You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sunanta ciki-ciki tace "Ummy ki gafarce Ni..."
Daga nan tayi wucewarta...

Abbah shima juyawa yayi ya haura saman upstairs rai a ɓace, kab mutanen wurin babu wanda yaji daɗin abinda ya faru amma masu faɗin madalla su sukafi yawa domin da yawan su babu wanda yake jin daɗin zama da Hajiya Kilishi saboda ta kasance mace marar son mutane, Aunty Yolash ɗan tsaki taja tareda wurga ƙwayar idonta kan Hajiya Maamie wacce itama tana wurin tace "waɗanda za'a kora ai sunada yawa, ina mai martaba shima yazo yahau kan layi, domin baza'a mayar mana da ɗan uwa bita zai-zai ba...."

Duk sauran mutanen suka tintsire da dariya tare da faɗin "wallahi kuwa..."

Hajiya Maamie dogon tsuka taja tana hararar Aunty Yolash da sauran ƴan uwansu tace "Ni kuwa an mutu dani wallahi, babu yanda aka iya dani, mutu karaba takalmin kaza Ni da mai martaba, dole a ganni a barni domin na zamo ciwon ido..."

Aunty Yolash tace "yooo wa kika ajiye balle ki zauna dashi har ƙarshen rayuwa? To dai kina gani wacce ta ajiye har ƴaƴa biyar ma ta fita balle ke ko ɓatan wata baki taɓa yi ba...."

Hajiya Maamie tace "au gorin haihuwa ne ya tashi? ey gwara Ni a gidan mijina nake ba yawon tsinantaka ba, anyi shekara kusan arba'in amma babu mijin Aure..."

Aunty Yolash ta gama ƙuluwa matuƙa tace "bari kiji Madam! Bawai rasa miji nayi ba, niyya ne banyi ba kuma ko a yanzu naso yin Aure zanyi kuma na haihu da yardar Allah..."
Hajiya Maamie tace "to kiga dama mana yanzun ma, wa ya hanaki ƙirrr kutu kutu..."

Aunty Yolash tace "Uhmmm! Kin yanda nayi Aure yanzu ke kuma ki samu ciki a wata ɗaya zuwa biyu?..."

Hajiya Maamie Saida taji bugun zuciya domin a asibiti an tabbatar mata cewa mahaifarta yayi ƙarami a ɗaukar ciki sannan ta gama yawon bin bokaye da dama amma ba'a dace ba,
Harara ta wurgawa Aunty Yolash sannan tace "shi haihuwa daga Allah ne Dan buro ubanki...."

Aunty Yolash a ruɗe ta dafa ƙirji tare da faɗin "buro ubanaaa?! kika ce buro ubanaaa?!! buro ubanaaa kika ceee?!!!..."
Nan danan idon Aunty Yolash ne ya kaɗa yayi jawur domin tin tana cikin mahaifiyarta ta rasa mahaifinta memakon a bishi da addu'a sai kuma zagi, ai bata san lokacin da tayi sufa ta cabko wuyan Hajiya Maamie ba,
Hajiya Maamie ta tsorata sosai da ganin yanayin Aunty Yolash, mutanen wurin ne suka rirriƙe Aunty Yolash domin ba ƙaramin shaƙa tayi mata ba, duk yawan mutanen falon babu wanda ya iya ɓanɓaran Aunty Yolash daga jikin Hajiya Maamie,
Abbah jin hayaniya yayi yawa ne yasa shi sauƙowa dasauri, shima daƙer ya iya fizgar Aunty Yolash ganin bazata saurari abinda zai faɗa ba,
Cikin faɗa yake magana tare da faɗin "wannan wani irin hauka ne? babu dama a barku ku kaɗai sai an samu matsala?..."
ya kalli Aunty Yolash yace "ke meyasa bakida haƙuri ne? to ku same Ni acan falo ɗina yanzun nan..."
yana kaiwa nan yayi ficewarsa,
Aunty Yolash harara ta wurgawa Hajiya Maamie itama tayi gaba, Hajiya Maamie itama bayanta tabi, a falo duk suka tarar da Chief yana zaune akan tsararren Soparsa kai a sunkuye yanata karkaɗa ƙafafu, duk zama sukayi a ƙasin carpet domin falon Chief indai ba manya-manyan baƙinsa bane ba'a zama masa akan sopa,
Chief ɗaukar waya yayi ya ƙira wata dattijuwa a can falonsu wacce tana wajen akayi komai, can sai gata ta shugo da sallama a bakinta, amsa mata yayi tare da nuna mata saman kujera ta zauna, zama tayi tare da faɗin "to gani naga an ƙira Ni..."

Chief yace "Uma shin kina nan suka fara faɗa?.."

tace "tabbas kuwa "

Chief yace "toh inaso ki gaya mun gaskiyar abinda ya haɗasu kar kiga cewa kinada alaƙa da Yolash kawai tsakanin ki da Allah zaki sanar mun...."

Tsohuwa tace "tsakani da ALLAH kuwa zan gaya maka.."
nan ta kwashe komai ta sanarwa Chief abinda ya haɗasu...
Chief ya kalli Aunty Yolash yace "bakida gaskiya Auntyn Yara, meyasa bakida haƙuri ne? meyasa ZAKIYI mata gorin haihuwa? shin ba Allah ne yake badawa ba ne? ko kin isa ki bata haihuwar? ko kuma ita ta isa ta bawa kanta haihuwar? ko kuma mijinta ya isa ya bada haihuwar da Allah bai sauƙar ba? kuna abu da tunani mana, komai sai ku rinƙa nuna rashin ilimi akai, wannan ai zunzurutun jahilci ne gori akan abinda Allah ne mai bada shi bawai wani halitta ba, toh wallahi daga yau kar Na sake jin wannan kalmar daga bakin ki..."

Aunty Yolash tana hawaye tace "Amma Yaya itama tamun gorin Aure fah..."

Chief yace "Aure ai ke kika hana kanki, Allah ya baki damammaki da dama amma kin ƙi amfani dashi, nawa ne mazajen Aure suka zo nemanki amma duk kin ƙisu, kuma dan anyi miki gori sai kiji haushi?
Ai gorin haihuwa yafi na Aure ciwo, har yanzu damarki bai wuce ba, akwai waɗanda suke zuwa neman Aurenki, aciki akwai Governor Kaduna da Governor Bauchi ga Alhaji Tafidan Bauchi ga manya-manyan shuwagabannin nan Abuja da dai sauransu idan kuma kince a'ah TOH saiki cigaba da toshe kunnuwanki da jin duk wasu ƙananun maganganu akan ki,
Ku tashi ku ban wuri...."

Dasauri Aunty Yolash ta miƙe ta fice tana kuka,
Hajiya Maamie kuwa zaro idanuwa ta fara yi jin manya-manyan mutanen da suke neman Aunty Yolash da Aure, da hassada acikin zuciyarta tabar falon Chief,
Ita kuwa Tsohuwa zama tayi ta cigaba da tattaunawa da Chief akan yanda bikin zai kasance gashi ɗaurin Auren har da nashi....

Aunty Yolash tana shiga babban falonsu kai tsaye room ɗinta ta wuce ta danna sakata,
Mutanen da suke falo babu yawa duk sun kutsa kai ɗakin da Amarya take itama Baiwar ALLAH ta kulle kanta a cikin Bathroom taƙi buɗewa, sunyi da ita akan ta buɗe amma taƙi, gashi har lokacin dinner yayi, sauran yaran gidan ma ko wacce tana ɗakinta cikin damuwa ganin yanda Abbah ya wulakanta Mommynsu kuma sannan sunji labarin shima zaiyi Aure,
Angwaye sun jira har sun gaji basu ga ko mutum ɗaya ba acikin matan gidan balle suga idon Amarya,
Da haka har lokaci ya ƙure aka bantsar da hidimar Dinner, amma ba ƙaramin takaici suka shaƙa ba kaf Abokanan Ango da shi kanshi Angon,
Daman Aunty Yolash ce kawai zata iya tsawatar wa Baiwar ALLAH akan ta buɗe TOH itama ga a halin da take ciki itama ta kulle kan natan, Ummy ma wacce itace Yakamata ta rarrasheta itama ta zama uwar ɗaki....


🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️

Razhdeen shi da Mohandas layin mabarata suka nufa da isar su tsayar da motar sukayi a dai-dain layin suna baza idanu ko zasu hango Ƴar Amana, a wannan lokacin ma sun yi rashin Sa'a basu ganta ba, ɗan tsuka Razhdeen yaja tare da jan mota zai bar wurin Mohandas yayi saurin dakatar dashi tare da faɗin "wait Major! Bayan barin ka Nigeria nasha zuwa nan duba yarinyar nan amma bata nan, banyi tunanin sauƙa daga motar zuwa tambayarsu ita ba amma a wannan lokacin dole zamu je mu tambayesu ita, ina tunanin rashin zamanta anan ba lafiya ba..."

Dasauri Razhdeen ya juyo yana kallonsa cikin yanayin damuwa, ƙirjinsa ba ƙaramin bugawa yayi ba jin abinda Marshall ya faɗa..."

Mohandas yace "let me go and check her, stay inside the car..."
yana kaiwa nan ya fice kai tsaye wurin tsofin ya nufa, shi kuwa Razhdeen yana daga ciki yana kallon wurin da take yawan zama...
Mohandas tsugunawa yayi a gaban tsohuwar da Ƴar Amana take suka gaisa sannan yake tambayarta labarin Ƴar Amana,
Nan tsohuwa ta fashe da kuka tana faɗin "Allah sarki kurmiyar Allah, Amanar Allah sun ɗauke ta..."
Mohandas cike da mamaki ya furta cewa "daman kurmiya ce?..."
Tsohuwa tace "ey kurmiya ce, ɓarayi ne suka sace ta..."

Dasauri Mohandas ya miƙe tsaye tare da faɗin "whattttt!!!!...."

Juyawa yayi da gudu ya nufi motarsu, buɗewa yayi ya shiga yana jan numfashi ido a zazzare,
Razhdeen ganinsa ba ƙaramin tsorita yayi ba ganin halinda ya kasance, tsoronsa kar wani mummunan abu ya faru da ita..

A ɗan ruɗe Razhdeen yace "what's wrong?..."
shuru Mohandas bai bashi amsa ba,
A tsawace Razhdeen yace "ina maka magana ka bani amsa mana ..."
Razhdeen bai taɓa buɗe murya yayi magana kamar yanzu ba, cike da mamaki Mohandas ya juya yana kallonsa ganin yanda ya rikice lokaci guda,
a ɗan tsorace Mohandas yace "someone kidnap her..."

Razhdeen cikin go slow ya juyo yana ƙarewa Mohandas kallo ido a zazzare,
Jin bai gamsu da maganar Mohandas ba yasa ya buɗe murfin motar ya fice, kai tsaye wurin tsofaffin ya nufa yana zuwa ya tsaya yana binsu da kallo, a tsawace ya fara magana yana faɗin "Who kidnap her?,
tell me please who come and kidnap my sarah?..."

Duk tsaya kallonsa suke domin babu wacce tasan mai yake faɗi domin da turanci yake maganar,
tsohuwar ƴar Amana ce tace "kayi haƙuri yaro Bama jin Yaren nan..."

Razhdeen hannu bibbiyu yasa a cikin sumar gashinsa yana cakurkuɗawa cikin zafin rai yace "nace waye ya sace mun Sarah? ..."

Anan duk suka sanar masa duk yanda akayi da cewar suma basu ga fuskarsu ba domin baƙar hula ce akan su...."
tsohuwar ta miƙa masa jitar Ƴar Amana...

Razhdeen kamar zai dungura haka ya nufi motar yana shiga ya finciki motar a ɗari suka bar wurin,

A wannan ranar Razhdeen da Mohandas ba yanda basu shiga ba neman Ƴar Amana amma babu ɗuriyarta, duk yanda suka san ƙungiyoyin Dabanci Saida suka je amma basu samu labarinta ba, Saida suka yiwa wasu ƴan Daba dukan tsiya ganin zasu raina musu wayo,
yanzu misalin ƙarfe 2 na dare suna hanya, Mohandas gaba ɗaya ya gama gajiya daƙer ya lallami Razhdeen suka koma gida akan washe gari zasu ƙara fitowa nemanta......


asmeetah writer ✍️




*MY ENEMY _*

🫦 مقىينا 🫦


Mallakin
أسماء محمد أولا 🥳

Asmeetah (giaɗe writer)




https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v

💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️


STEP TWO
👇
*11_ TŌ _12*


Misalin ƙarfe uku na dare, agogo ne yake harbawa a hankali ƙit-ƙitt-ƙittt a yayin da Razhdeen yake kwance saman katafaren gadonsa, yana rufe da mayafi sai iya fuskar sa ne a waje yana kallon ceilling, kashe hasken ɗakin yayi sai ɗan hasken lamp da ya bari mai launin green,
A daren yau Razhdeen bai samu yin bacci ba sakamakon abin da yasa a ran sa, ɓatar Ƴar Amana ba ƙaramin girgiza shi yayi ba domin a halin yanzu bai san a wani hali take ciki ba, gashi an bayyanar masa cewa zuwa akayi har wurin da take aka ɗauke ta, duk yanda akayi sun haɗa mata tarko ne,
Tunani ne barkatai acikin kwakwalwar sa, mafita yake nema yanda zai samu yarinyar nan domin a halin yanzu ita ce raunin sa!...

Washe garin ranar ɗaurin Auren Roshan da Baiwar ALLAH, kowa ya hallaru baƙi ne a gidan Chief kamar basa mutuwa tsabar yawan family, misalin ƙarfe 12 na rana Ango da Abokan sa kowa yayi shirin zuwa ɗaurin Aure dake can babban masallaci, Abbah shima da abokansa waɗanda suka zo ɗaurin Aure sun sha manya-manyan kaya, kowa ya hallaru sai fita ake da wasu manya-manyan motoci ga motocin sojoji suma zasu yi rakiya, kowa ya tafi sai iya Ango ne kawai ya rage shima yasha farar gizner da babbar gariya sai shining giznar take, ga wani irin ƙamshin da yake fitarwa kai kace wanka yayi da zallar turare,
Roshan ba ƙaramin kyau yayi ba, ga hular kalar kayan, sai wasu Abokansa guda uku motar su ce kawai ta rage basu tafi ba, ganin Roshan yaƙi tafiya yasa suma suka ƙi tafiya domin saboda Angon za'aje wurin ɗaurin Auren shi kuma bai tafi ba, Roshan ba kowa yake jira ba illa twins ɗinsa Razhdeen, duk taron mutanen da akayi babu Razhdeen a ciki, kowa sai tambayar sa yake, domin shine twins ɗinsa kuma babban Abokin Ango, an ƙira wayarsa switch up, anje gidansa baya nan babu wanda yasan yanda yake hatta Mohandas shima ya halarci wurin ɗaurin Auren Roshan,
Ganin shuru babu labarinsa yasa Abokanan Roshan suka ja shi cikin motar nan da nan kamar walƙiya suka bar gidan domin iya su kawai ake jira a wurin taron ɗaurin Aure...

Baiwar ALLAH tana bedroom ɗinta tare da masu kula da ita ba abinda take sai kuka, gaba ɗaya fuskar nan tayi jawur tsabar kuka kamar ba Amarya ba, ji take kamar ta sanar cewa bata son Auren Roshan amma sai dai idan tayi hakan tayi butulci sannan aikin gama ya gama tinda an tafi ɗauro Auren, har cikin ranta bata cire son Razhdeen acikin zuciyar ta ba kuma gani take bazata taɓa cire soyayyarsa ba, kulle kanta da tayi a bathroom tayi niyar tasha poison ta kashe kanta amma tayi tunanin kashe kai ba abu ne mai sauƙi ba, tana ciki Abbah ya shugo domin a lokacin har anje an gayo masa dake tana jin shakkar Abbah,
tana zaune a bakin bed tunanin samawa kanta mafita take, amma zuciyarta na sanar mata cewa "kiyi haƙuri ki zauna da mijinki haka ƙaddarar ki tazo miki, a duk yanda kika tsinci kanki to ki gode wa ALLAH..."
Sauƙe numfashi tayi domin tayi na'am da shawarar da zuciyarta ta bata, a hankali take ɗago da kanta tana bin mutanen ɗakin da kallo, ganin kowa yana cikin farin ciki yasa ta yin maganar zuci cewa "Allah sarki farin cikin ku kawai kuka sani amma baku san tawa farin cikin ba..."
tana cikin saƙe-saƙe kwatsam taji an dafa kafaɗarta, da sauri Baiwar ALLAH ta juyo tana kallon wacce ta zauna gefenta tare da ɗora mata hannu akan kafaɗa,
Ramlat ce tasau mata murmushin takaici da kuma kishi ta ce "Sannu Amarya bakya laifi, Amma fah kin ciri tuta gaskiya duk da baki da asali amma haka Yaya Roshan ya nace miki, kuma ba wani dace wa kuka yi da juna ba, kina nan kamar wata farar goɗiya..."

Duk mutanen ɗakin ne suka juyo suna kallon su, wata daga ciki ne ta ce "toh ikon Allah duk meya kawo wannan maganar?..."

Ramlat ta kalleta sama da ƙasa sannan ta ce "bakin da Allah ya tsaga baya rasa ta cewa, don haka abin da ke raina na faɗa..."

wacce tayi maganar ce ta kuma cewa "Amma ai bai kamata kiyi irin wannan maganar a cikin mutane ba..."
Ramlat ta ce "Oh ashe dai a cikin mutane nake, ai Ni kuwa na ɗauka dabbobi ne..."

Duk shuru suka yi saboda ba mai iya tanka mata, tsoron Ramlat ake saboda Hajiya Maamie domin ba ƙaramar masifaffiyar mata ba ne, yanzu sai ta iya hargutsa taron bikin,
Ummy uwar masu gida wacce jugowarta cikin ɗakin kenam, kalmar da Ramlat ta furta ne ya daki dodon kunnenta, ai kuwa nan itama ta buɗi baki ta ce "dabbobin suna da yawa ai amma sai dai wacce take agolanci tafi dabbobin dabbanci..."

Ramlat miƙe wa tayi tsaye tana bin Ummy da kallo cike da mamaki ta ce "Ummy Ni kike ƙira da Agola?..."

Ummy ta ce "to ƙarya akayi miki ne? ko gidan Uncle mai martaba da kike zaune a gidan Ubanki ne shi? kin samu matsayi ne albarkacin zaman da kike a gidan sarauta amma in ba haka ba kin isa ki buɗe baki kiyi wani maganar banza ne anan, duk mutanen da kike gani acikin gidan nan duk jini ɗaya ne babu bare sai ke, Yayarki ce matar mai martaba ita kuwa ba haihuwa take ba hakan yasa ta jawo ki gidan sarauta kizo ki ci arziƙi babu a house..."

Ramlat ita kaɗai tasan takaicin da take shaƙa a yanzu buɗar baki tayi ta ce "au gorin haihuwa zakiyi wa Aunty nah? eh naji bata haihuwa amma ai ta kama kanta tana zaune a gidan mijinta, wata uwar kuma zubar da ƴaƴanta tayi take bin yawon hotel..."

Ramlat tana kammala fitar da abinda ke ranta tayi saurin barin room ɗin domin tasan uwar Ummy ce take yawon hotel,
wani abu mai kama da kibiya ne ya soki saitin zuciyar Ummy tsabar takaici da baƙin cikin har an fara mata gori akan mahaifiyarta,
Da sauri ta juya zata bi bayan Ramlat taji an riƙo ta juyawa tayi taga Baiwar ALLAH ce take ta faman girgiza mata kai alamar karta biye mata,
Ummy tsabar takaici bata san lokacin da ta rausa uban ihu ba tare da durƙusa gwiwowinta ƙasi, duk mutanen ɗakin ne suka rufu kanta suna bata haƙuri akan abinda ya faru, Ummy kuwa kuka take ko sauraron

Please Login or Register in order to submit comment