google.com, pub-8772996913092952, DIRECT, f08c47fec0942fa0
ArewaNovels

Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tunko jiya dan bacci rabi da rabi yayi yana tunanin ta saisa yazo da wuri danda yay niyyan sai da daddare zaizo amma yakasa daurewa ya shiryo yataho yana zuwa kuma hayaniya da ihu dayaji yasa yafada gidan nan yaga aika aikan da Aneesa takeyi, Allah ya gyara yarinyar nan she seriously need therapy and insha Allah kadan kadan ahaka zaita bata har saita gyaru.








Gaban wani tangamemen gida a GRA yay horn budemai kofanBudemai kofan akayi yaja motar ya shiga ciki gidane babban gaske irin na yan gayun nan, parking motar yayi yasauko yana tafiya ahankali har zuwa flat dinsu bude kofa yayi, wata yar matace dakana ganinta zaka gane mahaifiyar shice a zaune sabida mugun kaman dasuka yi tana binshi da kallo wata mata haka na gyara mata kumban hannu, maida kofar yayi yarufe yace "Mum sanunku" hararanshi tayi ta kalli matan datake gyara mata kumban tace "please excuse me Charity" da sauri matar tabar falon, ganin haka yasa yafasa zuwa saman ya zauna kusada ita zaiyi magana ta kama lips dinta tace "kamin shiru I didn't ask you to talk" shiru yayi yana kallonta, cikeda masifa tace "zan sabamaka fa Hafiz, Allah inhar kana wasa da cikinka bazamu shiryaba, now just silenty stand up ka wuce dinning ka zauna nazo nabaka abinci, breakfast bakayiba kafita, jiya da daddare dudda uban hanyan dakashawo ga tuki all the way from Abuja lipton kawai kasha ka kwanta eh wani irin abune ina fama da little Fareeda taci abinci kaima ina fama dakai are you a baby" dan dariya yayi cikeda tsokana yace "to what I am before? Am your baby Mummy amman big baby ki" dariya Mummy tayi ta tallabemai keya tace "common tashi" tashi yayi ahankali yabita tana tafe tana mitan rashin cin abincin shi yana murmushi yace "Mum where is Princess?" kujera Mum tajamai yazauna akai tace "sunje saloon itada Rumana yin kitso" dan gyadakai yayi batare dayace komiba ba, lafiyayyen abinci ta zubamai jellof rice dayaji kaza sanan ta zauna kusada dashi ya turamai gabanshi kallon abincin kawai yake dan yasan bazai iya gamawa dashiba ko kadan amma yana tsoron magana Mum ta haushi da bala'i, spoon yajawo ya shiga ci ahankali kaman wani dan jariri.
*********************




































_Bayan Sadakan Bakwai_


Yau kimanin kwana tara da rasuwan Rauda. Tun ranan da Rauda tarasu rabon da Ammi tasa Daddy a ido amma ko ajikinta dan ta tsani ganinshi daman, Alhamdulillah tsawan Kwanaki taran nan bata waniyi wahalan laulayi ba banda aman safe da kullum saitayi daganan kuma ko ciwon kai bataji, cikinta yafito sosai kaman cikin dayakai wata biyar, kullum saita kira Baffa yahadata da Aneesa su gaisa dudda daidai daso daya baitaba gayamata cewa ga wani abu dangane da Aneesan ba, kullum gayamata yake lafiyan ta kalau karta damu tacigaba da rayuwan gidan mijinta tana aikin lada domin aljanna ta na karkashin kafanshi ne, sunan zasu cigaba da kulamata da Aneesan.




Yau tunda ta tashi take da niyyan zata wanke kayan ta da sukayi datti dudda tanada yar aiki bazata taba bama yar aiki kayan ta ta wanke mataba, iyakan aikin yar aikin shine share tundaga dining har falo sai sharan gaban flat dinsu dakuma share kitchen da wanke wanke dudda uban laulayin datake daidai daso daya bata taba bari yar aikin taje sama ta gyara mata bedroom dinta ba da kanta takeyi hakama girki saidai randa batada karfin yi saita cema yar aikin tadafa mezataci da yamma saita tafi gidansu.


Hada duka kayan dazata wanke tayi a basket yawacinsu hijabai ne saikuma dogayen riguna datafi sakawa kwanan nan dansu sukafi mata dadin sawa, hijabi ta daura akan riga da zanin dake jikinta na atampa tabude kofar dakinta tafito ta sauko downstairs tana shakan kamshin hadadden turaren wutan da dakinta keyi wanda yar aiki ta kunna a burner ko ina yadau kamshi, kofar flat dinsu tabude tafito rikeda basket din tana zura slippers dinta ahankali.






Tunda tabude kofa Dady dake cikin mota da tundazu yadawo yakasa fita sai tunane tunane yake ya kafeta da ido yana kallonta, yarame sosai kana ganinshi kasan yanacikin damuwa bana wasaba, ga rasuwan Rauda, ga Aliyu na fushi dashi sosai, gakuma Rukayya da wani irin nauyinta da kunyan ta yakeji dako lokacin dayazo neman aurenta baijin yaji kunyanta da nauyinta hakaba, yagama wulakantar da yarta akan abinda ba ita ta aikata ba, baimasan tayaya zai fara bata hakuri da neman gafarar taba, shikadai yasan abubuwan dake damunshi arai, tunda tafito yake binta da kallo ya kafe cikinda dayadan fito ta hijabi da ido yanajin wani irin sonta da kewanta na ratsa kowani bangare dajijiya na jikinshi, ahankali yaga take tafiya da kafafunta dasuka sha Jan lallin gargajiya na salatef gwanin van sha'awa harta shiga laundry dinsu.




Matan Dady biyu tagani a laundry suna dan fira suna jiran kayan dasuka saka a washing machine din yagama wanke musu yasa taji kaman tajuya sabida ganinsu datayi saikuma tafasa ganin akwai washing machine har guda biyu dat are free, dan 4 manya manyan washing machines ne a gidan, ahankali takarasa ciki saida takai daidai wurinsu sanan tace "sannunku" wani irin banzan tsaki amaryan Dady taja ta kalli Amina matar Dady tabiyu tace "Amina ana magana fa" dan dariya Amina tayi tajuyo takalli Ammi daga sama zuwa kasa ta tabe baki sanan tajuya ta kalli Amarya tace "kinsandai ninafi karfinta wlh tayi kadan tasa akaini gidan yari kokuma tahadamin wani makircin saidai ke Amarya" wani irin dogon tsaki Amarya taja tace "wutsiyar rakumi tai nesa da kasa itama tasan nafi karfinta takowanni fanni, bana maulan abama y'ata aiki a bakery, bana tura yarana gantalin duniya ana zuwa ana lalle ana nemo kudi, gidan hutu na tashi ko anjiman nan nakira babana nacemai inason kaza zai aikomin dashi, tafitar da Kareema da makircin ta kullum sai uban saka hijabi kaman mumina ni tai bala'in kadan, tagama makircinta bata isa ta fitar dani daga gidan Alhaji ba tai kadan ne ina gayamiki, kuma kigayama yar agolanki ko an sakota daga gidan yari ta tafi gidan ubanta bazata zo tanacin kudin ubanda banata ba taje taci na ubanta mai gona, matsiyaci mai bar........" tass Ammi ta zuba mata wani irin mahaukacin mari kirjinta namata zafi ta nunata da yatsa tace "ki zageni dagayau har jibi ko tak bazan cemiki ba, wlh kika zagi marigayin mijina saina chanza miki hallita da duka, ki kama kanki" wani irin shafa inda Ammi ta mareta Amarya takeyi da sauri Amina tace "wlh bazaki yardaba saikin rama, duk abinda zai faru yafaru karki damu zan shigan miki, wlh saikin rama, ke tsaran wasanta ne dazata mara, haukace mata amarya" Amina tafadi cikeda zigi tana taba Amarya, cikin fushi Ammi tace "zoki rama mana" cikin zafin nama Amarya ta fizgi omon dake gaban washing machine din wajen kafin Ammi tace me Amarya ta watsama Ammi omon a fuska kadan yashiga idanun Ammi cikin ikon Allah hakan yasa ta shiga sosa ido, kallon Amina Amarya tayi, Amina tawani irin kashema Ammi idanu kafin atare suka sa hannu suka hankade Ammi ta bugu da bango Ammi tai yar karan azaba.




Daidai Dady yazo zai shiga shashin shi yaji karan muryan Ammi har cikin zuciyan shi da sauri yay hanyar laundry Ammi dayagani akasa ga Omo duk fuskarta sai Amina da Amarya suna tsaye akanta suna dariya sabida yanda Ammi ke cije lips sabida zafin Omo daya shiga idanunta takasa bude ido ga mugun bugewan datayi abaya, bama susan da Dady ya shigoba, saidai suka ganshi tsugunne gabanta yana kakkabe mata fuska da hannu, kamshin shi kawai Ammi taji tagane shine awurin, ahankali Dady yakama bakin babban rigan jikinshi ya share mata fuskar sanan yasa hannu yadaga ta tsaye tareda juyowa ya kalli su Amarya dasukai zuru zuru suna kallonshi dan basusan ya dawoba, cikin wani irin fushi yace "nabaku nan da awa daya ku tattara kubarmin gidana, bazaku maidamin da gida na mahaukata ba I've tolerated you people's enough not anymore, karwacce ta tafinmini da yarana, na sakeku saki biyu! Kuma wlh nadawo nasame ku a laundry nan sai kunsha mamaki na bazan kara zama da wacce bata neman zaman lafiya ba" yanaji suna salati Amarya nacewa. "wlh Alhaji sonkan ka yay yawa, ai harda ita, itafa tafara marina, mesa baka saketa ba" cikin fushi Ammi dake kokarin fizge jikinta daga nashi tace "inda yamin danaji dadi danna mugun gajiya da aurenshi nima nabarmuku mijinku ku cinye" hannun Ammi Dady yaja yafita daga laundry yaji kalaman ta har tsakiyan ranshi yay flat dinshi da ita, bedroom dinshi yabude ya shiga yasa hannu ya yaye hijabin jikinta yana kallon cikinta daya fito yay wani irin murmushi sanan yakama hannunta suka shiga bathroom, ahankali ya kunna tap ya debo ruwa yawanke mata fuskan tass sanan yace "bude idanun mugani ko da omon aciki" ahankali tabude idanun ganin babu yajin omon yasa yace "sannu, muga bayan dakika bugen" yay maganan yanakai hannunshi kan bayanta, ture hannunshi tayi batare data kalli fuskarshi ba tace "am fine thank you" sanan tajuya tabude kofar bathroom din tafito hijabinta dake kan gadonshi tadauka tazura tai hanyar fita.
















Da sauri Dady yarike bayan hijabin nata, wani irin fushi ne yazoma Ammi wuya batasan sanda tacire hijabin ba tabarmai tabude kofar bedroom din tafita daga dakin dasauri, binta Dady yayi da sauri yana kiranta. "Ummu Aliyu, Ummu Aliyu" flat dinta Ammi takai ta shiga zata maida kofar tarufe Dady ya shigo da sauri tareda sa hannu yarike waist dinta yana maida kofar yarufe kaman zaiyi kuka yace "Ummu Aliyu dan Allah ki saurare ni" dudda tana bala'in fushi dashi bazata tabaso wani ko wata yaji matsalansu da Dady ba, waigawa Ammi tayi yar aikin ta tagani zaune akasa afalo kanta akasa, kiranta Ammi tayi. "Larai harkin gama aikin" "eh nagama hajiya" yarinyar tafadi kanta akasa ahankali Ammi tace "to zoki tafi anjima zan kiraki kinji" tashi tayi da sauri dan itama duk kunya yacikata tace "to hajiya zanbi ta kofar kitchen" gyadakai Ammi tayi tace "daganan kidau abin nan kikaima babarki" gyadamata kai tayi tace "Allah amfana" daga Ammi har Dady juyawa sukayi suna kallonta har saida sukaji karan maidai kofar kitchen tarufe sanan da sauri Dady ya kalleta yana rikeda waist dinta har lokacin yace "Ummu Aliyu dan Allah ki saurareni" wani irin juyowa Ammi tayi ta kalli Dady shi kanshi baisanta da irin wanan fushinba hannunta tadaura akan nashi dake kan waist dinta tana turewa tace "karka kara cemin Ummu Aliyu, kaman yanda ka nunamini kaiba mahaifin Aneesa bane kuma bazaka taba zama mahaifi gareta ba haka nima babu abinda ya shafeni da danka kowa yarike nashi kaji kasha Alhaji, kasakeni banda lokacin sauraronka wlh" sosai kalaman ta suka daki zuciyarshi, ahankali yace "ni mahaifine ga Aneesa har gobe wlh kuskure na aikata danake danasani yi amma hakan baya nuna niba mahaifi ga Aneesa bane har gobe ni mahaifi ne gareta" wani irin murmushi Ammi tayi irin murmushi nan mai ciwo tace "Alhaji kenan, bari na tuna maka wani abu, katuna ranan daka daga hannu ka wankama Aneesa mari agaban kowa atsakar gidan nan?" Ammi tai maganan tana kallon fuskanshi, lumshe ido Dady yayi da sauri yakasa kallon Ammi yanajin wani iri, Ammi tacigaba. "ka jata kaman kanajan dabba kai dakin computers dinka da ita" dan shiru tayi sabida yanda abin kemata ciwo ta fuzar da iska sanan tace "katuna yanda ka kikkifa mata mari am sure Aneesa saida idanunta sukaje dark mode for some few minutes sabida marukan dakamata kafin karufeta da mari kaman kasami jaka, dudda haka banji haushin ka ba a lokacin still namaka uzuri dan aganinka itace tabama dan gwal dinka zinare, na saukar da guiwowina biyu kasa tareda hade hannayena ina rokanka Alhaji nasan kana cikin fushi na rokeka da Allah abi abinan ahankali kowani hukunci zakama yarinyar nan kamata amma karkasa polisawan nan sutafi da ita, Alhaji Muhammad Ibrahim kaji rokona kaji kukana amatsayina na mahaifiya lokacin danake maka? Kaji tausayin kukana? Karka kara kiran y'ata yarka, karkuma ka kara kiran kanka da mahaifinta, Allah karya bama y'ata mahaifi irinka, ga danka ko yarka nan wanda ina gayamaka ka rubuta ka ijiye ranan dazan haifomaka kome acikin nan ranan aurena dakai zai kare, ko yanzuma tsoron Allah ne yasa nabar kaina dashi" ganin yanda Ammi kemai masifa yasa zuciyarshi ta katse ahankali yasaki kafadarta ya tsugunna mata yana rikeda hannayenta gudun karta tafi, wani irin dauke kai Ammi tayi danko kadan baya freaking nata, cikin wani irin murya na bala'in ban tausayi Dady yace "ki yafeni, ki yafemin Rukayya, nai kuskure, naci amanan ki dana Aneesah, shirin shaidan ne da kuma kaddara wanda Allah ya kaddara sanan yarubuta cewa zai samemu, inason Aliyu bazan miki karyaba sanan ina sonki son dabanjin zan iya rabuwa dake aduniyan nanba, kidena maganan saki wlh inhar ina cikin hayyacina bazan taba sakinki ba" dan shiru yayi yana kallon fuskan Ammi yanda take kallon gefe kaman bada ita yakeba, ahankali yace "Aneesah na ina? Inaso naje naganta nabata hakuri na roketa gafara" dan murmushi Ammi tayi mai kara tace "Aneesah na bata bukatan roko koma menene naka, yarinya na have moved on, bazaka sake ganinta ba har abada" da sauri Dady ya girgiza mata kai zuciyarshi tamai wani irin nauyi kaman hawan jininshi nagab da tashi yace "karkice haka, Aliyu na bala'in son Aneesah da aure, banda burin daya wuce nakara karfafa zumuncin dake tsakanin mu, kiyakuri komi yawuce for the sake of yaranmu dakeson juna" da yatsa Ammi ta nuna kanta tana kallon Dady tace "inhar nine nan na tsugunna na haifi Aneesa da kaina y'ata bazata taba auran dan gwal dinka ba, Aneesah bazata taba auran danka ba namaka wanan alkawain walla...." da sauri Dady yatashi yadaura hannunshi kan bakin Ammi yana girgixa mata kai hawaye yacika idanunshi sosai, ahankali yace "karkice haka Rukayya, nina miki laifi, yanzu haka haryau Aliyu fushi yake dani wlh bayamin magana, don't punish Aliyu akan laifin da mahaifinshi ne ya aikata, Inaso yau around karfe biyu na dare ki leko ta window kiga, zakiga Aliyu a tsakar gida yana exercise kaman zai kashe kanshi, my son is suffering, Aliyu nacikin damuwa fiyeda tunanin ki kina ganin fuskanshi zaki gane hakan, Rukayya namiki laifi, namiki laifi kimini duk hukuncin daya dace dani anan gidan, amma karki hana marayan d'ana abinda yakeso dan girman Allah, ki barshi ya nemi auren Aneesah" hannunta daya rike Ammi ta fizge tace "lokacin daka kulle mini Aneesah karabani da ita baka taba tunanin ita marainiya bace dake kallonka amatsayin uba, ko maza sun kare aduniyan nan saida ta mutu ba aure data auri danka daka kulle ta agidan yari akai, gaka ga danka nan kajika kas......." kasa karasa maganan tayi sabida turo kofan da akayi atare daga Ammi har Dady suka dagokai suka kalli kofan Aliyune ya shigo babu ko riga ajikinshi saidan boxer idanunshi sunyi jajir yana kallon Ammi kaman yanda take kallonshi da shanyayyun idanunshi, daga Ammi har Dady kasa cemai komi sukayi, kama kofan Aliyu yayi yarike gam cikin wani irin murya kaman na wanda y yake abuge yace "Mummmmm, An...e.s" kasama fadin sunan yayi da kyau yawani irin zube awajen da sauri Dady yay kanshi. "Gadanga na, Aliyu, Gadanga na" ya shiga tapping kumatunshi yana kiranshi, kafe fuskar Aliyun Ammi tayi da ido kafin tawani irin juya tai sama ko kallo na biyu bata basuba.
[17/04, 08:37] Aishat Muhammad: _*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_










_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤








_✍🏿M Shakur_






6️⃣3️⃣ & 6️⃣4️⃣


_how to subscribe_
_zaki turo 300 ta account number na 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta WhatsApp number na 07012181461 sainai adding naki a group din a tsakanin soyyayya, marasa bank can also send MTN card to WhatsApp number na_




_GGM you guys have my heart abeg, thanks for loving ATSAKANIN SOYAYYA_




_inma bakida kudi karki karanta banyi forcing kowa ta karanta littafi na ba, dan wlh kika karanta baki biyaba ban yafeba_




_masu fitarmin da littafi waje kunma kanku kuma bazan gaji da fadi muku ban yafeba sai Allah ya sakamin_












Ko kadan Dady baya feeling heart dinshi na beating hakan yasa da sauri yadauko ruwa ya yayyafamai, bude idanunshi dasukai jajir yayi yadaura hannunshi akan kirjinshi yana nishi sama sama da sauri Dady da yagama rudewa yace "sorry Aliyuna, kirjinka kema ciwo? Sannu kaji karka damu Mummy ka zata hakura zata baka Aneesah, tashi muje nakira Dr yadubamini kai" da taimakon shi Aliyu ya iya mikewa tsaye yakaishi flat dinshi sanan yafito da sauri yaje mota yadauko phone dinshi danya kira Dr....








***
Sosai Aneesah tasaba da Dr Zaid, shima Dr Zaid din yasaba sosai da gidan dan Baffa ma yacemai inya zo ya dinga shigowa kai tsaye, tuni Aneesah tabama Inna da Ibrahim da Mubarak hakuri duk sun hakura yanzu suna zama peacefully thanks to therapy da Dr ke bata, banda haka Baffa yakarbo mata wani ruwan rubutu datake sha duk narage yawan fushi da zuciyan datake yi and Alhamdulillah yaragu sosai, tadawo kaman da, Baffa yanasamin kudi yabata dubu biyar yace Inna tarakata tadinko hijabai, aiko sukaje kasuwa ta dinga hijabai kala hudu har kasa Black, pink, maroon, da milk tadinka.
In kika karanta min littafi batare dakin biyaba ban yafeba.
Zaune suke a tsakar gida kan tabarma tana sanye da dogon hijabinta milk dayasha guga tana gyaran shinkafan hausa, Mubarak zaune kusada ita yana grating kayan miya da grater shikuma Zaid dake sanye da fararen kaya na wani soft yadi yana karanta musu wani english novel mai suna the killer tree sai murmushi suke labarin da dadi gaban tsoro, fece shinkafan Aneesa ta juya ta shiga yi tana sauraron labarin da Hafiz ke karanta musu, wani irin faduwa gabanta yayi dayasa tasaki farantin akasa hannunta ya shiga rawa, karan farantin yasa Hafiz yadago kanshi da sauri dagashi har Mubarak, Mubarak ne yace "laaaa kin barar da shinkafan Aneesah menene?" da sauri ta girgixa kai tasa hannunta ta shiga kwashe shinkafan tana cizan lips sabida kirjinta dataji yana mata ciwo sosai, kafe hannunta dake rawa sosai suna kwaso shinkafan tana zubawa a farantin Hafiz yayi yana nazarinta ganin all of a sudden kaman an tsikareta, wani irin lumshe ido tayi tareda daura fuskanta kan cinyarta tana sauke wani irin ajiyan zuciya, kwannan tamanta da batun Aliyu danta dade batai tunaninshi ba menene yanzun nan yake shigomata rai haka, dan juyowa tayi ahankali ta kalli Mubarak dake kallonta, hannu ta mikamai tana murmushi kokarin boye damuwarta ahankali tace "dan aramin wayarka nakira Ammi na Ya Mubarak" turo baki Mubarak yayi saikuma ya dauko yar wayan toculan nashi yamika mata yace "wlh karki cinyemin kudina" fizge wayan tayi. Inma baki da dari ukun biya karma ki karanta, in kika karanta ban yafeba.












Kika karanta min littafi batare dakin biyababan yafemiki ba, hakkina kuma saiya biki wlh.
Tamike tsaye dan satan kallon Hafiz tayi ganin idanunshi akanta yake yasa tadanyi murmushi tawuce labulen dakinta tabude ta shiga zama tayi abakin gado ta saka number Ammi data haddace sama da number kowa aduniyan nan tai dialing, ringing daya Ammi ta dauka murya chan kasa tace "Aneesah Ammin ta" murmushi sosai Aneesa tayi tace "Ammi na bacci kikeyi muryan ki chan kasa" yatsine fuska Ammi tayi tana kokarin danne baccin ranta ta gyara zama tace "no baby girl nagaji ne, ya kike yasu mamanki na wurin kowa lafiya ko?" gyadama Ammi kai tayi tace "eh lafiya" saikuma tai shiru, jin yanda tai shiru dan normally inta kira surutu kawai zataita yima Ammi amma yausatai shiru hakan yasa Ammi tagane akwai wani abu, murya chan kasa tace "menene Aneesah, akwai abinda kikeso ne? What is the matter?" sosai bakinta kemata nauyin fadin abinda takeso tafadi tace "a...a...ummmm" gyara zama sosai Ammi tayi tabata duka attention dinta tace "uhum ina jinki kiyi magana mana, menene eh babyn Ammin ta" ahankali cikin wani irin muryan rashin gaskiya dinan irin idan yaro yay laifin nan tace "Ya.......A...li...yy....u" saida zuciyan Ammi yawani irin girgiza da Aneesah ta tambaye ta Aliyu, Aliyu yasha cemata suna soyayya bata taba yarda ba saiyau da Aneesa da kanta takira mata Aliyu, shiru Ammi tayi dan batason tarufe ta da fada ko kadan ance idan kanason kasamu information din dakake nema awajen danka inya kawoma magana don't attack him immediately kasakin mai harya gama fadi maka komi kafin ka daki bakin gatarin da zafi, kaman babu komi Ammi tace "Yayanku Aliyu lafiyanshi kalau, menene dawani abune?" girgixa ma Ammi kai tayi hawaye na taruwa akan fuskarta kaman zata sakinma Ammi kuka ahankali tace "inaso nai magana dashi ki kaimai wayan Ammi" sake danne zuciyanta Ammi tayi kai tsaye tace "kicemai me?" kaman jiran tambayan Ammin take tasakinma Ammi kuka ahankali mara sauti sosai, cikin kuka Aneesah tace "Ammi kaman baida lafiya inajin haka ajikina sosai, gabana sai faduwa yake kirjina namin zafi duk in yafadomin arai saisa nakeso nayi magana dashi" karkada kafa Ammi ta shiga yi daga inda take zaune anatse tace "son Aliyu kike Aneesah?" tambayar da Ammi tamata saida yasa gabanta yafadi hakan yasa tasake sakinma Ammi wani kukan batare datai magana ba, sosai zuciyan Ammi ke suya tace "karki sake kimin karya Fateema, stop that crying and tell me the truth, son Aliyu kike?" yanda Ammi tamata tambayan cikin kakkausar murya yasa ta tsagaita kukan kirjinta na dukan uku uku cikin wani irin yanayi na kuka tace "Ammi nima ban saniba" karkada kafa Ammi tayi tai wani irin sound da iyayen nan keyi da baki idan yara sukai karya. "huhuhum" cikin wani irin muryan fada fada tace "batun yau nasan kina soyayya da Aliyu ba shida kanshi yafadamini, Fateema!" Ammi ta kirata dawani irin harsh tone dasaida yasa gabanta yasake faduwa murya chan kasa tace "na'am Ammi" tace "Aneesah ina sonki sama da yanda kike ganin baban Aliyu nason Aliyu banbancin shine soyayyar danake miki bata makatar daniba, I know the difference between right and wrong, ban sangarta kiba, I train you Aneesah, na koyar dake abubuwa da dama wanda koda yau nafadi na mutu zaki iya amfani da abubuwan dakika iya ki kula da kanki dasu, I train you nabaki ilimi, sanan nakoma miiki yan hikimomin rayuwa, yanda baban Aliyu ke takama danshi maraya ne baida mahaifiya haka kema kike marainiya bakida mahaifi, da ace da muka shiga gidan nan Aliyu ne yabaki poison koda sama da kasa zasu hade mutumin nan bazai taba iya hukunta yaron nanba talk more of yakaishi har gidan yari, Aneesa ninedai na haifeki ko, sanan jinina ne ke gudana ajikinki ko, inhar ni mahaifiyan nan naki na isa dake, sanan ke yar halak ce zakimin hallacci inaso kicire Aliyu daga ranki, kifadama zuciyanki mahaifiyarki tacemata ta nisanci Aliyu, bazaki taba auren Aliyu ba, bazan taba bari ki auri dandan wanda ya wulakanta mini ke aduniyan nan ba, bamu da kudi amma munada Daraja, zan nunamai ciwa inhar sone shi baima Aliyu komi ba danni babu wanda zai wulakanta mini abin sona na yafemai har abada! Bazaki taba auren Aliyu ba, kicire sonshi daga zuciyanki can you do that for me Aneesah?" hawayen dasuka kasa zubowa ta share da bayan hannu ahankali tace "eh Ammi n....aji" shiru Ammi tayi tana sauraron yanda muryanta ke rawa tasan kuka take, murmushi Ammi tayi tace "ke yarinya ce bazaki gane me nake miki ba, just stay put ki kulanmini da kanki kinji, nakusan zuwa wurinki kinji" gyadama Ammi kai tayi ahankali tana goge kwalla, dan shiru Ammi tayi for a while kafin ahankali tace "Dr Zaid fa meye tsakanin ku? Baffan ku yacemin kullum saiyazo wajenki meye tsakanin ku?" hawayen dasuka zubomata ta goge tace "babu komi yace shi Yayanane, kome ke damuna nadinga fadamai" murmushi Ammi tayi tace "to shikenan, jeki taya Inna aiki, sai anjima" katse wayan Aneesah tayi tafashe da kuka sosai tama rasa meke sakata kukan nan, tayi kuka na almost 10min sanan ta lallashi kanta tasa bayan hannunta ta share fuskarta tass, kafin tasa hannu ta dauki wayar Mubarak din tamike

Please Login or Register in order to submit comment