You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya son hayaniyar gidan Sarauta ko kadan. Da kyar Maimartaba ya amince da wannan tsarin na Yareema, amma yana adduar ta gama karatun kafin watan haihuwar ta ya tsaya ta zo ta haihu a gaban su. Yana da jikoki kusan guda 20 amma na Yarima isspecial domin babu kamar sa cikin duka jikokin da zai haifa ko ya haifa a baya. Yana masa adduarsamun nasara akan duk abinda ya sa gaba kuma ya gama rubuce-rubucen da zai je ya yi na tsawon shekara guda a ANKARA UNIVERSITY wanda zai bashi damar hawa Professorial Chair.
*****
Kin faya nawa, kin faya yanga Saade, don kin ga Askirama na biye miki, shin sau nawa zan aiko Fanna ta gaya miki Yareema na cikin mota tun dazu yana jiran ki zaku wuce ne? Duk wani shiri da za ki yi meyasa tun jiya baki yi shi ba?
Saade ta cuno baki hadi da marairaice murya Fulani gashi na fa nake gyarawa kawai, ya ce baya son ganin sa a cukurkude, nikuma bana so kowa ya taba min kai, shine nake tajewa da kaina.
Fulani ta karbi katon matajin dake hannun ta tace bari ni in taje miki, in ba haka ba zaki yi awa guda kina abu daya. Ta taje mata, ta tufke mata shi da murtukekiyar kalbaa tsakiyar ka. Ta kawo katon hair-bound kalar kayan jikin ta wato sky-blue ta zagaye mata shi. Fuskar Saade ta fito tsam, tayi cute da ita. Fulani ta taimaka mata ta nannada laffayar. Sannan suka fito.
Ko kusa bata gaya mata kasar zasu bari ba don ta san halin shagwabar Saade da rigimar ta, cewa zata yi bazata iya shekara babu Fulani ba.
Sun bata lokaci suna sallama, kamar kada su rabu,finally suka rabun. Saade na kwallah Zarah na kukan sai ta bi ta, da kyar Fulani ta rarrasheta da cewa asibiti zata je ta dawo, kafin Fanna ta raka ta wajen Ya Gumsu.
An jinginar ta jikin pillow bakin da ya karkace ya sha gashi ya koma daidai. Amma har yanzu bata motsa daya hannun yadda ya kamata amma kana iya gane abinda take cewa. Sauki dai yana ta samuwa cikin yardar Ubangiji da kulawar yayan ta.
Idan Allah ya baka yaya masu jin kan ka ya baka komai na duniya. Kishiyoyin ta ma baa bar su a baya ba wajen nuna kulawar su akan iftilain da ya same ta.
Ya Gumsu na ganin shigowar su ita da Fanna ta mika mata hannun ta mai lafiya, da sauri Saade ta karasa ta zube gaban Ya Gumsu. Hannu ya Gumsu ta dora a kanta tana shi mata albarka tare da cewa cikin harshen barbarci.
Wa gafurne kla awodune nyiro dikkuna samma so ro, Nadimtikna.(Ki yafe min na yi nadama a akan duka abinda na aikata, na yi nadama).
Saade tace baki yimin komai ba sai alkhairi Ya Gumsu, Allah ya baki lafiya.
Ta mika hannun ta mai lafiya kasan filon ta ta dauko warwaron zinare guda uku ta zura a hannun Saadatu. Saade ta rike hannun Ya Gumsu tana godiya.
Daga nan Fanna ta rakata unguwar Yaa Kirjiloma da unguwar Yaa Hibbani duk tayi musu sallama, kowacce da dan abin arzikin ta na sallama don tun faduwar Ya Gumsu jikin kowacce yayi lakwas, musamman Hibbani ta rage daukan zancen kowa ta kaiwa Askirama.

Impatientlykuma admiringlyYareema Sageer ya dubi Saadeda hanzari, lokacin da aka bude mata motar da yake ciki mai duhun glassai ta yadda baka iya hango wanda ke ciki.
Zaquwar son ganin ta na tsayin wannan lokacin da ya dauka ba tare da ita ba yasa ya hadiye fushin sa na jiran data bar shi yana yi a mota.
Data shigo ma aka rufe kofar motar jikin kofa ta koma ta makure ta juya masa keya.
Da ta san yadda zuciyar sa ke racing a cikin kirjin sa sabida excitement din ganin ta finally by his side da bata juya masa keyarnan ba.
Yarima ya girgiza kai yace ki yi lokacin ki ne Maman Chiroma, ko ba haka Askirama yace sunan Baby ba?
Ba ta san ya san da wannan maganar ba don haka ba shiri ta sunne kanta cikin cinyoyintadireba na barin kofar masarautar sai taji sanyin hannun Yarima a gadon bayanta a janyo ta sosai barin jikin sa sannan hannun sa ya kurda kasan marar ta yana shafawa cikin a hankali, ya sunkuyo daidai saitin cikin nata yace.
Stay blessed Chiroma.
A ranta tace shin in kuma ya mace ta haifa fa? Yarima da Baban sa zasu yi farin ciki? Yadda Mai askira da Yarima suke ta ambaton haihuwar da namiji? Zata so ta yi wa Yarima wannan tambayar, amma jin nauyi bazai bar ta ba. Kamar ta yi azarbabi in tayi maganar nan tun yanzu amma curiousity na cewa ta daure ta tambayi Yarima tun yanzu.
A dan zamanta gidan sarautar ta fahimci burin kowacce mace a gidan shine ta haifi da namiji har murna suke da Fulani Bilkisu ta haifi Zarah. Kuma a karan kanta gani take Askirama bai damu da Zarah ba kamar sauran yayan sa. Bata ji yana fadin a kawo ta fada ba. A ganin taHaihuwar dai ta janyewa Fulani Bilkisu gorin rashin haihuwa ne kawai a gidan amma da ita da babu sammakal.
Direba ya ja mota suka dauki hanyar Abuja. Inda zasu yi visa su tashi zuwa Ankara. Basu tsaya ba sai lokacin sallahr Azahar a gidan mai. A motar ma Yarima bai bar ta sakat ba da nauikan soyayyar sa mai tsayawa a zuci wato (sumba). Ta amince shi din expert ne a wannan fannin, ta yarda yayi missing din ta fiye da yadda zai iya bayyanawa, ta ga hakan cikin emotions dinsa da rawar da jikin sa ke yi a kan ta, tun da shi mai karancin magana ne sai dai actions da shaukin dake cikin zuciyar sa su fadi halin da yake ciki.
Sai dare suka shiga Abuja, kuma ba gidan su suka nufa ba kai tsaye hotel din (Fraser Suites)Yarima ya baiwa direban umarnin shiga.
Tuni ya sa an kwashe komai na su daga gidan malamai na NTNU dama gidan mallakar jamiar ne. Suna shiga dakin da suka kama Yarima ya maida kofar ya yi azamar rungume Saadeverytightly,
this seems like eternity! Ya Allah! Na roke ka, kada ka hora laifuka na ta hanyar nesanta ni da abinda na fi son kasancewa da shi a rayuwata. I missed you Saadatu!.
Ta kara narkewa a jikin Yarima sai yanzu ta san itama tayi kewar wannan kulawar ta Yareema Sageer, zaman ta tare da jamaa ne yasa bata gane hakan ba, ajiyar zuciya take saukewa a jejjere, tace
Prince, ina cikin damuwa, an ce ina da ciki, kuma na ji kuna ta kiran sa Chiroma tun ban haifa an ga me na haifa ba..
Ina cikin damuwar idan mace kuma na haifa fa? Wata zaka auro ta haifa maka namiji? Ko kuwa ita din bazaka so ta ba tunda bazata yi sarauta ba?
Yadda ta karasa maganar cikin karaya sai da ta sanya Yarima Sageer dariya. Ya dago fuskarta bisa tafukan sa. Ya ce
Saadatu in kin so ki jero min dozen na yaya mata, ki gani in zan so su ko ba zan so su ba, ki gani in zan kara auren wata matar don ta haifo min namiji.
Namiji baya alkawari akan aure musamman Basarake wanda ya gaji aure-aure amma ni Sageer! A yau ina mai tabbatar miki da cewa idan harba kaddara ce ta bi raayin kan ta ta aura min wata ba, na gama aure a rayuwa ta.
Abin da baki sa ni ba niSageer shaanin sarauta ba ya gaba na, Maimartaba na so in haifi namiji ne don ya tabbatar ba zan yarda in karbi sarauta ba. Amma ba don in kin haifi mace ba zamu so ta ba, ko hakan ne zai sa a kara yi min aure.
Mun dade da gane illar hakan cikin gidan mu wato fifita haihuwar maza akan ta mata don haka in kina tunanin hakan, to ki dai na.
Ajiyar zuciya Saade ta yi, a kalla yanzu ta samu peace of mind don ta san Yarima ba ya fadin abinda ba haka yake a zuciyar shi ba. Daga nanwanka su kayi kasancewar sun yi duka sallolin su a hanya.
Suna idarwa ya yi musu odar abinci mai rai da motsi, amma kallo daya Saade ta yi wa abincin tace bazata ci ba, dan wake take so mai manja da yaji.
Dan wake Saadatu? Yarima ya fada cikin damuwa. To yanzu ina zamu nemo shi a daren nan? Ta yarfarda kai ta ce mu je mu zazzzaga na san bazaa rasa mai dan wake ba.
A take Yarima ya mike ya dau mukullin mota, Bukari ya kwanta yanzu (direban da ya kawo su) mu je mu nema.
Ko dama so take ta fita din ta shaki freshair, ta gan ta Yariman Askira na tuka ta a mota da kan sa, wannan priviliged yana sanyata nishadi, shiyasa ta kakalo dan wake, in tace haka kawai su fita cewa zai yi ya gaji kuma dare yayi, yanzu kuwa ko don dan sa ya samu abinda yake son ci ta san ba shi da zabi banda su fita din.
Shiga wannan titi fita wancan suna tafe suna hira har ya samo mata danwaken a wani karamin eatry.
Basu dawo ba sai 11 na dare, tun daga bakin kofa Saade ta soma tausayin kanta, domin Yarima bai yi duka wannan wahalar neman danwaken ba sai da ya fanshe ta. A hakan ma yana tausayin ta sabida cikin jikin ta amma ta biya duka basussukan sa da ta ci tun kafin barin ta Abuja zuwa yau da kyakkyawan reward.
Washegari suka nufi Turkish Embassy suka shigar da neman visa. A kwanaki bakwai da suka yi suna jiran fitowar visar su ta tafiya Ankara sai suka zama kamar renakun honeymoon cikin hotel din Fraser Suites. Abin ki da mace mai yaron ciki, komai na jikin ta ya canza, don haka mannewar da Yarima yake mata har tsoro yake bata tamkar bai taba aure ko kusantar mata a rayuwar sa ba.
Auren sunnah daban yake, kuma macen alfarma daban Allah ke halittawa mijin ta ita. Shikansa ji yake kuruciyar sa na karuwa, lafiya da kuzari na kara shigar shi. Auren kananan yara ga maiyawan shekaru yana da wannan advantage din.
Yayi amfani da zaman hotel din ya nema mata transfer ta yanar gizo daga NTNU zuwa ANKARA UNIVERSITY.
A ranar da visar su ta fito transferdin Saade ma ya samu. Washegari suka bi Turkish Airlines zuwa kasar Turkiya.
Duk wasu memories na zaman ta a kauyen Tsanyawa tare da Baban ta, zuwan ta Askira wajen mahaifiyar ta, zuwa Abuja zaman gidan Dr. Sageer da yayi sanadin auren ta da Yarima Sageer din,ta kasa manta ko daya. Ta yi musu kundi (littafi na musamman).
Wato shi bawa tun haihuwar sa an rubuta masa dukkan kaddarorin sa. A hankali zaici karo da kowanne.Ta debo duka memories dinta taho dasu Ankara cikin kundin adana tarihin ta.
Kuma bata san shirin Yarima ba sai bayan saukar su a babbanfilin jirgin saman birnin Istanbul wato HavalimanıİşletmesiA.Ş. Istanbul Airport.Cewa ita da gida sai ta gama karatun digirin ta, ko ta haihu ko kafin ta haihu. Zai aika a dauko mata Fanna.
A lokacin da Yarima ya gaya mata hakan a filin jirgin ne suna tafiya zuwa terminal, hannayen su sarke cikin na juna. To ko taji damuwa ba kamar yadda ya zata ba, sabida a halin yanzu shakuwar da suka kara yi a dan tsukin ta zarce ta baya, a dan takaitaccenzaman su na kwanaki bakwai a Hotel dinFraser Suites, a halin yanzu tafi son kasancewa da shi har fiye da kowa a rayuwar ta.
Daga Istanbul suka bi jirgin kasa (Turkish Railways) daga Halkali wanda zai kai su zuwa Ankara (capital of Turkey).
******




ANKARA
Basu bar Ankara ba sai da Saade ta shiga watan haihuwar ta bayan bikin yaye su (convocation) na kammala digiri akan (Pure&Applied Chemistry) inda Saadatu Hashim Askira ta fiddo kwalin ta mai daraja ta farko. In aka duba kuma da idon basira duka nasarar karatun Saade sai ace hobbasar Yarima Sageer ne, miji mai cin tudu ukku a rayuwar Saade; malami kuma masoyi, ta wani fannin Yayan da bata da shi, kuma wanda babu kamar sa a rayuwar ta.
Alkawarin da ya daukar wa Mai Askira ya cika shi, ya rike Saade da dukkan amana, ya rike ta da dukkan kauna da soyayya haka ya zama mijin marainiya.
Ya gama appliedresearches din da ya je yi, yayi nasarar rubuta littafai muhimmai akan fannin sa. Wadanda suka bashi damar zama Farfesa, domin bayan dawowar su Askira da dan lokaci kalilan ya kama aiki da jamiar Maiduguri (UNIMAID) wannan ne dalilin komawar rayuwar su garin su Askira bakidaya, ko ya je Maiduguri baya wuce kwanaki biyu ko uku zai shigo Askira. Har gobe yana nan akan burin sa na kafa privateuniversity a garin Askira kuma yana cigaba da fafatukar hakan.
Saade da ta tashi haihuwa sai ga kyautar Allah ta yaya mata har guda biyu. Wadanda suka ci sunan Ya Gumsu da Fulani Bilkisu. Soyayya ta karshe yan biyu (amaren Askirama) yadda ake kiran su cikin gidan sun gan ta wajen Mai Askira. Dr. Sagir kuwamaida Sahlah da Suhailah ciki ne kawai ba ya yi sabida soyayya.
Ya Gumsu ta dade da samun lafiya kuma tuni ta kama girman ta ta kuma daina adawa da Fulani Bilkisu. Ta yarda da duk abinda Askirama ke fada a kan ta. Sun hada kai sun samarwa Mai Askira madauwamin kwanciyar hankali a shekarun tsufan sa.
Yayin da Sahlah da Suhailah suka zamo masu debe masa kewa don kullum sai ya fita da su fada ya ajiye a hagu da daman sasuna kiriniyar su yana gudanar da alamuran mulkin sa.
Ko kusa babu wanda ya yi mummunan furuci akan haihuwar yaya mata da Saade tayi a masarautar bakidaya, sabida yara ne masu shiga rai, da ko baka yi niyyar daukar su ba sai sun ja hankalin ka ka dauke su. Jinin BAGGARA ne dana BABARBARE ya hadu ya bada wadannan twins masu tsananin kyau da shiga zuci. In har ba UNIMAID zai tafi ba zaka same shi tare da yan biyun sa a cinyar sa ko a gefen sa ko a hannun sa. Prof. Sageer Yusuf Askira.
******




MURFI
Nakuda take tamkar bazata tashi ba, nakuda ce da ko haihuwar yan biyu bata yi mai zafin ta ba. Ta riga ta fidda rai da rayuwa, tana kwance ne a cinyoyin Yarima Sageer ta hada gumi kashirban, gashin kanta ya watsu bisa jikin sa. Idan na taba cutar da kai a tsayin zaman mu ka yafe min Baban Suhailah, ta fanni na baka yi min komai ba sai alheri da soyayya Yaya Yareema. Idan na mutu,kada ka kara aure zan yi ta jiran ka aljannah har ka iso, ka ji? Ka cewa Fulani ta yafe min its not easy being a mother! Na kara daraja ta fiye da baya, na kara son ta fiye da wanda nake mata, na kara ganin kimar ta da martabar ta.. na so in yi tsawon rai in biya mata Hajji Allah bai yi ba..
Sai ga wani uban nishi ya biyo baya, Sageer ya dauka tafiyar kenan! Sabida haka numfashin sa ya soma kokarin barin kirjin saamma sai me? Kafin ya bude ido sai ya ji nurse Aisha na cewa cikin farin ciki.

HERE COMES OUR PRINCE!
Sai kuma baby data taro ya callara kuka wanda ba kwanyar Yarima kadai ya shiga ba har da ta unconscious Saade, kuma kukan ne ya maido ta a hayyacin ta.
Nurse Aisha ta nade jaririn a tawul bayan ta goge masa jiki daman zaitun (olive oil) ta zo ta dora shi a ruwan cikin Saade wadda ke kwance kane-kane a jikin Yarima tana mai kallon komai kamar cikin mafarki.
Yau itace da haihuwar namijin finally. Bayan ta fidda rai, domin kuwa bayan Twins sai da ta kara wasu setin twins din again duka mata, wadanda suka ci suna Rahimah da Hannatu. Sai yau haihuwa ta uku taji ana kiran Prince.
A hankali ta lumshe idon ta da wahala tasa duk suka zurma ciki suka kankance, ta bude su akan kaykkyawan Babyn ta wanda bata ga fuskar kowa a kan fuskar sa ba sai Ahmad autan su Yarima, wato dai daYa Gumsu yake kama. Hakika La taqnadou min rahmatullah. Allah yana jinkirta maka abunda kake so zuwa lokacin da ya ga yafidacewa ya baka, abin so shine ka kasance cikin yin tagociya a adduaarka, wato idan kaza alkhairi ne a gare ni Allah ka bani, idan ba alkhairi bane Allah ka musanya min da mafi alkhairin sa. Not Allah ka bani kaza anyhow.
Yarimah ya dauki babyn yana kallowith affection sannan ya lakuce masa hanci. kai Chiroma shine ka wahalar min da mata ko? Kasa har ta fara bada wasiyyar hana ni aure idan ta zarce? Daidai lokacin da Askirama da Fulani da Ya Gumsu suka shigo fuskar su fal fara don tuni albishir din isowar Chiroma ya je musu.
Nan nurse Aisha take basu labarin wasiyyar Saade ga Fulani da Yareema. Suka ce me zasu yi ba dariya ba. Fulani ta ce yanzu ma bata baci ba a bani kujerar makkah na in je in yi azumi acan ni da takwarata, ban daukar takwarar Ya Gumsu tunda bata zuwa kwana waje na. Askirama yace to kai an ce kada ka kara aure ka jira sai an hade a aljannah, nikuwa da har na shirya maka kwarkwarori uku tunda Saadatu jego zata fara. Yaa Gumsu tace lala-lala Askirama in wasa nea bari, kaima ka haramtawa kan ka naka, a na me shi zaa takura shi a kai Alanguburo? Cewa yayi bai iya jiran matar sa ta gama biki? Kunya ta lullube Saade amma ta ji dadin yadda Ya Gumsu ta dage ta hana a baiwa Yarima concubones, ta san da watakila shikenan ta bar shakar numfashi daidai a duniyar subhanah.yammata hudu rus! Ga Yarima Sageer? Ai karshen ta a barrow zaa kwasheta zuwa asibitin masu dan karamin tabin hankali.
Shima Askirama jin baki ne irin nasa, don ya san ba abinda Yarima ya ki jini irin ace ya kara aure. Da an fadi hakan zai jawo ayar Allah ya ce sai zaku iya adalci, shikuma bai iya adalcin tsakanin Saadatu da wata diya mace, da muguwar rawa gwamma kin tashi. Shiyasa Askirama yake so ya dauki kwarkwarori duk adadin da yake so, amma wani zubin har zuciyar sa yana ganin Yarima ya hada da concubines zai kara fiddo da kimar sarautar sa.
A yanzu dai Yareema Sageer ya ce baya da bukata bai sani ba dai ko can gaba in ya fara tsufa.
Baby ya ci sunan Askirama YUSUF. Ana kiran sa Chiroma. Tsakanin Mai Askira daYa Gumsu ban san wa ya fi son jikokin nan ba. Ya Gumsu kullum ta dubi yaran sai ta kara nadama ta yi dana sanin ja da hukuncin Ubangiji, lalle ne ko rabon wadannan yaya biyar ya isa ya kayar da ita kwanan ta bai kare ba.
A halin yanzu ta fi kowa alfahari da auren Yarima da Saade ta kuma yardada abinda Askirama ke fadi cewa Saadatu diyar Bilkisu,rufin asiri ce, suttura ce ga dan su Yareema Sageer Yusuf Askira.

Masha Allahu laquwwata illa billah.

Nan na kawo karshen littafin MASARAUTARMU 3&4. Kurakuran dake ciki ku tayani rokon Allah ya yafe mini. Abin alfanun da ke ciki Allah ya hada mu a ladan nida ku bakidaya.
Sumayyah Abdulkadir
18/11|2021.

Ina mukualbishirda sabonlittafinamaisuna NA HUCE!Wanda zaizo a matsayingoronsabuwarshekarainsha Allah.


TUNA SUNAN SA;
NAHUCHE (DagaFushina)






NA HUCE..
LITTAFIN
SUMAYYAH ABDULKADIR
Hawayen da yake ta rikewa ne suka kwace masa, ya juya kadan ya dubi Rahinah wadda ke kallon bayansa a lokacin, suka kuma hada ido, ji ta yi zuciyar ta na son karyewa (rauni irin na diya mace na son mamayar ta) amma ta amince wannan shine decision mai kyau ga rayuwar ta.
Sai ta maida idanunta ta lumshe su a hankali. Tana sauke ajiyar zuciya.
Shi kuma ya sa kai ya fita daga dakin, babu ko waiwaye. Kamar yadda yake ji a ransa ba zai kara waiwayar RAHINAH OMAR a rayuwarsa ba. Ko da bayan cikar burin ta, na zama cikakkar otorhinolaryngologist.
****
Ta dauki hoton karamin kyakkyawan yaron mai kama da ubansa a komai tana kallo with so much adoration, hawaye na sauka a kan fararen kundukukin ta. Ta san yanzu ya girma, watakila aji hudu na firamare? Cikin kowanne hali dai ta san zai kula da shi. Damuwar ta ba a kan kulawar da yaron zai samu ba ne domin hakika tana da tabbacin HABIBUNAHUCHEzai kula da dansa har fiye da yadda yake kula da Hotels din sa. Damuwar ta akan yadda har gobe ta kasa kallon kowanne namiji da idanun sigaraure, kowa ya zo sai ta ga bai kai shi ba, ko farcen kafarsa bai kama ba, ko da kuwaya fi shi komai na rayuwa.
Duk da cewa ta san shi ne kawai a matsayin dalibin jami'ar Cologne ba'a matsayinsa na yanzun ba (mamallakin NAHUCHE HOTELS) amma tana bibiye da duk wani fadi-tashinsa na rayuwa tun daga ranar da ya raba ta da Dan su.
Dalilin bibiyar ne ba ta sani ba har yau, tunda ita ta ce bata son sa. Farin jini kam har bata san irin nata ba, manema ba irin wadanda Allah bai ba ta ba, kuma burin Dada shine ta yi aure tun kafin Allah ya dau ranta, amma har gobe ta kasa kallon kan sauran maza daga shi sai dan mutanen NAHUCHE. The one that took away her pride na diya mace. Wanda ta tabbatar zuwa yanzu ya manta da ita, a irin shuhurar da Allah ya yi masa cikin shekaru goma kacal da rabuwarsu.
Bata san hawaye take ba. Sai da ta ji dandanon gishiri a bakin ta. Hawayen da ta tabbatar ba za ta daina zubar

Please Login or Register in order to submit comment