min magana a cikin tsanane damuwana a lokacin.
Da yammane ina zaune a keance a dakina ban dade da fitowa daga gurin maizube ba da yanzu kusan duk zaman daki muke a gidan ga baki dayan mu.
Naji an turo kofan dakin nawa bayan an kwankwasa saudaya sai turo kofan da akayi din lokaci daya da kwankwasan kofan.
Ba tare dana juyoba ina kwance a yadda nake jin kamshin turaren yasa kirjina bugawa lokaci daya nayi yun kurin juyowa da sauri don ganin wanda nake zaton ya shigo dakin nawa.
Yaja ya tsaya a bakin gadon da nake kwance din yana kare min kallo na dan lokaci guda yana karewa dakin dake gyare fes da kallo.
Ido nima na dan dago na kalleshi na lokaci guda kafin in mayar dasu kasa ina kokarin mikewa zaune.
Ki kwanta abinki ba wani abu nazo yiba dama na shigone in ganki tunda kina wasan boyo dani a gidan nan yanzu.
Yana fadin hakan fuskan shi yana a kaina dauke da bada umurni a gareni lokaci guda.
Ban kwanta ba kamar yadda ya bukata din sai gyara zama danayi ina mai sadda kaina kasa lokaci guda dan kallon da yake min din.
Da kyar na iya buda bakina ina fadin kayi hakkuri koda zan fito ka fita lokacin yasa baka gani na.
Yace ke nan ba,a koya maki gaida mutane ba kike nufi ko me daba zaki iya shiga ki gaidani ba ?
Na dago ido da sauri don in saci kallon shi don jin abinda ya fada lokacin still dai ni din yake kallo har wanan lokacin.
Ya tsura min idanuwan shi manya shi da suka canza cikin kankanin lokaci da fara maganan shi a kaina .
Karasa saukowa saman gadon nayi ina gyara bujen jikina dayan yi squeeze nadan hade hanaye a wuri daya ina fadin .
A cikk kyarma ina gudun naje dakin nakene kuma ai min wani fassara na daban shiyasa na daina shiga amma kayi hakkuri dan Allah.
Har zuwa lokacin baiyi magana ba sai na kara dukar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna a hankali.
Hannu ya tura a cikkn aljihu yana fadin nasan matar malam ta gaji da zama a garin nan don haka gobe za a mayar da ita gida ita kuma halimatu tunda tana karatu sai a barta a nan tare dake .
Kai na dago da sauri ina kallin shi wanan karon nan kawar da idona ba daga kallon shi cikin murya mai dauke da son yin kuka nace.
Don Allah ka barta ta kara min wasu kwanaki kafin ta koma don idan ta tafi zan shiga damuwane sosai ga hjy har yau ban daina kewar ta ba a gidan nan.
Babu mutanene a gidan ko kinmata itama tana da aure ne kamar ki da zan aje matar mutane anan na wata da watannk ai sai a yaba min rashin hankali.
Hakan da naji ya kara sa hankalina tashi sosai ya juya kamar zai tafi yana fadin gobe ma zanso na roke shi arziki yai min ai.
Kinga yanzu ai gidan kine zaki iya zama ke kadai yadda kika girman a lokaci guda da sauri nabi kaina da kallon dan jin abinda ya fada min din.
Yes ya fada tare da sauke min wani irin kallo daga sama na har zuwa kasa yana fadin wa zai ganki a yanzu ya dauka kece zainab din mami a baya mai gudun mutane.
Baki na turo gaba ina fadin niban wani girma ba dan Allah ka barmin ita nidai mu zauna a nan tare na fada kamar zanyi kuka a lokacin.
A dan rikice yake fadin me akai maki kuma yanzu don shagwaba kawai daga magana kina shirin yiwa mutane kuka yanzu kuma.
Idona dago kamar zanyi kuka nace bakai bane kake shirin mayar da sai nayi shiru kuma dan na rasa abinda zan fada mai a lokacin.
Yace a cikin zaro idanun shi waje da akai maki me a hankali na furta zaka maida maizube gida mana.
What me kike fada dama nufin ki a nan zata tabba tare dake ko me kedai yarinyar nan da alama shagwababiyar mace ce ke .
Zama nayi a cikin fushi saman gadon na basa baya yasa kai ya fice daga dakin saina tsunci kaina da sake hawaye lokaci guda.
Shike nan yanzu maizube zata wuce ta barmu ke nan ba zan sake ganin wani dan gida ba sai yadda hali yayu ke nan dani duk da naji bada halimatu za,a tafi ba hakan bai hana hankalina tashiba a lokacin.
Karshe na mike zuwa dakin nata sai dai na kasa fada mata abinda nayi niyar fada har na shigo dakin a lokacin dan bansan yadda zance da ita kada ta tafi ta barmu ba tunda itama tana son zuwa gidan a lokacin duk da daulan da muke cikin sa kuwa.
Washe gari ba karamin mamaki nayi ba abinda ya hadawa maizube na tafiya kowa sai sam barka da ita da anty fadila da take hada mata kayan tafiyan a wuri daya don kuka ya hanani tabuka komai a lokacin.
Nasiha da bn baki nasame su gwargwado wurin boyar Allah nan sai kara jadda min kalman inyi hakkuri da rayuwa wata rana idan Allah ya yarda zan dara kan aurena.
A mota sukai tafiyan don har gida za a kaita ga tsaraba mai tarin yawa an hadata dashi ban tsaya naga tafiyan ta ba don kukan da yazo min a lokacin dole na koma gida na fada saman gado.
Duk dauriyan halimatu itama da taga zasu wuce saidai tayi hawaye a lokacin ranan haka muka wuni sukuku damu sai gidan ya koma muna shiru kamar babu kowa a cikinsa lokacin.
Ban fito ba wunin ranan ina daki rufe sai faman tunanen da nakeyi na gida wayana yai kara na dauka innan muce a layi ta kirani tana min godiyan abinda ya jafar ya aika masu dashi.
Saidana hade wasu hawayen bakin ciki tare da saita muryana nake fadin inna ai hakan yiwa kaine duk da bansan abinda ya aika masu dashi ba a lokacin.
Bayan mun gama waya da inna na sake wani irin kuka mai karfi ni kadai a daki babu wanda zai ban hakkuri dole na kyale naba kaina hakkuri.
Suna zaune da ya mamud a haraban gidan mami zaune suna shan iska yazo mami bata gida ta fita zuwa unguwa yasa shi fitowa haraban gidan ya zauna nan ya mamud ya saneshi suka zauna suna magana.
Ganin yadda yake ta bayani dan uwan yai shiru ya zurfafa a cikin tunane yasa ya mamud din dan kiran sunan shi a cikin kulawa tare da mayar da hankalin shi gare shi.
Jafar meke damun ka na ganka haka yau ko wani abu ya farune yana kallon fuskan shi cikin kulawa yake tambayan shi.
Ya sauke ajiyan zuciya firgigit yana kallon dan uwan nasa ya mamud din ya sake fadin meye matsalan kane jafar a cikin yan dakiku ya mamud din yake jera mai wanan tambayan.
Ido ya lumshe a hankali tare da sauke numfashi mai kama da ajiyan zuciya yana fadin watau mamud ina cikin matsala da damuwa dani kadai na sani.
Sai kuma wani abin mamaki shine a dawowan nan nawa da nayi sai na sake tarar da wani abin mamaki a gidana wanda shine ke kara ban mamaki a yanzu.
Shiru yayi na dan lokaci kafin ya numfasa yana kada kafa a hankali yayin da mamud din ke sauraren shi.
Ido ya bude yanaci gaba da kada kafan shi yace abin mamaki wanda ban taba tunane bashine waina dawo gida na samu wanan yarinyar gaba daya ta sake min lokaci guda.
Guntun tsaki ya mamud din yaja lokaci guda yana fadin yanzu akan wanan har kabi katada hankalin ka haka sai kace wanda yake cikin wani babban matsala.
Shi girman ya mace aiba wani abu bane duba ga irin rayuwan da a yanzu take a cikinsa ko kana nufin a yadda ka dauketa haka zata tabbata a gidan ka koda yaushe.
Kai ya girgiza yana fadin bashine nufina ba mamud sai ka jira kaji karshen zancen mana kafin ka yanke min hukunci kasan abinda ya sakani a damuwa akan hakan.
Ya mamud din yayi kasake yana sauraren dan uwan nasa tare da zuba mashi ido don a yanzu ya tabbatar da duk abinda kanin nasa ke shirin fada mai matsalace babba don ba akan girman nawa dayaga na masa bane lokaci guda.
Huci yayi ga bakinsa sai wani gumi dake tsarso masa a goshin sa tankar wanda ya watsa wa kansa ruwan zafi a lokacin.
Shikan mamud yana ganin yanayin dan uwan nasa yayi saurin fadin wai jafar meke damuwan kane haka ?
Nifa gaba daya duk ka sauya min kamar ba kaiba wanan wani irin damuwane akan zainab din wanda ya susutaka haka har ka tayar da hankalin ka haka wai ?
Mumushin karfin hali yayiwa dan uwan nasa yana fadin mamud kafi kowa sanin bawai na auri yarinyar nan bane don na zauna da ita irin na ma,aurata a yanzu.
Jafar wai wani irin magana kake kokarin fada min a yanzune wai don me ake aure a rayuwa badan mutum ya aje iyali ya haiyayya fa shima ya bar baya kamar yadda iyayyen mu suka barmu.
Yanzu fa jafar kana kokarin rufe bayan talatin da biyar ne a rayuwa don in ban manta ba wacan zuwan naka mami ke fadin kana talatin da biyu a duniya.
Me zaka jira da matar ka Allah ya baka mace ta gari da zaka inya controling dinta yadda kake so agidan ka tun a yanzu kan kanta ya karasa wayewa.
Nida aca tun farko irin matar da mami ta zaba min ke nan ba wanan ba da nake fama da ita a gidana yanzu don ban isa in tsayar da Nuriya wuri daya ta tsaya ba.
Shine abinda nake lurar da mami akan auren ka da yarinyar nan zainab a kullun do ko ita mami Nuriyan bata ragawa ba kasani.
Jafar din ya dukar dakai kamar yana sauraren dan uwan nasa abinda yake fada nan ko wani duniyan tunane ya fada a lokacin.
Can ya dago kai yana kallon dan uwan nasa kafin yace a cikin kyarmar murya kaman mai shirin kuka a lokacin, mamud mafita nake so a yanzu kan wanan auren nawa.
Shiru mamud din yayi don ya rasa inda dan uwan nasa ya dosa da maganan shi yaji jafar din na fadin bana son in rasa wanan yarinyar a yanzu mamud don ina matukar jinta a cikin raina rasa zainab a rayuwana tankar rushewan wani bangaren rayuwanane a yanzu.
Cikin mamaki ya mamud ya dago kanshi yana kallon dan uwan nasa da mamaki don har yanzu ya bai fahinci abinda dan uwan nasa yake nufi ba.
Can ya dago kai yana ftambayan kanin nasa No jafar ka daina fadan haka don Allah ko akwai wani abinda yarinyar nan tayi makane kake son ka boye min dai ?
Kai ya girgiza yana gyara zaman shi tare da lasa saman labben na sama yana mai shafo kanshi a hankali cikin damuwa.
To jafar wanan wani irin wullakanci kake son yiwa yarinyar nan haka koka mai damu mutanen banza a daukemu wawaye wadanda basu san abinda sukeyi ba .
Nace ka fada min meye damuwan ka da ita kana kawo min wasu dalilai marasa tushe a yanzu.
Mamud ba zaka gane bane amma gaskiya nasan bazan iya kula da hakkin yarinyar nan a yanzu ba ko nan gabama.
Innalillahi ya mamud ya fada tare da wani irin zabura daga inda yake zaune din kafin yakai ga cire hulan dake kanshi yana dan fifita dashi a hankali don ya samu iska a jikinshi.
Kafin ya iya buda baki ya furta a sanyayye jafar baka da lafiyane ko wani abinne ya sameka kake boye muna.
Kai jafar ya kada mai alaman a,a ba hakan yake nufi ga maganan shi ba da akwai dai wani zance can kasan zuciyar shi.
Jafar ka tuna koni wani abin ya shigewa duhu daya shafi rayuwana kai nake nema in fadawa ka ban shawara akan hakan don me kai a yanzu ba zaka fada min naka damuwan ba a gabana.
Mamud nasan da hakan shawara kawai nake son ka ban har lokacin da komai zai daidai min a rayuwa na fuskanci matata.
Wani irin ajiyan zuciya ya mamud din ya sauke lokaci guda tare da fadin anya jafar kana da lafiya kuwa ?
Yanzu dai na gama fahintar wanan yarinyar batai maka komai ba don haka koma menene yake damun ka a rayuwa ka lalaba matar ka ta hanyan kyautata mata a rayuwa ta yadda zaku zauna lafiya da ita.
Saidai ka tuna kada ka yarda ka cutar da yarinyan nan da yawa katuna ba a duniyan nan zamu tabbata ba har idan ka cutawa rayuwan wanan boyan Allah Allah zai saka mata ta ida baka zata ba.
Kai jafar din ya sunkuyar a kasa don baida abinda zai fadawa dan uwan nasa a yanzu saidai ina son wanan maganan ya tsaya iyani dakai kafin komai ya daidaita ya mamud din ya fadawa dan uwan nasa.
Da sauri jafar din ya dago kai yana
Book Chapters
Chapter 44
Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48