Downloaded From https://tknovels.com.ng _BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM_ *_TABARMAR K'ASHI_* *SAFIYYA HUGUMA* _AREWABOOKS:Huguma_ https://arewabooks.com/u/huguma Page 01 K'awataccen bedroom ne me yalwa,wanda ya wadatu da kyawawan kayan gado da suka kasance cikamakin ado da kyawun dakin,komai dake cikin dakin an hada masa color iri daya CREAMY WHITE da ratsin gold me daukar idanu,ya wadatu da sanyin ac da kuma haske sosai tarwai. Saidai kuma abinda zai baka mamaki shine,duk da irin kayan ado da qawar da bedroom din ya mallaka,kusan komai na dakin a hargitse yake,hatta da tattausan farin bedsheet din da comforter din dake daga gaban gadon a yamutse suke guri guda,uwa uba kuma dukkansu sunyi staining da wasu abubuwa da bazaka iya tantance meye a jiki ba,illa dai ka ragewa kanka wahala ka kirasu da datti kai tsaye. Daga can tsakiyar gadon kuwa, matashiya ce zaune sannan a cure waje daya,tamkar wadda ke shirin saka kanta cikin gangar jikinta ta koma abu guda,ta rungume gwiwoyinta sosai a qirjinta. Baka iya hangen fuskarta,amma kana iya hangen sassalkan gashinta me tsaho da santsi daya cukurkude,kwatankwacin yadda zare yake cakudewa guri guda,tsahon sumar ya sanyata barbazuwa har saman qafafunta,ya kuma rufe dogayen fararen singalalin hannunta. Rigar jikinta doguwar riga ce ta wani material ne ruwan madara,kallo daya zakayi masa kasan me tsada ne,saidai shi kansa ya canza yanayi yayi wani irin azababben squeezing. Idan ka kasa kunne da kyau zaka iya jin sautin kukanta,sautin da bashi da wani qarfi ko karsashi a cikinsa ko misqala zarratin,saboda rashin wadatacciyar garkuwar jiki da zata bata wannan damar,uwa uba kuma.......tayi kukan tayi kukan har batasan adadi ba,ta zubda hawayen har sai data daina sanin lokacin tahowarsu......har sai da idanunta suka fara gani dishi dishi,ta yanke tsammani daga samun dukkan dauki,ta kuma gama sallamawa qaddara rayuwarta. Duk da cewa a hankali ya bude qofar dakin amma hakan bai hanata jin alamun an bude din ba,a hankali ta daga kanta,ta kuma sauke dubanta ga bakin qofar,duk da mummunar wahala da ibtila'i me gigita hankali da gusar da imanin me raunin tauhidi da take fuskanta,amma har yanzu kyakkyawar fuskar nan tata tana nan yadda take,wani irin kyau na daban me matuqar tasiri da fusgar hankali da ya gagara gushewa shimfide saman fuskar tata,saidai kana kallonta kasan ba haka take ba,abubuwa da yawa sun canza wanna fuskar. Shi da ita suka zubawa juna ido kamar yau ce ranar farko da suka fara ganin juna,kowannensu da kalar kallon da yakewa dan uwansa. Dariya ya saki ya cire hannuwansa daga aljihun trouser din jikinsa,ya fara takowa zuwa cikin dakin bayan ya sanya hannu ya maida murfin qofar dakin ya rufe. Yana takowa yana tafa hannayensa, idanuwansa kuma a kanta kamar yadda dariyarsa bata yanke ba,ita kuma taci gaba da binsa da kallo,zuciyarta tana la'antarsa,tana sake daukaka qararsa zuwa ga sammai wajen ubangijin al'arshi. A haka ya qaraso,ya jawo stool zuwa gaban gadon,ya zauna sosai yana fuskantarta hadi da taka gefen gadon da qafarsa guda daya "Kewai kina tunanin akwai abinda zakiyi da zai warware dukka shirina?,ko kina zaton zaki kubuta da sauqi haka?" Kyawawan idanunta da suka sake zama manya manya ta lumshe,ragowar hawayen da basu samu damar zubowa ba suka gangaro,sannan ta budesu tarwai a kansa "Bani da tsumi kuma bani da dabara,ban isa na fidda kaina ba,amma na kaiwa me kowa me komai,mai iko akan kowa qararka,koda kayi ajalina.....koda bayan raina ina fatan nutsuwa da salama suyi qaura daga rayuwarka,ka girbe fiye da abinda ka shuka" ido ya runtse ya kuma bude a tare yana sakin qaramin murmushi,sai ya miqe tsaye "Dadina dake tawakkali....." Yayi furucin yana qara taku biyu zuwa gaban gado,ya haye gefan gadon ya zauna,sai tayi saurin sake tattare qafafunta ta rungumesu da kyau,kamar wanda yake shirin raaba mata maciji a jikinta. Qafafun nata yabi da kallo har ya zuwa fuskarta,sai ya sake qyalqyalewa da dariya "Ina sonki.....kuma banajin zan daina sonki,saidai kin shiga hurumin daba naki ba,kin shigar gonar daba taki ba,kin tsallake iyakarki,kuma a yanzu nafi buqatar wadan nan abubuwan fiye dake,ki daukominsu ki damqamin,ke kuma na barki kici gaba da rayuwarki cikin salama" kai take girgizawa tana hawaye,wani irin mamakinsa tana jin kamar zai kasheta, kowacce rana da zata bullo zuwa faduwarta cikin shakka da kokwanto take,anya wannan din ADAM NE?,anya adam dinta ne?,anya musanyensa akayi mata ba?,ko kuma wata rundunar mugayen shaidanun aljanu ta shige jikinsa ne ta samu mafaka?,don abinda yakeyi a yanzun da ainihin wannan suffar tasa ta yanzu.......bata taba ganinta a tattare da adam dinta ba,koda kuwa cikin mafarkan bacci bare a kai ga rayuwa ta zahiri,adam din da ko quda baya qaunar ya sauka a kanta?,adam din dake kuka da idanunsa idan bata da lafiya?,adam din da yake kasa bacci saboda ta shiga damuwa?,adam din da yake kasa sukuni idan tana da buqata har sai ya adar mata?,dole ta shiga shakka.....amma kuma kullum yana qara tabbatar mata da cewa shi dinne fa,bawai kama ko musaye bane,to me yake faruwa?. "Bazan taba baka ba.....burinka bazai taba cika ba,saidai na rasa rayuwata,kayi duk abinda kaga dama" ta fada tana jin bacin rai yana taso mata,tare da wani irin qwarin gwiwar tunkarar duk nau'in kalar azaba tuggu da makircin daya shirya mata. Wani murmushi ya kuma saki yana dubanta,da wani irin kallo na qasa qasa mai cike da tarin mugunta "Ke kike jawa kanki koma meye,tunda ke muguwa ce ba zaki iya sallamamin abinda kikafi qarfinsa ba tako ina,to nima bazan sassauta miki ba har sai sanda kika gasu,kikaji cewa zaki iya sallamawa" daga haka ya miqe,ya fara fidda kayan jikinsa yana zubarwa a wajen. Idanu ta bude da kyau cikin tsananin tashin hankali tana dubansa,kada dai ace haqqinsa na aure yake shirin karba kamar yadda ya saba?,zallar rashin imanin da yake gwada mata bai sanya ya daga mata qafa ba,yakance "Har yanzu fa a sunan matata kike,ban saki igiyar ba,wannan abun dake faruwa wani issue ne na daban daya shafi interest dina da kuma naki". A duk lokaci irin wannan idan ya rabeta tana jin inama zata bude idanu taganta kwance cikin ramin qabarinta?,banda addininmu ya haramta kisan kai,naka ko na Wani,tabbas da tuni ta tsufa da kai kanta kiyama. Da gaske so yake ya kusanceta alhalin yasan cewa cikin jinin al'ada take,rashin imanin nasa qara gaba yake,dole tace rundunar shaidanun aljanu ne suka shigeshi,don lamarinsa yafi qarfin shaidani guda daya. Kansa tsaye ya nufota gadan gadan,kamar ba adam din nan da abaya a lokutta irin wanann yake sanyata taji babu ya ita cikin 'ya'ya mata ba,ya sanyata taji duk duniya babu macen da tayi sa'ar abokin rayuwa irinta ba,a yanzu ya koma mata wani tsohon annamimin ifritu mashayin jinin bil'adama da ko motsinsa bataso ji bare ya rabeta,bashi da maraba da qaton shaidani a idanuwanta. Ringing din wayarsa ya dakatar dashi daga sake tunkarota,sai ya koma cikin aljihun wandonsa da ya yasar yana lalubar wayar. Cikin hanzari ya karata a kunnensa,sai kuma yace "Ok,yanzu yanzu?,tom" ya latse wayar da sauri ya maidata,sannan ya soma mayar da kayan jikin nasa tana daga zaune tana kallonsa. Ga mamakinta sai taga yana bi yana balle button na rigarsa yana watsarwa,ya kama gaban rigar da qarfin tsiya ya ciccisge,sannan ya tsugunna ya jawo plate din tangaran din dake ajjiye gefe wanda ya kawo mata abincin da bata budawa bare ta taba,ya dagashi har abincin ya tamfatsa shi da qasa ya tarwatse,ya dauki wani yanki daga ciki ya yanki jikinsa ya kuma shashshafe maiqon a jikinsa. Sake miqewa yayi ya fara fatali da kayan dake saman madubi da duk wani abu na glass dake dakin yana cewa da matuqar daukaka murya "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,ki tsaya......ki tsaya don Allah,ya salam,karki jiwa kanki ciwo, Hasbunallahu wa ni'imal wakeel,ya hayyu ya qayyumu ya baki lafiya" yana fada hawaye na sauka a idanunsa,yana kuma ci gaba da tarwatsa dakin tare da sake hargitsashi,bayan tsaiwa da tayi tayi masa gyara na nutsuwa,waiko hakan zai sanya wani daga cikin ahalin nata su ankara da cewa akwai hankali tattare da ita. Sanqamewa tayi a zaune,tunaninta ya dinke cifff kan meye manufar adam na aikata haka?,saidai koma meye tasan halinsa,ungulu ne baya jewar banza,ba shakka akwai abinda yake shirin sake qullawa. Kafin takai ga lalubo abinda ke shirin faruwa sai ta tsinci muryoyin mutanen da a kullum take addu'ar isowarsu gareta,qila akwai wani haske da zai risketa,ya kuma zama silar fitarta daga duhu zuwa haske. Da mugun qarfi ta yunqura zata dira daga gadon,yayi caraf ya tsallako ya damqeta ya cukuikuyeta da kyau yana sake yamutsa rigata da yamutsatsen gashinta. Ya mata mugun riqon da bazata iya qwacewa ba,saboda banbancin qarfi da kuma qarancin garkuwa jiki dake tare da ita,don haka ta bude baki da zummar kiran daya daga ciki "Koda kin kirasun ma sun shigo sunanki bazai canza ba a idanunsu,sunanki mahaukaciya har yau har gobe,sai ranar da kika fanshi kanki,ni kuma zan wankeki a idon duniya" daga haka yaci gaba da qaraji da ambaton sunan Allah yana mata kyakkyawan riqo,ita kuma taci gaba da yunqurin qwacewa hawaye na gudu bisa fuskarta, kokawa ta barke a tsakaninsu duk da cewa ba wata nasara a hakan sai azabar riqon da yayi mata da takesha,dai dai sanda aka turo qofar da sauri aka shigo,ya saki wani lafiyayyen murmushi daga can qasan zuciyarsa,burinsa ya cika,plan dinsa ya tafi a dai dai,dama abinda yakeso kenan. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [7/25, 5:41 AM] +234 803 931 9517: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_* 💔 _Arewabooks:Huguma_ https://arewabooks.com/u/huguma Page 02 *_1988_* Cikin madaidaicin falon matsakaicin gidan,wanda bai cika da wani kayan ado da qawa na rayuwa ba,saidai tsananin tsaftar data bayyana kanta jikin kowanne loko da saqo na gidan zai matuqar burgeka tare da daukar hankalinka,har kayi sha'awar matsakaicin gidan. Kyakkyawar macace fara sol,irin farin da zai iya daukan hankalinka,tare da alamta maka cewa lallai mutum yana da nasaba da wani yare cikin yarukan nigeria zuwa afrikaans da kowa yasan fatar duk wani dan yarensu farace,koda akwai baqaqe suna wahala qwarai. Duka duka shekarun haihuwarta a ido ba zasu haura ashirin ba. A gurguje take sakawa yaron dake tsaye a gabanta uniform dinsa,tana gyara masa kwalar rigar uniform din,lokaci guda kuma tana jijjiga yarinyar dake goye a bayanta daketa faman tsala kuka kamar wadda ake yankar naman jikinta. Kana kallonta zakasan a rude take,uwa uba kuma alamu sun nuna sauri takeyi sosai,fadi takeyi cikin yanayin damuwar dake shinfide akan fuskarta "Yi shuru......yi haquri yanzu zamu wuce kyasha iska a hanya" ta fada fana durqusawa tana qoqarin sanyawa kyakkyawan yaron da sumarsa mai yawa da santsi ke sake kwantowa gaban goshinsa saboda duqawar da yayi zai karba safar da take qoqarin saka masa "Zansa da kaina ummee" "Bari na dauko maka lunch box dinka da hijabina saimu wuce,kaima ka kusa makara yau" tayi maganar tana miqewa,dai dai lokacin da aka bankada labulen falon aka shigo. A nutse ta daga kai ta kalli matar,wadda zasuyi kusan sa'anni da ita,idanma ta girme mata duka duka baifi ta bata shekara daya ba. Ita dinma ita ta kalla suka hada ido,saita dauke kai tana yatsine fuska,ta kuma tattara dukka bacin ran duniya ta azawa fuskarta,ba tare data ko kalli sassan da matar gidan take ba,ta wuce kanta tsaye zuwa kitchen din gidan. Wani abune yazo ya tsaye mata a wuya,duk da cewa idan da sabo yaci ace ta saba da mummunar hali da dabi'ar ta,amma akance,duk mutumin da yasan daraja da martabar kansa baya iya jurewa cin xarafi daga wajen ko waye,tana da dukka hanyoyin da zata cusguna mata ta hanata jin dadin zaman tarensu,to amma wannan ba shine muradinta ba a halin yanzu,don haka tayi qoqarin share wannan daga ranta,ta wuce kitchen din tana dan bubbuga goyon nata data samu ta lafa da kuka zuwa yanzu. Tsaiwa tayi turus tana dubanta cikin kitchen din,lunch box din yaron da tazo dauka tuni ta budeshi,ta kuma zazzage duka soyayyen chips da indomie din data dafawa yaron,wanda su kenan sukayi saura cikin gidan nasu,sai yau da take sanya ran samun albashi take tunanin ta biya kasuwa ta taho masa dasu. Ba yau ne karon farko data fara yi mata irin hakan ba,saidai na yau din yafi na ko yaushe bata mata rai da quntata matuqa,idan a baya tanayin hakan ta qyaleta ta debo wani ta dafa masa,yanzun basu da sauran abinda zata dafa masan,don haka cikin muryarta data cika da bacin rai tace "Wanne irin abune haka?,bakisan abincin waye bane da kika juye kina ci?" Cikin gadara ta waiwayo,ta watsa mata wani banzan kallo da ya sake tunzurata matuqa "Ko abincin me gidan ne ina da right din naci qarewa ma kenan,tunda dai yaya na ne ya kawo,guminsa ne,saboda haka banga wanda ya isa ya dinga yimin shamaki ba" wani mummunan bacin rai ya yunquro mata,taji ya tsaye mata a wuya,kamar ma da qyar take zuqar numfashi,har batasan sanda ta isa gareta ba ta tankwabe plate din abincin ya warwatse a qasa ba. Itama abun yazo mata a bazata,don bata taba tanka mata ba,duk da ire iren wadan nan abubuwan da take mata masu yawan gaske. Da yatsa ta nunata tana kafeta da idanunta da suka canza launi "Wannan abincin dama saurana binciccikan da kike zuba rashin mutunci da rashin tarbiyya a kansu to ba yayan naki bane ya kawosu ba,gumi na ne ke dashi duka kuke ci,kuma daga rana irin ta yau kinci iya rabonki kenan,duk ranar da kika qara saka hannu kika taba min wani abu dana ajiiye cikin kitchen dina,bama kitchen dina ba gidana ma gaba daya sai nayi maganinki naga uban daya tsaya miki" tuni ta miqe tsaye,gabanta yana faduwa saboda ta tsorata da yadda ta ganta,ta jima tana burin wannan ranar dama "Ni kika zaga?" A fusace ta daga kai daga kwashe lunch box din yaron ta dubeta "Muddin wannan shine zagi to na zagekin,kiyi duk abinda kika iya" "Wallahi wallahi sai na sakaki kinyi nadamar wannan abun da kikayimin,zakiga iya matsiyina a wajen dan uwana" "Na nawa kuma?,annamimiya?,wadda ta sanadinta na rasa duk wani walwala jin dadi da fahimtar junan dake tsakanina da mijina kuma me yayi saura?,ai ba abinda ya rage sai abu daya......" "Wannan abu dayan shi zan ida" ta fada idanunta carr a tsaye cikin nata. Haka kawai ta samu kanta da faduwar gaban fitar lafazin daga bakin FAUZIYYA,amma saita gyada kai "Karki fasa shashasha wofi" kai ta jijjiga da qarfi,sanna tabi takan indomie din da tayi kaca kaca a qasan kitchen din ta fice. Kasa tsayawa ta tsaftace gurin tayi,sai ta juya kawai ta fice ta saka yaron a gaba zasu fita,har taje tsakar gida ta dawo,ta laluba maqulli ta datse qofar falonta ta wuce da key din,abinda bata taba yiba tsahon zamansu da fauziyyan. Tun daga cikin gidan harta isa titi,bus ta iso suka hau kwanyarta empty take,babu abinda yake mata kai kawo sai zallar illar da zaman fauziyya cikin gidanta tayi mata,ta jima da sanin cewa FAUZIYYA annoba ce cikin gidanta,tun daga randa ta tsoma qafarta cikin gidanta bayan rasuwar mahaifiyarsu......komai ya fara jagule mata,makira hatsabibiya kuma annoba,wadda ta kwashe dukkan wani walwala da jin dadi gami da fahimtar juna dake tsakaninta da mijinta da sukayi auren soyayya.....tayi amfani da matsananciyar qaunar dake tsakaninsu ta jini daya,uwa daya uba daya,take juya akalar gidan,take kuma juya komai yadda taga dama. Bata taba damuwa da furucinta ba,amma a yau abinda ta fada din ya tsaye mata a rai,har ta sauke yaran bayan ta siya masa biscuit da drink ta hadashi dashi,ta kuma wuce zuwa nata gurin aikin. Sukuku ta wuni,har zuwa lokacin tashi aiki yayi. Tana tsaka da tattare kayanta kira ya shigo wayarta,a mamakance ta dakata tana duba number,number makarantar yaronta ne,gabanta ya yanke ya fadi,to me ya faru?,saita koma ta zauna tana rungume yarinyarta a qirji ta amsa wayar. Tayi mamaki sosai jin cewa har yanzu yaron yana makaranta fa ba'a zo an daukeshi ba,mamaki ya cika kwanyarta,ta sani abbansa baya wasa ko jinkirin zuwa daukarsa,to amma a yau din meye ya faru haka?,sai ta katse tunanin ta soma laluben layinsa. Sau uku tana kira ana rejecting,zuwa sannan mamakin dake qasan zuciyarta ya gaza boyuwa ya bayyana har saman fuskarta "Anya kuwa lafiya?" Ta yiwa kanta da kanta wannan tambayar,irin hakan bai taba faruwa ba,don haka ta sake gwada kiran nasa a karo na hudu,amma sai take yankewa kafin ma takai ga shigar,alamun dake nuna anyi blocking dinta,ko akwai qaqqarfar matsalar network,don haka ta katse dukka wasu wasi wasi nata,ta hada komai nata a gurguje a jaka,ta dauki yarinyar ta baro office dinsu. Tana gab da bakin gate taji ana matsa mata hon,a dan hanzarce ta waiwaya,matashiya ce data kusa shekarunta zaune cikin motarta,suka hada idanu saita sakar mata murmushi yadda fuskar waccar din take shinfide da murmushi,duk da bata shiryawa hakan ba. Abokiyar aikinta ce kuma qawa a gareta,duk da ita din tana dan jan jiki da qawancensu,ganin cewa akwai tazara me yawa a tsakaninsu cikin gidan auren kowaccensu,amma tsananin kirkinta da kulawar da take bata ba zata iya sanya hannu ta tankwabe ba "Yauma guduwa zakiyi,to Allah ya kamaki,shigo na saukeki" murmushi ta sake sakar mata,duk da cewa ba'a nutse take ba "Ayyah,ba haka bane wallahi,yau din ba gida na nufa kai tsaye ba,saina tsaya na dauko yaro a makaranta" harara tadan jefa mata "Shi din ba yarona bane nima?,ki shigo kawai muje" "Na gode" ta fada tana zagayawa daya side din,batason zancan ya tsawaita,don hankalinta ba'a jikinta yake ba,gaba daya yana kan yaron. Suna hanya tana janta da hira,saidai gaba daya bata da wanna sukunin,lokaci lokaci tana sake gwada number wayar data kira dazu,amma sam taqi shiga ko sau daya ne. Da gudu ya taho ya rungumeta yana sauke ajiyar zuciya,farar fuskarnan tasa tayi ja,kwantaccen gashinsa duka ya hargitse,bai taba dogon zaman jira irin haka ba,yana cikin sahun daliban da mahaifansu ke fara daukarsu saboda yadda ya damu da al'amuransa. Har qofar gida ta ajjiyeta,ta fito rungume da babyn,yaron yana dauke da jakarta,ta zagaya ta bakin window tayi mata godiya sosai "Wai meye a ciki?,ai mun zama daya" qaramin murmushi ta saki tana juyawa zuwa cikin gidan,cikin Zuciyarta cike da mamakin karamcin matar,da yadda take sonta,yaron yana biye da ita yana mata qorarin yunwa yakeji "Abinci zan fara dafa muku in sha Allah"ta fada tana jin tausayinsa na tsahon zaman da yasha,gashi bai samu tafiya da abinci ba,tasan dole kuwa yasha yunwa. Zaune yake a tsakar gidan saman kujerar plastic daga dai dai bakin qofar falon,shi din ta fara gani,sai a sannan ta tuna cewa ta kulle falon,bata bar masa key din baa,kuma koda wanne lokaci yana iya dawowa tunda bashi da tartibin lokacin fita ko dawowa,tun bayan da ibtila'i ya fada masa. "Subhanallah" ta fada a ranta,sai tayi sallama a nutse tana sake qoqarin karantar yanayinsa,kai ya cira a hankali ya sauke kallonsa a kanta. Mummunar faduwa gabanta yayi,wani irin hargitsatsen kallo daya watsa mata shi ya sanyata cikin rudani,batasan me tayi masa banda kulle qofa da tafiya da key din,kallon daya watsa mata yafi qarfin wannan laifin,kallo ne na zallar qasqanci da kuma tsana,tasan dai ranar yau lafiya qalau suka rabu,ya fita cike da murna zai karbo upper dinsa aiki ya samu,suna ta murna dukkansu tare da saka ran fita daga tsanani zuwa sauqi,sai dukka gwiwarta tayi sanyi da irin nau'in kallon da yake jefa mata. Kafin ta qaraso ainihin tsakar gidan sai wulgawar fauziyya ta gani,wadda kanta ke daure da bandeji da yayi tsatstsafar jini gaba daya daga samansa,ta nufeshi a gigice ta cukuikuyeshi tana neman mafaka a bayansa,bakinta na wani irin rawa na zallar tsoro da firgici take cewa "Na shiga uku akh,gata nan ta dawo,don Allah ka boyeni,kada ka bari ta qaraso,wallahi zata qarasa illatani kamar yadda taci alwashi" tayi maganar tana wani irin haki da tawar jiki,kamar wadda tayi gudun kwana da wuni. Baki kawai ta saki galala tana kallon fauziyya,qwaqwalwarta gaba daya ta rikice,me take nufi ne?,saita maida dubanta ga bandejin kanta tana mamakin me ya sameta daga fitarta "Bata isa tayi miki komai ba,a yau qarshen al'amarinta yazo,muguntarta a kanki kuma ta qare!" Muryarsa mai zurfi dake fita da amon fushi ta fusgi hankalinta,saita maida dubanta kansu gaba daya,kwanyarta na sake rikicewa da salon maganganunsu da ba ganewa takeyi ba. _uhmmm,me karatu bari mu tsaya a nan,bazance komai ba_ FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [7/25, 5:41 AM] +234 803 931 9517: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 _Arewabooks:Huguma_ https://arewabooks.com/u/huguma PAGE 03 Ɗaya daga cikin yammaci ne wadda ke jerin yammacin da albarkar ubangiji ke sauka daga sama zuwa ga bayinsa dake rayuwa a doron qasa sanadiyyan haduwar hadari da samuwar saukan ruwan sama,kama daga mutane dabbobi aljannu da sauran halittun dake qarqashin ruwa saman bishiyu da sauran bingiren da idanuwa basa iya ganinsu,raunin hankali,nakasa da kasawa irin ta abun halitta ya yiwa hankali shamaki da fahimtar wanzuwar wadan nan halittu dake kewaye damu masu tarin yawa,wanda kowanne yana qarqashin kulawa da tasarrufin ubangiji,bai gaza ba dai dai da qiftawar idanu wajen rabon arziqi ga bayinsa,da kuma isarwa da kowanne bawa gwargwadon rabon da ya kasance mallakinsa ne. A dai dai wannan lokacin,cikin qawataccen gidan abincin,muhalli me daukan hankali,sanyaya zuciya da bawa ruhi nutsuwa, sakamakon yadda aka qawata wajen da wani irin tsari mai ban sha'awa da burgewa,kwatankwacin yadda zai ja hankalin abokan kasuwanci suji basu qagara ko gajiyawa da zuwa kashe yunwa da qishirwarsu a wajen ba. Saman kujerun dake zagaye da teburan dake jere a wajen bisa tsari na rukuni rukuni,daga hannun damanka bayan ka shigo wajen zaka iya hangenta. Kyakkyawar matashiya,fara sol data mallaki wani irin hasken fata,irin farin da ko makaho ya shafa yasan natural ne,wanda ya cakuda da tsantsar kulawa tsafta da kuma hutu,yake kuma nuni da zurfin gogewa da wayewa da mamallakiyar fatar ke da shi. Idan har kayi hanzari ko azarbabi zaka iya kiranta da doguwa,saidai kaso me yawa na tsahon nata babu shi sakamakon murjewar da jikinta yake dashi da ya shanye tsahon ya maidashi moderate. Wasu irin manyan idanu gareta amma kuma a russune suke,wannan ya boye girman idanun nata,kai tsaye ba zaka ce suna da girma ba har sai idan taso fidda girman nasu ne. Siraran labbanta masu kalar pink sun dace hancinta mai tsaho da tudu wanda ya hade da kwantacciyar eyebrows dinta dake bisa tsari kamar an zanata. Sanye take da wata tattausar exclusive atamfa da bata tara tarkacen kaloli ba,hatta da zanen jikinta bai wuce dayan biyun ba,kalolin da suka dace da yanayin jikin da aka raɓawa atamfar,dinkin doguwar riga ne daya bude sosai daga qasa,daga sama kuma ya zauna mata cas kamar a don ita aka halicci atamfar dama dinkin gaba daya. Ta lullube kanta da wani madaidaicin mayafi wanda yayi mata aikin mayafin dama dankwalin da bata damu da daurashi ba,sai kwantaccen gashin daya kwanta daga gaban kanta,wanda duk bayan minti daya zuwa biyu take sanya zara zara yatsun hannunta tana jan mayafin tana sake rufe gaban kanta da kyau. Wasu lafiyayyun plate shoes ne a qafarta,mahadin qaramar handbag dinta ta kamfanin saint laurent dake ajjiye tsakiyar table din dake gabanta wanda ta gagara zama a kai. Duk da daya hannun nata wayarta ce a ciki,amma hakan bai hanata harde hannayen nata a qirji ba, kyakkyawar fuskar nan babu digon fara'a ko daya akai,sai dan qaramin bakinta da take dan motsawa kadan kadan,alamun dake nuni da cewa a matuqar qagauce take da tsaiwarta a wajen. Ba ita kadai ba,koda kaine a wajen wala'alla ka shiga sahun masu tayata ginsa da tsaiwar,sakamakon yadda idanu sukayi yawa a kanta a wajen. Duk da cewar wannan din ba shine karo na farko ba a rayuwarta ba,ba koma. Sabo ko baqon abu bane cikin rayuwarta ba,amma a yanzun da komai ya canza cikin rayuwarta,al'amura masu yawa suka kutsa cikin rayuwarta suka kuma shude da abubuwa masu yawa da matuqar muhimmanci a wajenta ya sanya komai ya sauya......ya dasa mata tsanar kowanne kalar kallo da zai fito daga qwayar idanuwan da suka kasance mallakin ƊA NAMIJI,idan ka dauke mutane hudu rakkin dake da matsanancin muhimmanci cikin rayuwarta. Har yanzu guri daya idanuwanta suke kalla ba tare data barsu sun gusa da kallon gurin ba ko sau daya,nisan taku masu dan tazara ne a tsakaninsu da budurwar data zubawa idanu,wadda ke tahowa gurin da mabanbancin yanayi tsakaninta da wadda ke a tsayen ta kasa zama, idanuwanta cikin nata tana sake karantar zallar tsanar data yiwa wanzuwarsu a gurin harta iso "Am very sorry bestie......" Ta fadi a taqaice cikin son kaucewa ganin yanayin fuskarta,ta miqa hannu ta gyara mata zaman kujerar dake bayanta,sannan ta mayar da dubanta gareta "Have a seat" ta fadi mata suna hada idanu. Tsareta da ido tayi na wasu sakanni,ba tare data shirya ba dariya ta qwace mata,tasa hannu tana qoqarin rufe bakin "Afifa....." Ta buda baki ta kirayi sunanta da wata irin murya me zaqi da laushi,fararen manyan idanunta na ragaita saman fuskar wadda ta kira da afifan "Kiyi haquri ki daina kallona da manyan idanun nan naki haka,sai ki saka na daburce,kiyi haquri ki zauna,mintuna kadan zasu kawomin na gaya musu sauri mukeyi" jimmm tayi na wasu sakanni sai kuma tasa hannu ta matso da kujerar dab da ita ta koma da baya ta zauna. Hirarrakin mutanen dake zaune daura dasu ta fara shiga mata kunne tana haura mata ka,duk da cewa ba suna magana bane da sauti sosai,zamanta tsakiyar halittun da a wajenta suke masu ban tsoro yasa takejin kamar a kunnenta ake maganar,sai tasa hannu taja jakarta ta fara kici kicin fiddo earpiece ta maqalawa kunnenta ko zata samu sassaucin jin muryoyin da bata qaunar jin irinsu. Tsaf afifa ke karantar ta,ta zuba mata idanu tana kallon yadda gaba daya walwala tayi qaura daga kan fuskarta,kamar wadda ke zaman waqafi cikin kurkuku. A nutse ta sanya earpiece a dukka kunnuwanta bayan ta sadar dashi da wayarta,tana jin feeling na insecurity a tattare da ita. Duk da taqi yarda idanuwanta su kalla kowanne sashe na wajen,gudun yin tozali da mugayen halittun MAZA dake wajen,amma all her body tana jin akwai wani ido dake karakaina saman jiki da fuskarta,bayan idanuwan da suka jima suna kallonta na mafi yawan mazan dake zaune a wajen. Cikin wani irin coolness take latsa wayarta,ranta yazo mata iya wuya,tayi watsi da hirar da afifa keta qoqarin sanyata yi akan dole dole. Rashin samun hadin kan SÃAHAR din ya sanya afifa kama kanta bisa dole,tana zuge zip din jakarta order dinsu ta iso,waitress ta ajjiye tray din a tsakiyarsu cikin nutsuwa da girmamawa,tana kuma basu haquri na delay din da aka samu "Ki maidashi takeaway" saahar ta fada a taqaice da sassanyar muryarta tana miqewa a nutse,karo kuma na biyu kenan da tayi magana tunda sukazo wajen,ta miqa santala santalan fararen yatsun hannunta tana daukar kyakkyawar handbag dinta tare da zare earpiece din kunnenta ta riqesu a hannu daya,ta tura kujerar baya ta fice a tsakiyarsu tana laluben hanyar fita da kyawawan fararen idanunta da suke da wani irin sheqi da daukar hankali "Ki making payment kafin ki fita" afifa ta fada a gaggauce tana miqewa hadi da tattara sauran kayansu dake kan table din,tasan tsaf saahar din zata fita ta barta da karbo kayan da kuma biyan kudin. Kallo daya ta yiwa gun biyan kudin ta sauya akalarta zuwa parking lot na gurin cikin takunta me jan hankali,koda karen hauka ne ya cijeta ba zata yarda ta qarasa da qafafunta wajen ba,ba don komai ba sai don gun cike yake da maza,mai amsan pyment din,wanda zai bata receipt.....kai kowa da kowa ma,wannan ya qarawa zuciyarta qunci da damuwar data tashi da ita yau,damuwar da bata shura wasu satittika bata tsinci kanta a ciki ba,wani abune daya zame mata tamkar JARRABI,duk kuwa da irin qarfin tuwo dana qwanji da take sanyawa kowacce fitowar rana da faduwarta gurin yaqar komai da komai,tare da sake samun nutsuwa da tabbatuwar binnuwar komai,binnewa ta har abada,saidai tasan cewa......ba komai KADDARA ke shafewa ba.....ba komai tsahon zamunna ke samun nasarar lullubewa ba...ba kuma komai zuciya da ruhi ke sarayarwa shekaru ba. Amsa kuwwar sallamar dake ratsowa daga bayanta zuwa cikin kunnuwanta tayi dai dai da sanda take zura key zata bude kyakkyawar qaramar farar motar,cak ta dakata da abinda take shirin yin yanayin fuskarta yana sauyawa kadan kadan kamar wahainiya,kwanyarta ta sarqe da tunani da kokwanton ba ita ake aikewa da saqon sallamar ba,wannan ya bata karsashin sake zura key din tana murzashi. Kamar yasan abinda kai kawo a zuciyar tata ya rage mata wahala ta hanyar sake kusanto inda take tsayen yana maimaita sallamar da muryarsa mai sanyi,ta dan runtse idanunta kadan cikin salon da yafi kama da lumshesu sannan ta budesu kai tsaye tana zubesu saman fuskar matashin dake tsaye a gabanta,cikin jikinta tana jin kamar ya yarfa mata garwashin wuta. Wani irin kwarjini ya dakeshi,karon farko da ya fara jin irin haka kaf tsayin rayuwarshi akan wata diya mace,cikin salo da gogewa ya dunqule hannunsa yakai bakinsa yana jan gyaran murya tamkar mutumin daya qware,idanunsa cikin nata yana son ya koyawa kansa juriya a kallonta. Ba tun yanzu ba,tun sanda suka wanzu a cikin wajen cin abinci ya fahimci akwai wani kwarjini na musamman a tattare da ita,wanda yayi imanin shine ya zame mata qaqqarfar garkuwa daga zamantowa abar tayawa ko tunkarar kowanne irin namiji,yayi imanin a irin kyan da Allah yayi mata,ba kowanne namiji bane zai iya mata kallo daya ya kauda kansa,koda ya kauda kansa yana da yaqinin ba kowa keda qarfin mallakar zuciyarsa ya hanata qyasata ba "Am sorry,kiyi haquri na tsaidaki ba tare da nasan naki uzurin ba.....but......da farko dai sunana mahmud,ko zan iya sanin naki sunan tare da yimin alfarmar aron lokaci koda mintuna biyu ne rak cikin tsadaddun lokutanki?" Kyansa,ajinsa da qwalisarsa masu dukan zuciya da idanun kowacce diya mace da suka bayyana muraran basu nata narkakkun idanun da matacciyar zuciyar ke kallo ba,abinda take gani yasha banban da abinda kowacce mace zata hanga daga gurin mahmud din......tafi hangen wata muguwar dabba dake neman abun farauta......muguwar halittar ɗa namiji dake laluben halitta mafi rauni irin ta diya mace ya cutar da ita.......dukansu haka suke!,dukansu halinsu daya!,gaba dayansu basu da tabbas!,babu imani ko tausayi a qirjinsu!. Kalmomin da suka tasowa daga qasan zuciyarta suna mata amsa kuwwa a kowanne kunne nata,suka kuma taso da wani lullubabben yanayi me tarin daci dake danqare qasan narkakkiyar zuciyar dake dauke da tarin ciwo,suka soma sauya kalar launin fatarta zuwa bacin rai qarara,saita juya tana jan siririn tsaki,ta dora hannu zata buda murfin motar ta shige don yiwa kanta katanga da kuma kariya daga shaqar inuwa guda ita dashi. Hannu yasa ya dafe murfin motar yana karyar dakai "Kar muyi haka dake beauty.......kaina bisa wuyana indai cikin kalamaina akwai wadanda suka bata miki rai" sakar masa murfin tayi,taja da baya a nutse ta zagaya daya side din motar,zuciyarta tafasa takeyi kamar ta ballo ta fito daga qirjinta,ta bude kujerar zaman banza ta fada,ta maida murfin ta rufe ta kuma saka lock ta kulle kowanne murfi. Relaxing bayanta tayi da makarin kujerar hadi da lumshe idanunta,don ko inuwar mahmud batason gani a wajen bare mahmud din kanshi,ta fitar da siririyar iska me zafi daga bakinta hannunta na dafe da kanta. Ba zata ce ga yadda mahmud yayi yabar gurin ko kuma adadin mintunan daya dauka a wajen ba,itadai taji afifa na knocking glass din,tunda ta buda ido sau daya taga itace,saita maida idanun ta rufe,tasa hannu ta laluba key din ta cire mata lock din hadi da dora key din daga gaban motar. Sau daya afifa ta kalleta ta dauki key din ta saka ta tayar da motar ba tare da tace mata komai ba,bata da buqatar ji ko tambayar komai daga bakin saahar,tunda ta tarad da mahmud a gurin,to amma shin rayuwar saahar zataci gaba da tafiya a haka?,da kanta ta bawa kanta amsa ta hanyar girgiza kanta,dole dole......koda zasu dinga fada sau dari a rana suna shiryawa......ya zama dole ta dinga gayawa saahar din gaskiya,koda yau bata gani ba.....koda a gobe bata gane ba zuwa jibi lallai hankalinta zaikai kai,lokaci kuma zaiyi mata aikinsa,da wannan tunanin bayan sun danyi nisa saman hanya,motar shuru kamar kurame ne matafiyan,afifa tayi gyaran murya qasa qasa,cikin nutsar da muryarta tadan kalleta ta gefan ido kafin tace...... FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [7/25, 5:41 AM] +234 803 931 9517: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 _Arewabooks:Huguma_ https://arewabooks.com/u/huguma PAGE 04 "mahmud abba gana.....kinsan wayeshi kuwa saahar?" Afifa ta jefa mata tambayar cikin kwantar da murya da salon rarrashi,kamar saahar din ba zata tanka ba,sai kuma ta motsa labbanta a hankali "Ban damu insan waye shi ba,bana kuma buqatar na sani" "Amma me yasa zaki wulaqantashi saahar?" "Me yasa ba zasu gane ba.....me yasa ba zasu rabu dani nayi rayuwata ni kadai ba?" Ta jefawa afifa tambayar tana ware dukka idanuwanta akanta "Ba zasu gane ba ba kuma zasu rabu dake ba,saboda qaddararki daban tasu daban,abinda kike hangowa daban abinda suke hangowa daban,kina yaudarar kanki ne kawai.....amma a irin surarki kinyi qarya ki hana maza su biki ko su soki" maida idanunta tayi ya lumshe zuciyarta na bugawa,bata taba jin kyanta na neman zame mata barazana ba irin a wannan dan tsukin da take gujewa mazan irin gudun da rai zai yiwa mutuwa,ta tsanesu fiye da yadda dukka wani abun halitta yake gudun kishiya,tanaji inama ace bata da wannan kyan da ya zame mata jarabta,inama ace ita mummuna ce,qila wannan munin zai siya mutu da nutsuwa,zai kuma barrantata daga dukkan wata barazana,ya hutar da zuciyarta da kwanyarta "Duk yadda mace takai ga muni.....duk yadda takai ga zamantowa cikin matakin qasa qasa na rayuwa...... ba'a rabata da samun soyayyar maza wadda take dai dai da matsayin tata rayuwar......" Afifa ta fadi idanunta nakan hanya,kamar tasan abinda ke kai komo a zuciyar saahar din,saidai batakai ga qarasawa ba saahar ta dakatar da ita "Na roqeki kibar kiramin sunansu a wajen nan" duk da yadda tausayin saahar ya tabata amma sai data murmusa don dole "Bayan tsanarsu da kikayi,i think harda tsoronsu ma yanzun kikeji ko?,keda mukayi dake zaki qarasa kiyi biya kudi saiki gudu ki barni dasu suna jifana da tambayoyin ina kudinsu?, anyway alhmdlh, mahmud ya fansheki ya biya" ta qarasa fada tana waiwayowa cikin son ganin reaction na fuskar saahar din,akayi sa'a itama ta waiwaya din,saita watsawa afifa wani irin kallo kafin ta janye idanunta tana gyara kwanciyarta sosai cikin motar hadi da fadin "Allah ya baki sa'a" kalma data sanya afifa dariya sosai,tasan sarai me saahar ke nufin aikatawa muddin tace mata haka. A haka suka qarasa gida,saidai duk yadda tayi da saahar ta tsaya ta dauka musu takeaway din cewa tayi "Ban fara yunwa ba da zanci abinda wani ne ya siya da kudinsa,i have enough da zan iya siya cikin account dina nima,dama asali ni rakiya nayi,so na yafe" ta wuce cikin gidan cikin nutsatstsen takunta,afifa ta bita da kallo tanason sakin dariya. Yalwataccen falo ne da ya sha shimfidu da ado cikin kalolin silver and royal blue,rukunin kujeru guda biyu kenan,daya nau'in kalar silver,daya kuma kalar royal din,stairs guda biyu ne qawatattu kewaye da falon da ya cika dukkan sharuddan zama qawataccen falo na alfarma dake nuni da zallar dukiya da kuma wadatar da ahalin suke ciki. Kana sanya qafarka abu biyu zaiyi maka maraba,sassanyan qamshin turaren da humidifier ke bayarwa da kuma qamshin girkin dake fita a kitchen din gidan dake manne da falon qarqashin daya daga cikin stairs din. Mutum biyu ne cikin falon,kyakkyawar baqa ko muce black beauty din macace da a qiyasin da idanuwanka zasu iyayi ba zata haura shekaru talatin da biyar ba. Kallon farko kawai da zaka yi mata zaka san cewa GIDAN GAYU ce,gayu da iya ado da kashewa jiki kudade masu nauyi saboda gyaransa ya samu mazauni a tattare da ita,cikin furucinta idan ka nutsu da kyau kana iya tsintar yadda harshen KANURI ya ratsata da kyau yadan gurbata hausar tata kadan,cikin matuqar girmamawa take magana da kamilar matar data kusa ninka shekarunta kadanne babu,MAAMA me shekara hamsin da biyar,farace sol da take da kamannin da SÃAHAR ainun,zallar jin dadi da samun sukunin rayuwa ya boye shekarunta sosai,saidai shi girma duk yadda kakai ga son tureshi da bawa jiki kulawa baya hanashi bayyana,illa dai ana samun sauqi yazo cikin cikakkiyar qoshin lafiya da kuma siffa nagartacciya. Sallamar sãhaar din taja hankulansu,fuskar matar ta fadada da fara'a idanunta bisa fuskar sãahar din "Yanzun nake shirin kiranki,ya akayi kuka dade haka?" Ta tambayeta sanda take gaggawar isowa ga matar,dukka idanunta suna kan kyakkyawar yarinyar dake kwance a gefanta saman kujerun falon tana wutsil wutsil da qafafuwanta cikin wata overall me taushi,yalwataccen gashin yarinyar yayi luf saboda gyara da yasha cikin zallar tsafta da kulawa,wannan ya sake fidda kyan yarinyar sosai. "Sannu da gida maama" sãahar din ta fada dai dai sanda take duqawa ta dauki baby girl din,fuskarta na sake wadata da fara'a,ta daga yarinyar tana kallonta,tana jin wani tsohon emotion yana taso mata,saita sanya yarinyar cikin qirjinta ta rungumeta tana sumbatar ta. Dukkansu a fakaice suke kallonta,kowannensu tausayinta yana ratsa zuciyarsa,duk da cewa suna qoqarin dannewa sa hana bayyanuwarsa saman fuskarsu "Afifa ce,haka kawai ta lallabani ta jani rakiya zata kaini inda......" Sai kuma ta kalmashe ragowar maganarta cikin cikinta,tana dan shafa kan yarinyar a hankali,yarinyar tayi luf a qirjinta kamar wadda barci ke shirin dauka. "Ina afifan takaimin ke?" Matar da suke kira da suna anty farheen matar aure ga dan uwanta shaqiqi ta furta cikin nuna kulawa,dukka idanunta suna kan sãahar din tana son jin amsar tambayarta "Anty,ki tayani tambayar qanwarki dai,bayan tsanar data yiwa maza,hala ta fara tsoronsu kuma" afifa dake shigowa Parlor din hannunta riqe da ledar takeaway dinsu ta fada fuskarta yalwace da murmushin da baka rabata dashi,akasin hali da dabi'ar dake tsakaninta da sãahar kenan. Kafin anty farheen tace komai sãahar taja wani dogon tsaki tana sakarwa afifa harara "Don dai tuwon gobe ake wanke tukunya" ta fada mata tana takawa a hankali zuwa gaba,dariya ta subucewa afifa,yayin da maama da anty farheen suka murmusa "Inyeeee,to barkanki da kike sake jin hausa haka da kyau" afifa ta fada cikin salon tsokana tana neman gurin zama. Ta fuskanci idan ta biyewa afifa surutu zata yita sanyata,bayan ciwon kan data so saka mata yanzu,don haka ta waiwaya ga anty farheen "Brother fa?" "Yana gurin abba,inajin dama ke yake jira tun dazun" kai ta jinjina,ya kirata a dazun sanda take zaman jiran afifa,don haka ta fara takawa a hankali zuwa hanyar da zata sadar da ita da sashen mahaifinta,baby aleena na kwance saman kafadarta "Nazo nayi rakiya?" Afifa ta fada tana bude ledarta,ci kanki batace mata ba kamar yadda tayi zato,ta wuce abinta,sai afifan ta saki dariya tana fidda kayan cikin ledar "Me yasa kikeso ki dinga tunzuramin qanwa ne afifa?,za'a ji kanmu fa" anty farheen ta fada dukka idanunta akan afifa bayan maama ta miqe zuwa dakinta dauke da ledar kayan da farheen din ta kawo mata kyautarsu,fuskar farheen din a sake ta yiwa afifa tambayar. Ta buda takeaway dinta ta saka fork a ciki tana dariya "Abun sãahar ne anty kamar sake gaba yake,duk waje idan akwai maza suka wuce uku saita sakawa gurin karan tsana?,me yayi zafi haka?" Kai farheen ke gyadawa a hankali idanuwanta akan afifa,ta bude baki a nutse tace "Babu halittar dake saurin ruguza dukkan buri mafarkai yadda da aminci na diya mace irin halittar da namiji,idan ta dace da abokin rayuwa na gari......sai kiga tana yiwa maza dukka kallon abu daya,hakanan idan aka samu akasi shima haka abun yake,a dukkanin kafatanin rayuwa kuma babu abinda yakai ciwo irin cin amana ha'inci ko yaudara daga wajen wanda ka miqawa dukkan yarda aminci da kuma qauna,a maimakon ka samu ninkin abinda ka bayar.....ko ka samu koda ace kwatankwacinsa ne, a'ah......sai ka samu akasin dukkan abinda kai din ka miqa,ba kowanne yanayi muke fahimta ba.....har sai lokacin da muka samu kanmu a kwatankwacin irin wanna hali ko yanayin" kai afifa ke gyadawa,maganganun farheen sun shigeta,musamman daya kasance kamar wani tuni ne ta sakewa afifa bawai kuma don afifan ta manta ba,a'ah.....don dai kawai zuciyarta ta kwadaitu dason ganin wasu abubuwa masu kyau na wanzuwa cikin rayuwar sãahar din tata,gyara zamanta sosai afifa tayi tana fuskantar farheen tana kuma ajiiye meatpie din hannunta data gutsura saman dan qaramin farantin tangaran din data kirayi baaba sa'a ta kawo mata,ta kawo seriousness ta dora saman fuskarta,da gasken gaske abinda bakinta zai furta a yanzu yana daya daga cikin abubuwan da ya shiga list na burikanta a yanzu "Amma anty......shikenan sanadiyyar kuskure ko son zuciyar wani sai kabi ka kashe taka rayuwar?,saboda wani laifi na wani can mutum guda sai ayiwa kowa kudin goro a tsundumashi cikin matsalar da babu ruwansa?,matsalar da baisan da wanzuwarta ba?" Kai farheen ta girgiza,bata kai ga cewa komai ba afifa ta dora "Mahmud abba gana fa anty....... bakiga cin kashin da taso yi masa ba yau,don kawai yayi mata magana" tun kafin afifa ta qarasa farheen ta fidda dukka idanunta waje tana dubanta cikin yanayi mamaki matuqa da gaske "How comes afifa?" Dukka kafadunta ta dage tana yarfa hannu,alamun abun itama sam bai mata dadi ba FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 _Arewabooks:Huguma_ https://arewabooks.com/u/huguma LAST FREE PAGE PAGE 05 "Ban sani ba anty,nazo na sameshi ne a tsaye yana kallon motar,Tayi disappointing nashi sosai wallahi anty,ni kaina i was so shock da naganshi tsaye a wajen,nasan halinta,may be banza tayi dashi,ko kuma ta gaggaya masa maganganu marasa dadi" shuru farheen tayi tana juya kai cike da jimami,mahmud was so familiar,kusan sananne ne shi da mahaifinsa,matashin dake da arziqi da kuma nasaba cikakkiya,dan asalin garinta ne wato borno,wanda tayi imanin babu a inda bazai nema aure ko ya nemi mace a dauka a bashi ba da gudun gaske "He really broke her heart........yayi mata illa da yawa,that's why ta kasa bari ta warke har yau" farheen ta fada tana sake ci gaba da juya kanta,kallonta afifa keyi itama tana hadiye wani abu me daci,ko zancansa ta tsani ayi itakam,batason tuna komai daya wuce a baya,tana jin kamar ba zata iya yafewa ba tabar komai kamar yadda abba yayi umarni ba "Amma dolen dole......she need to move on,bazai yiwu ta rayu har abada a haka ba" "Haka nake gayawa kaina kullum,nidai na riga na bashi phone number dinta,saidai ta hadiyi zuciya bayan yayi kiranta idan taso" qaramin murmushi ya subucewa farheen "Babu wannan zancan,zamu ci gaba da lallabata ne tayi accepting koma meye zaizo mata,inajin yau da ita zamu wuce gida ma" "Hakan yayi anty,nima dama yau zoo road zan wuce". Tana rungume da aleena tayi sallama da muryarta me cike da wani irin sanyi da maganadisun dake fusgar hankali,dukkansu mutum biyun dake falon suka waiwayo suna amsa mata sallamar cikin bata attention dinsu,fuskokinsu suka wadata da murmushi,farin dattijon dake zaune cikin sofa qafafunsa miqe,daga gefansa takardu ne masu yawa da kuma wani kyakkyawan biro a hannunsa,da alama yana signing ne,sai matashi me jini a jika me surkin kala wanda ya kwashe kamannin dattijon tsaf!,nutsuwa da cikar kamala ta lullube fuskar nan dake cike da danyan jini da jin shekaru da yake ganiyar yi. "Abba......barka da warhaka" ta fada tana rusunawa a gabansa,ya saki murmushi yana ajjiye takardun hannunsa ya miqa mata hannun nasa yana cewa "Bani amaryar nan tawa da batayi dani" wani dan qaramin murmushi daya fidda ainihin kyanta ta saki,ta matsa tana miqa masa aleena din,ya karbeta yana tsokanarta,saita maida kanta ga dan uwanta ta zauna sosai tana tanqwashe qafafunta "Yaaya barka da yamma" hararar wasa yadan watsa mata bayan yadan dauke kansa daga takardun kadan "Yamma ko dare,tunda na shigo nake nemanki da kyakkyawan albishir amma baku tashi shigowa ba sai yanzu,nima komawa zanyi da albishir dina" yanayin yadda yake magana da ita kadai ya isa ya gaya maka zallar shaquwa da kulawa da suke bata,yadda ita dinma take ganin girmansu da basu dukkan wani respect daya dace. Kai ta langabar gefe guda "Haba yaaya,kada muyi haka don Allah,ban taba abu naji na matsu na samu feedback ba Allah sai wannan abun" "Naqi nima" ya fada yana buda shafukan gaba da na takardun hannunsa. Idanunta ta maida ga abbansu dake zaune yana jinsu ba tare da yace komai ba "Abba ka saka baki don Allah" murmushi ya saki,yana sauke qafafunsa dake harde a dazun waje daya yada gyara zamansa,yatsunsa na riqe da yatsun aleena daketa bangala masa dariya "Kayi haquri mana yaaya qarami a gaya mata ko?,nima na matsu na tayata ji" kansa ya daga daga takardun yana rufesu fuskarsa da murmushi,ya ajjiyesu gefansa sannan ya dubeta kai tsaye "Shikenan tunda abba yasa baki,zan gaya miki amma bisa sharadin kome na buqata zakiyimin?" Ya furta yana murmushi qasa qasa hadi da dan juya kansa,alamun deal ne idan har ta amince din. Ba tare data kawo komai a ranta ba,don ta dokanta taji feedback din ta gyada kai,lallausan murmushin nan nata yana fita a fuskarta "We made it!" Ya fada with full excitement idonsa a kanta,don sosai ta sakashi jin alfahari da ita,musamman lokacin da yake gaban alhj ahmad girema yake lissafa masa benefits da za'a iya samu a tattare da ita. Manyan idanunta a yaunta fiddo waje cikin jin mamaki da kuma farincikin da taji yana ratsata,yanayin data jima bata ji irinsa ba,sai tasa zara zaran yatsunta tana rufe fuskarta,qaramin kyakkyawan bakinta yana furta "Alhamdulillah" can qasa,cikin zuciyarta tana jin dadi data zama solution na problem din dan uwanta,a rayuwa tana qaunar taga ta zama silar warwarewar matsalar wani,yana daya daga cikin abubuwan dake faranta mata rai a duniyarta,bayan son yara da Allah ya jarabceta dashi "Thank you sãahar...... thank you ummin abba(sunan da suke kiranta kenan sometimes,saboda taci sunan mahaifiyar mahaifinsu wato kakarsu kenan KHADEEJA)" "Don't mention it yaaya" ta fada tana girgiza kai, murmushi har yanzu bai bar fuskarta ba,sai dukka hakan ya sanyaya musu rai,don sun jima basuga hakan ba tattare da ita,lallai abun ya sanya farinciki me yawa a zuciyarta "Yauwa......saura deal dinmu kuma" ya fada yana tanqwashe qafafunsa "Eheennn" ta fada tana gyada kai "Yadda kika tsara komai muka bi kuma aka kai ga cimma gaci,wannan ya burge alhaji sosai,ya sanya masa interest akanki,ya nema alfarma a wajena ta ki karba aiki a company dinsa dake shirin durqushewa a yanzu yake fafutukar tayar dashi,zaki tsaya tare da yaronsa kuyi aiki tare alfarma ce ya roqeni,nayi rushing wajen accepting,saboda girma da kimarsa,na kuma san cewa bani da matsala ta wajenki" ya qarashe maganar yana ritsata da idanu. Kaf! Ya gama daureta da dukka wata jijiya dake jikinta,ya salam ya alhadi,me yasa yaya muhyi zaiyi mata haka?,yafi kowa saninta ciki da bai,yasan a yanzun bata da wani sauran buri,bata buqatar aiki ko kadan,infact fita ma waje tun bayan kammala karatunta bata dameta ba,tana ma daya daga cikin abubuwan data sanyasu a jerin ababen takura a wajenta,wannan ya sanya ma hatta da key din motarta ta dade da bada ajiyarsa,ta yaya zata iya fita kullum da sunan aiki?,ta kuma tunkari wata matsala,matsalarma ta company?. Yadda ta gaza cewa komai haka falon yayi Shuru,hakanan kuma daga abba har yaa muhyi basu janye idanuwansu daga kanta ba,abinda ya sake mata nauyi kenan,ta kasa motsawa bare ta amsa. "Mama na" muryar abbanta ta yanke shirun dake wanzuwa a falon,ta daga kai a hankali "Na'am abba" "An baki dama kije kiyi tunani" "To abba,na gode" ta fada har ranta tana jin dadi, atleast ta kubuta daga titsiyen da yaa muhyi yakeson yi mata "Karki manta da istikhara" abba ya fada sanda take dab da fita a falon,kai ta jinjina "In sha Allah" tanajin a ranta ta yaya zata sakeyin sake?,ta yaya zata manta da istikhara?, bayan taga illar hakan?,har abada ba zata sake yankewa kanta hukunci kai tsaye ba,bata fatan ruwan daya shanyeta a baya a yanzun ya sake mamayarta. Sanda ta isko falon tuni afifa ta gama cin nata takeaway din,hira ma sukeyi da farheen,dukansu suka bita da kallo,yanayinta ya sauya ba kamar yadda tabar wajen ba a dazun,saidai ba wanda yace komai da ita,ta dora aleena saman cinyar farheen ta zauna itama,dai dai sanda baaba rabi ta fito "Tunda kuka shigo nake cigiyarki,akace kin shiga wajen alhaji" ta fada cikin fara'a da nuna kulawa,hannu tasa ta zame veil din kanta baya tana lumshe ido,cikin jikinta tana jin wata gajiya da weakness yana ratsata,wanda tasan bata komai bace ta zancan yaa muhyi ne,sumarta me santsi dake gaban goshinta ta fito sosai "Zan samu coffee?" Kai ta jinjina da sauri "Ai bana zama babu shi saboda ke" daga haka ta juya cikin kitchen din a gaggauce. Bata ce da kowa komai ba,sai suma basu tambayeta ba,tana da zurfin ciki sãahar din sosai,ba komai take iya bayaninsa kota fadi ba "Ki rakani gida mana kiyimin weekend din nan a can?" Farheen ta fada tana duban sãahar,saita bude idanunta tana kallon farheen,cikin zuciyarta tana jin ta gamsu ta bita din,to amma kuma kamar ta kusanta kanta ne da yaa muhyi da take fatan a kwanakin da abba yace taje tayi tunani daga nan har abada zancan da yazo mata dashi yabi ruwa,bata da wani interest akan aikin ko kadan,amma kuma qin amincewarta tamkar ta damtsi qasa ta watsawa idanun yaa muhyi din "Zaki din?,khalipha nata kewarki" ta fada cikin kwnatar da murya,khalipha shine makami daya da zatayi amfani dashi ta amintar da ita ta bita gidan,Allah ya jarabceta da son yara matuqa da gaske. Sai da baaba rabi ta kawo mata coffee din taji tana cewa ta hada mata kayanta kala biyu sannan ta fahimci ta aminta zata din "Miskili kafi mahaukaci ban haushi" anty farheen ta fada a ranta tana murmushi,a hakanma ita daya ke iyawa da sãahar,tana da dadin zama idan ka karanceta,idan ba haka ba kuma ba zaka taba jin dadin zama da ita ba,infact ma ba zaka taba fahimtar tata ba. Tana rungume da aleena a seat din baya,yaa muhyi da anty farheen na gaba suna hirarsu,komai suke tattaunawa tana jinsu amma bata sanya musu baki ba,ta dade tana kwatanta cewa inama ace dukkan maza nagartattu ne kamar yayun nata,lallai inda addini ya halasta aure tsakanin dan uwa da dan uwa,ta tabbatar cewa bata da sauran matsala a rayuwarta. Tafiyar da bata wuce minti talatin da biyar ba suka isa unguwar,ya muhyi dake tuqi a nutse ya saka signal,ya shiga layin da ya shiga hannun damansa a hankali. A qofar wani qawataccen gida dake dauke da manyan katangu ya tsaya,a ido kawai idan ka kalleshi zaka san cewa akwai sukunin rayuwa me yawa tattare da me gidan. Ya danna hon,cikin sakannin da basu wuce biyar ba aka wangale masa qofar,daya daga cikin masu tsaron qofar gidan mutum biyu ya rusuna cikin girmamawa har zuwa sanda motar ta sulala ta shige ciki kai tsaye zuwa yalwataccen parking lot na gidan. Ko kafin yakai ga tsaida motar su fita masu aikin farheen su biyu sun iso,daya nanny dinsu khalipha ce daya kuma tana kula da tsaftace sashen farheen,don sam bata yarda koda wasa me aiki ta karbi wani abu da ya shafi hidimar mai gidanta ba komai qanqantarta. Cikin girmamawa suke yiwa sãahar barka da zuwa,don dukkaninsu bawai baquwar su bace,kai tsaye ma za'a kirata da 'yar gida,saboda zaman shekaru kusan biyu da tayi dasu,har yanzu kuma bata rufa wata biyu bata zo tayi kwana daya ko biyu ba,daki ne da ita na musamman a gidan. Baraka ta miqa hannu zata karba aleena sãahar ta hanata,tadai barta da hand bag da kuma qaramar luggage dinta ta wuce ciki rungume da yarinyar dake lafe a qirjinta,don tuni tayi bacci. Bata sauketa ko ina ba sai data dangana da ita har gadonta dake dakin farheen,ta fito Parlor ta samu farheen din na gayawa baraka ta tsaftace dakin da sãahar din zata sauka,duk da fes yake,sannan kuma lubabatu ta tambayi abinda sãahar din zataci a dora mata. Kai sãahar ta girgiza,cikin lallausar muryar ta take fadin "don't mind,I can take care of myself" "Really?,kinsan dole a kula da amanar auta" farheen ta fada cikin sigar tsokana kamar yadda ta saba takan zolayeta haka time to time. Dole wani murmushin ya sake kubcewa sãahar,ta motsa bakinta kadan,farheen na daya daga cikin mutane masu matuqar muhimmanci a rayuwarta,ba zata iya fadin adadin yadda taji dadin zama da ita ba a shekarun baya,har yanzun kuma tana jin dadin kasancewa da ita,shi yasa duk duniya ba inda take iya tafiya ta kwana idan na nan gidan ba. Cikin qanqanin lokaci baraka ta gama kintsa dakin ta kuma shirya mata kayanta, bath set dinta ta fitar,ta zare kayan jikinya ta daura babban lallausan farin towel,ta zare farin ribbom din kanta,yalwataccen gashinta mai tsaho da sulbi ya baje saman lallausar farar fatar jikinta,hakan ya qarawa fuskarta wani kyau da haiba,tamkar ire iren jaruman indai mata,kai tsaye ta dauki kayan wankanta tana takawa a nutsenta zuwa toilet,ta hada ruwan wanka me dumi sosai ta shige,tayi wanka sosai da ruwan ya ratsata, idanunta a lumshe cikin shower din tana qoqarin tattara dukka wasu qananun damuwoyi da taci karo dasu a wunin yau tana watsar dasu daya bayan daya,so takeyi yau din tayi bacci me kyau ta kuma huta sosai,daga qarshe ta dauraye jikinta dake faman fidda qamshin shower gel dinta mai matuqar kyau da tsada,ta nade fatarta daketa sulbi cikin towel ta fito bayan ta sanya pad,kasancewar tana fashin sallah ne. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 06 *Arewabooks:huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Sai data fara busar da kanta da ya jiqe,sannan ta shirya cikin wasu cotton kayan bacci masu tsananin taushi,riga da wandon da bai sauka har qasa ba,kadan ya rage yakai idon sahu,ta mulke kanta da turaren gashi kamar yadda ta saba ya zame mata al'ada,hakanan ta shafe jikinta da nau'ikan turarukan da sai zatayi bacci take using nasu. Cikin sofa bed ta kalmashe qafafunta bayan ta rage haske dakin,ta ja wayarta ta kunna data,tanason shiga media ta karanta news ko zata rage tsahon daren sai taji ana knocking,ta daga manyan idanunta da suka rusuna zuwa lokacin ta kallo qofar sannan ta bada izinin shigowar. Baraka ce,cikin girmamawa ta isar mata da saqon farheen na ta fito taci abinci,kai ta girgiza "Am okay,kice mata saida safe ma hadu" kai ta jinjina sannan ta juya zata fice "Ammm,amma idan zan samu black tea ko coffee ina so" "Babu amma yanzu yanzu saina hada miki" "Na gode" ta fada a tausashe,baraka ta juya ta fita tana ja mata qofar. Tana shirin buda wayar saiga kira ya shigo mata,tsaiwa tayi cak tana kallon numbers din dake faman harbawa saman screen din wayar,baquwar number ce don babu ita cikin kaf 'yan tsirarun contact da ta adana cikin wayarta. Ba kowacce number take saving ba,sai number dake da matuqar muhimmanci da amfani a tattare da ita. Wannan yasa taqi daga kiran,har ta gama ruri ta katse,saita sake kunna data din ta shiga abinda tayi niyyar yi tun farko. Ba'a dauki dogon lokaci ba kiran ya sake shigo mata,taja qaramin tsaki tana jin kamar tayi rejecting,amma saita fasa,taci gaba da kallon yadda wayar ke neman a kawo mata agaji,harta gaji da ɓurari ta sake yankewa,katsewarta da minti daya kacal saqo ya shigo _"please......do me a favor,ki daga kirana koda na second biyar ne,zan gode da hakan,mahmud abba gana"_ Wani dogon tsaki ta saki kamar zata cire halshenta,wani abu mai tauri yazo ya tsaya mata a wuya,ta lumshe ido tare da danne makashin wayarta yana kasheta gaba daya qirjinta na wani irin dokawa,kenan afifa ta raba number wayarta?,me yasa afifa zatayi mata haka,ta rufe ido kamar batasan komai ba......kamar komai bai faru ba?". Ita daya cikin dakin amma bacin rai ya cikata,haka ta dinga hararar wayar dake ajjiye a gefe kamar itace mahmud din,cikin ranta tana qiyasta gamuwarta da afifa,a haka farheen dake cikin shigar wasu lafiyayyun kayan bacci masu matuqar kyau da daukan hankali ta turo qofar ta shigo dakin, hannunta dauke da coffe din sãahar. Da kallo sãahar din tadan bi farheen,zamanta da ita ta koyi abubuwa masu tarin yawa,ta kuma gane ashe a baya ita din amsa sunan mace kawai takeyi ba tare da tasan ma'anar hakan ba,sai data zauna da farheen din na tsahon shekaru biyu da Wani abun,taci gaba da kallonta cikin rai da zuciyarta tana jin inama itace farheen din,bata da wata damuwa kaf rayuwarta,Allah ya bata miji irin yaa muhyi dinta,ya kuma azurtata da zuri'a yara lafiyayyu har guda biyu,gidanta tamkar ita ta zabawa kanta shi,duk ko me takeso tana samu,inda itace ita me zata nema kuwa a duniya?. "Gayamin ta yaya zakiyi kumari,kin kama black tea da coffee kin riqesu tsam" farheen ta fada tana dire cup din saman bedside,idanunta akan fuskar sãahar tana qoqarin karantar yanayinta da take shinshinar kamar ya sauya. Karamin murmushin da yafi kama da yaqe ta dan saki "Bana jin yunwa,bazan iya cin abinci kuma banajin yunwa ba" kallonta farheen tayi tayi murmushi "Koda bakiji yunwa ba ki kamanta ci koda babu yawa" lumshe ido kawai tayi ta gyada mata kai "Ba wani abu da kike buqata ko?" Kai ta sake gyadawa tana qoqarin zama sosai saman sofa bed din "To sai da safe" "Khalipha fa?" Waiwaya kadan farheen tayi "Kina buqatar dan tayin kwana ne?" Kai ta gyada "Kin manta ne tare muke kwana dama duk sanda nazo?" "Haka ne,zan sa baraka ta kawo miki shi,saida safe" "Allah ya kaimu" ta amsa tana miqa hannu ta jawo mug din tana kaiwa bakinta. Ba jimawa baraka ta shigo da khalipha wanda keta faman barci,an shirya shi cikin kayan bacci da alama ya jima dayin baccin,ta kwantar mata dashi saman gadon taja mata qofar. Ko rabin coffe din bata sha ba taji ya isheta,ta maidashi saman qaramin plate din tangaran din da farheen ta hado mata dashi,ta miqe a nutse ta shiga toilet tayi brush sannan ta dawo ta rage hasken fitilun dakin,ta hanye gado tana lullubesu da bargo ita da khalipha bayan taja yaron cikin jikinta tana jin tamkar ita ta haifeshi. Ajiyar zuciya ta saki mai nauyi sanda ta lissafa shekarun yaron,yazo dai dai da shekarun faruwar wani abu daya sameta a baya,ta gyarawa yaron kwanciyar cikin jikinta,tana iya jinsa sanda yake sauke ajiyar zuciya,sai wasu hawaye masu dumi suka ratso ta idanunta,ta sanya tafin hannunta da sauri tana gogesu,qasa qasa bakinta na furta "Aamantu billah, Alhamdulillah ala kulli haal" ta qarashe maganar ne tare da rintse idanuwanta hadi da tilastawa zuciyarta kauda dukka wani abu da zai kawowa mata hutu da nutsuwa cikin sassanyan daren da wata iska me dadi wadda ke dauke da hadari take kadawa. Sai Allah ya taimaketa bata jima a duniyar tunani tana bulayi ba bacci yayi nasarar daukarta yayi awon gaba da ita. Washegari tun bayan sallar asuba bata koma ba,wannan din kusan dabi'arta ce,tana zama ne saman abun sallah har sai alfijir ya keto gari ya danyi haske. Ko yau dinma tana zaune,tana dab da kammala addu'o'in ta khalipha dake barci farka,ya miqe ya zauna sosai saman gadon yana murza idanunsa,a nutse ta waiwaya tana kallonsa,suka dan zubawa juna ido na wasu sakanni,sai ya sauko daga saman gadon da sauri,ta bude masa hannayenta ya fado ciki ta maida ta rungumeshi tsam tana sakin murmushi "Kaji dadin ganina?" Ta tambayeshi har cikin ranta zuciyarta na mata sanyi,sanyin daya hadu dana hasken azkar din data gama yi,ya kuma gauraya da iskar safiya me dadi dake kai kawo tana kutsowa harta windows din dakin bayan ta samu nasarar daga labulen dake maqale a jiki kadan kadan. Kai ya jinjina yana dariya "Na cewa daddy dama ya kaini,yace sai weekends,i missed you small mom" kyakkyawan murmushi ya qwace mata,tasa hannu taja kumatunsa "I missed you too my little dad". Tun daga lokacin bai barta ta huta ba,akwai sabo sosai tsakaninta da khalipha din,wanna yasa yake sakewa sosai da ita fiye da momynsa farheen,yayita mata hira da tabara ita kuma tana biye masa. Allah ya halicci zuciyarta da matuqar soyayyar yara da kuma qaunarsu,duk inda taga yaro hankalinta yana kai,haka tayita hidima dashi,tayi masa wanka itama tayi,ta kintsa dakin da kanta ba tare data jira su baraka ba,taja hannunsa suka wuce kitchen abinda ta jima batayi ba,tana tambayarsa me yakeson ci,ya gaya mata ta soma fiddo kayan da zata hada breakfast din dashi. Mamaki ya kama lubabatu sanda ta samesu a kitchen "Da kinyi magana saina taso na hada miki abinda kike da buqata,yau din hutun qarshen mako ne,nasan masu gidan basa tashi da wuri,shi yasa banyi safkon fitowa ba" "Karki damu" ta amsata a taqaice,saita miqa mata abinda zata tayata dashi taci gaba da hidimar hada break din tana sauraren khalifa. Ita kanta a jikinta yau dadi takeji,ko ba komai tadan motsa jikinta,don ta jima batayi girki ba,duk da yana daya daga cikin hobbies dinta,amma wani dalili mai nauyi ya kasheshi murus daga ruhinta. Awa biyu ta gama komai ta zubawa khalipha komai a plate daya,yanata murna yau an hada mishi delicious,yaqi yarda ko lubabatu ta dauka masa plate din takai masa Parlor. Sãhaar na murmushin wauta da dadin quruciya irin na yaro ta sakashi a gaba suka fito. Suna fitowar sukayi kacibus da farheen,a shirye tsaf tana zuba qamshi,hannunta dauke da aleena da tayi mata kwalliya da wata designer overall kusan shigarta ta ko yaushe kenan "To bismillahi,shi yasa yau banji ifce ifcensa a parlor ba,ashe an tafi inda akafi kauri" farheen ta fada tana kallon khalipha,wanda tuni shi ya samu guri yayi zaman dirshan abinsa. Sãahar dake kallon khalipha tana sha'awar rayuwarsa,bashi da wata matsala ko damuwa,abinci kam zaici duk wanda aka bashi a sanda kuma yaso,baisan ma mommyn nasa nayi ba,ta maida idonta ga aleena daketa bangala mata dariya tana kuma dago mata hannu alamun tanason ta dauketa ne "Beauty na baxan daukeki na bata wannan kwalliyar ba,banyi wanka ba" "A hakan?" Farheen ta fada "muna tashi kitchen muka shiga,bari na watsa ruwa nazo muyi hira" sãahar din ta fada tana juyawa da dan hanzari "Dubiya ma zaki rakani,kada ki jima,so nake muje mu dawo daddyn khalipha yacemin da azahar zayaje daurin aure". Batason zuwa yau ko ina saboda jiya ta fita,to amma dubiya ce tasan daga asibitin ba wani gurin zasu wuce ba. Minti kusan talatin ta kwashe a toilet din sannan ta fito,ta tsane jikinta ta fara mulke fatarta da lotion. Cikin qasa da minti talatin ta shirya cikin vintage bubu gown ta chiffon material,ta yane kanta da dan siririn veil din da yazo hade da rigar tayi rolling dashi, kyakkyawar fuskarta ta fita ta tsakiyar mayafin,siririn agogon casio ta daurawa tsintsiyar hannunta wanda yazo ne tare da qaramar barimar data sawa kunnuwanta,don ba kasafai takeson kaya masu damu ko nauyi ba,saidai idan ya zamana ba yadda zatayi. Bata dauki komai ba banda wayarta data riqe a hannunta bayan ta feshe jikinta da turarukanta na dindindin guda biyu masu tsananin sanyin qamshi da jimawa a waje basu bar gurin ba,ta zura takalmanta masu matsakaicin tudu Golden goose brand ta fita a dakin. A tsaye ta samu farheen tana serving yaa muhyi dake sanye da jallabiyya,da alama tashinsa a barci kenan yunwa ta fiddo shi,don ba kasafai yake cin abincin a sassan ba. Tana juya masa tea ta dago ta kalli sãahar "Tabarakar rahman" farheen ta fada tana murmushi,saboda har ga Allah ta gaza jurewa kyan da sãahar din tayi,cikin ranta da zuciyarta ta cika da fatan ubangiji ya shiga lamarinta. Daga kai yaa muhyi yayi ya kalli farheen din "Me ya faru?" "Bakaga auta ba?" Idanunsa ya maida ga sãahar sannan ya dawo dasu kan farheen bayan ya karbi tea din daga hannunta,shi kansa kowacce rana sallolinsa biyar tana cikin addu'o'in sa,ajjiye mace kamar sãahar din a gida abune da bazaiyiwu ba,duk kuwa girman jarrabawar data fuskanta,gidan aure shine solution. Cikin girmamawa ta qaraso ta gaida yaa muhyi din,cikin ranta tana addu'ar Allah ya kauda hankalinsa,kada ya sake tayar mata da dukka wata magana data shafi aikin company din nan,saidai addu'artata bata ci ba,suna gama gaisawa ya jeho maganar "Kiran wayar professor ne ya tasheni......yanamin tuni game da batunki" shuru ne ya ratsa saboda ta rasa amsar bashi,shi kuma kamar bai kula ba ya dora "Kiyi qoqarin hada amsarki nan kusa,don kusan nashi shirin ya kammala,cikin satin nan ko sati na gaba zaku kama aikinku" "To,in sha Allah" ta amsa masa a sanyaye,gabanta yana dan faduwa,zasu kama aiki ko ita dawa dawa?,ta tabbatar harka ce data shafi mu'amala da maza,magana ake ta company wanda bazaiyiwu ace mata bane zallah. Wannan maganar ita ta sake sanyata ta zama so silent sanda suke hanyar asibiti ita da farheen,duk da cewa ita ke driving,amma yadda ta bawa kwalta dukka hankalinta ya isa ka fahimci tana wani nazari ne da daban. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 07 *Arewabooks:huguma* https://arewabooks.com/u/huguma "yayanki ya saka hope da yawa a kanki,ya kambamaki da yawa,Allah yasa dai zaki fishsheshi" sãahar dake tsakiyar duniyar tunani ta tsinciki maganar farheen kaman daga sama. Kadan ta waiwayo ta dubi farheen,kamar zatace wani abu sai kuma ta fasa,ta sake maida kanta ga tuqin,wanda har suka isa asibitin bata kuma cewa uffan ba. Tunda suka shiga dakin suka gaisa da mara lafiyan da relatives na anty farheen,sai ta kama hannun khalifa suka fita a dakin,saboda idanun mutum biyu da suka fara uzzura mata,zata iya cewa tasan daya,saboda tana ganin pictures dinsa cikin hotunan farheen,dayan ne batasan daga ina yake ba,amma tana kyautata zaton dan uwan mijin thurayya me haihuwar ne. Ta bayan asibitin suka bi ta fara shawagi cikin asibitin,dukka guraren da take bi din gurare ne da babu yawaitar mutane sosai,sai majinyata jifa jifa,abinda ya sake karya mata zuciya,tana sake godewa ubangiji da ya barta da lafiyarta bata salwanta ha,tabbas inda burin ADAM yakai ga cimma gaci,tayi imani dari bisa dari cewa har kamar wannan lokacin itama tana cikin jerin sahun wadanda zasu qulla kyakkyawar alaqa da asibiti,idan ma bata samu gurbin zama a cikinsa ba,zaman da ba wanda yasan ranar yankewarsa da ubangijin daya qaddara mata komai. Tafi tafi sai gata ta bulla ta bangaren 'yan haihuwa,cikin jiki da zuciyarta taji tana mararin shiga ta basu gudunmawa,don ta tabbatara akwai tarin mata masu raunin gaske a wajen,saidai ta manta cewar yau din bata riqo koda purse ba bare ta fito da kudi. HIBBA HASHIM ta tuna,wata qawa ga afifa dinta,idan bata manta ba kamar ta taba jin afifa na maganar anan take aiki,saita koma gefe daya ta tsaya,ta kunna wayarta wadda tun daren jiya take a kashe. Bata gama daidaita ba saqonnin kar ta kwana suka fara turereniyar shigowa da baquwar number da bata sani ba. Qaramin tsaki taja ta share saqonnin ba tare data duba ba,ta kira afifan. Ta bata tabbacin a nan take,kuma ana samunta a yau din,cikin minti biyu ta kira mata ita,sai gata a bakin gurin,fuskarta fal fara'a. Tanason sãahar,tana masifar burgeta,gayunta kyanta da kuma iliminta,macace me ajin da jerawar mutum kadai da ita ya isa ya sake siya maka daraja da aji,don haka cikin girmamawa ta yiwa sãahar jagoranci zuwa gurin. A hankali take takawa,jiki da zuciyarta gaba daya sun raunana,tsohon ciwon dake danqare a zuciyarta ya fara balle kansa,wannan ya qaranta walwala sosai daga fuskarta. Muryar wata nurse shine abu na farko daya fara dukan dodon kunnenta,fada take sosai kamar me shirin antayawa matar dake tsaye a gabanta dauke da tulelen ciki zagi,ba abinda jikin matar keyi sai rawa,tana kuma share hawayen dake zarto mata "Nidai don girman Allah malama kiyi haquri,ki bani gado,idan na haihu koma meye sai ayi,amma yanzu inajin haihuwata a kusa,koda yaushe zan iya haihuwa" "To ina ruwan wani?,ki haihu din mana,wanda yayi miki cikinma bai damu ba bare mu da rana tsaka muka ganki dashi" saita juya tana niyyar wuce matar. Cak sãahar tayi a wajen,ta gagara zama samam kujerar da hibba ke mata tayin zaman,a nutse ta dauke manyan fararen idanunta daga kan matar zuwa kan hibba "Me ya samu waccan matar" baki hibba ta tabe "Kin ganta nan,ta kawo kanta asibiti da sunan haihuwa,amma ko pant din da za'a sakawa jariri babu,bare ayi maganar katin da tayi awo kudin gado da sauran abubuwan da ba gwamnati ce take biya ba,da aka tambayeta ina mijin sai tace ta baroshi gida yana bacci,muka ce lallai sai yazo,saboda yaronta breach ne,zamuyi qoqarin gyara masa kwanciyarsa,idan an samu nasara shikenan,idan ba'a samu ba dole sai ya biya kudi anyi mata C.S. Dajin haka hankalinta ya tashi,muka bata aron waya ta saka numbers dinsa ta kirashi,wallahi sai data kusa kiransa sau goma kafin ya daga,da gasken kuma baccin yakeyi abun mamakin,daya daga yaji itace sai cewa yayi 'dalla malama meye?' tayi masa bayanin komai,amma budar bakinsa cewa yayi,kada ta dameshi,idan ya gama baccin zaizo,idan zata iya jiransa ta jirashi,idan ba zata jirashi ba tayi duk yadda taga zata iya,sai ya kashe wayarsa.....kinsan abun takaicin?" Kasa cewa komai sãahar tayi bare ta amsa mata ba,duk da hakan hibba bata damu ba ta dora "Dukka kudin matar nan idan tayi aikin tayi wahalar mijin take bawa wai a taru a rufawa juna asiri,wallahi duk da abinda yayi matan nan muna ta masifa amma bashi kariya takeyi a fakaice,abinda ya bamu haushi kenan mu duka,har yanzu kuma in gaya miki baizo ba,maganar da nake miki tun jiya fa abun nan ya faru,kudin data tara inda a hannunta ta ajjiye ba yaro daya ba ko biyar zata haifa zai mata komai ba" idanunta sãahar ta mayar ta rufe tana jin wani radadi tun daga cikin idanuwan nata har zuwa zuciyarta "Allah ya tsinema makahon so" kalmar ta subuce daga bakinta ta fita da wani irin zafi da amo me motsa rai da zuciya. "Wallahi kam" hibba ta amsata ba tare data lura bada ita take ba "Kuyi mata komai ni zan biya,ku bani number wayar mijin nata,he must pay na duk neglect dinsa akan matarsa,ba baiwa bace d'iya ce kamar yadda yake d'a ga wasu" ta fada a mugun zafafe. Har yanzu maza suna bautar da mata?,har yanzu maza suna amfani da raunin 'ya'ya mata suna cutar dasu,suna illata su,wadda ke kan wani doro mai matuqar hatsari ga dukka rayuwar kowacce d'iya mace na mutuwa ko rayuwa ma basu barta ba bare me lafiya?. Ta daga idanunta da suka canza launi daga inda take zaune tana duban inda matar ke tsaye,kallo daya zakayi mata ka tabbatar tana cikin tsananin tashin hankali,kuka kawai takeyi,bata ko duba da cewa ita din ba qaramar yarinya bace,taimako da agaji kawai take nema,ya manna mata abinda zai iya zama ajalinta ya kuma gaza bata kulawa a sanda tafi buqatar hakan,koda da kudinta ne wanda ta hada da guminta da qarfin jiki dana zuciya,ba tare datayi la'akari da nauyinta yana bisa wuyansa ba "Ina danginta?" "Ba 'yar nan qasar bace,aurota yayi,kamar nijer naji tace" daidai sanda hibba ta gama bawa sãahar information matar ta kama qugunta ta durqushe tana murqususun dake nuna ciwonta ya fara kankama da gaske. Sãahar din na tsaye sanda nurses din suka kamata bisa jagorancin hibba suka shiga labor room din da ita. Kasa zama tayi,wani tsumammen bacin rai yana taso mata kamar zai shaqeta,wasu abubuwa da suka shude mata cikin rayuwarta a yau suka fara motsawa,suna son dawo mata da abinda ya shude a baya, situation din da matar ke ciki yayi mata baban famin data kasa shanyewa,saida wasu hawaye masu zafi suka sauko mata,ta saka tissue din data riqo a hannunta saboda khalifa ta daukesu a mugun sanyaye. Muryar farheen ce ta katseta,ta waiwaya daga sashen da takejin amon muryar tata "Nayita nemanku ban ganku ba,inason nace ku dawo ciki,dakin babu kowa" farheen ta fada tana karantar wasu abubuwa masu zafi dake fita daga qwayar idanun sãahar. Kai ta girgiza "Zan shigo,amma saina gama wani dan aiki a nan" "Patient dinki ta sauka fa,ta samu baby girl" muryar hibba dake qarasowa gurin da hanzari ta katse tambayar da farheen ke shirin jefawa sãahar "Alhamdulillah" sãahar ta fada tana lumshe idanunta,har cikin ranta tana jin bacin ranta yana raguwa,wanne irin sa'a akayi haka komai ya daidaita cikin hukuncin ubangiji?,ba tare da ankai ruwa rana ba duk da babyn ba'a dai dai take ba?. Tun kafin farheen ta jefa tambayarta ta gama karantar komai, saita harde hannuwa tana saurarensu ita da hibba har suka gama maganganunsu,hibba ta koma dakin ta gani idan an gama gyara babyn ta dauko musu ita. "Amma......daga haka ba wani abun zaki sake aiwatarwa ba?" Farheen ta tambayi sãahar sanda taga tana latsa wayarta. Karamin murmushi kawai ta fidda ba tare da tacewa farheen komai ba,ta riga ta qudirta a ranta,sai kuma ta aiwatar. Bugu biyu aka daga wayar daga can bangaren,suka kuma fara magana da matar dake riqe da wayar a daya sashen. A nutse farheen ta dauke dubanta daga kan sãahar dake shigar da qorafi tamkar aleena ko afifa aka yiwa hakan ta juya ga bayanta,inda muryar magidancin da duka duka bazai wuce shekara arba'in ba a duniya ke tashi cike da hayaniya da kuma hargowa,cikin nuna zallar gogewa a rashin mutunci. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 08 Daga shigowarsa zuwa isowarsa gurin duka duka mintuna qalilan amma ya cika wajen da hayaniya da fadace fadace,sãahar ta lumshe idanunta tana jin wani bacin rai yana sake ratsata,ko ba'a gaya mata ba ta tabbatarwa kanta wannan shine mijin matar,sai taja kujera kawai ta zauna tana qare masa nazari hankali kwance,domin tayi imanin babu abinda zai hanashi karbar hukuncin dukka wannan haukar tashi. *_Bayan awa d'aya_* Duk da yadda lamarin ya zamo mata Wani babban fami a rayuwarta,amma sai ta dinga jin nutsuwa tana shigarta da aikin data aiwatar yau cikin asibitin,duk kuwa da cewa bata da Wani relation da matar,amma tana jin tayi abinda ya kamata na ceto ta daga azzalumin namiji data tabbatarwa da kanta ire irensa suna da yawa a duniya,wasu matan da yawa saidai a lahira ubangiji zaiyi wannan hisabin,don basu da gata basu da me tsaya musu,babu kuma me qwato musu yanci da haqqunansu da mazan suka sanya takalma suka tattake. Karon farko taji tana da sha'awar bude qungiyar da zatayi aiki akan ire iren wadan nan zalunci da akewa mata,to amma gaba daya bata da wannan qwarin gwiwar a yanzu,ita kanta akwai sauran tarin matsaloli da qalubale,wasu sun shude wasu tana cikinsu,wasu kuma jikinta yana bata suna gaba suna jiran isowarta "Sannu da aiki" farheen ta fada sanda sãahar ta saka key tana qoqarin kunna motar bayan ta kammala duk abinda ta qudirta yi a asibitin. Waiwayowa sãahar tayi ta kalli farheen din,qaramin murmushi yana subuce mata,duk da yadda zuciyarta ke wani irin zafi,tanason lallai saitayi mata bitar tata rayuwar,yayin da ita kuma ya sanya dukkan wani qarfi nata tana tanqwarata,tare da gaya mata bata da wannan buqatar,sãahar din bata amsa ba ta tayar da motar cikin nutsuwa tayi reverse suka fice daga harabar asibitin,anty farheen na sake jinjina mata qoqarin da tayi,da kuma yabawa sãahar din kan hannun wadanda ta danqa me gidan matar,ta tabbatar matat zata samu adalci. Saboda raunin da zuciyarta ta samu wannan ya sanya takejin jikinta gaba daya ba qwari,don haka suna isa gida ta fidda kayan jikinta ta watsa ruwa,ta sanya wata riga me taushi da akayita da zallar auduga,ta rage ribbom di kanta tabar wani siririn band. Tana zura slipper a fara sol din qafarta wayarta dake yashe saman madubi ta dauki tsuwwa,a kasalance ta isa gaban madubin tana kallon wayar. Baquwar number ce dai still,sai ta kauda kanta daga kallon wayar,sai a sannan ta tuna da saqonnin da ta gani a dazu,taja qarami tsaki tana barin gaban madubin,ta wuce Parlor abinta. Kadan ta taba abincin ta baro anty farheen acan ta dawo daki,idanunta akan agogo,tanason ganin lokaci zai bata daman yin baccin awanni biyu kafin sallar magrib,sai qarar wayarta ta sake mata kutse cikin tunaninta. Wannan karon tun batakai ga wayar ba ta fara jan tsaki,tana jin haushin kanta da bata sake kashe wayar ba. Sai data daga sannan ta lura da sunan BESTIE,tadan karyar da kanta gefe tana maqala wayar a kunnenta,ta koma bakin gadon ta zauna qafafunta zube a qasa tana sallama cikin lallausar siririyar muryarta "na gode sosai bestie,na gode,kin gwadawa mahmud iya matsayina a wajenki,na gode" "Oops......" Sãahar ta fada a hankali tana dora yatsunta saman goshinta,she really need a rest......ga afifa da tata rigimar a gefe "Dama munyi haka dake?,ko ya nemi izinin kirana?" "Oh sorry,na miki shishshigi ko?,am so sorry" afifa ta fada tana gimtse wayar. Siririn murmushi ya qwacewa sãahar,ta sani sarai rigima afifan keji,dakuma son cusa mata mahmud din qarfi da yaji,batasan yaushe ya samu wannan fadar haka a wajen afifan ba,har takeson mata tutsu saboda shi. Aje wayar kawai tayi gefe ba tare data bi bayan afifa ba,tasan zata gama fushinta ta huce ne,infact ma a yanzu hutawa takesonyi,idan ta tashi koma meye taji dashi. Ta sauke ajiyar zuciya ta kwanta sosai a tsagin hannun damanta kamar yadda ta saba,ta lumshe manyan idanunta a hankali,eyelashes dinta masu tsaho da baqi suka yiwa kyawawan tsagar idanunta rumfa. *********K'arfe takwas da mintuna na dare agogon dake maqale a bangon falon ya nuna,farheen na tsaye daga dining area tana hadawa yaa muhyi fruit salad,daga qasan falon kuma,can saman qawatacce kuma lallausan carfet din da aka yiwa Parlor din ado dashi,sãahar ce zaune,sanye cikin wata farar long sleeve shirt turtle neck da aka yiwa adon flowers qananu daga wajen qirjin da pink flowers,kanta babu dankwali sai band data matse gashinta daketa qyalli yana daukar idanu,duk da cewa dare ne,amma hakan bazai hanaka jin sassanyan qamshin da jikinta yake fitarwa ba,wanda ya riga ya gama runewa a jikin fatarta komai gumi da zafi,fuskarta tayi wani fresh farinta me surkin ja ya bayyana sosai,duk kuwa da cewa ko dan kunne babu a kunnuwanta amma hakan baya hanaka hango baiwar kyan da Allah ya bata. Aleena na zaune tsakiyar qafafunta,khalifa kuma yana zaune daga gefanta tana masa homework. Lokaci lokaci farheen na daga kai tana dubansu sannan taci gaba da aikinta,yanayin yadda sãahar din ke matuqar son yara zai baka mamaki,a haka a ido sam batayi kama da meson yara ba. Sallamar yaa muhyi cikin Parlor din ita ta tashi karatun,khalipha yayi gurinsa da gudu aleena ta fara daga masa hannu tana bangale masa da dariya,dole ya qaraso ya dauketa,ya zauna saman kujera yana ji dasu duka su biyun,da khalipha dake surutu,da aleena dake gwaranci. "sannu da zuwa yaa" sãahar ta fada tana miqewa tsaye da zummar barin falon. Waiwayowa yayi yana dan karkata hankalinsa a kanta "Barkanki khadijatou" "Ya aikin?" Ta sake fada tana duqawa ta dauki wayarta "Alhamdulillah.....zan shiga ciki yanzu zan watsa ruwa,after one hour ki sameni" "Okay" ta fada tana jinjina kai,sai ta juya ta wuce zuwa dakinta tana jiyo 'yar hayaniyarsu da yaran. Saman sofa bed ta zauna tana gwada kiran afifa wadda ta dauki fushi da ita,bugu biyu ta daga "Me kika kirani kice min?" "Relax mana" ta fada very calm "Dadina dake hayaniya sa saurin daukan temper" "Eheeen,ya muke dake?" Maganar ta saka sãahar sakin qaramin murmushi saman kyakkyawar fuskarta,tasan magana ce kawai afifa keson gaya mata "Koma ya muke din ba wani abu bane,nayi miki laifi kiyi haquri,am sorry" ajiyar zuciya afifa ta sauke,sãahar din tana da wata baiwa cikin halaye da dabi'unta,tasan dukka hanyar da zata zauna da kowa da zamantakewa ya hadasu,hakanan tasan hanya mafi sauqi na sauke mutum daga kan fishinsa nan take "Is ok" "Everything will be alright......but for now please,ki manta da issue dinsa.... mahmud ko?" Ta fada calmly. Idanu afifa ta fidda kamar tana gabanta "Ya salam...... you can't remember his name sãahar,Allahu yahdik" ta qarashe maganar tana dafe goshinta "Whatever afifa,i need space don Allah,ki dakatar dashi" "Zan gwada" "Zaki gwada..... like how?" "You are more than you think,ya dauki al'amarinki da girma sãahar,ba lallai don na mishi bayani ya fahimta ba" "Ya rage nashi" ta fada very careless tana dage kafadunta. Ita gaba daya al'amarin maza baya burgeta sam,ko meye zasuyi,shin meye bata gani ba?,wanne hali nasu ne yayi mata saura?,hirar gaba daya bata burgeta don haka ta sako wani topic din daban. Sai da suka cinye awa dayan da yaa muhyi din ya bata sannan ta ajjiye wayar,ta shiga bandaki ta daura alwala,ta dawo ta fidda abaya ta dora saman rigar jikinta,ta yane kanta da mayafin abayar. Duk da agurguje ba tare kuma da nufin tayi kwalliya ba ta shirya,amma kyanta ya fita sosai,zakayi tsammanin zama tayi tayi wata kwalliya ta musamman,tana da baiwar komai ta raɓa a jikinta yi mata kyau yakeyi. Cikin takardu ta sameshi,gefansa ta zauna tana wasa da yatsun aleena dake zaune jingine da pillow don kada takai ga faduwa,ya dubeta yana ture takardun gabansa,ya zaro wani file mara nauyi,saidai ya banbanta da dukka takardun wajen,bangonsa fari ne tas,anyi masa ado da zaiba,kallo daya zakasan na musamman ne ko kuma yana dauke da wasu muhimman bayanai. Budawa yayi daya bayan daya yana dan dubawa cikin nazari,daga bangon farko har zuwa bangon qarshe,sannan ya maidashi ya rufe,ya ajjiye shi a tsakaninsu yana kiran sunanta idanunsa a kanta "Na'am yaaa" "Kiyi haquri na miki laifi,na karba takardun amsar aiki daga MT GROUP OF COMPANY,ba tare dana jira jin hukuncin da kika yanke ba,am sorry na miki katsalandan" kanta ta daga a hankali,ta sauke dubanta ga yaa muhyi din tana jin wani abu me nauyi yana sauka saman kanta zuwa qirjinta,wani abun kuma da bata tantance meye ba yana mamaye qirjinta,maganganun nasa sunyi mata nauyi qwarai,saboda bata zaci jinsu a wannan lokacin ba,saidai abu daya da take tunawa,yaa muhyi din yafi qarfin komai a wajenta,ta tabbatar shi din masoyi ne me qaunar dukka wani abu da zai baiwa zuciya da rayuwarta farinciki,bijirewa saka hannun karbar aikin dai dai yake da ta tozartashi "Ga file din ki wuce dashi daki,ki duba sosai ki saka hannu a duk inda ya dace,amma kafin sannan,har yanzu kina da chance,idan kikaji baki nutsu ba ko baki gamsu ba,kada ki damu ki dawo da dukka takardun" ya fada yana miqa mata su. Hannu ta miqa itama ta karba,sannan ta miqe cikin sanyi da mutuwar jiki,kamar wadda aka bibbigewa gwiwoyi ta doshi qofar fita,yaa muhyi din ya rakata da kallo har sai data bacewa ganinsa. Kansa ya jinjina,cikin ransa yana fatan saituwar al'amuranta,yana jin kamar ya runtse idanu ya bude yaga sãahar dinsu ta baya ta dawo,ba wannan sãahar din da duk wani buri na rayuwa ya fice daga rayuwarta sa tunaninta ba da mugun gudun tsiya,sanadin wani abu daya shude shekara biyu baya. Kamar wani abun tsoro haka ta ajjiye file din saman madubi,ta koma gefan gado ta zauna,ta dafe gefe da gefe da dukka tafukan hannayenta tana kallon file din daga inda take zaune tamkar wadda ke nazarin karatu daga allon computer,tako ina tana jin sanyin jiki,mutuwar jiki dama rashin karsashi,saidai ko daya cikin istikharar data sanya a gaba takeyi bataji a ranta ta fasa aikin kota watsar da tayin yaa muhyi ba. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 08 Daga shigowarsa zuwa isowarsa gurin duka duka mintuna qalilan amma ya cika wajen da hayaniya da fadace fadace,sãahar ta lumshe idanunta tana jin wani bacin rai yana sake ratsata,ko ba'a gaya mata ba ta tabbatarwa kanta wannan shine mijin matar,sai taja kujera kawai ta zauna tana qare masa nazari hankali kwance,domin tayi imanin babu abinda zai hanashi karbar hukuncin dukka wannan haukar tashi. *_Bayan awa d'aya_* Duk da yadda lamarin ya zamo mata Wani babban fami a rayuwarta,amma sai ta dinga jin nutsuwa tana shigarta da aikin data aiwatar yau cikin asibitin,duk kuwa da cewa bata da Wani relation da matar,amma tana jin tayi abinda ya kamata na ceto ta daga azzalumin namiji data tabbatarwa da kanta ire irensa suna da yawa a duniya,wasu matan da yawa saidai a lahira ubangiji zaiyi wannan hisabin,don basu da gata basu da me tsaya musu,babu kuma me qwato musu yanci da haqqunansu da mazan suka sanya takalma suka tattake. Karon farko taji tana da sha'awar bude qungiyar da zatayi aiki akan ire iren wadan nan zalunci da akewa mata,to amma gaba daya bata da wannan qwarin gwiwar a yanzu,ita kanta akwai sauran tarin matsaloli da qalubale,wasu sun shude wasu tana cikinsu,wasu kuma jikinta yana bata suna gaba suna jiran isowarta "Sannu da aiki" farheen ta fada sanda sãahar ta saka key tana qoqarin kunna motar bayan ta kammala duk abinda ta qudirta yi a asibitin. Waiwayowa sãahar tayi ta kalli farheen din,qaramin murmushi yana subuce mata,duk da yadda zuciyarta ke wani irin zafi,tanason lallai saitayi mata bitar tata rayuwar,yayin da ita kuma ya sanya dukkan wani qarfi nata tana tanqwarata,tare da gaya mata bata da wannan buqatar,sãahar din bata amsa ba ta tayar da motar cikin nutsuwa tayi reverse suka fice daga harabar asibitin,anty farheen na sake jinjina mata qoqarin da tayi,da kuma yabawa sãahar din kan hannun wadanda ta danqa me gidan matar,ta tabbatar matat zata samu adalci. Saboda raunin da zuciyarta ta samu wannan ya sanya takejin jikinta gaba daya ba qwari,don haka suna isa gida ta fidda kayan jikinta ta watsa ruwa,ta sanya wata riga me taushi da akayita da zallar auduga,ta rage ribbom di kanta tabar wani siririn band. Tana zura slipper a fara sol din qafarta wayarta dake yashe saman madubi ta dauki tsuwwa,a kasalance ta isa gaban madubin tana kallon wayar. Baquwar number ce dai still,sai ta kauda kanta daga kallon wayar,sai a sannan ta tuna da saqonnin da ta gani a dazu,taja qarami tsaki tana barin gaban madubin,ta wuce Parlor abinta. Kadan ta taba abincin ta baro anty farheen acan ta dawo daki,idanunta akan agogo,tanason ganin lokaci zai bata daman yin baccin awanni biyu kafin sallar magrib,sai qarar wayarta ta sake mata kutse cikin tunaninta. Wannan karon tun batakai ga wayar ba ta fara jan tsaki,tana jin haushin kanta da bata sake kashe wayar ba. Sai data daga sannan ta lura da sunan BESTIE,tadan karyar da kanta gefe tana maqala wayar a kunnenta,ta koma bakin gadon ta zauna qafafunta zube a qasa tana sallama cikin lallausar siririyar muryarta "na gode sosai bestie,na gode,kin gwadawa mahmud iya matsayina a wajenki,na gode" "Oops......" Sãahar ta fada a hankali tana dora yatsunta saman goshinta,she really need a rest......ga afifa da tata rigimar a gefe "Dama munyi haka dake?,ko ya nemi izinin kirana?" "Oh sorry,na miki shishshigi ko?,am so sorry" afifa ta fada tana gimtse wayar. Siririn murmushi ya qwacewa sãahar,ta sani sarai rigima afifan keji,dakuma son cusa mata mahmud din qarfi da yaji,batasan yaushe ya samu wannan fadar haka a wajen afifan ba,har takeson mata tutsu saboda shi. Aje wayar kawai tayi gefe ba tare data bi bayan afifa ba,tasan zata gama fushinta ta huce ne,infact ma a yanzu hutawa takesonyi,idan ta tashi koma meye taji dashi. Ta sauke ajiyar zuciya ta kwanta sosai a tsagin hannun damanta kamar yadda ta saba,ta lumshe manyan idanunta a hankali,eyelashes dinta masu tsaho da baqi suka yiwa kyawawan tsagar idanunta rumfa. *********K'arfe takwas da mintuna na dare agogon dake maqale a bangon falon ya nuna,farheen na tsaye daga dining area tana hadawa yaa muhyi fruit salad,daga qasan falon kuma,can saman qawatacce kuma lallausan carfet din da aka yiwa Parlor din ado dashi,sãahar ce zaune,sanye cikin wata farar long sleeve shirt turtle neck da aka yiwa adon flowers qananu daga wajen qirjin da pink flowers,kanta babu dankwali sai band data matse gashinta daketa qyalli yana daukar idanu,duk da cewa dare ne,amma hakan bazai hanaka jin sassanyan qamshin da jikinta yake fitarwa ba,wanda ya riga ya gama runewa a jikin fatarta komai gumi da zafi,fuskarta tayi wani fresh farinta me surkin ja ya bayyana sosai,duk kuwa da cewa ko dan kunne babu a kunnuwanta amma hakan baya hanaka hango baiwar kyan da Allah ya bata. Aleena na zaune tsakiyar qafafunta,khalifa kuma yana zaune daga gefanta tana masa homework. Lokaci lokaci farheen na daga kai tana dubansu sannan taci gaba da aikinta,yanayin yadda sãahar din ke matuqar son yara zai baka mamaki,a haka a ido sam batayi kama da meson yara ba. Sallamar yaa muhyi cikin Parlor din ita ta tashi karatun,khalipha yayi gurinsa da gudu aleena ta fara daga masa hannu tana bangale masa da dariya,dole ya qaraso ya dauketa,ya zauna saman kujera yana ji dasu duka su biyun,da khalipha dake surutu,da aleena dake gwaranci. "sannu da zuwa yaa" sãahar ta fada tana miqewa tsaye da zummar barin falon. Waiwayowa yayi yana dan karkata hankalinsa a kanta "Barkanki khadijatou" "Ya aikin?" Ta sake fada tana duqawa ta dauki wayarta "Alhamdulillah.....zan shiga ciki yanzu zan watsa ruwa,after one hour ki sameni" "Okay" ta fada tana jinjina kai,sai ta juya ta wuce zuwa dakinta tana jiyo 'yar hayaniyarsu da yaran. Saman sofa bed ta zauna tana gwada kiran afifa wadda ta dauki fushi da ita,bugu biyu ta daga "Me kika kirani kice min?" "Relax mana" ta fada very calm "Dadina dake hayaniya sa saurin daukan temper" "Eheeen,ya muke dake?" Maganar ta saka sãahar sakin qaramin murmushi saman kyakkyawar fuskarta,tasan magana ce kawai afifa keson gaya mata "Koma ya muke din ba wani abu bane,nayi miki laifi kiyi haquri,am sorry" ajiyar zuciya afifa ta sauke,sãahar din tana da wata baiwa cikin halaye da dabi'unta,tasan dukka hanyar da zata zauna da kowa da zamantakewa ya hadasu,hakanan tasan hanya mafi sauqi na sauke mutum daga kan fishinsa nan take "Is ok" "Everything will be alright......but for now please,ki manta da issue dinsa.... mahmud ko?" Ta fada calmly. Idanu afifa ta fidda kamar tana gabanta "Ya salam...... you can't remember his name sãahar,Allahu yahdik" ta qarashe maganar tana dafe goshinta "Whatever afifa,i need space don Allah,ki dakatar dashi" "Zan gwada" "Zaki gwada..... like how?" "You are more than you think,ya dauki al'amarinki da girma sãahar,ba lallai don na mishi bayani ya fahimta ba" "Ya rage nashi" ta fada very careless tana dage kafadunta. Ita gaba daya al'amarin maza baya burgeta sam,ko meye zasuyi,shin meye bata gani ba?,wanne hali nasu ne yayi mata saura?,hirar gaba daya bata burgeta don haka ta sako wani topic din daban. Sai da suka cinye awa dayan da yaa muhyi din ya bata sannan ta ajjiye wayar,ta shiga bandaki ta daura alwala,ta dawo ta fidda abaya ta dora saman rigar jikinta,ta yane kanta da mayafin abayar. Duk da agurguje ba tare kuma da nufin tayi kwalliya ba ta shirya,amma kyanta ya fita sosai,zakayi tsammanin zama tayi tayi wata kwalliya ta musamman,tana da baiwar komai ta raɓa a jikinta yi mata kyau yakeyi. Cikin takardu ta sameshi,gefansa ta zauna tana wasa da yatsun aleena dake zaune jingine da pillow don kada takai ga faduwa,ya dubeta yana ture takardun gabansa,ya zaro wani file mara nauyi,saidai ya banbanta da dukka takardun wajen,bangonsa fari ne tas,anyi masa ado da zaiba,kallo daya zakasan na musamman ne ko kuma yana dauke da wasu muhimman bayanai. Budawa yayi daya bayan daya yana dan dubawa cikin nazari,daga bangon farko har zuwa bangon qarshe,sannan ya maidashi ya rufe,ya ajjiye shi a tsakaninsu yana kiran sunanta idanunsa a kanta "Na'am yaaa" "Kiyi haquri na miki laifi,na karba takardun amsar aiki daga MT GROUP OF COMPANY,ba tare dana jira jin hukuncin da kika yanke ba,am sorry na miki katsalandan" kanta ta daga a hankali,ta sauke dubanta ga yaa muhyi din tana jin wani abu me nauyi yana sauka saman kanta zuwa qirjinta,wani abun kuma da bata tantance meye ba yana mamaye qirjinta,maganganun nasa sunyi mata nauyi qwarai,saboda bata zaci jinsu a wannan lokacin ba,saidai abu daya da take tunawa,yaa muhyi din yafi qarfin komai a wajenta,ta tabbatar shi din masoyi ne me qaunar dukka wani abu da zai baiwa zuciya da rayuwarta farinciki,bijirewa saka hannun karbar aikin dai dai yake da ta tozartashi "Ga file din ki wuce dashi daki,ki duba sosai ki saka hannu a duk inda ya dace,amma kafin sannan,har yanzu kina da chance,idan kikaji baki nutsu ba ko baki gamsu ba,kada ki damu ki dawo da dukka takardun" ya fada yana miqa mata su. Hannu ta miqa itama ta karba,sannan ta miqe cikin sanyi da mutuwar jiki,kamar wadda aka bibbigewa gwiwoyi ta doshi qofar fita,yaa muhyi din ya rakata da kallo har sai data bacewa ganinsa. Kansa ya jinjina,cikin ransa yana fatan saituwar al'amuranta,yana jin kamar ya runtse idanu ya bude yaga sãahar dinsu ta baya ta dawo,ba wannan sãahar din da duk wani buri na rayuwa ya fice daga rayuwarta sa tunaninta ba da mugun gudun tsiya,sanadin wani abu daya shude shekara biyu baya. Kamar wani abun tsoro haka ta ajjiye file din saman madubi,ta koma gefan gado ta zauna,ta dafe gefe da gefe da dukka tafukan hannayenta tana kallon file din daga inda take zaune tamkar wadda ke nazarin karatu daga allon computer,tako ina tana jin sanyin jiki,mutuwar jiki dama rashin karsashi,saidai ko daya cikin istikharar data sanya a gaba takeyi bataji a ranta ta fasa aikin kota watsar da tayin yaa muhyi ba. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/4, 1:54 PM] KYAUTA: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 09 Kwana file din yayi a nan,bayan sallahr asuba ta kammala azkar dinta ta jawoshi tana zaune daga saman abun sallarta,ta buda a hankali ta fara karantawa kamar yadda yaa muhyi yace tayi din. Very interesting,komai na kamfanin a tsare yake cikin wani tsari mai burgewa,banda batajin son aikin cikin ruhinta zata iya cewa company din ya burgeta,kuma kamar tana da gudunmawar da zata iya bayarwa tabbas gurin saitashi. Tsayawa tayi cak da biron dake hannunta bayan ta kammala signing tana duban sunan CEO din dake rubuce cikin ruwan gold daga gefen takardar MUHAMMAD TAUFEEQ. Zame hannunta tayi a hankali daga saman takardar tana kallon sunan,a hankali tunaninta ya koma can baya,sai yanzun ta tuna yaa muhyi ya gaya mata zasuyi aiki ne tare da yaronsa "Jaffal qalam" ta fada can qasan ranta tana maida file din ta rufe,ta riga ta saka hannu,tabbas data janye,batason a kaita sashen da zatayi aiki tare da kowa,amma ya zatayi?,yaa muhyi ya riga ya daureta da jijiyar jikinta. A gaggauce ta isa parking lot na gidan sanda yake shirin shiga motarsa,ya dakata ya waiwayo yana dubanta tana dan haki saboda saurin da takeyi,file din ta miqa masa "Ya akayi?" Ya tambayeta tun kafin ya buda bayan ya karba "Na cike yaaya" ta fada tana langabe kanta,sosai murmushi ya wadaci fuskarsa,alamun maganar tayi masa dadi sosai,ya fara buda file din ya duba sannan ya dora idonsa a kanta "Thank you sisi,na gode da baki bani kunya ba baki kuma watsa min qasa a ido ba" yadda yayi appreciating nata saita kasa neman komai daga wajensa,ta saki qaramin murmushi ta gyada kai kawai "Next week on Monday zaki fara shiga office dinki,komai da kike buqata kiyimin magana baki da matsalarsa in sha Allah,already shi partner din naki ya fara shiga cikin wannan satin" yana maganar yana danne danne a wayarsa. Daga kai yayi "Na saka miki kudi ko zaki buqaci yin siyayya" "Oh no yaaya,ina da kudi a account dina fa,sannan last week yaa Saifullahi ya sakamin shima" "I know,hal jaza'ul ihsani illal ihsan" kai ta jijjiga a hankali,sai taji cikin ranta tana jin dadin abinda tayi masan,tunda shima har qasan zuciya da fuskarsa abun ya faranta masa. Ciki ta koma ta fara shiryawa don wucewa gida,already dama tana da intention na zuwa yin shopping din,akwai kayayyakin amfaninta da sukayi low. **********Lafiyayyun motocine qirar range rover baqaqe sidik ke wulwula gudu saman kwalta wata nabin wata har guda hudu a jere. Tun daga inda suka taho wato cikin filin sauka da tashin jiragen saman malam aminu kano wato aminu kano international airport har zuwa cikin rukunin gidajen dake unguwar nasarawa GRA,duk inda suka gifta daukan idanu da kuma hankulan al'umma sukeyi tare da saka kokwanton cikin zukatan al'umma na tunanin mamallakan motocin da babu cikakkiyar number a jiki kamar ta kowanne abun hawa,sai wasu qididdigaggun haruffa da kuma lambobi da sukazo a jere data sauran kowacce mota dake bin 'yaruwarta. A hankali suka nutsa cikin nasarawa,sannan kai tsaye suka fada titin guda abdullahi road,kafin su tsaya qofar bristol palace. Cikin gaggawa kuma security din dake tsaron qofar gidan suka wangale musu gate ba tare da tsananta bincike ba,dukka motocin suka shige ciki,suka kuma samu wajena gurbin da aka tanada don ajjiye motoci suka faka. Cikin qasa da minti daya dukka qofofin motar suka bude banda guda daya tak,mutanen dake ciki sanye da baqaqen suit suka firfito,kowa ya samu guri ya tsaya,biyu daga cikinsu kuma suka bi hanyar da zata sadasu da reception na hotel din cikin sassarfa. A qalla mintuna biyar kyawawa sai ga mutum biyu daga cikinsu ya dawo,cikin azama da zafin nama ya isa ga motar dake tsaye dukka qofofinta a kulle yayi knocking baqin glass din motar,aka dan zugeshi kadan,yayi magana ta mintina sannan yabar wajen,ya koma bayan motar ya dage,yasa hannu ya fidda wasu kyawawan luggage guda biyu,biyu daga cikin mutanen dake tsaye daga bayansa suka matso,kowa ya riqe guda daya,sannan ya sake zagayawa right side na seat din bayan motar ya bude qofar,yaja baya cikin girmamawa don bawa mamallakin motar fitowa. Sakanni sittin cif kafin qafarsa ta fara fitowa,Sannan ya zuro qafarsa cikin kyakkyawan takalmi qirar kamfanin hermes na qasar france,sai daukar idanu yake saboda tsananin kyau da tsafta,ya sake daukar wasu sakannin kafin ya zuro dukka jikinsa zuwa waje. Zara zara yatsun hannunsa ya sanya yana qoqarin cire wayar dake maqale a kunnensa,kyakkyawar fuskarsa mai cike da wani irin kwarjini haiba da cikar zati a dinke tsaf!,babu alamun fara'a ko kadan tattare da ita. Fari ne,amma ba zaka kirashi kar ba,wani irin fari da bai cika haske da yawa ba,me murjajjen jiki da babu wani waje da yake a rame ko ya nuna alamun qashi,saima qaqqarfar siffarsa da cikakken zatinsa daya nuna kansa da kansa ta jikin lallausan yadin vicuna mai asalin kyau da tsada dake jikinsa,wanda aka yiwa wani irin dinki na musamman mai jan hankali,duka duka tsahon rigar bai wuce gwiwarsa ba,dogon hannu ne da rigar daya bai qarasa tsintsiyar hannu ba,an qawata hannun rigar da wasu irin links masu zubin gold,daga qasansu kadan kuma kyakkyawan agogon hannu ne baqi qirar kamfanin Casio daya kwanta luf saman fatarsa dame lullube da gargasa baqa sidik mai santsi,wadda ta fito har zuwa saman hannunsa da kuma saman kowanne yatsa nasa,zobe ne qwaya tal daga tsakiyar hannun nasa na wani irin qarfe mai daraja,wanda shi ba gold bane,hakanan ba azurfa ba. Yadda sumar kansa take baqa sidik a nannade sannan kuma a kwance,hakan gashin daya qawata gefe da gefen fuskarsa,zaka iya kiransa qasumba,saidai baiyi kama da qasumba hakanan baiyi kama da saje ba,saboda wani irin gyara na musamman da akayi masa,wanda yasa yafi qasumba kyan gani,yafi kuma saje tsari da qawatuwa,tun daga kumatunsa zuwa habarsa,ya kuma hade da qasan hancinsa. Baqar sumar da baqin yadin dake jikinsa suka hadu suka haska farar fatarsa tarrrr tamkar fitowar rana a farkon wuni. Eye glasses din daya sanya kuma ko kadan bai boye kyawawan qwayar idanunsa ba dake da wani irin shape mai matuqar fusgar hankali,idanun dake cike da wani irin kwarjini mai tarin yawa,kwarjinin da a kullum yake lullube da fushi da kuma fusata. Ko yaya ka qara taqi kadan kusa dashi kana iya shaqar daddadan qamshin turarensa da ba lallai ka gane ainihin wanne irin turare bane,saidai yakan sanya nutsuwa ga duk wanda ya shaqeshi,ya kuma qara kwarjini ga ma'abocin qamshin. Dukka hannayensa ya zube a aljihun lallausan yadin jikinsa,ya kuma daga kai yana kallon tsororuwar ginin hotel din cikin kamewa da nutsuwarsa,tamkar wanda yake nazarin wani abu,yayin da dukka mutanen suka zamana a tsare cikin shirin kota kwanar karbar umarni daga gareshi. Iska ya furza ya taka zuwa gaba,abinda ya sanya mutum biyu daga ciki sukayi gaba kamar masu masa jagora,sauran kuma suna biye dashi,yayin da daya daga gefansa wanda ke riqe da wani babban folder ya matso gefansa kadan "May I continue sir" ya fada cikin matuqar girmamawa a russune,da hannu yayi masa nuni da eh,yaci gaba da takawa shi da sauran mutanen,yana biye dashi yana karanto masa komai daki daki. Dukkansu suka fara kutsa kai zuwa cikin main entrance na hotel din. A gaggauce suka wuce zuwa lipter da zai sadasu da dakin da zai sauka,cikin mintunan da ba zasu wuce sakanni sittin ba ta tsaya,suna biye dashi har a sannan ta bude dukka suka fito. Kai tsaye har zuwa qofar dakin. Daga daga ciki yayi scanning card a bakin qofar,tayi qaramar qara alamun samun izinin shiga. Palace suit,babban dakin dake da aqalla zai iya daukar mutum bakwai cif,two ensuite bedroom da kuma master bedroom guda daya,living room dining room kitchen da kuma corridor. Wannan shine cikakken zabinsa ga masauki,bayason takura bayason matsi,duk sanda tafiya ta kamashi zuwa wani gari da bashi da gida nashi mallakin kansa,ko kuma yake buqatar kebewa ko sauka ya huta sosai ba tare da kowa yasan ya shigo ba. Yadda yayi cak a tsaye yana sauraron bayanin da inyamurin ke kwararo masa haka sauran mutanen da suka shigo tare dashi suke a tsaye,dukkansu na jiran wani umarni nasa ne. Sosai ya kafe mutumin da idanu,duk da cewa bai kalleshi ba amma tsantsar kwarjinin da idanunsa ke dashi ya hudashi,tun daga fatarsa har zuwa jinin jikinsa ua harbawa kwanya da zuciyarsa,take muryarsa ta fara rawa,ya fada kwan gaba kwan baya cikin bayanansa,sai ya lumshe kyawawan idanunsa kawai, qwaqwalwarsa ta fara kaishi inda yake zato ko hasashe. "Where is musaddiq?" Karon farko da muryarsa me taushi da wani irin amo a cikinta ta bayyana cikin sigar tambaya da alamun gajiya da jin soki burutsun bayanan da ake masa. Daya daga cikin mutanen ya matso da hanzari ya amsa masa "Sir.....on his way" "Ka kirashi,ka gaya masa yayi sauri,idan yazo ya karbi dukkan folders din dake hannun peter kafin ya nemeni,you can go" ya fada a taqaice yana sanya kansa ciki. Gaba daya gumi ya rufe mutumin da aka kira da peter din,tabbas yasan qaryarsa ta qare,tun daga watan da aka sanar da yiwuwar zuwansa kamfanin,yaketa shige da ficen ganin ya binne komai,ya kuma rufe bakin dukka wanda zaiyi ruwa da tsaki wajen kawo tarnaqi cikin walwalarsa,sai gashi a karon farko......tun ba'a je ko ina ba alamu sun fara nuna kansu. Ya san yaron sarai,bawai tun yau ba,aiki ya taba hadasu sau daya tak dashi kafin su suma ya karkata hankalinsa zuwa wata qasar,bai kwashe da dadi a hannunsa ba,yaji babu dadi qwarai,sai gashi wata mummunar qaddarar ta sake dawowa tana neman budadeshi. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/4, 1:54 PM] KYAUTA: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 10 Har yayi taku biyu mutumin da yafi yawan magana dashi yadan sassauta muryarsa "Am sir,am sorry.....akwai mutum biyu dakeson zama dakai,yanzu haka suna zaman jiranka" "Who and who?" Kadan ya buda wani dan qaramin abun rubutu dake hannunsa sannan ya gaya masa sunan "Mr Paul and mr isaac" fara takawa ya sakeyi zuwa ciki sannan ya amsashi "Tell them to give me an hour,I will take a bath". A nutse ya tura daya daga cikin dakunan daya fi zabar zama a ciki,rabin hankalinsa nakan wata qaramar wayar hannu 'yar firit me qarancin tudu yana latsata. Ya lalubo wata number ya fara kira,dai dai sanda ya zauna gefen sofa bed,idanunsa na bisa fuskarsa data fito tarwai ta babban madubin dake dakin,sai kayi tsammanin ita yake kallo,saidai ko kadan,tunaninsa ya lula wata duniyar daban. Ba dadewa na'ura ta gaya masa layin a kashe yake,yaja tsaki yana sauke wayar a kunnensa,ya sake laluba wata number,wadda ita din bugu daya ta shiga. Muryar dattijuwa ce ta bayyana cikin wayar,muryar dake nuna zallar dattijanka da kamalar mamallakiyar muryar "Barka da dare yallabai" shine abinda ta fara fada bayan amsa mata sallamarta da yayi "Barka,kuna lafiya?" "Lafiya qalau walhamdulillah......yanzun nan tayi barci ko mintuna goma batayi ba" lumshe idanunsa masu kyau da daukan hankali yayi "Alright......a shafamin kanta" kafin ta sake cewa komai ya katse wayar,ya durqusa a mugun kasalance yana zare takalmin qafarsa zuwa socks yana cillarwa waje daya,gaba daya yayi loosing duk wani interest akan aikin,abban bai taba nufarsa da wani aiki da yaji sam bayaso ba irin wannan,baisan me yasa ba. Sai daya cire kayan jikinsa tsaf ya daura babban towel ya wuce bathroom. Wanda a qalla sai da ya shafe mintuna nasu dama kafin ya fito,tamkar wanda yake sauya fatar jikinsa. Lokacin daya fito din ya samu na'ura na gaya masa yana da baqi a living room,ya kauda idanunsa da suka dan canza launi sakamakon shigar ruwa cikinsu ya mayar ga madubi yana qoqarin tsane sumarsa data jiqe da ruwa,abu guda daya tak da zai fara gaya maka shi din ba asalin bahaushe bane,yana da jibi da wani yaren da aka sansu da irin wadan nan sumammakin. Kamar babu wanda yake jiransa haka ya kammala shirinsa a nutse cikin wasu farare qal din pajamas,ya zura dogayen qafafunsa wadanda kamar basa taka qasa cikin wasu lausasan baqaqen flip flops,sannan ya kwashi wayoyinsa ya wuce zuwa living room din. Mutum biyu ya samu a zaune,daya yasan da zuwansa,dayanne baiyi tsammanin zuwan nasa ba a dai dai wannan lokacin. Dukkansu suka miqe,daya matashin dake sanye da wata danyar shadda getzner daketa faman maiqo da qyalli ya miqa masa hannu kai tsaye sukayi musabaha,cikin salon da kana kalla zakasan akwai sanayya da shaquwa me qarfi a tsakaninsu,duk da fuskar dayan bata nuna hakan ba,har yanzu dai tana nan a yanayinta na dazu,daurewa da kuma rashin walwala. Matsowa daya matashin yayi,cikin girmamawa ya russuna "Barka da yamma" kai yadan gyada masa sannan yace "I hope ka karbi komai kamar yadda nace?" "Eh na karba,but yace na gaya maka....." Kasa qarasawa yayi yana dan sosa kansa kadan,a nutse ya zauna,ya kuma zuba masa idanu bayan ya dora qafarsa daya akan daya,yayi relaxing sosai cikin kujerar,abinda ya sanya musaddiq ya sake diriricewa kenan,ya kuma yi nadamar karbar saqon peter "Idan baka da abun cewa get out,i don't have time to wasted" salin alin musaddiq ya sanya kai zuwa waje,don bayajin zai iya qarasa fadin saqon,kwarjininsa yayi masa yawa,yana saka kai zai fita,daya daga cikin ma'aikatan dake aiki a restaurant din dake hotel din ya sako kai dauke da dukka nau'in kayayyakin buqata naci da nasha,wanda daya daga cikin aikin ma'aikatansa ne wato jibril,he's very serious akan dukka abinda yakeso,kafin ya fada anyi,wannan ya sanya yake ji dashi matuqa,baya kuma rabo dashi duk inda zashi. Tsaf aka shirya komai,jibril kuma ajjiye masa wanda zaici a dining room,sannan ya sanar masa "Saina gama da mr isaac first,but before....." Sai ya waiwaya gareshi "Kana da buqatar wani abu ne?" Kai ya girgiza "No,banajin gaskiya" "Okay,i will be back,zan sallamesu......ban cup daya na coffee" ya buqaci hakan. A duniya idan ka cire mahaifinta da yayyenta maza guda uku da Allah ya bata,babu wata sauran halitta ta d'a namiji data yarda dashi,babu wani d'a namiji da take masa kallon me imani,babu kuma wani d'a namiji da take dubansa a mazaunin nagartacce,dukkansu tana aunasu ne kan mizauni guda,ma'auni guda da kuma dabi'a guda daya,suna kuma tafiya ne a nata ganin kan tafarki guda. Su biyu ne cikin motar kan hanyarsu ta dawowa daga shopping ita da ya zaid,suna tafe a hankali yana qoqarin cusa mata ra'ayin aikinta,ta bashi aron kunnuwanta kawai,bawai don tana jin qaunar abun ya shigeta ba,abinda ta lura dashi dukkansu suna supporting aikin,suna kuma so tayi,ta karanci a nasi ganin suna hasashen hakan zai rage mata zaman kadaici ne,yayi attaching nata sosai da mutane,ya dawo mata da dukka yarda aminci da walwala da kuma mu'amalarta da kowa yadda take a baya. Signal din da taga ya saka yana niyyar shiga guda abdullahi road bayan suna kan hanya dai dai shi yadan ja hankalinta "Yaa zaid.....ina zamu qara zuwa?" "Oh my goodness" zaid ya fada yana dariya harda dukan sitiyarin mota "Anya zancan afifa bai zama gaskiya ba?" Saita waiwayo da hanzari "Da tace me?" Yadda ta tambayeshi da sauri tana narke fuska ya sake bashi dariya "Tsoron duka mutane kikaji,you didn't trust anyone". Tabbas gaskiya afifa ta fada,idan kai tsaye akace ta tsani maza ba'a yi mata qarya ba,ita kadai tasan abinda ta fuskanta,wani abun bazai fadu ba. Sai taji zuciyarta ta tabu,har hakan ya bayyana baro baro saman fuskarta,ya zaid yadan juya kadan ya kalleta kafin ya maida hankalinsa akan tuqin da yakeyi,cikin sigar lallashi da kwantar da murya yace "Ba duka aka taru aka zama daya ba,dole duk runtsi duk tsanani akwai mutane na haqiqa,akwai nagartattu fiye da tunaninki,akwai masu soyayya saboda Allah,suke kuma nemanta ido rufe,banason wannan kudin goron da kike mana,saboda saka hakan da zakiyi a ranki zaiyita hunting dinki to the rest of your life idan har baki canza ba" "Bazan maka musu ba ya zaid,amma I doubt gaskiya" ta fada da karyayyar zuciya da kuma karyayyar murya,har taji kaman hawaye suna tsatstsafowa daga qwayar idanunta. Murmushi ya saki kadan,baisan ta yadda zasu sauya tunaninta ba a kullum,amma suna fatan watan wataran HASKE zai bayyanar mata. Yasan duk yadda zai kwatanta mata a yanzun babu lalallai ta miqa hankali nazarinta da tsinkayenta zuwa wajen,don haka ya rufe chapter din ya dauko wani batun na daban,saidai ya riga ya karya zuciyarta,ta kasa sakewa. Riqe da glass coffee mug din a hannunsa da yake kurba time to time,yana zaune daya daga cikin kujeru hudu dake gurin,sauran biyun baqinsa ne a kai,idanunsa akan takardun dasu Mr Paul suka gabatar masa yana irga adadinsu da idanunsa ba tare da yakai ga tabasu ba. A nutse ya ajjiye mug din yasa hannu ya rufe file din "We will contact you after two weeks" kai suka jinjina cikin fara'a suka miqa masa hannu,saidai kafin yakai nasa hannun muryarta ta ratsa dodon kunnensa "Hi......" Ta furta, cikin qasa da second biyar kuma ta bayyana a gabansu. Dukka su ukun suke kallonta,saidai kowannensu da irin kallon da yake mata,mr isaac da Mr Paul kallo suke mata na zallar burgesu da tayi,kyawunta kuma ya ratsa har cikin jininsu,yayin da nasa idanun suka cika da tsananin bacin rai da haushi mara misali. Idanunsa ya janye daga kanta ya miqa musu hannu sukayi musabahar da basuyi din ba,sannan ya miqe yasa hannu daya ya dauki mug dinsa,daya hannun kuma ya fara danna wayarsa yana son kiran jibril yaso ya shiga masa da file din. Cikin second kadan ya iso,ya masa nuni da takardun,yasa hannu biyu ya dauka ya wuce dasu. Tana tsaye a gurin,ta zuba masa dukka idanuwanta,tana jin wata mahaukaciyar qaunarsa tana tasiri a jikinta da zuciyarta,tana jin kamar ta taka da gudu ta rungumeshi cikin jikinta,ta kwantar da kanta saman ingarman qirjin nan nasa,ta kuma shafi gefan fuskarsa dake dauke da lallausan gashin da tana iya hango gyaran da yasha ya kuma kwanta luf. Saidai inaaaa,tasan hakan shine babban kuskuren da zata tafka a rayuwarta,tasan wayeshi qwarai da gaske,ko a yanzun ma tana cin albarkacin wani abu ne,tabbas!,da bata isa ta bibiyeshi har haka ba. Ganin ya fara barin inda take din ba tare daya nuna wata alama na sanin wanzuwarta a wajen ba yasa itama ta cira qafarta dake sanye da high heels ta fara binsa "Hello" ta gada da muryarta mai yauqi,shuru ba amsa,wannan ya sanya tadan qara daga qafa "Muhammad" tayi kiransa da ainihin zallar sunansa. Shi kansa a karan kansa yasan girma qima da martabar me asalin sunan,mahaifinsa ya dauka ya bashi shi,zaiyi wuya ka kirashi da sunan zalla ya iya tafiya ya barka a guri saboda girmamawa ga sunan kansa,batasan hakan yana masa tasiri ba,tana kiransa ne kawai duk sanda taji nishadin kiran nasa da sunan nasa. Ya tsaya cak,har zuwa sanda yaji qarasowarta bayansa dab dashi,cikin deep voice dinsa yace mata "Ki juya ki koma inda kika fito" "Saboda me?,don kai fa nazo" "Ba matsala bace......i said ki juya ki koma inda kika fito,if not....." Maqale hannayenta tayi a qirji,alamun gargadinsa ko a jikinta "Idan nace a nan zan kwana fa,kuma a kusa dakai?" "You are mad,ki gwada ki gani" ya fada yana jin zallar tsanarta tana shigarsa,cikin second kadan tasa kansa ya fara ciwo,duk duniya ita daya ta isa ta tsaya haka a gabansa a matsayinta na MACE ya fada sau daya ta maida masa,ita dimma tana cin wata daraja ne guda daya,sai ya fara yin gaba ba tare daya waiwayo ba. Baisan daga ina ba,baisan ya akayi ba......saiji yayi an masa wawar runguma ta baya,he was shock beyond the words,bai taba zata ba bai taba kawowa ba,bai taba tunani haukan LABIBA yakai haka ba. Wani irin mahaukacin fushi ya yunquro masa,yana waiwayo ya zube mata yatsunsa guda biyar saman fuskarta. Hannu bibbiyu ta saka tana dafe dukka kuncinta guda biyun hadi da rintse idanu tamkar ita aka mara bayan ta saki wayar hannunta da take dannawa don rage tsahon lokacin jiran yaa zaid,sai kuma ta bude idanun nata a hankali tana laluben daga inda wannan zazzafan marin ya fito,dai dai lokacin da ya fara magana cikin deep voice dinsa data cika da tsananin fushi "Shashasha wawiya, I can't tolerate it, next time kika sake gwada irin haka kiyi tsammanin abinda yafi haka" yayi wurgi da mug din hannunsa ya hadu da qarfen dake riqe da fitilun gurin ya tarwatse,baiko bi ta kansa ba ya wuce yana taku da sassarfa duk da hakan kuma majestically. Mutuwar zaune sãahar tayi,kunnuwanta suna bitar mugayen maganganun da yanzun nan kunnuwanta suka saurara,duk da cewa bataga fuskarsa da kyau ba amma muryarsa ta fita clearly kamar a gabanta yake maganar,a hankali kalaman suka fara mata suya a qirji tamkar ita aka gayawa,me yasa maza suka raina mata?,itace tambayar data dinga yi mata sukuwa cikin tsakiyar kanta,idanunta nakan labiba data sulale a gun tana kuka,kukan nata ya dinga taba sãahar,ta lumshe ido tana jin kamar ita ya zaga. Me tayi masa ne da har zai daga hannu saboda zallar rashin sanin darajar mace ya zabga mata irin wannan marin?,bata iya shiga abinda babu ruwanta ba,da ta qarasa ta daga labiba data zube a gun tana kuka sosai,ta bata haquri tare da bata shawarar ta manta dashi koda ba zata iya rama abinda yayi mata ba. Kasa jure sautin kukan nata tayi,saboda yana son taso mata da nata tsohon ciwon,don haka ta miqe a gaggauce ta zagayawa zuwa inda yaa zaid ya ajjiye motarsa,tayi amfani da key din daya bata ta bude motar ta shige tana maida numfashi ranta a matuqar jagule. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 11 A gaggauce yake komawa cikin hotel din cikin sassarfa da wani irin bacin rai kwance saman kyakkyawar fuskarsa da bata da annuri tun asali ko kadan,jibril dake biye dashi yana maida qafarsa duk inda ya ajjiye,tabbas yasan yau an taboshi fiye da ko yaushe,saidai baiga laifin fushin nasa ba,don shi kansa yarinyar ta fara gundurarsa bare kuma shi da ake bibiyar. Suna shiga lobby ya waiwaya ya dubeshi,zuwa sannan fuskarsa harta fara yin ja,musamman hancinsa,abinka da farar fata "Ka kiramin dukka wadanda muka shigo wajen nan tare,su sameni a living room now!" Yana fadin haka ya qara sauri ya wuce zuwa elevator. Da sauri matashin daya bari zaune cikin living room din ya daga kai yana dubansa,yasan yana da matuqar zafi da rashin fara'a,amma yana saurin gane canzawarsa idan wani abun ya sameshi,kamar dai yanzun daya kasa zama,sai iska mai zafi da yake furzawarwa daga bakinsa "What's going on?" Ya jefa masa tambayar yana binsa da kallo,kai ya girgiza masa ba tare da ya iya ce masa komai ba "Come on please,take it easy mana man" yayi maganar yana sauke qafafunsa dake harde qasa,tare da yunqurin cooling temper din da hanga cikin idanunsa,dai dai lokacin da aka nema izinin shigowa living room din. Dukkansu suka dinga shigowa daya bayan daya,kowanne a yanzu wasu kayanne a jikinsa ba baqar suit din dazu ba,da alama kowanne yana dakinsa ne yayi shirin kwanciya. Da wani zazzafan kallo ya bisu,dakin ya dauki shiru na wasu yan daqiqu,sannan ya buda bakinsa da zuzzurfar muryarsa data qara nauyi saboda bacin rai "i regard one of you was betrayal" yayi furucin da gasken gaske,babu alamun sassauci ko wasa ko kadan saman fuskarsa. Tsit dakin yayi,jikin kowa ya amsa,aka rasa me motsawa bare ya bashi amsa "Who told her I was there?" Dif dakin ya sakeyi,yayin da yake sake bin fuskarsu da kallo daya bayan daya,yana hucin bacin rai yana fita daga fuskarsa,ya dauke kansa daga dubansu,ya maida hannayensa cikin aljihun wandonsa ya soma takawa a hankali zuwa gaba "I will not repeat my question....." Ya fada bayan ya basu baya "Nine" daya daga cikinsu dake rakube acan gefe ya fada,zufa tayi wani irin wankeshi,yasan sakamakonsa,babbar asarar ce zata sameshi wadda ba lallai ya maida gurbinta,sai ta ninka abinda ya samu daga gareta bayan dogon lallashin data masa ta ciyo kansa ya shaida mata sun sauka a bristol din. A nutse ya waiwayo ya kuma zuba masa idanu,zuciyarsa tana tafasa "All this while......." Sai kuma ya kasa qarasawa saboda bacin ran dake sake taso masa idan ya tuna yadda ta rungumeshi,yanajin kamar ya zauna ya daye fatar wajen,ko ya maido da lokacin ya goge faruwar hakan "You're fired!" Ya fada kawai bayan ya duqa ya dauki wayarsa yana nufar qofa "Anyone who deliberately does what he has done deserves to be fired from his job" statement dinsa na qarshe kenan,yasa kai ya fice daga dakin ba tare daya sake waiwayar kowa a cikinsu ba. A nutse saurayin SAJJAD ya miqe yabi bayansa,yana shiga dakin shima yana sanya qafarsa "Me kake aikatawa ne TAUFEEQ?,firing a person from work is not a joke" "Did I tell you I was kidding? I really mean what I said,i dismissed him,idan kuna tunanin wasa ne na ganshi cikin maaikatana gobe" yayi maganar yana bude fridge,ya cire ruwa me sanyi ya balle murfin gorar yana tuttulawa cikinsa ba tare daya nema koda cup ba. Da kallo SAJJAD ya bishi,tabbas shan ruwa me sanyi sam ba dabi'ar taufeeq din bane,idan kaga hakan ya faru to alamu ne na tsananin bacin ransa,ko meye zai gaya masa a yanzun bazaiyi tasiri ba,sai yaja qaramin tsaki "since that's how you choose to be,sai kaci gaba,sai da safe" "Ka sallamesu ka rufemin qofofina" ya fada masa a taqaice yana cillar da robar ruwan gefe,ko a jikinsa na fushin da sajjad din yayi,bazaita zama bai takawa yarinyar burki ba ita da duk wanda yake bata information na wanzuwarsa a waje ba,tabbas muddin akaci gaba da haka to babu shakka watarana zata zubar masa da mutunci kima da kuma martabarsa,tunda har ta farajin takai hannu jikinsa,the worst part ma a waje na jama'a irin wannan,daya daga cikin dalilan da yasa yake sake tsanar mata a ransa,zasu iya yin komai.......zasu iya aikata komai da gajeran tunani da qwaqwalwarsu. Qarar wayarsa ce ta dakatar dashi,ya fidda hannayensa daga aljihunsa ya taka a hankali zuwa inda ya ajjiye wayar,kiran dake shigowa ta cikin wayar me muhimmanci ne,ya ajjiyeta ne kawai saboda ire iren kira masu muhimmancin da suka shafi family dinsa. Wani abun mamaki qaramin murmushin daya ratsa murtukekkiyar fuskarsa har labbansa suka motsa,wani irin sirrintaccen kyau ya bayyana kan fuskarsa,ya dauki wayar yana daga kiran "Daddy" siririyar muryar qaramar yarinyar ta bayyana cikin wayar,ta kuma ratsa kunnensa,ya lumshe idanunsa ya budesu a hankali,yana jin duk wata damuwa da bacin ransa suna narkewa "Daddy's angel" ya maida mata a tausashe "Wai da gaske kazo?" "Ki fara gaisheni tukunna" ya gyara mata bayan ya bude dukka idanunsa yana kallon gabansa "Good evening daddy" "That's my girl......kina lafiya?" "Lafiya lau daddy,da gaske kazo?" Gyara zamansa yayi ya zauna sosai sannan ya amsa mata kanshi tsaye,don bai saba yi mata qarya ba,bare ma kwata kwata shi din yana cikin jerin mutanen da komai tsanani komai wuya basa barinsa yayi qarya,tun daga yarinya har kawo yau,komai girman situation din da za'a shiga "Na dawo angel,but wani aiki ya riqe daddynki,i really miss you, I can't wait to see you,but in sha Allah gobe komai dare,you will be next to your daddy,please apologize me" dariya ta qyalqyale dashi cikin nishadi da siririyar muryarta sannan tace "Apology accepted daddy" "Thank you princess" ya fada cikin nuna kulawa. Sosai zakayi mamakin yadda ya saki jiki yana hira da ita cikin kulawa,a hankali kuma bacin ransa yana narkewa,ita din duniyarsa ce,wata qwayar halitta guda daya dake da mazaunin komai na rayuwarsa,baya wasa da dukka abinda ya shafeta,matsayinta da qaunarta a ransa ta zarta komai. Bugu da qari lalurar dake tattare da ita tana sake sanya masa wata qaunar yarinyar tare da mugun tausayinta,tattalinta da kuma bata dukkan kulawar daya kamata,idan ba tayi mugun takewa ba,baya bari ko kadan yayi nisa da ita. *_F R I D A Y_* K'arfe d'aya da rabi na rana suka fito daga town hall meeting,wanda ya sake maida kowanne ma'aikaci cikin nutsuwarsa,ya kuma girgiza zukatan duka wasu marasa gaskiya. Iya abinda aka tattauna a gurin kawai tsaiwarsa da yadda ya tsara abubuwa ya tabbatarwa da kowa ba wasa yazo yi ba,daga nan suka wuce sallar juma'a da dukkan Wani ma'aikaci musulmi,sannan ya sallami kowa da zazzafan gargadin haduwarsu da fara aiwatar da komai ranar litinin. Suit coat dinsa ya cire yana ratayeta,sannan ya jawo kujerarsa ya zauna bayan ya nade hannun rigarsa zuwa sama kadan,yakai hannu ya dauki drink din da jibril ya ajjiye masa yana duban mutum biyun dake zaune,ya tsaya ya saurari dayan ya sallameshi,sannan ya maida dubansa ga sajjad "Who is my new president?" "she didn't come" komawa yayi baya yayi relaxing jikin kujerar,idanunsa a lumshe yana jin kansa ya dauki caji da yawa "Is she a female?" "Eh" ya amsa masa yana kallonsa,don yasan anzo gurin,idanunsa ya bude tarwai,ya zubesu kan fuskar sajjad "A female president? why?" "it's dad's choice" shuru ya danyi,kamar bazai sake magana ba,sajjad ya kafeshi da ido,sai ya janye nasa idanun,ya janyo system dinsa yana budewa "If she is not ready to work with us, we will replace her with someone else,let her know,dole ta zama serious,ba zamu dinga biyanta tana abinda taga dama ba" "Za'a gaya mata,but wannan dogon statement din yayi yawa sir" ya fada yana bincika jerin sunaye da address phone number da email address na ma'aikatan dake hannunsa,duk wasu ayyukan ba nasa bane basa a wuyansa,amma sanin hali ya sanya abba ya hadashi dashi,yace kuma ya dinga zama by his side lokaci lokaci,yana monitoring wasu abubuwan,yasan taufeeq din da zafin kai qwarai. Bazai iya challenging daddy din ba,amma tabbas da ya sauya ta da namiji,matsayine da yake ganin mace sam ba zata iya riqeshi ba,koda zata iya din ma,zuciyarsa bata basu wannan amincin na riqe babban matsayi har haka ba,rashin amanarsu kadai ya sanya baya qaunar wani hulda a tsakaninsu,bare har akai ga zama na aiki da musayen ideas. Kwata kwata ma basu cancanci dukka wata mu'amala data qunshi aminci ba,yana musu kallon wata halitta ta daban,KUDI shine abinda sukafi bawa daraja kima mutunci da muhimmanci,zaifi kyau su tsaya iya nan. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/8, 3:54 PM] Maman Aslam: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 12 Tunda yaa zaid ya sauketa a jiyan abun yaqi barin ranta,kusan zata iya cewa dashi ta kwana,wanda ya haifar mata da wani irin bacci mara dadi,da mafarkai barkatai wadanda suka shafi wasu al'amura dake da alaqa da rayuwarta. Cikin dare ciwon kai ya saukar mata,wannan ya sabbaba mata makara a sallar asuba,kuma ko bayan tayi sallar wani baccin ya sake daukarta,sam ta mance da batun fara zuwa aikinta a yau,wanda dama zataje ne kawai don ta fara karantar yanayin yadda abubuwan suke. Kwata kwata bata tashi farkawa ba sai qarfe goma na safe,ta tashi da sauqin ciwon kan,ta miqe daga gadon tana shirin shiga toilet akayi knocking qofarta. Maama ce ta shigo,cikin kamalar nan tata wadda kusan a nan da wajen abba sãahar din ta gadota "Kina lafiya kuwa?" Tayi mata tambayar tana kallon qwayar idanunta tare da fatan ba damuwarta ce ta sake motsawa ba "Ina kwana maama" ta maida mata da gaisuwa "Lafiya qalau,kin tashi lafiya?" "Alhamdulillah,na dan tashi da ciwon kaine,bayan asuba kuma saina samu bacci" "Subhanallah,Allah ya sawwaqe,ko zaki asibiti?,banason zama da ciwo" ta fada cikin damuwa,saboda tasan yanayin ciwon kan sãahar din,baya yi mata da sauqi idan ya tashi,saboda ciwo ne da ya samo asali ta Wani dalili,ba hakanan ta sameshi ba "Alhamdulillah naji sauqi yanzu,wanka kawai zanyi na sauko" "To alhmdlh,yayanki ne ya dameni da waya tun dazu,yace yana kiran wayarki bata shiga ba" "Ya muhyi" ta fada kai tsaye,tasan yanason jin ta fita aikinne ko kuwa "Zan kirashi idan na fito a wanka" "To madalla,yayi" saita juya tana shirin fita "Abbanku ya fita,amma shima ya tambaya kafin ya fita din" "Zan kirashi shima" ta sake fada tana yunqurin zare rigar baccin jikinta "Don Allah maama,baba rabi ta kawomin ruwan dumi a cup" "Shikenan" ta amsa tana qarasa fita a dakin. Da ruwa me dumi sosai tayi wankan nata,ta fito fatarta na wani irin sulbi da qamshi daya hade da tururin ruwan dumin da tayi wankan,ta fito ta tsaya gaban mudubi tana kallon fuskarta dake subul kamar ta jariri,babu tabo babu komai,sai tsananin taushi da sulbi da take sakeyi,alamun product din da take amfani dashi ya karbeta. Tasa hannu ta dauki mug din ruwan dumin da baaba rabi ta kawo mata ta aje ta soma kurba a hankali,saboda muhimmancinsa a jiki bata skipping shansa kowacce safiya kafin taci komai,koda kuwa ta makara bata tashi da wuri ba. Da wani irin sauri sautin marin jiya ya gilma a kunnenta,ta runtse idanu kamar a sannan abun ya faru,ta cire cup din da takai bakinta a hankali ta ajjiye saman madubin sannan ta bude idanunta tarwai tana kallon fuskarta. Tsantsar rashin sanin darajar dan adam ta tabbata ga duk mutumin da zai iya shimfida yatsunsa akan muhallin da yafi ko ina daraja a jikin dan adam,wani abu yazo ya tsaye mata a wuya,ta saka hannuwanta biyu saman kuncinta,tana tuna wani lokaci can baya daya wuce,tana tuna marukan da tasha saman fuskarta,wanda batasan iya adadinsu ba. Sauke hannuwanta tayi taja da baya tana barin gaban madubin ganin bacin ran da bataso tana yawan ji yana qoqarin taso mata,sai ta koma gefan gadonta ta zauna tana hadiyeshi,idanunta suka sauka kan ledar siyayyarta data shigo da ita jiya,ta miqa hannu ta janyota,ta fara buda kayan ciki tana sake dubawa,bawai don batasan me ta siya din ba,a'ah tanason kore bacin ran dake taso mata ne. Sai data shirya kayan cikin walking closet dinta sannan ta fara gyara jikinta,ta shirya kanta cikin wata sassauqar gown fara,alamu suna nuna ita din ma'abociyar son fararen abubuwa ne,musamman kayan zaman gida da qananun abubuwan amfani irin haka. Cikin qasa da awa daya ta sauko qasan riqe da system dinta tana amsa wayar afifa,ta saka system din a chargy,ta leqa ta gayawa maama ta fito wadda ke saman abun sallah zata tayar da salatud duha(sallar walaha),sannan ta nufa kitchen ta samo abinda zata iya ci. "Barka da fitowa" baba rabi ta fada cikin girmamawa,tadan murmusa kadan,baba rabin ba zata taba daina gaisheta ba "Ina kwana?" "Kin tashi lafiya farar d'iya" suna ne da takan kirata dashi lokaci lokaci "Lafiya qalau,me zan samu?" Fara bude mata abubuwan da suke dashi da safen a kitchen tayi,kusan duka ba cimarta bane,amma batason bawa kowa aiki da safen nan,ita kuma qyuyar aikin yau takeji,don haka sai ta jawo plate ta tsakuri iya abinda take ganin zata iya a plate daya,ta fice zuwa Parlor din. Tana cin abincin kamar wasan yara ta kunna laptop din nata,gidan gaba daya ya mata shuru ba dadi,afifa bata dawo ba kwata kwata wannan satin,shi yasa takeson yara,bata rabo da dauko 'ya'yan yayyen nata,to wannan karon su fadil suna umra duka gidan,khalifa na exam,aleena tayi qanqanta don ko yayeta ba'ayi ba,ya zaid kuma ya maidasu na'eem canada,cikin satin nan shima zai bisu,dole ta zauna zaman kadaici,idan taji ta matsu da yawa kuma tabi afifa. Sai data gama duk uzurinta sannan ta shiga ma'ajiyar saqonnin email dinta da nufin share saqonnin da suke kai ko zata ragewa computer din nauyi,har ta fara marking idanunta suka kai kan sabon saqon daya shigo mata daga MT GLOBAL COMPANY,ta dan tsaya tana tunanin inda tasan sunan,kafin daga baya hankalinta yakai kai,takai arrow din kai tayi clicking ta shiga. Dogon tsaki taja bayan ta gama karanta abinda saqon ya qunsa,and so what don zasu canzata da wata muddin bata shiga aiki ba on Monday,ko an gaya musu aiki da su damuwarta ne?,ko basusan alfarma zatayi musu ba saboda darajar masu daraja?,cikin jin haushi ta soma rubuta musu reply na basu damar sanya watan,cikin ranta tana jin ta samu hanya mafi sauqi ma da zata sabule wannan alaqaqai din aikin,saidai tana kammala rubutawa kafin ta tura taji muryar yaa muhyi yana magana da masu aikin gidan dake harabar gidan,saita dora hannuwanta saman fuskarta tana jin ba dadi,a sanyaye tayi highlight na duka rubutu tayi cutting dinsa,ta goge email din ta sauka daga ciki,tayi shutting down na system din,dai dai lokacin ya sanyo kansa cikin parlor din. A nutse ta amsa sallamarsa,tayi masa barka da safiya sannan ta miqe ta yiwa maama magana,ta kuma wuce kitchen ta hado masa dan abin motsa baki,ta kawo ta ajjiye masa "Ya na ganki gida,nayita kiran wayarki kuma bakiyi picking ba,kada dai ace tun ranarki ta farko kin fada wasa da aikinki?" Yaa muhyi ya fada yana kallonta hadi da dan kada key din hannunsa. Fuskarta ta tattare tayi alamun tausayi ta zauna daga kujerar dake gefansa "Da ciwon kai na tashi yaa,kuma ma Allah......" Kasa qarasa masa tayi,tadan lanqwasa yatsun hannunsa "Eheenn,Allah me?" Ya tambayeta kai tsaye yana dubanta bayan yadan tsuke fuskarsa kadan,don bayason jin wani zance sabanin wanda sukayi da ita "Yaa ko zaka taimakamin su sauyamin position din da suka bani,bana son president din nan wallahi" ta qarashe fada tana narke murya. Ajiyar zuciya yadan sauke yana furzar da iska daga bakinsa sannan ya sake maida dubansa kanta "Dr yana da matuqar kirki da sanin ya kamata,haka d'an nasa,yana da kamewa da sanin ya kamata,na tabbatar ba zaki taba fuskantar wata matsala wajen yin aiki dasu ba,inda nasan akwai matsalar kema kin sani,bazan karba miki ba,so please accept it,kiyi aiki tuquru,ko don saboda ni" qas tayi da kanta,tanason tilastawa zuciyarta da har yanzu taqi jin nutsuwa aminci wa aikin kan ta karba buqatar dan uwanta,sake gyara zamansa yayi sannan yace "Shi da kansa Dr yin ya zaba miki position din,ya fimu shekaru da hangen nesa,yana ganin kin cancanta ne,ko abba dana gaya masa baice wani abu ba,kuma koni din nasan you can do it,so please kada kiyi discouraging kanki,you will made it in sha Allah" Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya qasan ranta,bai fahimceta bane,bawai ba zata iya bane,ita sam harkar da duk zai hadata mu'alama da jama'a ne bataso. Ganin ta shiga tunani sau ya katse tunanin nata ta hanyar miqa mata key din mota "Gashi,gift na fara zuwa aiki,daga ni da kuma Saifullahi" hannu biyu tasa ta karba tana masa godiya,saidai sanda ta duba sunan motar sai da zuciyarta ta tsinke,motace sabuwar qira me kyau ta mata,tana kuma da dan tsada,lallai da gaske sukeso sai tayi aikin nan,zatayi addu'a ta kuma roqi Allah ya dafa mata,kada ya bata ikon watsa musu qasa a ido. ***********Duk daga inda ka daga kanka cikin layin,daga farko ne qarshe gaba ko baya na layin kana iya hangen katafaren ginin mansion house din daya amsa sunansa ta kowacce fuska a idanun me kallo,saidai daga ainihin cikin zuciyar gidan akwai naqasu me tarin yawa a ciki,birnannen tarihi da memories masu daci tsananin quna da soya zukata,memories da suka dakushe jin dadi da walwala mafi rinjaye ta dukka mutumin daya shafi gidan,gefe guda kuma akwai wani boyayyen muhimmin al'amari wanda yake sarrafa duk wani motsi da rayuwa ta al'ummar gidan. Idan nace al'ummar gidan kada ka dauka wasu jama'a ne masu yawa,a'ah......dai daikun mutane wanda rayuwa cikin gidan ga zame musu lazim. Kamar kowanne lokaci,qarfe takwas da wasu mintuna na dare,lafiyayyun hamshaqan motocin nasa suka tsaya babbar gate din gidan me kama da qofar masarauta ko shiga wata kasuwar duniya,cikin qasa da second biyar aka soma motsa qofar gate din bisa sahalewa da sarrafawar daya daga ckin security din gidan dake tsaron qofar,wanda ke tsaye daga gefe kusa da na'urar dake tura gate din cikin uniform din da dukka ma'aikatan gidan suke amfani dashi,wato baqin wando da farar riga,sai baqar hula me kama da hular 'yan sanda. A nutse suka kutsa kai lafiyayyar harabar gidan me matuqar girma da tsari,wadda aka qawatata qwarai da shuke shuke,fitilu masu tsananin kyau da haske,da kuma ainihin fuskar gidan dake manne da wasu gilasai tamkar dasu akayi bangon gidan. Tun daga harabar tsarin gidan zai fara tafiya da imaninka,tsaftatattun tsirrai masu bada wani irin iska qamshi da koke koken tsintsaye daban daban,wasu siyansu akayi aka ajesu don bawa gidan dukkan ni'imar data kamata,wasu kuma daga Allah ne,sukanzo su wuce,kosu samawa kanau gurin kwana cikin tsirran dake wajen wadanda suka dace da tsarinsu,hakan sai ya sake qawata wajen,ya wadatashi da wani irin yanayi me sanyaya zuciya. A nutse ya fito daga motar kamar kowanne lokaci cikin tsananin kamewa da izza,yauqi da aji irin na hadaddun mazan da suke ji da kansu suka san kuma waye su. Yana sanye da wani yadi da aka samar dashi daga merino wool dan asalin qasar spain me asalin kyau da tsada,wanda wani qwararren telan ya zauna ya shiryawa dinki na zamani daya sake qawata yadin fiye da kima,ya kuma qawata kwalliyar mamallakin suturar. Yana daya daga cikin jerin mutanen dake da tsari da kuma zabi a dukka sutturar da zasu sanya,hakan sai ya cakudu da baiwar dacewa da kowacce shiga keyi da jikinsa,koda kuwa pajamas ya sanya,duk da wasu matan dake da qarancin kunya a idanunsu......sun sha gaya masa yana da kyau ne,hakanan komai nasa me kyau ne,wannan ya sanya kome zai raba a jikinsa yake dacewa dashi,ya kuma sake qara masa kwarjini da cikar haiba da kamala. Daya daga cikin yaransa ne ya matso da sauri yana masa bayanin wasu tarin takardu dake hannunsa,sai ya masa nuni da matashin dake tsaye a gefansa,yayi handing over dashi sannan ya taka a hankali yana nufar ainihin main entrance na gidan,ya barsu a wajen kowa yana qoqarin hattama aikinsa na ranar. Duk taku daya yana jin yana qara masa kwadayin isa gareta,zuciyarsa ce ita,rayuwarsa ce,hakanan farincikinsa. A nutse ya buda qofar lafiyayyen falon farko da zaka soma tararwa,falon da dukka kalolin kayan ado da qawa da aka zuba masa warm beige color ne da ratsin rusty red,tun daga manya manyan curtains na alfarma,kujerun da aka zuba carfet da aka malaleshi dashi ac da paint na ainihin bangon,hatta da frames dake parlor din masu dauke da ayatul kursiyyu falaq da nas da sauran ayoyin tsari color din dake jikinsa kenan,sai ratsin gold kadan a jiki. Iya dubansa tsaf ya qarewa falon,ya sanya qafafunsa a hankali ya saka kai ciki hannayensa cikin aljihun wandonsa yana ratsa falon,wani yanayi yana saukarwa gangar jikinsa har zuwa zuciyarsa,wasu emotions da baisan yadda zai raba kanshi dasu ba,yayita kokawa da kansa yana danne fushin dakeson motsa masa yana ci gaba da saka kai ciki. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/8, 3:55 PM] Maman Aslam: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 13 Wani Parlor din ya tarar wanda baikai wannan girma ba,duk da dama abinda ya rabasu da wannan din babbar qofar glass ne da zaka turata,sai kuma labulaye na alfarma da aka zubawa qofofin duka,saidai wannan Parlor din nashi kalar daban da wancan,don komai da aka shirya a cikinsa minty blue green ne da ratsin creamy white. Dan matsaici ne da bai cika girma sosai kamar wancan ba,amma ya tsaru yadda jiki da zuciya zasu samu hutu yadda ya kamata. Shima shuru yake babu kowa,saiya taka zuwa hannun damansa,ya yaye labulen daya sadashi da wani tsararrren corridor wanda ya qawatu da wasu gold leaf picture frames,fentinsa olive green ne saboda qarawa idanu qarfin gani,kalar kuma ta dace da wajen sosai daya qawatau da fitilu masu haske tarwai,sai flowers a maqale a kowacce corner daga jikin bango,wanda suke bada qamshi na musamman da kuma samun kyakkyawar iska fiye da iskar da na'urar bature dake kafe a wajen zata bayar. Qofofin dakunan bacci ne guda hudu a wajen,kowacce da dan taqi kadan daga qofar dake kusa da ita,biyu na kallon guda biyun,sai yaci gaba da takawa a nutse kamar mai nufar full length mirror din dake maqale a bangon qarshe na wajen,ya isa qofa ta qarshen dake daura da madubin daga hannun damansa,yasa hannu ya murda ya tura sannan ya shiga. A nutse yake qarewa dakin dake a tsaftace kallo,yana watsa idanunsa tare da laluben daga inda zai hangota. . Daga saman gadonta ya hangi tattausan bargonta milk color me matuqar taushi cure waje daya,ya zubawa gurin ido sosai,alamun motsin da ya gani shi yaja hankalinsa,ya daga qafa da wani irin hanzari ya isa bakin gadon,bai tsaya jiran komai ba ya sanya hannu ya yaye bargon take ta bayyana. Kyakkyawar yarinya ce da duka duka shekarunta ba zasu haura biyar zuwa shida ba,fara ce qal siririya sosai,gashinta me tsaho da sulbi yana daure tsakiyar kanta da wani siririn ribbon pink color,kalar riga da wandon dake jikinta kenan. Cure take waje daya,ta qanqame ilahirin jikinta kamar wadda taga wani mummunan abun tsoro,saidai yadda bakinta yake rawa kawai ya isa gaya maka ta hadu ne da mummunan zazzabi. Da hanzari ya haura gadon gaba daya,jikinta na rawa,lokaci daya tashin hankali da rudewa suka bayyana qarara saman fuskarsa tamkar ba ingarman namijin nan da yanzu yanzu yake shigowa cikin gidan ba,cikin takun dake cike da karsashi ba. "Ya salam......ya salam" ya fada fuskarsa na wani irin sauyawa,tare da rungumota gaba daya zuwa jikinsa yana fadin "Zazzabi ne a jikinki fadeela?,ina baaba rabi?" Ya fada yana lullubeta cikin jikinsa tamkar yana shirin maida ciwon jikinsa ne. Bude qofar dakin sai ya zama kamar amsar tambayarsa,kamilalliyar matar tayi sallama,wankan tarwada ce,sanye take da atamfa riga da zani,sai kakkauran mayafi data yane kanta dashi,hannunta dauke da carbi "A'ah lafiya?,me ya sameta?" Ta fada cikin nuna tsantsar kulawa,itama fuskarta na nuna zallar alhini tana matsowa zuwa bakin gadon "Yanzu yanzu na fita nayi sallah,na barta tare da julia tana qoqarin bata kayan bacci ta saka" baaba Rabi ta fada cikin tsantsar alhini tana qoqarin karbar fadeela daga jikinsa,saidai yaqi sakar mata ita "Itace sabuwar nanny din da aka kawo?" Ya jefawa baaba rabin tambaya yana kallonta da idanunsa da suka kada suka canza launi,cike fal da wani irin zazzafan bacin rai "Itace" ta amsa masa dukka hankalinta yana kan yarinyar,kafin yace komai aka buda qofar dakin aka shigo. Matashiyar budurwa ce 'yar qabilar yoruba,sanye da uniform irin na ma'aikatan kamar kowanne ma'aikaci dake aiki cikin gidan. Cikin mugun razana taja da baya tana sauke idanunta qasa,gabanta yayi masifar faduwa,dukka jikinta ya dauki rawa,cikin matuqar kaduwa ta sulale ta duqa a wajen "You are welcome sir" Idanunsa fal da masifa da kuma tashin hankali yake kallonta,ya zare yarinyar daga jikinsa ya miqawa baaba rabi ita,cikin harshen turanci ya fara magana cikin masifa tamkar zai bugeta,saika dauka bai cikin hayyacinsa "Kin fadi adadin abinda kike da buqata na kudi,nasa an biyaki amma hakan bai hanaki kiyimin sakaci da rayuwar yarinya ba?,zaki barmin ita har zazzabi irin wannan ya sauka a jikinta ba tare da kin sani ba,banga amfaninki ba,ki tattara komai naki kibar gidan nan,na sallameki" ba ita kadai ba data rasa aikin da tayi mugun saka a rai kanshi ba,hatta baaba rabi tayi mugun kaduwa da hukuncin nasa,julia itace me aiki ta goma sha daya daya kora cikin qanqanin lokaci,kwata kwata baya daukan sakaci akan yarinyar,komai qanqantarsa shi ganganci ne a wajensa,duka masu aikin basa wuce sati daya suke rasa ayyukansu,masu nisan zango ne sukeyin sati biyu. Yana da mugun kwarjini da haibar da bazaka iya tsaiwa roqonsa ba,don haka tana share hawaye cike da baqinciki rasa aiki me gwabi da tarin albashi me tsoka,da kuma fita daga daular wannan gidan,wanda iya cima da AC din dake karakaina a lungu da saqo na gidan kawai ta isa sanyaka ka mallaki lafiyayyar fata me sheqi,ba tare da kana amfani da mai ko sabulu ba. Wayarsa ya ciro a aljihunsa cikin hanzari yayi kira na wasu sakanni,sannan ya matsa da sauri ya dauke yarinyar cak daga cinyar baaba rabi ya rungumeta cikin jikinsa,ya juya cikin kamewarsa da fushi ya bayyana a tsakiyarta yana fita a dakin. A nutse yake takawa da ita zuwa sashensa,yana jin kamar ya maido ciwon jikinsa,tana ruqunqume dashi itama duk da zafin zazzabin jikinta,yana takawa idanunsa na sauya launi,wani abu da yafi kama da bacin rai yana motsa zuciyarsa,yana jin wata qaqqarfar tsana ta wata halitta na sake haifuwar sabuwar yabanya a zuciyarsa. Da hannu daya ya bude qofar bayan ya ratsa wani hadadden balcony da aka qawatashi matuqa fiye da tunani,kyakkyawan falo ne na alfarma wanda ya kerewa dukka falukan gidan,komai da komai na cikin falon,hatta da door mat dinsa kalar creamy white ne me matuqar daukan hankali da burgewa,fararen fitilu qal da suka haska falon tarwai kamar safiyar da aka tashi da tsananin hasken rana sun taka rawar gani wajen qawata falon,tako ina qyalli yake,komai fes qal kamar rai bata rayuwa a ciki,duk inda ka waiwaya sai kaga kamar zaka ga fuskarka. Ba abinda falon yake bayarwa sai Wani irin ni'imtaccen qamshi dake cakude da qamshin air conditioner din dake tsaitsaye a kusurwoyin falon yadda zata wadaceshi tako ina saboda girman da yake dashi. Tsaf ya laqume saitin kujeru biyu na alfarma,iya wanzuwarka cikin falon ya isa ya baka wata irin nutsuwa da kwanciyar hankali,saidai banda taufeeq wanda babu abinda ya sauya daga abinda yakeji cikin zuciyarsa. "Welcome sir" ma'aikatan dake aiki a sassansa mutum biyar dukka maza suka fada cikin rusunawa da kuma girmamawa,baiko amsawa kowa daga cikinsu ba,sai hannu daya daga musu alamun ya sallamesu,suka juya da daya da daya suka fice a parlor din bayan kowa ya tabbatar aikinsa ya kammala,jibril ne qarshe,ya zube files din hannunsa da komai da komai ya juya shima ya fice. Ta hannun damansa ya bulla wani matsakaicin hallway da aka qawatashi sosai shigen na daya sashen,ya tura qofar dake a wajen,babban bedroom ne shima da komai na cikinsa creamy white ne kamar falon,tsararrren gado dan qasar italia da yasha shimfidu da lallausan farin zanin gado saqar qasar dubai,qarasawa yayi ya kwantar da ita akai cikin tsananin tausayawa,shi da itan duka yana jinsu shi da ita tamkar marayan da mahaifinsa ya rasu kafin haihuwarsa,mahaifiyarsa kuma ta rasu ta barshi yayin haihuwarsa,yakanji duniyarsu tayi musu fadi kamar babu wani me jibantar lamarinsu,bawai don sun rasa masoyan dake nuna kulawa da soyayya mara iyaka a kansu shi da ita ba,a'ah.....akwai wani boyayyen abu,wani internal love da dukka su biyun suke buqata,wanda suka rasashi,kuma shine sila sannan musabbabiyyar jin wannan kadaicin dake lasar zukatansu ta can ciki. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 14 "Daddy" ta fada da siririyar muryarta da zazzabi ya jigata ta qara laushi ainun,Hannuwansa yaji ta kama ta riqe tsam,sai ya waiwayo ya kama hannuwan nata ya sanya cikin nashi,idanunsa suna canza launi saboda bacin rai da damuwa,ya miqa hannunsa zuwa gefen wuyanta don sake jin adadin zazzabin,har yanzu dai kamar dazun "Am sorry angel,yanzu likita zaizo ya dubaki,zaki samu sauqi in sha Allah" da ido kawai take binsa,ya durqusa a tausashe yayi kissing bayan hannunta yana sake riqe hannun nata da kyau,yanajin kamar ya maidata cikinsa. Qararrawar falo ce tayi qara dai dai sanda wayarsa tayi qara itama,ya fara duba kiran "Ku shiga dashi waiting room" ya fada a taqaice,sannan ya zare bluetooth din kunnen nasa ya ajjiye,ya sunkuya ya sake daukan fadeelan suka fita. Qaramin clinic ne da ya kasance mallakin gidan,wanda ke dauke da dakin magunguna,dakin jinya guda biyu da gadajensu,da daki guda na gwaje gwaje da sauran ayyuka wato mini laboratory,kusan duk wani qaramin ciwo da zai samu iyalin gidan a nan ake dubasu bisa jagorancin likitan gidan wato Dr anwar ko kuma Dr raheema. Dukkan wasu kayan amfani da suka shafi magunguna na clinic din ana yawan dubasu da sabuntasu qarqashin jagorancin likitan amana Dr anwar bisa kulawa da kuma qwarewa,zallar karamcin MT jarma ya shafe idanunsa,ya kuma bashi dukkan wani matsayi da martabawar da baya iya tsallake kiransa shi da dr raheema kowanne irin aiki sukeyi,matuqar bai wuce gaban tasu buqatar ba. Cikin lokaci qanqani ya gama checking dinta,ya soma hada allurai zaiyi mata "Yanzu yanzu zazzabin zai sauka in sha Allah,ba wani ciwo bane me zafi,don't bother sir" a nutse ya gyada kansa,dukka idanunsa da damuwarsa suna kanta. Mutsu mutsu ta fara yi,qaramin murmushin da bai shirya zuwansa ba ya kufce masa,yasan anzo gurin dama,muddin idanunta suka qyalla akan allura to yanzu zata daga hankalin kowa,a tausashe ya matsa kusa da ita,ya dagata cak ya sanyata a jikinsa,ya dora hannunsa saman lallausan gashinta yana shafawa a hankali "Relax angel..... relax,bazaiyi miki da zafi ba" ya fada yana tausasa muryarsa sosai,saita tsaya cak din,ta runtse idanu tana jin shigar allurar a jikinta,ta kuwa matseshi gam har aka gama. Da kansa ya isa dining room bayan zazzabin ya saukar mata,ya dudduba abinda cook dinsa ya dafa,ya zari plate ya debo dai dai iyakar abinda yasan tanaci. Cikin tsantsar kulawa ya zauna ya dinga diban abincin da spoon yana bata,yana yi yana janye tab din hannunta,don daga saukar zazzabin har ta yiwa game dirar mikiya,tana masifar qaunar game,babu abinda yake bata nishadi kamar ita,idan ta kalleshi ta tabe baki zata sa masa kuka saiya kada mata yatsansa alamun a'ah. Yafi fahimtarta fiye da mahaifiyar data haifeta,ya gama haddace duk wani abu data fiso da wanda bai dameta ba,harma da wanda bataso,sai daya tabbatar ta qoshi sannan ya barta,ya miqa mata tab din yace mata zaije yayi wanka,ta gyada kai ta kuma waving masa hannayenta alamun bye "See you soon dad" qaramin murmushi ya fita a fuskarsa,ya kada mata nasa hannayen,sannan ya juya a hankali ya wuce bedroom dinsa,hankalinsa da tunaninsa yana kanta. Kayan jikinsa ya fara ragewa,yanayi yana kokawa da tunaninsa,hutu yake da buqata a yanzu,bawai tuna wasu tarkacen abubuwa marasa muhimmanci ba,tunasun da bazai haifar masa da komai ba sai zallar bacin da kwana cikin damuwa,damuwar da a wannan yanayin da al'amura suka cushe masa abubuwa sukayi masa yawa bashi da buqatarta,gobe ranar hutunsa ce,yana da buqatar ya wuni tare da ita,ya debe mata kewar data jima tanayi tasa. Babban towel fari qal ya daura iya qugunsa,faffadan qirjinsa dake cike da gargasa da murdaddun damtsensa ya bayyana sosai. *M O N D A Y* Tun qarfe biyar na asuba data kammala salla tana saman abun sallarta,koda ta gama azkar dinma saita samu kanta da sanyin jiki da kuma sanyin gwiwar kasa tashi tabar wajen,don haka ta buda qur'ani tayi tilawar wasu shafuka daga ciki sannan ta maida ta rufe. Agogo ta kalla,har yanzu akwai sauran lokaci kafin fitarta,sai ta jawo wayarta ta kunnata daga kashetan da tayi. Har yanzu cikin jikinta tana jin wani yanayi mara dadi,wanda duka baya rasa nasaba da fara fitarta aiki. Saqon barka da asuba daga wajen mahmud gana ta fara cin karo,ko da wasa bata taba gwada saving number dinsa cikin wayarta ba,to amma yadda yaketa binbininta,da yawan cikata da yakeyi da saqonni safe rana dare yasa ta fara shaida number din tasa a idanu. Qaramin tsaki taja,bata koda bari ta buda saqon taga cikakken abinda ya qunsa ba ta shareshi daga wayar tata gaba daya,kusan hakance take faruwa dama,duk sanda saqonsa ya shigo wayarta bata tsaiwa dubawa bare ta karanta,ta riga ta quna daga lamarin maza,batajin akwai wani abu nasu guda daya da zai burgeta,dukkansu a wajenta tamkar hankaka suke,gabansu fari bayansu baqi,kamar hawainiya dake iya canza ainihin launinta zuwa dukka launin da takeso,babu wani abu daga garesu da yayi saura wanda zai dauki hankalinta ko yaja ra'ayinta,tafi ganewa ita dasu din ya zamana kowa yana daga nesa yana sabgarshi. K'arfe takwas saura ta fito a wanka,tadan makara kadan saboda wani littafi data soma dubawa wanda ya dauki hankalinta har taso gota lokaci,babban towel ne daure ajikinta daya bayyana fararen fatar dake qirjinta zuwa bayanta da kuma sambala sambalan hannayenta. Gaban madubi ta tsaya tana tsane jikinta da towel,sannan ta saka hannu ta zare shower cap din dake kanta,take gashin kanta ya warwatsu a kafada da kuma gadon bayanta,ta ajjiye towel din,ta jawo wata qawatacciyat stool ta zauna a kai,sannan ta jawo cream dinta ta fara shafawa. Batayi nisa da shafan man ba kiran afifa ya shigo,wanda shi ya qara mata nauyin shiryawar,sai data cinye kusan awa guda sannan ta kammala komai. Ta fito d'as cikin wani atamfa me asalin tsada da taushi,wadda ta yane atamfar da wata tsadajjiyar laffaya ruwan golden yellow da brown,kalolin da suka hadu sukayi masifar fidda kyanta. Kanta irin daurin nan da ake kira zahra buhari ne,wanda ya baiwa gashinta data nannade damar fitowa ta qasa,tsadadden agogon rolex ne a hannunta da wani sisirin zobe me qananun fararen duwatsu masu walwali,ta zura fararen qafafunta cikin wani lafiyayyen takalmi me matsakaicin tudu qirar kamfanin gucci mahadin qaramar handbag dinta. Bata wani tsaya batawa kanta lokaci wai ta duba komai yayi perfectly fine ba ta fesa lallausan turarenta ta dauki wayarta ta fito. Kamar ko yaushe muddin bawai baqi ne dasu ba falon gidan nasu shuru yake,ta duba agogon hannunta taga dai dai yake aiki da na falon,saita maida dubanta ga dining dinsu. Dan qaramin murmushi ta saki,baaba rabi kenan,komai ta shiryashi cif,saboda tasan yau zata fara fita aiki,duk da cewa tasan ita ba ma'abociyar cin abinci bace koda rana tayi ma sosai bare yanzu da sassafiyar nan,don ko tara na safe batayi ba. Tana shirin bullawa sassan maama,idan bata sameta ba ta qarasawa wajen abba don tasan bata wuce can saiga baaba rabi "Allahu akhbar kabiran,dawisu gwanar ado,ummin abba uwar masu gidan,wannan kyau wannan kyau,hohoho" ba kasafai takeson wannan kodatan da baaba rabi takeyi ba,to amma ya zamewa baba rabin sara da dabi'a yabi jikinta,uwa uba kuma suna martabata saboda dadewarta dasu,suna bata wani girma na musamman "Barka da warhaka baaba" "Barka kadai uwarmu,an fito kenan,to ubangiji yasa a fara a sa'a,ya kauda dukkan abunqi,ya kuma kade fitina" "Ameeen ya hayyu ya qayyumu,maama fa?" Ta tambayeta har cikin zuciyarta tana jin dadin addu'ar da tayi mata "Ta shiga wajen alhaji" saita juya a nutse tana nufar can. Sai data tsaya ta ware igiyar takalminta a nutse tayi sallama ta shiga falon. Dattijon da fuskarsa me cike da kamala da kwarjini yana zaune cikin couch,hannunsa riqe da takardun qur'ani da yake zuwa pieces. A gefe ya ajiiye qur'anin cikin martabawa,ya daga kai yana dubanta tare da amsa sallamar tata,qaramin murmushi na fita saman fuskarsa,can qasan zuciyarsa kuma cike yake da fata,fata da buri me tarin yawa akan rayuwarta gaba daya. Daf da qafafunsa tazo ta rusuna har qasa "Barka da safiya abba" gyara zamansa yayi yana dubanta "Barka kadai ummin abba,an tashi lpy?" "Alhamdulillah abba ya qarfin jiki?" "Muna godewa Allah" "Allah ya qara lafiya da nisan kwana me amfani" "Ameen don nabiyyur rahmati,an fito aikin kenan?" Kai ta gyada a sanyaye "Eh abba" "To Allah yasa a fara a sa'a,yasa ya zamewa dukiyarki da lahirarki alkhairi,ki kare mutuncin kanki da kyau,don ke din ba yarinya bace qanqanuwa,duk da bani da haufi akan tarbiyyarki,amma dan adam saida tunasarwa da nuni,ki tsare gaskiya da amana,ki riqe aikinki da muhimmanci sai Allah ya dafa miki" "In sha Allah abba,na gode Allah ya qara girma" kafin wani a cikinsu yace wani abu an turo qofar falon an shigo,maama ce da afifa da alama wani saqon ta kawo mata suke magana akai. Tayi mamaki da taga afifa din,ta dauka da wasa take mata sanda tace ita zata zo da kanta ta kaita office a ranarta ta farko,ta duqa gaban maama suka gaisa,al'adarta ce ba kasafai take iya gaida babba a tsaye ba,musamman mahaifanta,saita juya ga afifa daketa kallonta,bakinta fal da magana,idanun su abba ne kawai ya hanata cewa komai,har zuwa sansa suka fito. Bayan sunyi addu'a sun shiga sabuwar motar sãahar din saita waiwaya tana dubanta "Bestie,kinga kyan da kikayi?,don Allah ki sassauta,karkije ki dinga hada ma'aikata fada a kanki" sosai sãahar ta tsuke fuska,saita sauke madubin gaban motar tana kallon kanta. Tabbas tayi kyau qwarai,komai data saka ajikinta ya haskata sosai,sai kawai ta sanya hannu zata balle murfin motar. Da sauri afifa ta tayar da motar tana dariya,saboda ta gama karantar abinda take da nufin yi "Kome zakiyi,ke koda kashi zaki shafawa jikinki hakan bazai hanaki yin kyau ba sayyada" harara ta watsa mata "Kinzo ne to spoiling my whole day afifa da maganganunki?" Ta fada manyan idanunta dake kan afifa kamar zasu fado. Kai ta girgiza tana dariya "Ni na isa?,kefa yanzu amanar mahmud ce a wajena" fuska ta tsuke sosai tana kallonta "Waye mahmud?,amanar me?" "Ba zaki gane ba,amma dole na kula dake don amana ba wasa bace" ranta ya sosu sosai,saidai afifa tafi gaban haka "Wai kasuwanci na kika fara afifa?" Dariya sosai afifa ta qyalqyale dashi har tana dan duqawa ga sitiyarin motar "Idan ma shi na fara aiba laifi bane,tunda hankalinki yaqi dawowa gangar jikinki har yanzu" rasa me zatace da afifa tayi,sai kawai ta dauke kanta ta maida gefe tana kallon hanyoyin da suke wucewa,hanyoyin kano da safe wandada suke da qarancin kai kawo na jama'a,maganar duniya afifa tayi mata amma 'yan miskilancin sun motsa,taqi koda waiwayowa bare ta tanka mata. ************* Kamar ko yaushe daya bayan daya motocin masu kama daya suke kutsawa kan titin da zai sadasu da katafaren kamfanin MT GLOBAL COMPANY,duk da cewa cikin combo suke,amma mota guda dayaa a ciki ta fita zakka,mercedes maybach s580 sand color dake masifar daukan hankulan jama'a duk inda ta gifta. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 15 Kofar tafkeken gate din kamfanin suka tsaya,kafin sukai ga sanar da isowar CEO OF MT GROUP OF COMPANY har jami'an tsaron dake kai kawo a qofar company din sun ture musu gate din gefe,sannan suka qame dukkaninsu suna sara musu har zuwa sanda suka gama shigewa tsaf,suka maida qofar suka rufe. Cikin nutsuwa da sanin doka da order dukkaninsu suka faka a matsayar motoci ta company din,saidai daga gefe guda dake nuna waje ne kebantacce saboda ajiyar ababen hawa na musamman,don akwai qarfen daya raba tsakaninsa da ragowar filin ajiyar motocin. Yadda motar ke daukan hankalin kowa haka ta dauki hankalin afifa data taqarqare a dazun tana zubawa sãahar bayanin da yasa takw kallon afifan kamar wata statue "Wai ta riqe amanar mahmud?,to shi mahmud qanin maama ne ko qanin abba?,yaushe ta karba amanar tasa da har zatayi mata roqon riqewa?,banda afifa duk duniya ba wanda ya isa yayi mata wannan zancan ta barshi tana kallonshi haka. Saida suka gama fakawa sannan ta maida dubanta ga sãahar "Kinga abinda na gani kuwa?" Ta jefawa sãahar tambayar cikin zallar mamaki,da kuma tafiya da hankalinta da motar tayi. Ido kawai sãahar din ta lumshe tare da budesu lokaci guda ba tare data amsawa afifa ba "Wow....wow.....mybatch vigil abloh fa?,kinsan mutum 150 ne duka duka suka mallaketa a duniya gaba daya?" "Zan iya tafiya?" Sãahar ta jefeta da wannan tambayar,cikin bawa maganarta rashin muhimmanci,saidai afifan ci gaba tayi da koro mata bayanin zallar tsadar motar da darajarta,sai kawai tasa hannu zata buda motar. Caraf ta riqo tsintsiyar hannunta "Don Allah ki barni naga wanne me sa'ar ne ya mallaki wannan motar,wanne DON dinne?" Idanu ta kafe afifa dashi tana mamakin qaunar da afifa kewa motar,already tasan halinta,she's a classy ladie,amma me yaja hankalinta haka?. Ido ta zuba mata tana kallon yadda ta natsu tana mata bayani tare da kallon sashen da motar take. A qalla an kusa kwashe minti biyar bayan fitowar duk mutanen dake cikin sauran motocin kafin motar ta bude a hankali ya kuma zuro jikinsa zuwa waje,zuwa sannan idanun sãahar nakan wayarta tana dannawar dole,saboda ta cika maqil da takaicin afifa data hanata fita,ga saukar yayyafi da aka fara samu siri siri,wanda ita kuma kwata kwata bata qaunar ruwa ya taba jikinta cikin shigar wata lafiyayyar suit ta zallar cashmere wool,charcoal color yake,idanunsa manne da baqin eye glasses,wanda zaiyi wuya ka iya ganin qwayar idanunsa,hannuwansa duka cikin aljihun wandon suit din,yana takawa da sassarfa sosai yana kuma magana a waya ta Bluetooth din kunnensa. "Tabarakallahu ahsanul khaliqeen,don Allah dago ki tayani ganin wani kyau a nan" afifa ta fada tana tabo hannun sãahar,tana kuma qunshe dariya a cikinta,ya tafi da ita matuqar tafiya,amma tanasl ne itama ta rama ta qunsa mata takaicin yin shuru da tayi sanda taketa babatun mata batun mahmud. A maimakon ta kalla inda afifa keson kalla saita kallo afifan "Na kalli me?,kedai da kika zabawa kanki ganin kyan dan maciji na d'a namiji ai sai nace miki bismillahi,Allah ya bada sa'a" ta fada wani fushi yana motsawa daga qasan zuciyarta,kai afifa ta girgiza "Ba haka bane sãahar,ban taba ganin irin wannan a zahiri ba Allah i swear,there was no denying that the handsome man was charming,he was elegant in every way Allah,don Allah ki kalla ki gani,zaki tabbatar ba qarya nakeyi ba" haushi ya sake qure sãahar,takaici da bacin rai yasa ta daga kai zuwa sashen da take roqarta ta kalla din,dai dai sanda yake wucesu cikin tarin ma'aikata zuwa main entrance na building din kamfanin. Siririn tsaki sãahar taja,ta kuma watsawa afifa harara "Wai me ya shiga kanki ne yau?,lallai ya zama dole na gayawa su maama suyi gaggawar aurar dake,tunda kin fara sumbatu" "Ba sumbatu nake ba,don Allah bakiga abinda na gani ba?,haduwa iya haduwa?,he was striking,no one could take their eyes off his good look" "To ina ruwana?" Ta fada tana jin ta fara hasala,sai afifa ta qwace da dariya,tasan tayi mata abinda tafi tsana a rayuwarta,zancan d'a namiji,kuma har ta zauna tana kodashi haka,duk sa cewa YES wannan din yakai ya wuce ma yadda idanun me kallo zai ganshi,yana da wani irin kyau me sanyi haiba da kuma kwarjini na musamman. Kafin afifa ta sake cewa komai sãahar ta buda murfin motar ta fice abinta "Zan wuce da motar,zan bayar a dawo miki da ita sanda zaku shiga lunch break" gyara yafen laffayarta tayi kawai,ta soma takawa a nutse zuwa ciki ba tare data amsa kota waiwayi afifa ba,yayin da afifan ke binta da kallo,murmushi na fita akan fuskarta. Komai na 'yar uwarta me kyau ne,komai na 'yaruwarta me aji ne,iyakar dukka inda mace takai ga aji da kyau takai,amma abu daya ya tsaida duniyarta cak,saita girgiza kai ta tashi motar bayan taga shigewarta building din. Cikin nutsuwa da kamewarta take takawa,a nutse kuma ba kai tsaye ba tana karantar yanayin kamfanin da kuma inda take takawar,tun daga wajen ta sake karantar girma da tsarin kamfanin,kusan kowa ya duqufa yana aiki sosai,tun lokaci baiyi nisa ba,amma kowa yana mazauninsa ya riqe aikinsa. "You are highly welcome madam" taji an fada daga gefanta,saita waiwaya a nutse. Matashi ne sanye da shirt da trouser lime green da baqi,yayi maganar cikin zallar girmamawa yana dan rusunawa kadan "Fourth floor zaki sauka,akwai ma'aikatan dake jiranki a can,zasuyi guiding naki akan komai" ya fada cikin girmamawa,saita jinjina kai ta kuma taka zuwa bakin elevator,ta danna ta shiga,tayi kuma selecting number din floor din da takeson sauka,sannan ta koma daya daga cikin corners din dake cikin elevator din ta goye hannayenta a qirji,idanunta qyar akan numbers din dake jere daga bakin qofar shiga na'urar, zuciyarta na fara ayyana mata ko yaya zamanta cikin wannan babban company zai kasance?. A second floor elevator din ya tsaya,da alamar akwai wani dakeson shiga shima,idanunta akan bakin qofar,har zuwa sanda ta bude. Fes ya bayyana daga gaban qofar,fuskarsa na kallon gefansa yana magana da wani cikin nutsuwa da kamewa,duk da cewa baka iya jin abinda yake fada,amma yadda yake maganar cikin izza da kamewa zai gaya maka umarni yake bayarwa. Yana gama maganar yayi taku biyu don isa cikin elevator din,karon FARKO idanunsa ya sauka a kanta,kamar yadda itama karon farko nata idanun suka shiga cikin nasa,tsahon tsaiwar da elevator din yayi sai a sannan ta dubi wanda ke bakin qofar da nufin shigowa ciki suyi tarayya na wasu sakannin da zasu kai kowa inda yayi nufin zuwa. Lokaci guda kuma a tare kowa ya janye idanunsa,ta kauda kanta gefe guda tana tsuke fuskarta,ta gane fuskar,fuskar mutumin da a dazu afifa ta cikata da zancansa,saita sake tsuke fuskartata,tana jin qyamatar hada guri dasu,kamar yadda takeji a ranta game da duk wani DA NAMIJI. Sanda taji anyi releasing elevator din ya wuce ba tare da an shigo ba sai taji mamaki kadan ya kamata,ta maida dubanta ga qofar taga taci gaba da hawa zuwa saman,saita yarfar da hannunta tare da tabe bakinta,ita dama hakan takeso,bata buqatar hada numfashi da jinsi irin nasu. Fitowarta daga ciki yayi dai dai da matsowar sajjad dake cikin aiki kace kace,amma Dr girema ya tasheshi takanas saboda ya marabci sãahar din,ya kuma tabbatar ya bata duk abinda take da buqata da zai sake jin ta gamsu da aikin da kuma kamfanin gaba daya. Kamar wancan data baro a qasa haka shima yayi welcoming nata,sannan cikin sanin kima da darajar dan adam daya sanyata tadanji zuciyarta ta saki kadan yace mata "If you don't mind......i will show you your office" kai ta jinjina kadan,yayi gaba tana biye dashi,sannan sauran ma'aikatan da suke qarqashin kulawar office dinta. Kusan kafin ya fita sai daya gabatar mata da komai da take da buqatar sani,tana zaune saman kujerar da sai da tayi addu'a sannan takai ga zama,ta bada dukka hankalinta ga bayanansa,abinda zai nuna maka zallar seriousness dinta,yanayin yadda kyakkyawar fuskarta ke a tamke ya isheka shiga taitayinka da tabbatar maka ba zata dauki wargi ko wasa ba,har ya kammala,saita dan lumshe kyawawan idanunta kadan sannan ta budesu "Inason a sanarwa suk department din dake qarqashin wannan office din akwai general meeting a gobe" "In sha Allah" ya fada sannan sukayi mata sallama suka fita don bata damar duba ayyukan da aka tsaya akai don ta dora. A nutse ta fara buda computer din dake gabanta,ta soma aika saqon email zuwa ga sauran department dake cikin kamfanin da sauran dukka board members,tare da introducing kanta,email guda daya daya rage zata turama,wani saqo ya shigo mata ta email,abinda ya janye hankalinta kenan ta shiga Wani aikin daban,sai kuma ta shiga binciken dame dame aka aiwatar cikin office din. Cikin qwarewa tare da amfani da zallar basira take sarrafa na'urar,da wani irin qwarin gwiwa da karsashi da batasan ya sauko mata ba. Ta kusan kashe awa biyu cur,kafin ta zame hannunta daga kan computer din,ta kuma maidasu saman fuskarta ta rufe fuskartata da kyau tana fidda numfashi me dumi daga bakinta. Ta fuskanci akwai jan aiki a gabansu,da kuma wasu al'amura na rashin gaskiya masu tarin yawa da aka aiwatar,wadanda sune suka taka rawar gani wajen kawowa company din naqasu da kuma koma baya,ta tura kujerar ta baya tana hade yatsunta da suka gaji guri daya ta lanqwasasu da kyau,dai dai lokacin kiran afifa ya shigo wayarta. Har ta saka hannu zata daga wayar saita fasa,ta jefawa wayar harara kamar itace afifa din,saita miqe bayan ta zare takalman qafarta,ta taka saman lallausan carfet din da zai sadata da qawataccen fridge din dake office din tana sake nazartar office din,komai an shiryashi base on her favourite colors,har ta soma zargin anya ba tare da yaa muhyi aka zuba furniture na office din ba?. Komai an tanadeshi,don hatta fridge din cike yake da kalolin drinks,ruwa kawai ta dauko,ta dawo ta zauna saman couch masu laushi da aka shirya daga gaban table dinta bayan ta dauko wayarta. Sms guda biyu ne suka shigo kusan lokaci daya,na afifa ne a sama,shi ta fara budewa _"I hope you are enjoying your work?,god bless you dear,All the best"_. Dole murmushi ya subuce mata,afifa ta wajenta,ayi dadi ayi tsiya,saita maida mata amsa a taqaice _"All is well bestie,thank you"_. Komawa tayi ta duba saqo na biyu _"assalam gimbiya,iam wishing you a joyful day,i hope you will remain blessed,fatan nasara,mahmud A gana"_ dogon tsaki taja kamar zata tsinke harshenta,saita goge saqon kamar yadda ta saba,ta bude gorar ruwan ta zuba a glass cup ta fara sha tana tunanin next abinda zata aiwatar. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/10, 2:28 PM] KYAUTA: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 16 Dogon tsaki taja kamar zata tsinke harshenta,saita goge saqon kamar yadda ta saba,ta bude gorar ruwan ta zuba a glass cup ta fara sha tana tunanin next abinda zata aiwatar. Tun daga sama zuwa qasa ta tsaya ta qarewa kanta kallo da kyau,tayi taku biyu gaba ta sakeyin taku biyu zuwa baya,taja rigarta baya kadan yadda zata dauki hankalin duk wani daka iya kallonta ko yakai idonsa kanta bisa tsautsayi ko kuma dace. Ta waiwaya kadan jikin wata qofar glass dake baka daman ganin fuskarka tamkar madubi,ta fito full hakanan dressing nata,saita saki siririn murmushi tana maida gashin kanta baya wanda tasa gantalallen scarf ta lullube rabin gashin dashi. A nutse ta koma ta zauna saman kujerarta ta zauna tana sake sakin murmushi,ita kadai tasan farincikin da takeji cikin ranta,tayi matuqar samun sa'ar da bata zata ba data zama secretary dinsa,bayan dogon hanyar da tabi me cike da tangarda kafin cimma muradinta. Tasan cewa a gata dukiya ilimi da kuma kyau na halitta da take dashi dukka tafi qarfin matsayin zama secretary,to amma....muddin akan MUHAMMAD TAUFEEQ ne,ta shirya zama massinger ma bawai iya secretary kawai ba. Maida qafarta tayi ta harde daya saman daya,ta bude computer din ta soma sarrafata. Cikin qasaita da izzar nan tasa data zame masa jinin jiki ya sanya kai zuwa babban office dinsa daya kasance na daya duk fadin company din,sauran ma'aikatansa da na biye dashi. Jibril ya buda qofar,dukka suka dataka ya fara shiga sannan suka rufa masa baya. Da sauri ta daga kanta tana duban qofar,saita miqe cikin sauri saidai kuma cikin salo na yanga da yauqin da take amfani dashi wajen farautar hankulan maza. Gabanta na wani irin faduwa,zuciyarta tana bugawa da qarfi sanadin ganinsa da tayi. Mamaki ya kusa daskarar da ita sanda taga baiko kallo koda sashen da take tsaye ba,tamkar ma baisan da wanzuwar wata halitta a wajen ba,dole ta tattare guntun iyayin kalamanta data tsara yi masa magana dasu,ta zare jikinta daga kujerar tabi sauran ayari zuwa cikin office dinsa gaba daya,gabanta na faduwa,tana fatan duk wani shiri nata ya dinga zuwa mata da sauqi fiye da yadda take tsammata. Kamar wanda tsaiwa ta zamewa dabi'a,ba kasafai ya fiya damuwa da zama saman kujera ba,yanzunma haka ce,daya bayan daya ya sallamesu,ya rage saura sajjad da jibril. Jibril din ya duqufa da duba wasu takardu,yayin da sajjad suke magana qasa qasa da ita,duk da cewa gaba daya hankalinta yana a kanshi,yayi mugun tafiya da ita,shigarsa ta yau ta dabance dake nuna aiki zallah. "Ehnnnn" ya fada a taqaie yana jingine da mulmulallen table dinsa dake tsare da files da suke jiran isowarsa,ya zuba duka hannayensa a aljihun wandonsa,yayin da yayi crossing qafafunsa. Da sauri jibril ya dago kansa,sannan ya fara magana "Sir,muna expecting ziyara daga gurin Dr at any moment" kyawawan idanunsa ya lumshe yakuma budesu a lokaci guda "Okay,the meeting has been postponed,a canza date zuwa gobe" "Zan sanarwa kowanne department" tayi caraf da zancan,ganin cewa dukka wannan abun aikinta ne,ita ya kamata ta sanar masa da kowanne tsari,amma jibril yana aiwatarwa,hakan na nufin ita 'yar kallo zata zama kenan?. Ta yiwa kanta tambayar da bata da amsarta. Har yanzun bai nuna alamun yasan da wanzuwarta a wajen ba,bare maganar da tayi,yaci gaba da magana da jibril ya sallameshi. Sajjad ma ya ajjiye masa dukka files din daya kamata ya juya ya fita,cikin zuciyarsa tausayin SAIMA yana kamashi,tabbas SON MASO WANI qoshin wahala ne,yayi imanin babu abinda zata tsinta daga wajensa face tsantsar bacin rai da kuma batawa kai lokaci,inda zata dauki shawararsa,abu daya zaice da ita,ta kama kanta,ta kuma kama martaba da kimarta ta diya mace,shine kadai abinda zaisa ta tsira a idanun TOUFEEQ din. Kujera yaja ya zauna har yanzu dai bai bata hankalinsa ko da na second guda ba,wannan duka bai sanya ta sare ba,ta tako zuwa gaban table din a hankali ta tsaya,dai dai sanda yake rubutu saman wani file "Sir.....akwai wani abu da kake buqata?" Tayi maganar tana dan zame rigarta kadan don ta bawa qirjinta damar fitowa,ko Allah zaisa ya daga kansa gareta,sai daya bude page din gaba na file din sannan ya fara magana,cikin muryar sa din nan dake cike da zallar qasaita da kuma izza "Banason yawan magana,bana kuma son shishshigi,kiyi qoqarin cire kanki daga dukkan abinda ban gayyatoki a ciki ba,karki soma wuce limit dinki,any moment kuma kamfani zai iya sauyaki idan aikinki baiyi ba,these are my conditions,you can go". Wani abune yazo ya tsaya mata a wuya,ta dan zuba masa ido tana jin sonshi yana ninkuwa a ranta,amma bata taba kawowa zaiyi mata irin wanna yankan qaunar da wuri ba haka,tasan halinsa,fes zai iya yanka mata jan card idan ta tsallake abinda ya gaya mata yanzun,dole ta miqe jiki a salube ta fita a office din,tana saqawa ranta abinda zai fishsheta,ba zata taba iya jure irin zaman da shi ya tsara zasuyi ba. K'arfe daya na rana zuwa biyu shine lokacin break na kamfanin,masu cin abincin rana da masuyin sallah ga musulman ciki,wannan kuma duk umarni ne na CEO,ya sauya fasalin abubuwa da yawa cikin sati guda a kamfanin,da yawan ma'aikatan abubuwan sun musu dadi,amma ga wadanda sharholiya kadai suka sanya a gabansu wasu abubuwan basu yiwa tsarinsu dai dai ba. Bata da ra'ayin zuwa kitchen,wanda aka tanadeshi musamman saboda manyan offices kamar nata,don haka ta umarci miss sameera ta samo mata coffee kadai. Ba kasafai take sakewa taci abinci ako ina ba,shi yasa ma baaba rabi taso shirya mata wani abun ta taho dashi,duk da tasan babu lallai ta maida kai taci yadda ya kamata. Cikin toilet dinta dake office din ta daura alwala,ta dawo corner ta musamman da aka tanadarwa office din don yin sallah,ta gyara lullubinta ta tayar da sallar. Kafin ta idar miss sameera ta dawo,ta ajjiye mata coffee din,ta koma ta tsaya tana jiranta ta idar da sallar. Cikin girmamawa ta matso bayanta kadan bayan ta idar "Akwai email da aka turo miki daga ceo office,kusan minti talatin kenan,ina kyautata zaton baki gani ba" kai ta gyada mata a nutse tana dubanta "Boss ne ya iso,yana office na ceo,he wants meet you" jim tayi na wasu 'yan mintuna,sannan ta maida dubanta ga miss sameera,kai ta gyada mata a natse,ita kuma ta jinjina kai ta juya ta fice. Fuskarta da daurinta ta gyara kamar yadda yake,kamar bata sanyawa fuskarta ruwa ba,tanana da qyallin nan da gogewar fatarta,saika dauka tayi amfani ne da powder. Ta gaban table dinta ta tsaya ta danyi sipping coffe din,bata ma iya shanyewa ba ta fito ta cimma miss sameera na jiranta a farfajiyar data fi kama da parlor wadda zata sadaka da office dinta. A nutse take takawa cikin shigar tsadaddar laffayar data lullube ilahirin jikinta,duk inda ta gifta sai tayi gaba da hankula da kuma idanun kaso mafi yawa na ma'aikatan kamfanin,walau maza ko mata,ko ina akwai shige da ficen ma'aikata,kasancewar lokaci ne na hutu. Ko daya babu wanda ta baiwa hankalinta,cikin kamewa da nutsuwa har suka isa qofar office din,mr sameera ta tura qofar tayi gaba,sãahar tabi bayanta. Wani irin katafaren office da babu irinsa kaf kamfanin,wanda ke dauke da sassa biyu zuwa uku,waitin parlor wanda saima ke ciki ita da tarin takardu da kujerun da aka qawata gurin,sai rest room daura dashi kuma main office din da zaka gudanar da ayyukanka. Idan ka kira office din da aljannar duniya akai tsaye sam bakayi laifi ba,saboda ya amsa sunan,wasu irin colors da design me matuqar tsari da aka qawata kowanne sashe na office din. Sallamar miss sameera ya sanya saima daga idanunta daga kan computer,maimakon idanunta su sauka kan sameera,sai suka fada kan sãahar dake qoqarin daga kiran daya shigo wayarta "Zaki iya sanarwa da sir isowar president?" Sameera ta yiwa saima tambayar,lokacin da ta tattara dukkan hankalinta akan sãahar da nata hankalin yake kan khalipha dake mata complain na tafiyar da tayi baya nan,lallausan murmushin dake masifar qawata mata fuska ne kwance saman fuskartata,har jerarrun fararen haqoranta da suka zama tamkar hasken lu'ulu'u suna fitowa,wani luguden abu taji ya saukar mata,tana da labarin dukka sabbin ma'aikatan kamfanin a yau zasu kama aiki kamar dai ita,tabi diddigin kowacce mace dake cikinsu,musamman wadanda ya zamana mu'amala zata iya hadasu da office din TOUFEEQ dinta,to amma ita din ita kadai tak! Ta kasa samun komai a kanta,ta gaza cimma wani bayani daya shafeta har zuwa lokacin data taka qafarta ciki kamfanin,sai yanzu,karo na farko "Excuse me,ko ta shiga ne?" Sameera ta fada cikin girmamawa da kuma zaquwar ganin yadda saima ta kasa amsa maganarta ta farko. Iska taja sosai a cikin hunhunta,ta qanqance idanu tana duban sameera,duban da zataso ace president din da kanta ta yiwa shi,saidai ba zatayi garajen aikata hakan ba,don batasan wace ita ba,kada ta aikata abinda zai zame mata matsala,ya kuma zama silar cisgeta daga bigiren data dora buri akai "Sir yana tare da babban baqo wato mahaifinsa,saidai ku dawo wani time din,kafin lokacin na sanar masa" tayi maganar tana ci gaba da dannan system dinta,dai dai sanda sãahar ta gama wayar,ta zameta daga kunnenta tana kallon sameera dake jiran ta kammala wayar tayi mata bayani. Kafin tace wani abu sãahar ta rigata "Thank you,na gode da rakiya,zaki iya komawa office" tayi maganar kanta tsaye tana kyakkyawar qofar da a samanta take liqe da takardar dake bayanin inane nan gurin ba tare data waiwayi saima ba. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/10, 2:28 PM] KYAUTA: *H U G U M A* _*TABARMAR ƘASHI*_💔 *Arewabooks: huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 17 Wani abu ne ya tasowa saima,yayi mata tsaye a wuya,ta riga ta saka hannu kan dokar yin biyya ga wanda yake sama da office dinka,me yasa bata nema matsayin president ba? "Neman kusanci da taoufeeq" zuciyarta ta bata amsa kai tsaye,ajiyar zuciyar baqinciki ta sauke,ta koma tayi relaxing cikin kujerarta tana qarewa qofofin guda biyu dake facing dinta kallo, zuciyarta na wani irin tsalle cike da luguden kishi,har tsahon wani lokaci toufeeq din zai kwashe kebance da wannan kyakkyawar halittar data bar mata sassanyan turarenta na yawo cikin dukka qofofin hancinta?. Cikin nutsuwa kuma dauke da sallama ta tura qofar office din. Kyakkyawan dattijone da shekaru sam basu samu nasarar ture kyakkyawan fuskar da Allah ya mallaka masa ba,fari ne sol,farin dake gwada tashen kyau da farin daya zuba zamanin quruciya,yana zaune saman sofa qwaya daya dake cikin office din,ya dora qafarsa daya kan daya,system dinsa na saman qafar tasa yana dannata cike da qwarewa. Cikin kamala ya waiwayo yana amsa sallamar tata,idanunsu suka gauraya,kwarjininsa da kuma kamalarsa suka cika idanun sãahar,yayin da murmushi ya wadaci fuskarsa "Lale maraba da 'yata,president dinmu" dattijon da shekarunsa suka suka rufa sittin ya fada yana sauke qafafunsa qasa. Da dan sauri ta daga kanta daga sunkuyar dashi din da tayi da farko tana duban dattijon duba na mamaki,ita dai zata iya cewa kaf rayuwarta yaune karon farko data fara ganinsa ma gaba daya,sani kuwa saidai na fatar baki kawai wajen yaa muhyi,to amma shi din ya akayi yasan wace ita "Daina mamaki diyata,kamanninki da d'ana muhyiddeen ta bayyana sosai a fuskarki....." Cikin girmamawa qaramin murmushi ya subuce mata,bata taba jin ance suna kama da yaa muhyi ba sai yau,tana shirin gaidashi ya tareta "Koma ki shiga resting room ku jirani keda d'an uwan naki" ya fada cikin kulawa. "Dan uwana?" Ta tambayi kanta cikin mamaki,waye cikin gidansu yazo company din ba tare data sani ba?,kodai yaa muhyi ne bai nutsu ba sai daya biyota?,bata sani ba,saita juya a nutse taja masa qofar ta fito. Qofa ta biyun ta dosa tana takawa a nutse,zuciyarta na qawatuwa da karamcin tsohon da kuma kirkinsa. Tsaiwa ta danyi kadan tana sauraren muryar dake fita daga dakin,wata irin husky voice me zurfi da wani irin amo,cikin fada da kuma tsawa muryar ke fita,saidai kuma a nutse sautin yake fita kuma a jejjere,cikin ginshiri da wani abu da yayi kama da QASAITA. Hannunta ta sauke daga kan handle din,tadan yamutsa fuskarta kadan,zuciyarta na mata fatan Allah yasa ba halittun maza aka tara a dakin ba,muddin hakan ta kasance bata jin zata iya dogon zama a tattaunawar tasu. Cikin bawa kai qwarin gwiwa ta sake dora hannunta saman handle din,kalmar da taji ta fita a bakin mamallakiyar fusatacciyar muryar me zurfi yasa ta sake dakatawa "You are fired,stupid woman" cikin qasa da second biyar qwaqwalwarta tayi mata rewinding,sak irin muryar da taji tana magana da wata mace cikin tsawa a bristol palace kwanakin da suka wuce,daga bisani kuma qarar mari ya biyo baya,qarar marin da ko a yanzun sai data sanyata rintse idanunta kamar a lokacin ake yinsa,ta kuma damqe hannunta abinda ya sanyata murda handle na qofar ba tare data shirya ba,saiji tayi ta tafi kai tsaye zuwa cikin dakin. Cak ta tsaya daga bakin qofar,idanunta yana nutsawa ga tsakiyar dakin. Kallonta bai sauka a ko ina ba sai akan budurwar dake sharban kuka,kyakkyawar budurwa wadda zubin dressing dinta ke nuna zallar iya gayunta da kuma wayewarta. Dauke idanunta tayi daga kanta tana jin zuciyarta na zafi,ta sauke a hankali a kansa. Tsayyayen namiji sosai mai cikar haiba izza da kuma kamala,hannunsa daya yana sanye a aljihun wandon suit dinsa,daya hannun kuma yana danna wayarsa da zafi zafi. Dai dai sanda yake sanya wayar a kunnensa ya juyo,idanunsu suka sarqe guri daya. A tare suka sake janye idanunsu kamar dai wancan karon,zuciyar sãahar cike da wani irin tsanarsa da kuma jin haushinsa,ko kadan maza basu da tausayi bare imani,suna amfani da raunin mata suna cutara musu,hakan wani karatu ne da take yawaita bitarsa a kwanyarta a duk lokacin da taga ire iren wadan nan rashin imanin na maza akan mata,saidai a yanzun shi din tamkar yana sake jaddada mata cewa haka tunaninta yake,karo na biyu data taba saninsa a rayuwa,amma duk sanda zata ganshi din cikin wulaqantawa da wofantar da kimar mata yake "Ka sallameta da albashinta na wannan watan,ka hada dana watan gaba,banason ka nemeni akan wannan issue din,case closed" ya fada da murkakkiyar fuskarsa wadda ko kusa batayi kama data mutumin daya taba gwada yin dariya ba arayuwarsa,ko da yake a wajen mutane da yawa da suka sanshi haka suke kallonsa,sukan tambayi kawunansu harma da abokan huldarsu "Wai shin yana dariya?" "Shin wai ya taba dariya kuwa?" "Ka taba ganin dariyarsa?". A nutse ta taka ta yiwa kanta mazauni saman daya daga cikin couches din dake zagaye da qawataccen dakin,wanda aka yiwa tsari me ma'ana da baiwa ruhi kwanya harma da zuciya hutu. Dai dai lokacin daya kammala wayar,a karo na biyu ya sake daga kai ya sauke sexy eyes dinsa a kanta,wani fushi ne ya sake taso masa,wacece ita da har zata shigo masa dakin hutawa a sanda yake da buqatar hutu ba tare da izininsa ba?,wacece ita da zata shigo dakin da ba kowa yake baiwa izinin shigowa ba,har ta yiwa kanta da kanta mazauni ba tare data nemi yardarsa ba?,me ta dauki kanta?,dukka wadan nan maganganun dake ransa,shigowar Dr mahmud JARMA ya datsesu daga kwanyarsa,sai ya maida dukka hannuwansa cikin aljihun wandonsa,ya tattara hankalinsa ga mahaifinsa. Sosai yake mata kwarjini da wani irin haiba dake bayyana a fuskarsa,don haka ta miqe tsaye sanda yake shigowar,cikin nuna girmamawa "D'iyata ina fatan ban bata lokacinki ba ko?" Kanta a qasa tana murza zara zaran yatsun hannunta,cikin siririyar muryar nan dake da wani irin taushi da amo tace "Babu komai abba" a hankali ya lumshe idanunsa yana zuqar numfashi da kyau zuwa hunhunsa,lokaci daya yaji wani abu me kama da rashin jituwa ya darsu a ransa,fitar sautin muryarta kawai yaji a ransa yarinyar batayi masa ba kwata kwata "I hate it" ya fada can qasa yana sauraren muryar tata sanda take magana da abban nasa a karo na biyu. Haka kurum yaji zuciyarsa tana zafi,sai ya koma a hankali ya yiwa kansa mazauni akan daya daga cikin kujerun da aka tanadesu domin hutawar,wadanda zasu bawa gangar jiki qafafu da kuma baya daman zama Sosai su samu nutsuwa. Yana jinsu sanda dr mahmud yake zama saman daya daga cikin sofa din dake dakin,har zuwa sanda yake umartar sãahar data zame ta zauna saman lallausan carfet din da aka ajjiye tsakanin kujerun "Tashi ki zauna saman kujera mana,wannan meeting ne zamuyishi tamkar sa'anni,bawai na uba da 'ya'yansa ba" yayi furucin sãahar din na sake shiga zuciyarsa,d'a'arta nutsuwarta da tarbiyya girmama na gaba data samu suna sake saka mata qaunarta tare da jinta a zuciyarsa tamkar TOUFEEQ dinsa. Murmushi ta danyi kadan,sannan ta koma saman kujerar kamar yadda ta buqata. A nutse ya waiwaya ya dubeshi,sai ya zuba masa idanu,yadda yayi kamar baya gurin da lumsassun idanunsa da eyelashes suka yiwa ado ya tabbatar 'yan halin sun motsa ko suna kusa,don haka yayi gyaran murya,ya kuma kirayeshi da sunansa na aihini "Muhammad" kiran sunan da ya sanyashi ware idanunsa a hankali,a nutse ya rabo bayansa da jikin kujerar,ya zauna sosai hadi da crossing qafafunsa dake sanye da wata shiny black socks guri daya "Ga khadijatou,itace sabuwar president na kamfanin nan da zakuyi aiki a tare,nake kuma fatan zaku kai kamfanin zuwa tudun mun tsira,inaso ka dauketa tamkar NADEEYA,infact....na damqa amanarta a hannunka kamar yadda yayanta na damqamin" idanunsa yadan lumshe kadan sannan ya budesu lokaci guda,yana jin maganar abban nasa wani iri,ba aiki tazoyi don a biyata ba?,ko raino aka kawota da za'a buqaci a bata kulawa?,kudi tazo nema fa,an yarda za'a biyata ita kuma ta yiwa kamfani aiki,fine.......ba shikenan ba?. "Na yarda da kaifin basirarta,na tabbatar kuma idan kuka hada gwiwa,kuka hada qarfi da qarfe za'a samu kyakkyawan result din da akeso" maganar abban a gaba ta biyu ta sake katse masa tunaninsa. Baiko tsaya din ta bakinsa don yasan halin kayansa,ya waiwaya ga sãahar data nutsu tana sauraren maganganun dattijon,duk da tafin hannunta take murzawa a hankali "Khadijatou,ga MUHAMMAD nan,a matsayin yayanki yake,kada kiji nauyi,idan kina da buqatar wani abu,koma meye ki tambayeshi,bashi da maraba da muhyiddeen,kinji ko?" Kai ta gyada masa,a taqaice tace "In sha Allah,we will do our best" "Barakallahu lakuma,zanyi alfahari da hakan". Duk su biyun ya saka a gaba yana nuna musu wasu muhimman abubuwa da suka shafi company din wadanda su basusan dasu ba,toufeeq na hannun damansa,ita tana daga hagunsa,a lokacin idan ka shigo zaka dauka duka 'ya'yansa ne,shi kansa cikin zuciyarsa sai daya ji hakan. Tsahon wasu mintuna kusan arba'in da wani abu sannan ya dakata yana dubansu bayan ya kalli tsadajjen agogon hannunsa,ya dan saki murmushi saman dattijuwar fuskarsa "Inajin a nan zan tsaya,kusan muhammad kasan komai,zan barka da khadijatu,sauran abinda ya rage saika qarasa nuna mata kayi mata bayani,for the first time zatayi aikin kamfani,but tana da talent sosai,zan wuce kada nayi missing flight" ya furta yana miqewa. Dai dai lokacin da daya daga cikin guard dinsa yayi knocking qofar bayan ya samu alert dake nuna Dr din yana buqatarsa. Komai ya tattarawa uban gidan nasa,dr ya miqe yana duban toufeeq da shima ya miqe "Koma ka zauna,ku qarasa kada lokacin tashi yayi" yadda yayi masa sallama haka itama sãahar,cikin girmamawa da ganin kimarsa,ya juya ya fita a office din,yana jin farinciki har cikin zuciyarsa. Shuru ne ya ratsa office din tamkar babu sauran wani me rai,shi din yana daga saman kujerarsa,yayin daya dora sambala sambalan qafafunsa akan leg rest na jikin kujerar,yana kuma sarrafa computer dinsa cikin qwarewa da hannu daya. Ko sau daya bai dago kai ko yayi wani motsi da zai nuna yasan da mutum cikin office din ba,dai dai lokacin da sãahar ke zaune don cika umarnin dattijon,wayarta itama take sarrafawa,lokaci lokaci tana duba agogon hannunta,tana jiran kuma lokacin data dibawa kanta ya cika tabar masa office dinsa. Kowanne a cikinsu jin kansa ya hanashi ya fara tankawa dan uwansa,cikin zuciyar sãahar tsanarsa da haushinsa ne fal suka danqare mata,ba tun yau ba tasan baisan darajar diya mace ba,bai martaba kimarta sam,a nasa sashen kuma ji yake sam batayi masa ba,tunda suke da Dr bai taba ganin mutumin daya jawo jikinsa har haka ba,farat daya ya maidashi tamkar ahalinsa,ya bashi dukkan yarda ya bude masa sirrinsa,yasan halin mata sarai,basu da kirki ko kadan muddin suna da wata manufa akan abu......tofa basa ji basa kuma gani harsai sun cimma muradinsu,suna iya komai,hakanan suna kuma iya jure komai har sai sun cimma gaci,musamman akan KUDI DA DUKIYA,suna sa masifar son kudi,tamkar wata halitta ce aka dasata cikin jininsu,basayin komai don Allah,bayason shi ko wani nasa ya sake fadawa MASIFA DA TARKON MACE,wannan wani HUKUNCI ne nashi da ya jima da yankewa akan kowacce mace idan ka debe MUTUM UKU RAK cikin rayuwarsa. Sai da ya mula don kansa sannan ya janye hannuwansa da idanuwansa duka daga kan computer din,ya sarqe yatsunsa cikin na juna yana fitar da sassanyar siririyar iska daga bakinsa,ya maida shanyayyun idanunsa dake da wani irin qarfin fusgar hankali a muhallin da take sai kuma ya janye yana jin wani qyashi yana kamashi,dai dai sanda take miqewa a nutse cikin nata jin kan,ta zura takalmanta a nutse ta fara takawa zuwa bakin qofa "Hey,da alama bakisan policies na aikin kamfani ba" ya jefa mata magabarya nutse ba tare daya kalli inda take ba,tsaiwa tayi cak,sautin muryarsa data tsana tana ratsa kunnuwanta,kamar tayi gaba,sai taga ya kamata atleast ta tsaya ta fuskanci wannan izzar tasa,don haka ta waiwayo cikin nutsuwa ta zube idanunta fes cikin nasa FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 *Arewabooks:Huguma* https://arewabooks.com/u/huguma Page 18 "Eheenn" sãahar ta furta a taqaice da alamun dake nuni da neman qarin bayani takeyi,sake zare hannunsa yayi daga kan system din,ya sanya idanunsa cikin nata a hankali kamar masu narkewa,wani abu me kama da fushi yadan ratsa ta tsakanin zagayayyun qwayar idanunsa "Waye ya sallameki?" Ya fada kansa tsaye yana qanqance idanunsa cikin nata. Sai data kalli agogon hannunta sannan ta amsashi,tana jin kamar ta bude idanu taganta ba cikin office din ba,inda yasan yadda ta tsani hada hulda da maza da bai bari ta zauna tsahon mintunan da tayi a tare dashi ba,tana qoqarin hadiye fushinta ta amsa masa,saidai hakan bai boye tata izzar ba "Lokacin daya kamata naci gaba da zama ya cika,inajin babu wani sauran abinda ya kamata na sani,inda akwai da ka sanar dani din" yadda take maganar with confidence ya bashi mamaki,karon farko da wata diya mace ta taba tsaiwa a gabansa cikin nutsuwa irin wannan ta bashi amsa takai tsaye,ta kuma amsa masa da abinda ya fito kai tsaye daga zuciyarta. Hannu yasa ya jawo wani file dake gefansa "Inason nayi alerting naki abu daya,ki tsaya iya matsayinki,kada maganganun Dr ya rudeki,kina da naki limit din,so do not exceed that limit,right?" "Don't bother" ta amsa masa a taqaice,duk da tanason ta gaya masa sama da hakan,to amma a yanzun bata da buqatar doguwar magana,sannan bai kamata ta take maganganun dattijon da bai dade da gama gaya mata su ba,bata sake bata koda second biyu ba ta juya ta fice abinta ba tare data tsaya jiran abinda yakeson gaya matan ba. Sanda ta koma office sai abubuwan suka yita dawo mata,tanason taci gaba da aikin,amma kuma abinda ya faru cikin office din yana ta dawo mata a rai,a hankali sai zuciyarta ta fara zafi,ta dinga jan tsaki a jejjere,daga qarshe ta tabbatarwa kanta ba zata iya ci gaba da aikin ba,sai ta ture komai ta fara hada tarkacenta,ta dan debi wasu files da take tsammanin may be zata iya dubasu a gida,tabar office din bayan ta yiwa miss sameera umarnin ta rufe,ta dan bita da kallo tana mamakin yadda ta tashi abinda duk da lokacin tashi baiyi ba,bayan qaqqarfan jan kunne da CEO ya ajewa kowanne ma'aikaci akan makara da kuma tashi kafin cikar lokaci,a taqaice ma dai a kwanakin kusan kowanne ma'aikaci yana d'ara lokacin tashinsa,saboda yadda kowa ya maida hankalin wajen kawo daidaito da gyaruwar lamuran kamfanin. Tana driving a hanya zuciyarta tana dada yin zafi,ta yaya zata iya aiki da wannan mutumin?,ta yaya zata jure aiki dashi?,kwata kwata nashi da manners,baisan darajar mutum ba,koda wayeshi,kowanne irin matsayi yake dashi,itakam ba zata taba jure ya takata ba,ba zata dauki kowanne banzan hali daga wajen kowanne d'a namiji ba yanzun. Da wannan fushin da zafin zuciyar ta isa gida,tayi parking ta fito tana tattaro files din data taho dasu,fuskar nan a dinke na walwala taji takun afifa. Ta cikin motar ta daga kai ta dubeta sanda take tahowa tana amsa waya,sanye da wata free gown,da alama tun dazun ta taso daga nata aikin,saita maida kanta taci gaba da abinda takeyi. Tana isowa gurin ta gimtse wayar tana dariya qasa qasa "Oyoyo mr president,bari na kwashi tabarraki" ta fada tana murmushi tare da qoqarin karbar folders din hannun nata,batayi jayayya ba ta sakar mata,ta fara kulle motar,afifa na gyara zaman folders din a hannunta tace "How was your day today?" Yi tayi kaman ta cilla mata harara amma sai ta fasa,ganin cewa ba ita takar zomon ba,don haka ta amsa mata cikin miskilancin nan nata "Bad" ta fada a taqaice tana soma takawa zuwa ciki,afifa tabi bayanta da hanzari "Kaman yaya?,your first day at work fa" kai ta jinjina mata kawai tana lumshe ido ba tare da tace mata komai ba,sai afifan itama bata qara tambayarta ba,sukaci gaba da takawa zuwa ciki. Maama ce zaune cikin falon,saman cinyarta wani dan bowl ne dake dauke da strawberry tana gyarawa,cikin kulawa ta amsa sallamar tasu idanunta akan fuskar diyar tata "Barka da gida maama" sãahar ta fada tana isowa gabanta gami da duqawa,ta kuma dora saman cinyarta kadan. Murmushi ta sauke tana dubanta,gaba daya jiki da zuciyarta sun nuna gazawa xda gajiyawarta,saita zare hannunta daga cikin strawberry din ta dora saman kanta "Barka kadai president dinmu,ya aikin?" Tabe baki tayi kamar wadda zata saki kuka,itako sunan batason a tuna mata,don da alama yaa muhyi ya bata aiki me wahala qwarai "Ba dadi maama,ya muhyi yayi punishing dina ne kawai da wannan aikin" dariya afifa ta saki yayin da maama tayi murmushi "Ba haka bane,da sannu dai zaki saba,qila ma ki dinga jin dadin aikin nan gaba kadan fiye da yadda muke tunani" miqewa tayi tana dan tura baki "Anya maama zanso wannan aikin?" "Ba wanda yasan gobe sai Allah" kai tadan jinjina "Abba bai iso ba?" "Ya kusa,inajin sai an idar da sallar magrib". Zasu wuce baaba rabi ta iso zata karba strawberry din da zata markada,cikin fara'a da girmamawa ta amsa barka da gidan da sãahar tayi mata "Barka dai farar d'iya,tun dazun nake dakon isowarki,abincinki ya kammala" "A shiryamin dan kadan,bamai yawa ba,ina fitowa yanzu" "A fito lafiya ummin abba" ta fada cikin nuna kulawa,maama dake zaue ta kalleta "Rabi kece kike sake sakalta sãahar naga alama" "Idan bamu tattalawa alhaji diya ba hajiya ai bamuyi halacci ba" sai kawai maaman ta bita da murmushi,kasancewar itadinma ba maison yawan magana bace. Tare suka shiga dakin ita da afifa,ta zube mata takardunta a kyakkyawar kusurwaf da aka shiryama wani kyakkyawan table da kujerarsa,dan qaramin study room a maqale da bedroom din nasu,gurin an masa shiri na musaman da zaiyi dadin karatu,ta koma parlor ta barta a dakin. A nutse ta cire kayanta ta watsa cikin laundry basket,ta daura wani lallausan farin towel,gab da zata shiga toilet din wayarta ta soma tsuwwa,dakatawa tayi tana duba number dake yawo saman screen dinta,zubawa numbers din dake jere reras idanu tayi,sai taja da baya ta wuce bandaki abinta,saboda number tayi mata kama da number mahmud,wadda a qalla kusan kullum tana ganin gilmawarta cikin wayarta da tarin saqonninsa da ko sau daya bata taba tsaiwa dubawa ba bare ta bashi amsa. Mintina kusan ashirin da biyar sannan ta fito,ta tsaya gaban madubi ta tsane jikinta,ta shafe lallausar fatarta me sulbi da mayuka sannan ta mutstsike jikinta da turarukanta masu taushin qamshin da kwantar da zuciya. Wani budadden cotton trouser ta saka,da wata free over size shirt me taushi,ta kama gashinta ta daure da band,idanunta suka sauka ga fuskarta da tayi wani irin fresh,babu alamun tabo ko qwarzane ko daya a kanta _"ki tsaya iya matsayinki,kada maganganun dr ya rudeki,kina da naki limit din_" ido ta lumshe tana jin maganar na mata zafi kamar yanzun ya furta mata su,waye ya gaya masa buqatar kanta ce wai ta kawota companynsu?,baisan aikin tamkar wata tursasawa bane da karan tsaye ne da aka yiwa rayuwarta ba?,batason shafe maganar dattijon,hakanan batason zubda yaa muhyi a idanunsu,dole wani abun ta kauda masa kai,amma bafa komai ba,kuma muddin zasuci gaba da hada hanya da guy din ta tabbatar babu jimawa zasuyi batacciya,don ba zata iya shanyewa irin wadan nan halayen nasa ba,yadda yakema mata ita ba zata iya dauka ba,don ba abinda take nema daga wajensu. Dogon tsaki taja,sannan ta juya tana fita a dakin bayan ta dauki wayarta,ta kuma goge duk wani miscall na mahmud da saqonsa da ya shigo bayan taqi daga wayar. Still maama da afifa na zaune suna hira a parlor din,saita wuce saman dining tana duba abincin da baaba rabi ta ajjiye mata. Cikin wanda ta zuba din ta sake tsakurar wani,duk da bashi da yawa amma ba zai iya shiga cikinta duk ba,hakanan yanayinta yake,sanda tana qarama maaman tasha kaita asibiti,ayita bata multivitamin ko cikinta zai bude a samu cin abincinta ya qaru,saidai babu wani ci gaba,dole aka rabu da ita hakanan bayan sun fahimci halittarta ce a hakan. Sanda ta kammala itama qasan ta sauko ta saka baki a hirar tasu,duk da kusan rabin hankalinta yana kan wayarta,ta shiga Instagram account dinta tana dubawa. Har ta gota wani post saita dawo da baya a hankali. Hoto ne da aka yiwa cikakken daukan daya bala'in fita tarrrr,kana ganin hoton zakasan cewa da babbar waya akayi,irin wayoyin da sukasan haqqin fidda hoto da kyau. _i'd never met anyone so quiet and beautiful simultaneously like him,his personality match his beautiful face MT JARMA_ Rubutun dake qasan photon kenan,sai tarin comments rututu,wanda kusan rabinsa na mata ne. Wani bacin rai ne yazowa sãahar iya wuya,ta fita gaba daya daga Instagram din,wasu abubuwan ba shakka laifin mata ne,irin comment data dinga gani a qasan photon kwata kwata babu tsari babu kuma aji bare kamun kai irin na 'ya'ya mata,kamar a duniya shi daya Allah ya bawa baiwar kyau?,ba dole ya dinga buga wannan iskancin ba, muddin a zahirance irin wannan rawan kan da digimin matan suke masa,ranta ya baci sosai,har afifa ta kula ta tambayeta,amma sai tace ba komai,ta jawo saman wayar ta kashe data dinta gaba daya,dai dai sanda yaa zaid yayi sallama cikin falon,yana riqe da jakar abba,abban yana biye dashi a baya. Cikin girmamawa kowa ke qoqarin masa sannu da zuwa,mutum me cikar kamala da kuma nuna qauna da sakewa da iyalinsa,yana da faran faran sakin fuska da kuma barkwanci,amma muddin zakayi ba dai dai ba da gangan da ganganci to fa baya lamunta,a nan ne zaka ga aihin Color dinsa. Sassansa ya wuce daga nan ta qofar data hada sassan biyu,maama tabi bayansa ta barsu da zaid din yana tambayar sãahar ya aikin "Lafiya" ta amsa masa a taqaice shima,afifa dake zaune daga gefanta dariyar da taketa dannewa ta taso mata "Adai dinga jin tsoron Allah ana fadin gaskiya,atoh" waiwayawa tayi ta kalli afifan,kaman zatayi magana saita fasa ta maida idanunta ga wayarta "Tell me,me ya faru?,da alama akwai magana tunda permanent assistant dinki ke dariya" shuru ta danyi kamar ba zatayi magana ba,sai kuma ta buda baki sound na bacin rai yana dan fita kadan a muryarta "Bashi da kirki yaa zaid,he was trying to insult me as kamar ina neman wani abu da kamfaninsu" dan zuba mata ido zaid yayi sannan ya saki murmushi "Try to relieve your anger dear,ki nutsu ki fuskanceshi,ki kuma fuskanci aikinki,ba don shi kadai kike zaune a kamfanin ba right?" Kai ta gyada "So no need ki damu kanki,do all the right things,amma don't be rude to him,ya girmeki,show some respect zaki samawa yaa muhyi din mutunci,ki zama me kawaici yadda na sanki,kada ki bari qananun abubuwa su dinga bata ranki,kin fahimta?" Nutsuwa taji tana saukar mata,Allah ya sani yadda yayyenta suke nuna qauna da kulawa a gareta ya sanya itama take qaunarsu,take kuma qoqarin bin dukka umarninsu,yanzun maganar da sukayi da yaa zaid din ya samar mata da relief sosai,sai ta dan sake sukaci gaba da hira,har zuwa sanda akayi kiran magrib,ya fita masallaci shida abba,su kuma suka wuce ciki ita da afifa. Ba kasafai take tashi daga saman abun salla da wuri ba duk bayan sallar magarib har sai tayi isha'i,kamar yadda takeyi bayan asuba har alfijir ya keto,saboda gurabene na amsar addu'a sosai. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 .. [8/14, 1:31 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 19 _____________________________ *_TAHO KI GANI_*👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 _shin kinsan da zaman wannan kuwa?,ko kina can kina bulayin neman inda zaki samu ingantattun kayan mata da SUPPLEMENT masu inganci cikin musulmin farashi?_ *Turqashi,ga biyan buqata ga sauqi*! *ZAHRA DANGE* 👉🏽 _face behind LADY APHRODISIAC AND MORE_ *dealer in all kind of supplement and herbal aphrodisiacs kayan mata* *Kayan mu will make you last on bed and permanently end the pain and embarrassment of weak eraction and premature ejaculation* *Muna hadin bridal package* *postnatal combination of natural herb's and supplement* *Akwai hadin uwar gida mai da tsuhuwa yarinya* *Akwai hadi na infection (sanyi herbs)* *Akwai Zuma Mai saukar DA niima nan take tare da dandano Na mussaman* *Muna kalolin gumbar Kamar gumbar madara, gumbar Aya, gumbar ridi, gumbar kasko, yar kicihi, Alhaji ba nan kake ba d.s* *Akwai kalolin tsimi kamar Dan la'asar, tabaje, tsimin yar gata d.s* *Muna DA kalolin gari nasha kamar sa buzu kuwa, sinadarin aya, abin sirri ne, emergency, rakumi DA akala, runbun dadi, kinfi Amarya d.s.* *Muna special kaza, danbu,ciccibi, Yan shila,zuciya d.s* *Akwai Na matsi different types DA sabulu na tsalki.* *TA BANGAREN SUPPLEMENT* *muna da na gyaran skin da kuma herbal aphrodisiacs supplement* *Akwaisu Juliet eve, royal jelly, ultimate maca, suprodine, frozen detox, frozen collegen, majakani,amirna, khusus, dara,cantik ayu, pesona d.s* *We have capsules, pills, chocolate, and different coffee that will make you sweet, firm, tight, young, beautiful and healthy.* *Akwai different oils both siyan d'aya ko sari* *Muna nan a garin SOKOTO sannan muna tura kaya ko ina a fadin duniya yaje maka cikin aminci IN SHA ALLAH*🌐 *_ZAKU IYA TUNTUBARTA KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_* 07034400732 *_SIYAN NA GARI MAI DA KUDI GIDA_*👌🏽👌🏽👌🏽 *Tasted and trusted*💪🏽💪🏽💪🏽 _______________________________ Afifa na kwance rub da ciki a saman gadonsu,tana kallo ta system din sãahar din,furera mataimakiyar baaba rabi ce tayi knocking,afifa dake kallo tayi mata izini,ta turo qofar dakin a shigo,cikin girmamawa tace "Maama tace a gayawa ummee,alhaji yana nemanta a sassansa" sãahar da takai ayar qarshe cikin surar da take karantawa ta maida qur'anin ta rufe "Gani nan zuwa" ta amsawa furera,ta miqe zata fice,afifa ta nuna mata plates din da sukasha kankana tace ta wuce kitchen dashi. Qur'anin ta mayar gurinsa,ta nade abun sallar sannan ta zura wasu slippers masu taushi a qafafunta tana mamakin kiran abban a irin wannan lokacin. Ko hijabin jikinta bata cire ba ta juya ta fice,afifa ta bita da kallo tana dariya qasa qasa,yau akwai daru kenan,sai ta gyara kwanciyarta sosai tana jiran dawowar rigimammiyar tata. A nutse tayi sallama abban ya bata umarnin qarasowa,ta zare slipper dinta ta shigo,ta zauna daga qasa gefe guda. Dubanta yayi ba tare da ya ajjiye wayarsa dake hannunsa ba "Ummin abba,ki duba setting room,kina da baqo". Jin maganar tayi kamar anyi jifa da abu ne nauyi cikin zuzzurfan rami,ya fada kansa tsaye ne ba tare da wata damuwa ko ganin nauyin maganar a tattare dashi,saita shiga ko kwanto,kodai bataji da kyau bane "Na'am abba?,afifa dai ko?" A natse ya dago ya kalleta sosai wannan karon cikin idanunta "Khadijatou nace" jikinta ne ya sanyaya gaba daya da yadda abban ya kira ainihin sunanta,wanda ta manta rabon daya kirata hakan,dukka gabobinta kamar an bi an doddokesu haka taji,ta tattara dukka qwarin gwiwarta,ta samu ta yunqura ta miqe,tana jin kamar iska na yawo da ita daga hagunta zuwa dama,daga gaba zuwa baya. Har takai qofa muryar abban ta sake cimmata "Idan kinje ki dawo zamuyi magana dake" kai ta gyada masa kamar me ciwon baki,ta zura takalminta da a yanzu takejin kamar qafafunta ba zasu iya riqesu ba ta fice. Minti daya ma ya isa ya kaita setting room din gidan,wanda babban qayataccen parlor ne dake farfajiyar gidansu,wanda a nan abban ke ganawa da baqinsa,to amma a yadda jikinta ya zama wani matacce,sai data debi mintuna biyu harda doriya sannan ta qarasa,zuciyarta cike fal da mamaki da kuma tunanin waye wannan?,me kuma yazoyi mata?. Muryar ya zaid ta fara ji sanda take dage labulen parlor din,suka hada ido dashi,yana zaune hannun kujera suna hira da baqon dake saye cikin wata dakakkiyar shadda,qamshin turarensa ya cika falon,a sake sosai suke hira da ya zaid kamar sun dade da sanin juna,suna hada ido ya miqe "Gata nan ma ta iso,sai nace ka gaida gida" ya furta yana miqa masa hannunsa sukayi musabaha,sannan ya zagayeta ya fice daga parlor din. Shuru parlor din ya dauka,yayin da taci gaba da tsaiwa a wajen kamar an dasata,bata fita ba bata kuma qarasa shigowa ba bare ta samu muhallin zama. Hakan ya baiwa mahmud abba gana damar kallonta da kyau,duk da cewa cikin hijab take amma sassanyan kyawun nan nata bai gaza fitowa fili ba muraran,wata qaunarta ta qara linkuwa cikin ransa,batayi laifi ba idan tayi jan aji me yawa,ta cancanta,tako ina ta cancanci dukkan wata izza da ginshira,saidai inda dubban matan dake binsa zasuya wahalar da yakesha akanta,tabbas da sun dara,da kuma yasha kunya "Me kake buqata?,me kake nema a gurina?" Ta tambayeshi kanta tsaye,don ta gundira da kallon da yake mata,kamar yadda taji ta tsani zaman falon. Murmushi ya saki sannan ya miqe tsaye yana mata nuni da kujera "Inaga zaifi kyau ki samu guri ki zauna,karki gaji da tsaiwar" ya fada yana murmushi,har cikin ransa yana jin dadin ganinta da wanzuwarsu guri guda "Kada ka damu da tsaiwata ko zamana,kai tsaye ka fadamin abinda kake ya kawoka, inason komawa ciki,nabar ayyuka da yawa " murmushi ya saki yana goye hannayensa a qijinsa "Ayyah,sorry,ina fatan ba aikin office ne ya gajiyarmin dake ba" idanunta tadan lumshe sannan ta budesu,ta gundura matuqa,da zai taimaketa daya taqaita komai da komai ya sallameta ta wuce ciki abinta "Have a seat please" ya fada yana karyar da murya. Bata fiyason ayita roqonta abu ba,hasalima tun asali mutum ce da bata qaunar mita da kuma jan magana,don haka ga qarasa ta zauna a hannun kujerar da ya zaid ya tashi a kai "Na gode" ya fada yana jin dadin yadda ta girmama buqatarsa,sai ya koma kan kujerar da ya tashi shima,idanunsa a kanta,abinda ya fara sanya ranta baci kenan,batason yawan kallo kwata kwata. "Basai mun dawo da doguwar magana ba, tunda na fuskanci abinda bakeso kenan,kaina tsaye zan gaya miki,sonki nakeyi sãahar,so kuma irin na aure,qauna ta fisabilillah,bance ki soni yanzu yanzu ba,a'ah ina son ki bani dana zuwa wani lokaci,har zuwa sanda zaki aminta a karan kanki da soyayyar da nake miki,ki kuma gamsu da cewa ke din zaki iya aurena" ya fada yana hade tafukan hannayensu biyu waje daya,kamar me neman gafara. Ji tayi kamar ya sanya wuqa ya yanki naman zuciyarta,tun bayan rabuwarta da adam yaune karon farko data zauna har kunnuwanta suka saurari kalmar soyayya daga bakin wani namiji,kalmar data jima dayin jana'izarta a kaf littafin rayuwarta,kalmar da takeji a ranta zuwa yanzu cewa qarya ce,babu wani so na gaskiya,saidai SON RAI da SON ZUCIYA da kuma SHA'AWA,sune zallarsu,ake musu ado da fenti a kirasu da soyayya. A ranta taji kawai mahmud din yazo ne don ya bata mata lokaci,eh....bata lokaci mana, tunda bazai taba samun abinda yakeso daga gareta ba,sai ta miqe tsam "Zanyi shawara" tayi furucin don ta samu ficewa a dakin,bawai don tana nufin yin shawarar bane da gaske,shawara akan abinda baida muhimmanci?,abinda ta riga ta sani ko sama da qasa zasu hadu bazai samu wannan buri nasa daga gareta ba "Alfarma ya biyu,don Allah badon ni ba" yayi hanzarin fada ganin ta doshi qofar fita,dole ta tsaya ba tare data waiwayo ba "Ko sau daya ne tak a rana ki dinga daga wayata" "Banyi alqawari ba" ta fada kai tsaye tana qarasa ficewa harda 'yar sassarfa wannan karon,kamar wadda akace za'a kama. Hanyar yabi da kallo harta bace masa,ya dunqule hannunsa ya kaiwa iska naushi,saidi fuskarsa murmushi ne a kwance,ko iya hakan yaji dadi a ransa,koba komai sunyi musayar kalamai duk da ba masu tsayi bane,a qalla an samu improvement ko yaya yake,zaici gaba da trying,bazai gaji ba,ya daga tsadajjen agogon rolex dake hannunsa ya duba lokaci,sai ya taka yana fita daga setting room din,wanda kafin ya iso tuni ya yiwa guard dinsa umarni sun shigo da uban siyayyar da yayo dukka domin sãahar din,karon farko daya fara tad'i da ita a cewarsa. Rana ce da kuma lokaci na musamman a rayuwarsa da bazai taba mantawa da ita ba,duk da ba wani abun kirki ta gaya mishi ba,bai samu hankalinta da lokacinta yadda yakeso ba. A wani mugun quntace take komawa zuwa falon abban,gaba daya ta shiga rudani da firgici,hankalinta a tashe yake kamar wadda wani mummunan abu ke shirin samunta. Tana sallama dr mamman ya zuba mata ido bayan ya dauke kansa daga kan takardar dake hannunsa kafin yakai ga amsa sallamar tata,yana sauke qafafunsa dake harde waje daya qasa tare da binta da idanu,yanason karantar yanayinta da gaske. Kanta a qasa ta tako lallausan carfet din dake shimfide a falonsa,madadin marbles din da aka qawata fiye da rabin qasan ginin gidan,ta zame a hankali cikin matuqar mutuwar jiki da wata fargaba ta zauna daura dashi "Gani abba" zama ya sakeyi sosai,ya ajjiye takardar yana dubanta "Ina kyautata zaton ba yau ne karon farko da kika fara ganinsa,nasan kuma zakiyi mamakin yadda akayi ya samu izinin ganinki direct daga wajena.....ya nema izinin soma ganawa dake ne kamar yadda shari'a da kuma al'ada ta tanadar,ya cika dukkan sharudda da akeson mai neman auren diyarka ya cika,wannan ya sanya na bashi izini,zaici gaba da zuwa har zuwa lokacin da zaku daidaita kanku,ku kuma aminta da junanku,kije kiyi addu'a,Allah yayi miki albarka" ya qarqare maganar ba tare daya bata damar cewa komai ba. "Ameen" tayi qarfin halin kalato jimlar daga kowanne sashe na bakinta ta hadata sanann ta furtawa abban. Sai da tayi namijin qoqari sannan ta yunqura ta miqe,kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,haka ta dinga ji tun daga zuciyarta zuwa gangar jikinta a birkice. Kasa qarasawa tayi cikin gidan,ta biyo ta farfajiyar gidan,sanna a hankali ta karkata zuwa sashen hagu na gidan,inda aka kebance wajen da wasu qawatattun kujeru domin hutawa musamman da yammaci,irin yammacin da zafin rana ke damun dan adam. Kujera daya taja ta zauna akai,daidai sanda take fidda wata ajiyar zuciya me nauyi da zafi,tasa dukka hannayenta biyu ta dafe kanta da taji yana niyyar fara mata ciwo saboda nauyin da maganar ta yiwa qwaqwalwarta. Ko da wasa bata taba sanyawa a ranta mahmud zai iya zama saua daga cikin matsalolinta ba a rayuwa,kwata kwata ma bata taba daukar batunsa da muhimmanci ba,shi yasa bata ja masa layi tunda wuri ba,ashe tayi sake,gashi yayi mata shigar burtu,yakai wani guri da idan batayi da gaske ba zai iya sawa a tanqwarata tayi abinda bata da niyya ko lissafin yi. Shurun da afifa taji yayi yawa sãahar din bata dawo ba,shi ya sanyata kashe laptop din ta sauko daga gadon,dakin maama ta leqa,ta sameta ta fito a wanka tana shiryawa "Bata shigo ba,tunda kuka wuce daki tacemin ta taho da ayyuka daga office zata rage banga ta sake fitowa ba" sai afifan ta juya zata fita,har takai qofa maaman ta kirata "Ko abbanku yayi maganar da ita?" Kai afifa ta gyada "Haka nake tunani maama" jinjina kai tayi fuskarta na bayyanar da damuwa "Dubata don Allah" juyawa afifan tayi ta fice itama jikinta yana bata lallai akwai damuwa. Ta jima lausasan tafukan hannuwanta kife saman fuskarta,tanason ta daidaita yanayinta ne ta kuma ragewa kanta damuwa kodon ayyukan data debo masu yawa daga office. A nutse taji an dafa kafadarta,ko bata juyo ba tasan wacace,amma sai tayi burus,a wannan gabar itama afifan ta shafeta,haushinta takeji sosai,ko banza ta taka muhimmiyar rawa wajen faruwar wannan abun,tasan babu ta inda mahmud zai samu cikakken information a kanta sai wajen afifan,inda ta barshi kamar yadda ta bashi tsaye a wajen..... tun a ranar,da tuni an wuce wajen,batajin zata sake bashi damar ganinta ma bare wani abu makamancin wannan ya biyo baya. Zagayowa tayi ta zauna ganin taqi waiwayowa gareta duk da ta tabata,tasan fushinta akanta,wannan din kuma da tayi alamace na tayi fushi. Sai data zauna sosai sannan tayi kiran sunanta,tsahon wasu sakanni ba tare data motsa ba,kamar bata jita ba,daga bisani kuma ta fara sauke hannuwan nata idanunta fes akan afifa. Kallon kallo suka yiwa junansu,kafin ta miqe a nutse tara ture kujerarta baya "Don't say anything......kinsan kome tunda kece silar faruwar komai din" ta fada calmly tana niyyar wucewa. Murmushi ne ya subucewa afifan,amma tasan cikin bacin ran da taketa kokawar dannewa take,don haka bata bari taga murmushin nata ba,ta miqe kawai tabi bayanta "A shirye nake na fuskanci kowanne irin hukunci,nidai na shirya sauya rayuwar 'yar uwata ta kowacce hanya me kyau,wannan karon tare nakeson a daura mana igiyoyin aure uku" kamar ta sanya waigi ta tsaida sãahar din,ta dakata da tafiyar da takeyi,sannan ta waiwayo ta zubawa afifa fararen idanun nan nata,ta motsa siraran labbanta a hankali "Aiba watanni shida masu zuwa ba,nan da shekara shida ma,ki rubuta ki ajjiye nan daura damaran yin aure ba" dukka girarta biyu afifa ta dage cike da tsantsar mamakin yadda kullum take dada zurfafa wajen tsanar maza,da kuma nisanta kanta da yin aure "Ahhh.....kice mun kusa bada sadakar wata yarinya a gidan nan" "Bismillah" ta fada a taqaice ganin afifa nason maida batun wasa,bata tsaya saurarenta ba ta wuce ciki. Aiki biyu ta hadawa kwanyarta kusan lokaci guda,damuwa ga aikin office din data debo,haka ta yita yaqi da kanta,har Allah ya bata nasarar wancakalar da wancan batun,tunaninta da hankalinta ya karkata sosai ga files din da take dubawa,tanayi tana hada wasu bayanai a system dinta tana saving. Ba ita ta tashi a wajen ba sai sha biyu saura,ta fahimci abubuwa masu yawa tarin naqasu da kuma gyare gyare,tana kuma saka ran daga gobe zata fara gudanar da aikinta da dukkan fikira da baiwar da Allah ya bata,kafin ta kwanta ta hada dukkan wasu bayanai masu muhimmanci,printing dinsu as document zatasa kawai ayi idan ta isa office. *_W A S H E G A R I _* Ta tashi a miskilarta sosai,har ta kammala shirinta,yau dimma cikin wata lafiyayyar lafaya me bala'i kyau da asalin tsada,wadda ta dace da takalmi da qaramin band bag dinta samfurin kamfanin Hermes,tayi wani masifar kyau,daurewar fuskar tata ta sake qara mata kyau da kuma kwarjini na musamman,tayi wani irin sassanyan kyau,sulbi da laushin fatarta a ido kawai kana iya fahimtarsa. Sarai afifa ta fuskanci fushi takeyi da ita,yau da alama 'yan miskilancin har a kanta suka sauka,don haka tana tsaka da nata shirin fita gurin aikin,hannunta riqe da towel tana goge jikinta "A sister like no other" ta fada tana kanne ido alamun tsokana,duk da cewa so take ta tsokaneta,amma har cikin ranta shigar ta sãahar tayi kyau sosai. Waiwayowa tayi ta jefa mata harara "Ki samu wanda zakiwa dadin baki" qaramar dariya afifa ta saki, sãahar ta gama daura agogon hannunta,tana fesa lallausan turarenta afifa ta sake cewa "Ki duba mudubi sosai fa kafin ki fita,gudun samun matsala" ta qarasa maganar tana qunshe dariya,datakawa sãahar tayi daga zuge zip na hand bag din nata,ta juyo tana duban afifa "Matsala?,kaman yaya?" "To ai wabillahi any moment za'a iya samun matsala,wannan kyan dake fita daga fuskarki kowacce safiya,kina zaton akwai namijin da zai iya gani ya kau da kai karon farko bai kawo kanshi ba?" Maganar ta fusgi hankalinta,saita waiwaya tana duban kanta da kanta a mudubi,tsahon wasu sakanni sannan ta dawo da dubanta ga afifa dake danne dariyarta,yanayinta yayi wani irin sanyi,kamae wadda ke shirin sakin kuka. Dukka kafadunta afifa ta dage ta yarfar da hannu "No way out fa malama,indai ba shafa kashi zaki koma yi ba,just kawai ki bawa mahmud kai bori ya hau,shine zaki zama cikin aminci" "Saiki auramin din mamata" ta fada adan fusace tana fusgar jakarta ta nufi hanyar fita,afifa ta saki dariyarta sosai "Yo kwana nawa ne" banza tayi da ita,tabbas da biyu afifa ke mata hakan,amma inda tasan yadda maganar ke sanyata cikin firgici da razani da bata dinga tsokanarta da hakan ba. Kamar kowacce safiya,a sassan abba ta samu maama,saidai ta taras ya Saifullahi yazo,suna breakfast tare da abban,ganin tayi musu sallama zata tafi bataci komai ba ya Saifullahi din ya tsaidata kan lallai sai taci wani abun,tsaiwar da zatayi tayi breakfast din zai iya bata mata lokaci,tana kuma son su shiga meeting din akan lokaci ko don cikar martaba da kamalarta,to amma sam ba zata iya ce masa a'ah ba,dole ta ajjiye hand bag dinta,taja kujera daya dake kusa da abban ta zauna ta hada tea. _____________ https://youtu.be/y6YMU120RZI Please subscribe to Rukayyat khalid YouTube channel fisabilillah. I only uploads videos na karatun Qur'an a tashar Please help me reach 1k subs soon insha Allah *RUKAYYAT KHALID* *Assalamualaikum warahmatullah* *Yar uwa shin mene amfanin wayar hannunki da bazaki koyi sana a da ita ba?* *Kullum kina yawo a social media irin su Facebook, WhatsApp, tiktok,Instagram, twitter da ma sauransu.* *Kina asarar data a banza kina zuba adashinda babu ranar dauka* *bakya chas bakya as? Se chart kika iya 🤔* *kin damu mijinki da BANI BANI?? Kizo nan ni* *~Graphics by Rukayyat~* *zan koya miki sanaar Graphics design wanda zaki samu abin dog dogaro da kai. Kina zaune daga gida kina sanaarki.* *Ga mai bukata a masa design ko wani iri, munayi insha Allah* SERVICES PROVIDED 🌹Logos 🌹Flyers 🌹data flyers 🌹Pos banner 🌹Book cover 🌹 Invitation Card 🌹 Business Card 🌹 Banner 🌹 Save The Date 🌹 Bank Sticker 🌹 Video Invitation card 🌹 Birthday Videos 🌹Business logo 🌹graduation poster 🌹e t c Muna kowani design a farashi mai kyau idan training kikeso ma munayi shima a farashi mai kyau insha Allah kedai kimin magana ta wannan number 👇🏻 *DM FOR ANY ENQUIRY* 07084515410 [8/14, 1:31 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 20 _____________________________ *_Wai wai wai_* _wani kaya sai amale,don raqumi bazai iya dauka ba_ *MAAB LUXURY* _GIDAN ADO DA KECE RAINI_ *MAAB LUXURY* _DUNIYAR QAWATATTUN KAYAYYAKI_ *MAAB LUXURY* _TUNQAHON GIDA DA GININ GIDAN GABA DAYA_ _IDAN NACE ZAN LISSAFO BAZAN GAMA BA A NAN KUSA,DON SUN CANCANCI KOWANNE IRIN SUNA_ *DAME DAME SUKE SIYARWA NE?*👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 _SUN KAWO MUKU DALLADALLAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAWATARWA DANA KITCHEN MASU HASKA DAKUNAN GIRKI… KWASHA KWASHA_ _SU DIN KARSHE NE A DUNIYAR KAYAYYAKIN GIDAH DANA KITCHEN NA KECE RAI NI… INA UWAYEN GIDAH, AMARE? ANTOCI, KAWUNNI, YAYYU MAZA, KANNE DA MA IYAYEN MU MAZA?_ _KU ZO A DAMA DA KU A WANNAN DAMAR ME DAUKE DA DIMBIN KAYAYYAKI MASU KYAU A KUDI DEDE MISALI WANDA KOWANE ZAI IYA MALLAKA IYA KARFIN SA_ _KU ZIYARCI SHAGON DA KE A KANO.. TITIN AHMADU BELLO WAY_ _KO KUYI ORDER DA GA SHAFUKAN SADARWA TA INSTAGRAM: @Maabluxuryhome_ _FACEBOOK:@maabluxuryhome_ _SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH,, INGANCI DA RAHUSA, KYAU A DADE ANA AMFANI DA SU SAI KAYAYYAKIN MAAB LUXURY HOME_ _A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY ORIGINAL HOME DECORS AND KITCHEN UTENSILS_ _MAAB LUXURY HOME GOT YOUR HOME AND YOUR KITCHENS COVERED… JUST A VISIT/CALL/DM AWAY_ _08034631010 MAAB LUXURY HOME👈🏽_ _______________________________ K'arfe tara saura mintuna goma na safiyar ranar motocinsa suka isa gurin ajjiye motoci na kamfanin,cikin hanzari cika aiki da sanin makamar aikin,daya daga cikin guards dinsa ya buda murfin motar,a yau din ba tare da wani tsaiko ba ya zuro baqi sidik din takalminsa kafin gangar jikinsa dake sanye tsadaddar suit charcoal color ta biyo baya,kunnuwansa manne da waya,ya waiwaya yana miqawa jibril daya wayar tasa,sannan ya fara takawa zuwa cikin kamfanin,cikin takunsa dake nuna zallar kuzari da kuma izza ta cikar mazantakar d'a namiji. Duk inda ya gifta ma'aikatane ke zubewa,kowa yana qoqarin miqa gaisuwarsa cike da girmamawa,saidai har a sannan waya yake amsawa,baya samun damar amsa gaisuwar tasu,hakan kuma bai sanya sun daina ba,har ya isa ga elevator,ya shiga shida jibril da mr samson,sauran kuma suka suka biyo bayansa. Har ya isa ga office din nasa waya yakeyi,wayar dake hannun jibril dince ta dauki tsuwwa,ya duba kiran sanna ya miqa masa da hanzari,sunan dake saman screen din yasa ya katse waccar wayar da yakeyi ya daga daya wayar,yana musu nuni da hannu. Rusunawa sukayi sannan suka juya cikin girmamawa suka fice. Yadda ya sake yana wayar kadai ya isa ya gaya maka da mutum me muhimmanci yake wayar,ya bata a qalla mintuna goma kafin ya lallabata sukayi sallama,ya sake kallon fuskar wayar yana furzar da iska daga bakinsa,a duk sanda zaiji sautin muryar yarinyar,sai qauna da kuma zallar tausayinta sun cika masa zuciya,inama ace ana iya sauyawa mutum uwa,ba shakka da tuni ya biya,komai tsadar uwar muddin zata maye gurbin waccan,zata shafe sunanta,jininta zai fita daga nata jinin fita ta har abada,lallai da zai iya sarayar da dukka abinda ya mallaka indai hakan zata tabbata,saidai inaaaa...... KADDARA TA RIGA FATA. Wannan tunanin kawai ya motsa zuciyarsa qwarai da gaske,har sai daya fidda baqin glass dinsa ya sakaye qwayar idanunsa a ciki,cikin hanzari kuma ya danna kiran jibril,gwara yayi hanzarin aiwatar da dukka schedules dinsa na yau kafin tunanun yaci galaba a kansa. Tsam saima ta miqe ta biyo bayan jibril dake yunqurin shiga office din,bata jin zata bari tayi asarar dare da wunin data bata taba zaben kaya da shigar da zatayi yau,ta lura,ko lokacin da ya shigo office din tana welcoming nasa,amma ko kusa ko alama bataga alamun ya ganta ba,bare ta sanya ran yaga dressing dinta. A nutse ya motsa labbansa yana amsa sallamar jibril,idanunsa sunga saima din dake biye dashi,kallo daya yayi mata ya janye qwayar idanunsa ya maida ga system din,yana qoqarin binciken ganin kowanne department sunsan da meeting din yau?. "Banason meeting din nan ya wuce nine thirty,a sanarwa dukkan board members din,banason makara,ina buqatar kowa a wajen on time" "Yes sir" jibril ya amsa yana rusunawa,sannan ya juya zai fice "Sir,am sorry,sai nake ganin dukka aikina ne fa?,so no need ka dinga kiran jibril,i can do it" ta fada gabanta yana dan faduwa,tana tunanin kalar amsar da zata samu daga wajensa. Kamar baiji abinda ta fada ba har jibril dinma tuni ya fita,dauke hannunsa yayi daga kan system din,ya zare gilashin idanunsa,qwayar idanun nasa da suka dan canza launi ta fito tarwai,ya kuma zube dukka wani nauyi da uban kwarjinin dake cikinta saman fuskar saima,wadda a take taji tana neman faduwa,cikin dabara ta qarasa ga ma'ajiyar kayan sanyi dake office din ta jingina kadan don hanawa qafafunta rawar da suka fara yi "Bake zaki tsaramin abinda ya kamata da kuma wanda bai kamata ba,aiki kika nema kuma an baki fine......wannan ya zama karo na qarshe da zanyi warning dinki,duk ranar kuma da kika sake......ki irga kanki a mazaunin korarriya" iya abinda yace da ita kenan ya maida gilashi fuskarsa ya sake tattara hankalinsa ga abinda yakeyi,kai ba zakace shi yayi wannan maganar ba a yanzu. Mutuwar tsaye tayi,kafin ta samu ta tattara dukka qwarin gwiwarta,ta juya a hankali ta fice. Cikin tsananin bacin rai ta zauna da qarfi saman kujerarta tana maida numfashi,sai kuma ta jawo jakarta dake saman teburinta ta ciro mudubi takai ga fuskarta,so take ta hango wani aibu nata da ya hana taoufeeq bata koda lokacinsa ne bare akai ga hankalinsa,tanason gano wanne irin naqasu take dashi da har ta gaza samun kansa,ta kasa samun soyayyarsa. Ba abinda ta hango sai doguwar fuskarta ne dauke da siririn hanci da kuma manyan idanu masu girma qwarai,ita kanta tasan tako ina bata da wani makusa ko aibu,KE KYAKKYAWA CE,kullum abinda tarin mazan da take tare dasu suke gaya mata kenan,taji hakan daga bakunansu ba sau daya ba ba sau biyu ba,amma a yau dukka wannan kyan nata ya gaza amfani a kansa?. Maida dubanta tayi ga shigar jikinta,kayan data kashe kudade masu nauyi ta siya,tasa aka zauna aka tsara mata dinki na jan hankali,amma ko sau daya,ko bisa kuskure bai kalli gangar jikinta ba bare tayi tunanin ya kula har hakan yaja hankalinsa. Madubin ta wurgar cike da bacin rai da kuma zallar takaici,ta kifa fuskarta saman jakar tata,tana jin kamar fa fashe da kuka ko zata samun sassaucin wannan musibar. Tare da miss sameera secretary dinta suka shigo office,ita ta riqo mata jakarta har ciki,tana shirin zama cikin dan sakewa tayi magana da sameeran "Ina fatan kowanne department a shirye suke?,qarfe goma dai dai zamu shiga" kai ta jinjina "Abinda na fara yi kenan ina shigowa office" "Alright,ki tattara dukkan bayanan nan ki fidda minsu as document,ko basu samu duka kafin lokacin ba ina da buqatar mafiya rinjaye" "Ok madam" sai ta amsa ta fice,yayin da sãahar din ta soma rage wasu ayyukan kafin cikar lokaci. Cikin girmamawa jibril ya dawo,yayi sallama ya amsa masa ba tare daya daga kai daga abinda yakeyi "Sir,akwai wani taron daga office din president,all employees daga dukkan departments,ten o'clock" da mamaki ya tsaya da abinda yakeyi din,ya zubawa jibril idanunsa "Akwai wani meeting da za'a yi irin wannan ba tare da an shaida min ba?" "May be an tura email zuwa ga secretary,shaida maka bane batayi ba" a nutse ya maida bayansa ga kujera ya jinginar,a yadda yasan halinta ya tabbatar ba zata kasa gaya masa ba "Koma daga office din waye a sanar nayi cancelling dinsa,wannan taron shine most important" "Yes sir" ya fada sannan ya juya ya fita don ya fara sanarwa saima,dole idan suna buqatar isar saqon akan lokaci ta tayashi tura sanarwar. Siririn tsaki yaja,ya tsani wannan power din da Dr ya bata,a wajensa kamar bata cancanceta ba,a matsayinta na baquwa,wadda batasan komai akan aikinsu ba,batasan kuma komai da ya shafesu ba,sai ya miqe yana cire suit jacket dinsa,yayi hanging dinta,sannan ya taka zuwa bakin qawataccen books shield da aka jera takardunsa da kuma litattafan cikinsa a tsare gwanin burgewa,ya zuge ya debo wasu takardu,dai dai sanda sajjad ya shigo. A nutse ya amsa sallamar tasa ba tare daya waiwayo ba,ya dauki abinda zai dauka ya rufe sannan ya tako zuwa inda sajjad ke tsaye. Hannu kowa ya dunqule ya miqawa dan uwansa kamar zasu daki juna,wani salon gaisuwa da suka saba yi a tsakaninsu,kafin daga bisani kowa ya ware hannun sukayi musabaha sosai,ya fara takawa zai koma kan kujerarsa "Tun jiya naga sanarwar general meeting daga office na president,yau kuma katsam sai gashi kayi cancelling ka maye gurbinsa da naka" sai daya zauna sosai sannan ya aza zagayayyun manyan idanunsa a kansa "Yes,anything else?" Kafada yadan dage yana samawa kansa gurin zama "Eh......kamar bai dace ba,bai kamata kayi cancelling ba dab da lokacin yin meeting din" ya qarashe maganar yana daukar wata calendar dake dake gefansa yana dubawa,baiyi maganar dama don ya bashi amsa ba,don yasan dama ba lallai bane ya amsa masa din. Shuru tayi tana duban Miss sameera bayan ta shaida mata anyi cancelling meeting nasu gaba daya daga office din CEO,an kuma maye gurbinsa da board meeting,ranta yadan baci kadan "Amma for what reason ne sameera?" "Madam,ban gani sun fada ba,amma dai i think wani babban uzuri ne ya taso" shuru ta sakeyi kafin daga bisani tace "Alright,ki shiryamin takardun da zan fita dasu" ta amsa mata a aladabce ta fice. Delay din da aka dan samu kafin miss sameera ta gama hada komai,shi ya kawo tsaikon fitarta on time,ta tsaya ta gyara yafen laffayarta,ta dauki wayarta da system dinta sannan ta fito,sameera na biye da ita "Madam,idan ba damuwa zan rigaki isa gurin" ta fada cikin girmamawa,kai sãahar ta gyada mata,dom ta fuskanci me take nufi,miss sameeran hard worker ce sosai,hatta da yanayin tafiyarta irin me gab gab din nan ne cike da sauri,ita a iya nata yanayin halittar iya saurinta kenan,amma ta tabbatar ya yiwa sameeran kadan,shi yasa ta bata wannan damar. A floor din dake qasan nasu za'ayi taron,ta isa gaban elevator ta bude ta shiga,ba kowa a ciki sai ita daya,wannan ya bata damar sakewa. Saidai qofar na shirin rufewa,sai taga ta tsaya,abinda ya sanyata dago kai kenan a nutse tana duban bakin qofar. Kafarsa dake saye cikin rufaffen baqin takalminsa ya sanya daga bakin qofar,abinda ya hanata rufewa kenan saboda na'ura na aikata da saqon akwai mutum dake shigowa ciki,duk da cewa yana magana da wani dake tsaye a bayansa,amma hakan bazai hanaka ganin gefan kyakkyawar fuskarsa wadda ke kwance lamban da suma ba,sumar dake baki sidik ta kuma kwanta da kyau saman farar lallausar fatarsa,sassanyan qamshinsa dake kai kawo har zuwa cikin elevator din ya karade gurin. Ido ta janye a hankali tana goye hannuwanta a qirjinta,ta lumshe idanun nata can qasan ranta tana addu'ar idan ya ganta ya koma kamar yadda suka saba,duk yadda takai ga qin hada hulda da maza,ba kasafai takejin tsanarsu ba indai ba harkarta suka shiga ba,amma shi wannan din,tana jin tsanarsa ne naturally daga qasan ranta,banda yana tsaye ne ta bakin qofar,ita kuma tana jin qyashin ce masa ya matsa,da tuni ta fice daga elevator din,ta gwammace ta jirayi wata,koda zata sake bata lokaci fiye da wanda ta bata dazun. Dai dai sanda tunaninta ya yanke ya kammala magana da mutumin,ya matso da niyyar shigowa idanunsa ya fada a kanta,ta karkatar da kanta daga fuskantar qofa ta maidashi left side dinta kamar me kallon wani abu na daban,sai ya janye shanyayyun idanunsa,yana tsuke fuskarsa da kyau,cikin ransa yanajin ya kamata a raba elevator din maza da mata a company,bai kamata aci gaba da cudanya haka ba,ya isa ga madannin ya bata umarnin inda zata saukeshi. Ganin ya gama shigowa kuma qofar bata kai ga rufewa ba,saita sauke hannunta,ta kuma nufi qofar da niyyar ficewa ta sauya wata,sarai ya ganta,ya kuma fuskanci fita zatayi saidai hakan bai dakatar dashi daga dannan madannin ba,wanda gab da zata fita qofar ta rufe ruf,sannan kuma ta fara sauka dasu zuwa qasan da sasarfa cikin cika umarnin da aka bata. Saukar data fara yi cikin ba zata babu zato wani jiri ya fusgeta,qaqqarfan tsoro ya mamayeta,ta runtse idanunta cikin hanzari ta dafe qarfen dake kusa da ita,tun asali ita ba me yawan son hawa lifter ko wani iri bane,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya tana sauke numfashinta a hankali,har zuwa sanda taji tsaiwar elevator,saidai abun takaicin tun bata bude idanunta ba taji floor din da suka sauka ba nan zata je ba,ta bude idon a hankali ranta yana baci. Daga bakin qofar ta ganshi a tsaye yana magana da daya daga cikin guard nasa. Sosai ranta ya baci,do meye zai maida elevator din jirgin yawo?,bayan yasan bashi kadai bane a cikinta,koda baiyi hakan ba already tasan shi din ba mai sanin darajar dan adam bane,yana da izza, izzar da a kallo daya zakayi masa ta karanceta tasss saman fuskarsa da motsinsa. Bata sake motsawa ba daga gurin,ta bawa banza ajiyarsa har ya gama abinda zaiyi,ya sake takowa ya zabi floor din da zata ajjiye shi tamkar baisan da mutum a ciki ba. Tana iya jin sanda kira ya shigo wayarsa,ya daga ya kara a kunnensa,saidai bata iya jin abinda yake fada clearly,taja tsaki qasan ranta kamar zata tsinke zuciyarta saboda haushi da kuma takaicinsa. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 21 ______________________________ *_Wai wai wai_* _wani kaya sai amale,don raqumi bazai iya dauka ba_ *MAAB LUXURY* _GIDAN ADO DA KECE RAINI_ *MAAB LUXURY* _DUNIYAR QAWATATTUN KAYAYYAKI_ *MAAB LUXURY* _TUNQAHON GIDA DA GININ GIDAN GABA DAYA_ _IDAN NACE ZAN LISSAFO BAZAN GAMA BA A NAN KUSA,DON SUN CANCANCI KOWANNE IRIN SUNA_ *DAME DAME SUKE SIYARWA NE?*👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 _SUN KAWO MUKU DALLADALLAN KAYAYYAKIN GIDAH NA KAWATARWA DANA KITCHEN MASU HASKA DAKUNAN GIRKI… KWASHA KWASHA_ _SU DIN KARSHE NE A DUNIYAR KAYAYYAKIN GIDAH DANA KITCHEN NA KECE RAI NI… INA UWAYEN GIDAH, AMARE? ANTOCI, KAWUNNI, YAYYU MAZA, KANNE DA MA IYAYEN MU MAZA?_ _KU ZO A DAMA DA KU A WANNAN DAMAR ME DAUKE DA DIMBIN KAYAYYAKI MASU KYAU A KUDI DEDE MISALI WANDA KOWANE ZAI IYA MALLAKA IYA KARFIN SA_ _KU ZIYARCI SHAGON DA KE A KANO.. TITIN AHMADU BELLO WAY_ _KO KUYI ORDER DA GA SHAFUKAN SADARWA TA INSTAGRAM: @Maabluxuryhome_ _FACEBOOK:@maabluxuryhome_ _SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDAH,, INGANCI DA RAHUSA, KYAU A DADE ANA AMFANI DA SU SAI KAYAYYAKIN MAAB LUXURY HOME_ _A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY ORIGINAL HOME DECORS AND KITCHEN UTENSILS_ _MAAB LUXURY HOME GOT YOUR HOME AND YOUR KITCHENS COVERED… JUST A VISIT/CALL/DM AWAY_ _08034631010 MAAB LUXURY HOME👈🏽_ ________________________________ Tana da tabbacin meeting hall din ya nufa,dole yana gaba tana biye dashi. Tun daga nesa dukka guards nashi suka zama ready da isowarsa,daya daga ciki ya iskeshi a hanya riqe da suit jacket dinsa,ya taimaka masa ya saka,sannan ya karba komai dake hannunsa suka take masa baya har zuwa bakin madaidaicin hall na musamman da aka tanada saboda ganawa me muhimmanci irin wannan da manyan masu ruwa sa tsaki cikin company din. Dai dai sanda ta iso dab dashi ya gama magana dasu,kusan lokaci daya suka tura qofar,suka kuma sanya qafafunsu,sai ya zamana tamkar dama a tare suke. Hankula da idanuwan dukka board members din dake hall din yayo wajen, kasancewar shi kadai dama ake jira,a hankali kallon dake saman fuskokinsu ya canza,idanuwansu na karakaina saman kyakkyawar fuskar sãahar dake cike da fushi,baquwar fuskar dake dauke da wani irin sassanyan kyau me jan hankali,wasu kuma cike da mamakin wacece ita?,meye alaqarta da CEO dinsu?,wanne irin matsayi gareta da har sai daya jirata suka taho tare?,take wutar kishi ta kunnu a zukatan matan dake zaune a wajen,harda wani sashe na mazan gurin,saura kuma zukatansu suka cika da wasu wasi,take wutar jita jita ta fara tsiro a wajen,aka fara qus qus a tsakanin juna,ko kusa daga shi har sãahar da ranta ke abace basu ma lura da hakan ba. Kujerarsa ce qwaya daya tal daga can saman qololuwar table din,daga gefanta ya tsaya ba tare daya zauna ba,sannan cikin husky voice dinsa dake da wani irin amo na zallar kwarjini yace "I apologize for not arriving on time" a nutse sãahar dake zaune cikin tata kujerar dake daura da tashi ta daga kanta,tanason kallon qwayar idanunsa ne cike da mamaki,bata taba tunanin zai iya apologizing wani akan wani abu ba "let's start for what brought us together here" ya kuma fada yana zube hannayensa cikin aljihun wandonsa,fuskarsa cike da seriousness dake cakude da kwarjini. Cikin wani irin salo na tsari meeting din ya fara gudana,tsarin da kana gani kasan ya samo asali da tushe ne daga wajen CEO din yasan abinda yakeyi,dukka tsahon zaman nan yana tsaye ko sau daya bai zauna ba, saidai time to time ya durqusa ya danyi rubutu a system dinsa ya same miqewa,duk kuwa da cewa saima tana wajen,kuma aikinta ne ta nadar masa dukka bayanai. Tunda aka fara tattaunawar batace komai ba,a nutse take sauraren komai tana kuma sake samun ideas sosai,saidai gaba daya a takure take,hakanan ranta kuma a bace yake. Tun daga sanda ta shigo gurin ido yayi yawa a kanta,daga mazan har matan wanda ita batasan meye dalilin kallon ba,bayan ta zauna ta samu raguwar idanun da sukayi mata caaa,saidai har kawo yanzu idanuwan mutum biyu hudu sun hanata sakat. Biyu daga cikinsu mata ne,don haka kallonsu bai wani dameta ba,sauran biyun kuma dukkansu sun fito daga jinsin da basa ga maciji watonJINSIN MAZA. Dayan ta fahimci shike riqe da muqamin chief financial officer (CFO) a bayanan daya gabatar,dayan kuma batace ga nasa muqamin ba,saidai tunda har yake cikin board members wani ne tabbas cikin kamfanin. A nutse ta maida dubanta ga takardar da take kusan hannun kowa dake wajen,wadda tsari ne na abinda za'a tattauna a wajen. Yadda tattaunawar ta dauki zafi,sai take ganin kamar ana shirin sauka daga kan ainihin abinda ya tattarasu,zuwa sanda MT jarma ya dan buga table din gabansa,dakin ya dauki shuru,ya gyara tsaiwarsa da take qara fidda zatinsa,cikin qwarewa da fasahar iya magana dake cakude da taushin muryarsa me zurfi ya fara nasa bayanin. Shuru gaba daya hall din ya dauka,maganganunsa da iya sarrafa harshensa sunja hankalin kusan kowa dake gurin,har zuwa sanda ya kammala ya rufe da fadin "Ina buqatar tattararren bayani daga kowanne member personally,you can ask question if anything seems unclear or confusing" ya qarashe fada yana sauke dubansa akan kowa dake cike da gamsuwa akan bayanansa,a hankali har idanunsa suka fada a kanta,lokacin da ta bude folder dinta tana dubawa,tamkar ma bata a wajen ake dukka wannan zazzafar tattaunawar. Janye idanunsa yayi,ransa na baci,baiga amfaninta cikin kamfanin ba har yau ,wannan zaman yana daya daga cikin tattaunawa me amfani da zata iya zama tushe na fitar company din daga matsalar da yake shirin afkawa,yaja qaramin tsaki,yana shigar da wannan bayanan cikin system dinsa. Cikin jikinta taji kamar ana kallonta sama da idanuwan da suke kallon nata a dazu,don haka ta rufe folder din nata a hankali ta daga kanta,ta jjiye folder din daga gefe ta gyara yafen laffayarta,dai dai sanda suka sake hada idanu dashi karo na barkatai. Qasa qasa taja tsaki tana gyara abun maganar dake ajjiye a gabanta,tunda suka zauna gurin yake qare mata kallo iya son ransa kasancewar yana zaune ne kujerar dake fuskantarta "Akwai muhimman abubuwan daya kamata ace anyi magana a kansu,saidai ba wanda yayi magana akansu din duk tsahon zaman, though dai we've got ten minutes left..." A nutse ya daga kansa daga system ya saukesu a kanta,a take idanuwansu suka gauraya waje daya,cikin qasa da second uku kowa yayi saurin janye nasa,saita juya ga abun maganarta ta fara nata bayanin a taqaice. Kamar sanda yake magana,ko a yanzunma shuru ne ya sake wanzuwa a dakin taron,amon muryarta da nata salon turancin tatacce kamar nasa,mintuna shida kacal ta tattara komai A taqaice,sannan ta miqa file ga mr sameera tace a sadar dashi ga office na ceo,suna buqatar sanya hannunsa don aiwatar da aikace aikacen da team dinta suka tsara. "Any questions?" Ya tambaya kai tsaye,saidai ba wanda yace komai,hakan ya tabbatar da zuwan meeting din qarshe. Tana zaune saman kujerarta bata motsa ba har sanda mutane suka fara fita,kusan hakan al'adarta ce,bata yunqurin fita daga guri irin wannan me hadakar maza da mata ba,har sai an samu ragowar cunkoso gudun hada jiki dasu. "Madam,banga kinsha komai ba" taji an fada daga gaba da ita kadan,a nutse ta daga kai tana kallon mai maganar,shine dai na dazun,me shegen nacin kallon tsiya,CFO,ya kafeta da mayun idanunsa yana jifanta da murmushi "Thanks" ta fada masa a gajarce,saita fasa ci gaba da zaman,ta miqe tana daukar hand bag dinta tare ta yima Mr sameera inkiya,ta fara takawa a nutse,nutsuwar data haifarwa da takun tafiyarta wani irin salo da zaka dauka tsabar yanga gayu da kuma yauqi ne,saidai ita din tun asali naturally haka halittarta yake. K'arfe shida da mintuna motocinsa suka dauki hanyar gida dashi,a mugun gajiye yake jinsa,kowacce gaba ta jikinsa tana da buqatar hutu,banda hutu na gangar jiki,harma da hutu na zuciya. Tare da sajjad suke cikin motar,duk da suna hanya amma sajjad din na hirar yadda taron ya gudana "But...... sabuwar president din nan,ta bani mamaki beyond my expectations,she's very talented" "I don't know" taoufeeq da hankalinsa ke kan qaramin screen din dake liqe a kujerar gaban seat dinsa ya amsawa sajjad a taqaice,sam baya son zancanta,tunanin da yaketa kokawa dashi kenan tun dazun,abubuwan data gabatar ne sukata yi masa yawo akai,to ko su din bayason tunawa,haka kawai zuciyarsa ke gaya masa ta fiya zaqewa,kamar tanayi saboda ta sake samun shiga jikinsu da sanin abinda yake mallakin dr ahmad jarma din. "She's the best president da companyn nan ya taba samu I think" zuwa yanzu maganar ta fara gundurarsa,ba a bakin sajjad ba,kafin sajjad din yace wani abu kusan mutum biyar daga cikin board members din abinda ya barosu suna tattaunawa,bashi da sauran shaida data rage akan diya mace,banda mutum uku zuwa hudu daya ware,don haka yasa hannu ya ciro headphone ya toshe kunnuwansa dasu yaci gaba da abinda yakeyi. Sam sajjad dake bin tsarin aikin nata yana dubawa gami da ci gaba da yi masa zancanta bai lura ba,sai daya waiwayo da nufin nuna masa wata agenda sannan ya gani,baki kawai ya sake yana kallonsa,ya gaji da jinsa,amma bazai buda baki ya fada masa ba,ya gwammace ya toshe kunnuwansa da bututun sauti?,sai kawai ya rufe folder din ya adanata cikin wata ma'ajiya dake jikin kujerun me kama da akwatu,ya maida gurin ya rufe. A yadda ya nuna baida interest muddin bai adana folder din ba yasan bashi da asara na koma meye da zai sameta,bazai damuwa ba,illa iyaka yace yayi cancelling,ko ya sasu wahalar sake tsara wani jadawalin. Su biyu ne rak a babbar farfajiyar gidan a zaune,kamilar dattijuwa baaba rabi na zaune saman couch din da aka qawata gurin da ko ruwan sama bai sauka,sai daddadar iska me sanyi,qamshin furanni da koke koken tsintsaye kala daban daban. Saman cinyarta kyakkyawar farar yarinya ce, siririya sosai mara jiki ko kadan,sai zallan madarar kyau da Allah ya zuba mata,wanda tayo gadonsa ne daga gurin mahaifinta,matashin attajirjn dan kasuwa MT jarma. Fararen kaya ne sol a jikinta,dogon lallausan wando da rigarsa me dogon hannu,saidai akwai zanen pink din teddy daga gaban rigar,da siririyar sarqa me ruwan gwal a wuyanta,sai dankunnen barima shima da yafi kama da na gold din,sosai mayalwaciyar sumarta ke a gyare kuma a daure cikin farin ribbom,yankan farce baba rabin takeyi mata,gefe daya kuma tanata qoqarin karbar surutun da take mata cikin nuna kulawa babu gajiyawa ko kadan saman fuskarta. Hon din motocin kadai taji ta gane dawowar mahaifinta,mahaifin da duk fadin duniya baaba rabi takance,ta jima bataga irinsa ba shida diyarsa,wata irin shaquwa da qaunar juna ce a tsakaninsu me tarin yawa,duk da nakasu me tarin yawa dake tattare da rayuwar kowannensu,kamar a duniya basu da kowa sai junansu. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma 22 Baaba ramatu bata hanata janye qafafunta da take yankewa farce da take qoqarin yi ba,ta sakar mata amma ta miqe tana cewa "Yi a hankali,gidan fa zai shigo gaba daya fadeela" baaba ramatu ta fada cikin tausayawa,ganin yadda taketa zirgillo,ta kasa tsaiwa guri daya,har sai data isa ta kama hannunta suka nufi gurin da yake ajjiye motarsa duk sanda ya dawo daga office. Ita dince mutum ta farko daya fara gani kuwa,don motar na tsaiwa,bai tsaya jiran guards sun bude masa ya buda da kansa ya zuro qafafunsa waje,dai dai sanda itama taketa kutsawa ta tsakanin ma'aikatan mahaifin nata,har sai data iskeshi,ya buda hannayensa dukka biyun ta fada ciki cikin matuqar farinciki,zakayi zaton ba dazu dazu bane yabar gidan,tamkar matafiyin da yayi watanni bai cikin ahalinsa. Ba wanda ya katse musu walwalarsu,domin idan da sabo dukka wanda ya kwana ya tashi cikin gidan ya saba da ganin hakan,saida ya fidda mata dukka wani nau'in kayan ciye ciye data lissafa masa tana so kafin fitarsa,ya damqa mata sannan ya samu ta barshi ya fito daga cikin motar,suna saqale da hannun juna suka doso hanyar ainihin cikin gidan. Dab da zai isa kusa da baaba ramatu ya dakata,cikin girmamawar da har yau har kwanan gobe bata gajiya da bashi ita tayi masa barka da zuwa "barka,ya gida,ya fama da me rigima?" Kusan wannan tambayar ta zame masa tilas,kullum sai ya yiwa baba rabin ita tare da yi mata sannu,abinda ke qara mata ganin kimarsa kenan. Murmushi ta saki,itakam a duniya rigimar fadeela bata taba damunta ba,idan ba'a tausaya mata ba bai kamata aga laifinta ba,duk da hakan yarinyar tana da wani irin hankali sanyin rai da kuma nutsuwa,kawai dai bata iya nutsuwa muddin taga mahaifinta "Alhamdulillah,mun yini cikin qoshin lafiya" wannan kusan itace amsar da tafi masa kowacce amsa dadi a rayuwarsa,hakan yana nufin fadeela bata hadu da hatsarin da kowacce rana,tun daga bullowar rana zuwa faduwarta zata iya fuskanta ba,lalurar dake sanyawa duk wanda suke tare dashi fargaba,suke kwana su kuma tashi cikinta. "Hajiya qarama ma ta dawo" baaba ramatu ta fada a ladabce,abinda yasa ya dakata daga tafiyar da yakeyi,sai ya sauya akalarsa zuwa sassan da 'yan aiki suketa kai kawo,da alama suna aikin gyaran sassan ne. Fadeelan na biye dashi tana ci gaba da bashi labarai,wanda ayanzun ta sauya akalar labaran nata ne kan MOMMY QARAMA,kayan wasan data kawo mata da sauran tarkacen wasan yara. Daya daga cikin tafka tafkan sashe ne cikin sassan dake gidan,wanda kusan a manne yake da sashen da fadeela da baaba ramatu suke rayuwa a cikin sa. Kamar kowanne sashe na gidan,shima masu aiki ne mata ke kai kawo tsakanin makeken falon da yayi girman wasu gidajen kitchen,dining area zuwa balcony din da bedrooms din sassan suke a tsare,har ya zuwa upstairs din sassan da nasa falon. Tun daga qofar falon suke zubewa suna gaidashi,ba tare da damuwa da cewa ko sau daya bai samu amsawa kowa ba a cikinsu. Sun riga da sun saba da wannan yanayin nashi,zasu iya cewa tsahon shekarun da suka dauka a tare dasu,basu taba katarin ganin koda murmushi akan fuskarsa ba bare akai ga dariya. "Hajiya qarama fa?" Ya tambayi matar data fito a kitchen ta kuma zube a gabansa cikin ban girma "Tana sama" bai amsa mata ba,ya fiddo wayarsa ya fara kiran wani layi. Bugun farko aka daga cikin qasa da second daya ya amsa da "Okay" ya maida wayar aljihu,ya zauna saman daya daga cikin kujerun yaja fadeela jikinsa ya dorata saman cinyarsa yana ci gaba da bare mata chocolate din. Minti daya tal motsi ya fara tashi daga upstair din,kafin daga bisani sautin takalmi dake bada d'as d'as ya biyo baya. Farar macace doguwa sambal,ma'abociyar tsaho da kuma qibar da batayi yawa ba,koda batayi kama da toufeeq ba,amma tun kallon farko zakasan cewa akwai alaqa ta jini me qarfi a tsakaninsu,dukkansu kuma babu qarya......a duban farko kadai zaka gane ainihin yare da qabilar da suka fito wato SHUWA. "Marhaban Muhammad" tayi maganar murmushi kwance akan fuskarta,muryarta ta sanya fadeela zamewa daga jikinsa ta doshi stairs din tana murmushin itama "Basai kin hauro ba,saukowa zanyi UKTIE" dai dai sanda ta qarasa saukowar,saita miqe hannunta duka ta riqe fadeelan da kyau,cikin wani irin duba me cike da zallar so qauna da kuma kulawa. Kujerar gefansa ta samu ta zauna tana bashi duka hankalinta "Yanzun kake shigowa?,sanda na dawo ai baaba ramatu tacemin baka jima da fita ba" kai ya jinjina,cikin nutsuwarsa yace "Barka da dawowa,i hope komai lafiya" murmushi ta kuma sakewa,tamkar kumatunta basa gajiya da fidda murmushin "Barka kadai jarma,lafiya alhamdulillah,inacan inata kewarku,hankalina gaba daya yana kan uktie,ina fatan tun tafiyata ba'a sake samun wata matsala ba?" Kai ya jinjina yana lumshe idanunsa hadi da budesu,da alama hakan kusan wata dabi'a ce tasa a duk sanda yake magana "Komai an samu sauqinsa, alhamdulillah" ya furta cike da fatan hakan taci gaba da kasancewa. Zai iya cewa komai na jin dadin duniya ubangiji ya mallaka masa shi,saidai ita rayuwa bata taba tafiyarwa bawa a yadda ya sota dari bisa dari,hakanan bata taba kubuta daga tarin qaddara da jarrabawa,lalurar fadeela na dukka abinda ya sameshi a can baya ya aminta na daya daga cikin qaddarorinsu,kuma sila na samun tawaya daga cikar jin dadin duniyarsa. "Na dawo na tarar julia bata nan" ta fadi fuskarta na nuna tsantsar fushi "Na sallameta" ya amsa mata a taqaice,don shi din mutum ne da bayason doguwar magana sam sam sam "Shine dai dai hakan da kayi,ta yaya za'a dauki a ninka miki salary dinki na asali sannan ki kasa aiwatar da abinda aka daukoki dominshi?,wannan ai tsantsar yaudara da kuma cin amana ne,naso ina nan,daa kafin tabar gidan nan ba shakka sai na hada mata da hukunci" sumarsa ya shafa da hannunsa daya sannan ya miqe "Ya wuce" "Allah ya tsare gaba,zan saka madam Stella ta sake lalubo wata,tsayayya da zata iya kulawa da ita" tayi maganar tana shafa sumar fadeelan cikin kulawa "Yayi,but idan aka sake samun kuskure kusa dana baya,itama zata rasa aikinta ne kamar su" "In sha Allah wannan shine karo na qarshe,masu aiki duka babu aminci,kowacce da irin nata sakacin" tayi maganar cikin salon fada. Dai dai sanda labulen daya lullube qofar balcony din dake falon qasa ya bude,budurwa dake ciki ta fito. Labiba ce sanye da kayan bacci,guntun wandon da iyakarsa cinya,sai wata fingilalliyar rigarsa wadda da kadan ta dara saman cikinta,cup hand ne da ita maqallalle iya dantsen hannunta,kanta baby dankwali,sai gashinta dake daure a ribbons,kusan kowacce sura ta jikinta a bayyane take. Ganin taoufeeq ciki falon sai ya qarasa kashe mata jiki,kowacce gaba ta jikinta ta amsa,amma kuma kallon daya watsa mata ya dakatar da ita daga tahowar da take izuwa gurin,ta tsaya cak tana tuna gamuwarsu ta qarshe,marin da fuskarta tasha da kuma irin zazzafan gargadin da yayi mata. Bai sake duban inda take ba ya juya ya fice abinsa daga falon a nutse cikin qasaitaccen takunsa. Wata ajiyar zuciya me qarfi ta sauke,sai daya fitan sannan ta samu sukunin qarasowa,idanun hajiya qarama a kanta har ta zauna "Lafiyarki ke kuma?" Sake sakin ajiyar zuciya tayi,tana karbar ruwan tea da fried egg da daya daga cikin masu aiki ta kawo mata "Muhammad" "Me yasa kullum tunaninki da dukkan furucinki ko yaushe a kansa yake?" Kai ta girgiza tana ajjiye cup din da tayi niyyar kaiwa bakinta ta fasa "Mommy,wani irin fitinannen so nakeyi masa,ba zaki gane yadda nake jinsa a raina ba,i can't imagine my life without him" wani irin duba na tsanaki hajiya qarama take binta dashi tsahon wasu sakanni ta ajiiye numfashi,sannan ta gyara zamanta. "Kiyi qoqarin ragewa,kinfi kowa sanin halinsa,bayasin shishshigi bayason kuma a fiya shige masa da yawa" "Zan kwatanta" ta fada badon tana jin zata iya ba,wani sashen na kwanyarta kuma na tuna mata marin da tasha a haduwarsu ta qarshe. Taji babu dadi amma bataji haushinsa ba,daga qarshe ta tattara laifin ta azawa kanta,saboda tasan kuskure ta tafka ba qarami ba,tafi kowa sanin halinsa,ita kanta batasan zata iya aikata hakan ba,amma SO DA ZUCIYA saidai a barsu kawai. Sanda ya isa sashensa cook dinsa ya gama shirya table dinsa,gurin kawai zaka dauka wani gurin cin abincin shugaban qasa ko wani governor ne,ya samu sajjad har yayi wanka ya sauya kaya daga cikin bedrooms din dake sassan,a nan yabar fadeela ya haura sama shima don ya watsa ruwan. Minti talatin da wani abu ya kammala shima ya sauko,cikin fararen pajamas marasa nauyi masu ratsin baqi kadan,mutum ne meson amfani da fararen kayayyaki,kusan first choice dinsa a color fari ne. Tare da tab dinsa ya sauko,ya samu tuni sunyi ready saman dining sai yayi joining dinsu. Yau kam babu laifi a sake yake,hakan kuma sajjad yasan baya rasa nasaba da alamun dorewar lafiyar fadeela. Suna kammala cin abincin aikin kamfanin da bayanan da jibril ya turo masa na taron yau ya saka a gaba yana dubawa. Shima sajjad din aikin yake ragewa,kowa hankalinsa yana kan na'ura,don haka falon ya dauki shuru. Sajjad ne ya fara motsawa,ya jawo wata folder ya tura gabansa,ya daga kai yana dubana alamun neman qarin bayani "Folder din president ce" qaramin tsaki toufeeq yaja,ba tare da yabi takan folder din ba yaci gaba da aikinsa. Tsam sajjad ya dakata yana dubansa "Wai me kake nufi?,wannan folder din ita ya kamata ka fara dubawa kafin ka duba komai fa" "Bani da lokaci" ya sake amsa masa a taqaice,sai kawai ya qyaleshi bai sake cewa komai dashi ba. Ba jimawa bacci ya dauki fadeela,ya tattara komai ya ajjiye,ya dauketa da kansa yabi ta siririn balcony da shi da fadeelan kadai ke amfanin dashi,ya bulla sassansu. Cikin falon ya samu baaba ramatu,su uku ne,ita da mai gyaran dakin fadeela zuwa sashen wato mabruka,da kuma wadda ke musu girki wato zuwaira,suna zaune suna hira,da alama daukewa baaba ramatu kewa sukeyi. Shigowarsa a sabe da fadeelan sai duka suka miqe,zuwaira da mabruka kawunansu a qasa suna masa barka da dare,baba ramatu kuma ta qarasa tana karbarta daga hannunsa. Idan da sabo ta saba,muddin yana gari ba kasafai fadeela ke zama suci abincin dare tare ba,yawanci sai dare idan tayi bacci yake kawota,idan kuma dare yayi sosai kwana takeyi a wajensa. Kafin baba ramatun ma ta gama karbarta zuwaira da mabruka tuni sun fece,mugun kwarjini yake musu,girmansa kuma suke gani sosai da har basa iya tsaiwa guri daya da shi idan ba shi ya nema hakan ba. Da kansa ya rarrage kayan wutar dake falon kafin ya juya ya fice shima. Inda yabar sajjad ya dawo ya tarar dashi,sai ya duqa ya tattare kayayyakinsa ya wuce daki bayan sunyi sallama. Saman bedside table ya ajjiye komai dake hannunsa yana dan sauke numfashi na alamun gajiya,ya cire bedroom slippers din qafarsa ya doshi qofar toilet. Alwala ya daura,sannan ya shimfida abun sallah ya tayar da sallahn. Cikin awa guda ya kammala komai,a maimakon ya hau saman lafiyayyen gadonsa dake lullube da tattausar shimfida,sai kawai ya jawo manyan duvets din dake kai har guda biyu ya shimfidasu a qasa ya sanya pillow,saidai yana kwanciyar yaji kaman ya kwanta akan wani abu. A nutse ya miqe yana duba wajen. Ido ya lumshe sannan ya bude yana furzar da iska "Sajjad......inda maye ne ya kamani bazai sakeni ba" ya fada can qasa,ya zaro folder din,har zaiyi jifa da ita ya fasa,ya jawo bedside drawer ya jefa a ciki ya rufe ya maida kansa ya kwanta. Baiyi cikakken awa uku ba ya farka a firgice sosai,saidai duk da haka bakinsa yana dauke da kalmar "La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" wani irin birkitaccen yanayi,hautsinannen mafarkin da baya rufa wata biyu baiyi shi ba. Ci gaba yayi da maimaita addu'ar,har ya samu dukka nutsuwarsa ta dawo,saidai jikinsa ya jiqe sharkaf da gumi har ta tsakiyar gargasar dake kwance a hannunsa qirjinsa zuwa qafafunsa,ya miqe a hankali ya doshi toilet. Alwala ya daura bayan ya kama ruwa,yayi tsaye a gaban madubin bandakin yana ci gaba da watsawa fuskarsa ruwa,sunayen mutum biyu suna masa yawo aka tare da mafarkin daya gama yi yanzun nan a kansu "Maji,ameesha" FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 23 Ya motsa bakinsa a hankali yana maimaita sunan,me yasa yake yawaita maimaita mafarkinsu?,ameesha tuntuntuni ya gama rufe babinta a rayuwarsa.....maji fa?,yasan babu ta yadda zai iya cire jininta daga jikinsa,amma yawaita mafarkin nata a yanayin da yasan a zahiri ba haka rayuwarta take ba shine abu mafi daure kai a wajensa. Har sai da yaji idanunsa suna dan masa yaji yaji sannan ya kulle famfon,ya jawo towel ya goge fuskarsa data qara wani haske,ya fito a hankali daga toilet din zuwa bedroom dinsa,baccin da bai samu ya koma ba kenan,daga qarshe ya matsa ya koma saman sallayarsa ya sake kabbara sallah.....boyayyar rayuwarsa kenan da ba kowa bane yasan hakan. Washegari da wani irin weakness ya tashi,babu karsashin nan da kuzarin da ya saba wayar gari dashi duk safiya,saidai makara da yayi bai fito lokacin daya saba fitowar ba,don a sanda ya fito din tuni fadeela ta wuce makaranta. Cook dinsa yana tsaye yana serving dinsa,yayin da shi kuma yake danne danne a wayarsa,sallamar hajiya qarama ta karade falon,sanye take da wani lace na alfarma,wanda ke nuni da zallar tsadar da yake dashi,a kallon farko zaka karanci mutum ce me izza tare da son komai na alfarma da kerewa sa'a,don a iya takun tafiyarta ma kawai ya nuna haka. Kujera daya taja ta zauna cikin kujeru shiddan dake zagaye da mulmulallen dining table din me wani irin siffa da tsari,a gurguje Noah cook din nasa ya kammala zuba komai bayan ya zube a qasa ya gaidata,ya sauka da sassarfa yana barin parlor din zuwa kitchen don ya tsaftaceshi hadi da kammale komai kamar yadda ya saba a duk sanda ya kammala girkawa uban gidan nasa abinci,daya daga cikin dokokinsa daya kafa masa akan tsafta ne,baya qaunarta sam sam,sai kuma akayi sa'a shima Noah din gwanin tsafta ne dama. "Kunyi waya da maji kuwa a kwanan nan?" Ta tambayeshi da kulawa,kamar ya dago kansa ya kalleta saboda ambatar sunan da tayi,wanda hakan ya tuna masa da mafarkinta da yayi a daren jiya,sai kuma yaci gaba da diban chips da yakeyi a fork "Bamuyi ba,bata kirani ba" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke,duk da hakan batajin nutsuwa a tattare da ita,shurun maji ta tabbatar bawai yana nufin tabar mata toufeeq bane,hakanan a duk sanda shurunta ya tashi maido da amsa......yana magana ne cikin amo da amsa kuwwa me qarfi,irin qarfin da ita kanta takejin sautin saman jiki da zuciyarta. Ta sani,ba sanin jiya ko yau ba......itadin jarumar macace,wadda bata yarda da faduwa saarewa ko gajiyawa ba,wannan dalilin ne ya sanya har yanzu burinkan mommy qarama ya gaza kaiwa ga gaci,duk da ta cimma nasara da galaba masu yawa a kanta "Ka qoqarta kayi kiranta" kai kawai ya gyada mata,shuru ya sake ratsa tsakani,tana mamakin yadda har yau bai iya doguwar hira da ita ba,duk da tana data cewa da yawa cikin al'amuran rayuwarsa "Nace ba" ta sake fada tana fifita masa tea din don ta saisaita zafinsa,qwayoyin idanunsa kawai ya daga ya kalleta ba tare da yace komai ba har zuwa sanda ya janyesu. Janyesun da yayi ne ya qara mata qwarin gwiwa,idanunsa na dabanne,haka kallon dake cikinsu,suna da kwarjini wanda har yau idan ya dubeta tana jin hakan sosai yana tabata "Yaruwarka HASEENA,nace kuna gaisawa kuwa?" Sosai tambayar tata ta bashi mamaki,ita kanta daya kalleta sai taga tambayar kamar bata hau dai dai ba,tunda tasan kome yake akwai tsakaninsu "Bani da lokacin biyewa shirmenta" ya amsa a taqaice. Yanason ya bawa hajiya qaraman haske amma kuma shi din bame sanin yadda zaiyi magana me tsaho bane,a ko yaushe yakanyi magana ne a dunqule,indai bamai matuqar muhimmanci ba,shine zai zauna bayani. Murmushi hajiya qarama ta saki tana tura masa cup din tea din "Me kakeso na gayawa daddynka?" Ta sake jefa masa tambayar tana dubansa. Bai amsa ba har sai daya kusa cinye abinda ke bakinsa sannan ya miqe alamun ya gama kenan "Ya kamata ya fahimceni don Allah" shine amsar daya bata,saiya ciri tissue guda daya ya soma sauka,da kallo ta bishi,sannan daga bisani tace "A dawo lafiya,Allah ya tsare" taci gaba da kallonsa har ya fita daga dining room din. Dubanta ta dawo dashi inda ya tashin,ta jijjiga kai,sai kuma murmushi ya kubce mata,tadan daki table din kadan sannan itama ta miqe ta fice a nutse cikin qasaitaccen takunta. ***********Kamar kowanne lokaci,yau yadan saba lokacin dawowarsa,don bai shigo gidan ba sai bayan sallar magariba,bayan sun tsaya sunyi sallah a masallacin dake gine daga farkon layinsu. A kullum itace mutum ta farko da yake fara nema idan ya shigo gidan,yau dinma hakanne,sassansu ya wuce kai tsaye,ya samu baaba ramatu tana gyara kayan ruwa lemo da ice cream kala kala da yake zubewa fadeela a fridge din. "Barka da dawowa yallabai" tafada cikin mutuntawa,cikin girmamawa shima ya amsa mata,tun kafin ya tambaya kuma ta amsa masa "Tana ciki ita da hajiya qarama" ta nuna hanyar da zata sadashi da bedrooms dinsu,baice komai ba yaci gaba da takawa da 'yar sasaarfa zuwa dakin,yanajin yadda gajiya takebin gabbansa. A nutse tare kuma da sallama ya tura qofar dakin,hajiya qarama na tsaye goye da hannayenta,fadeela da sabuwar nannynta na daga bakin toilet,nannyn tana tsane mata jiki da towel. Sallamarsa kadai ta zaburar da ita,ta watsar da towel din ta tako da gudu,sai ya durqusa mata kamar yadda ya saba,ya bude mata hannayensa ta shige tana fadin "Oyoyo" murmushi hajiya qarama ta saki "Shikenan,mun huta da complain din daddy yayi late" siririn murmushin da ba kasafai ake ganinsa akan fuskarsa ba ya saki,wani irin sirrintaccen kyansa ya bayyana "An dawo lafiya?,ina nan ina sake nunawa nannynta yadda zata dinga kula da abubuwa,bana fatan a sake samun matsala daga kanta" hajiya qarama ta fada,sai ya jinjina kai,yana maida hankalinsa ga fadeela data dauko wani kwali ta miqo masa "Mommy qarama ce ta bani,kai nake jira ka dawo ka hadamin" karban kwalin yayi hannu bibbiyu "I hope kince mata kin gode?" Kai ta gyada cike da zumudi "Good,me zai hana ki bawa mommy ta qarasa ladanta?" Kafada ta noqe,kafin tace komai ma mommyn ta daga hannunta sama "Inaaa,wannan kuma aikinku ne,nidai na gama nawa tunda na cika alqawari" ta fadi tana dariya gami da nufan qofa "Allah ya bamu alkhairi tunda tsohonki ya dawo ai kuma shikenan" ta fadi tana ficewa daga dakin. Duk yadda yaso fa barshi yaje yayi wanka yaci abinci sannan a hada qin yarda tayi,abu daya ta bari akayi,ta kira nanny din nata,tazo ta saka mata kaya,tana riqe da kwalin suka fito zuwa sassansa. Ta harabar gidan suka sake fitowa maimakon yayi Linkin ya bulla ta sassan nasu,tana gaba yana biye da ita,dai dai sanda qaramar motar da aka gama parking dinta yanzu ke budewa. Labiba ce ke fitowa,sanye da wani skinny jeans da shirt mai gajeran hannu, high heels ne a qafarta me azabar tsini kamar idan ka takashi da kyau zai iya karyewa,yalolon mayafi ne saman wanda baida maraba da mayafin yaran da shekarunsu ba zasu zarta tsakanin uku hudu zuwa biyar ba "Hi fadeela" abinda ta fada kenan,idanunta a kansa tana jin wani qunci a ranta,duba daya yayi mata,kallon da bata tunanin ya b'ata second uku yana yi mata shi,ya dauke kansa kamar yaga wani abun qyama "Hi" yarinyar ta maida mata,sannan ta taka da hanzari tabi bayan babanta da yayi gaba tuni tana kiran ya jirata. Tsaye tayi a wajen har suka bace mata,sai a sanann ta samu qwatar kallonta daga kansu,taja wani dogon tsaki "Yarinyar sai shegen rashin saurin yarda da sabo fal cikinta,ta kwashe halin tsohonta tsaf" tayi maganar cikin salon mita tana maida murfin motar ta rufe,sannan ta saka mata key tana takawa cikin gidan,zuwa yanzu ta fara tuqewa,zuciyarta ta fara gazawa daga yadda ganinsa yake neman fara yi mata wuya,ta jigata sosai da yadda a yanzun ya sake daure mata fiye da baya. A baya koda zai watsar da ita,koda bazai kulata ba,koda bazai kalleta ba amma bazai kyaret ba,bai kuma taba shata mata layin zama inda yake ba,saidai yayi kamar baisan da ita a wajen ba,ita kuma ko babu komai iya hakan ma tasan wata alfarma ce ta samu,wadda dubban matan dake yawo,suke kamar zasu mutu a kanshi basu samu hakan ba,ko babu komai tana samun daman zama ta kalleshi iya son ranta. Sai daya tsaya ya hada mata komai,ta sake tubure masa sai daya zauna suka fara yi tare sannan ta barshi ya shiga ciki,wanka ya fara yi,ya dawo ya shirya cikin gajerun pajamas. Yana tsaka da taje kansa wayarsa ta dauki tsuwwa. A nutse ya jawo wayar yana duba me kiran,MAJI shine ya bayyana saman screen din,sai ya ajjiye comb din hannun nasa,ya jawo stool ya zauna akai yana daga kiran. Sassanyar muryar dattijuwar,dake cike da wani irin amo dake nuna zallar sanyinta koda a yanayi na halitta ma,tayi cikakkiyar sallamar data saka zuciyarsa dokawa,ya lumshe idanunsa yana amsa sallamar tata,tare da qoqarin tuno watannin da ya shafe ba tare daya kirata din ba "Ka manta dani ko moha?" Ta kirayeshi da sunan da ita kadai ke kiransa dashi,kuma koda a wani guri yaji wannan sautin ya tabbatar ita dince,ko kuma wani dake da alaqa da ita. Cikin tsananin jin kunya da nauyinta ya motsa labbansa "Kiyi haquri" ya fada a sanyaye,qaramin murmushi ta saki,ta saba da jin wannan kalmar ta ban haquri daga bakinsa,har batasan iya adadi ba,bada haqurin da kuma ba wai yana nufin ya daina bane,wani abu ne da yake faruwa tsahon shekaru masu yawa,wanda batasan ranar yankewarsa ba,duk da cewa idan har ta bugi qirji ta kuma daga hannuwanta da sunan samun nasara ba shakka batayi laifi ba. Cikin wani irin rashin sakewa da kuma rashin sabon da baisan daga ina yake taso masa ba a duk inda suke waya ya fara gaisheta,saidai kuma cike da girmamawa ne "Ina fatan komai yana lafiya?" "Alhamdulillah" "Ma sha Allah,kada kayi wasa da addu'a a dukka wani gaba ta rayuwarka,komai yana da lokaci,kuma nan kusa nake fatan samun wani haske da fatahi daga rayuwarmu gaba daya,ina jikata?" Ta tambayi fadeela cike da shauqin son jin muryarta,wata irin qauna me gauraye da tausayi takewa yarinyar. 'Yar halak din kamar tasan ita ake nema kuwa,sai gata ta buda qofar dakin riqe da games dinta tazo kawo qorafi. Kai tsaye ya miqa mata wayar "Maji ce" ya fada qasa qasa,saita ajjiye kayan hannun nata duka a qasa,ta tako da sassarfa ta karbi wayar. Gefe ya koma ya harde hannayensa yana kallon yadda suke waya da maji,kamar sun san juna sosai da sosai,duk da batasan maji ba,amma akwai wanda wani irin sabo tsakaninsu qwarai da gaske,tasan maji a baki kamar me. Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/17, 6:49 PM] +234 806 578 4295: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 24 Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela. Sun jima kafin daga bisani suyi sallama,ta kawo masa wayar,fuskarta qunshe da murmushi "Daddy,wai a ina maji take?" Ta jefa masa tambayar da baiyi zaton jinta daga bakinta ba "Bata a nan qasar angel" "Tana ina?" Ta sake tambayarsa,da alamar da gaske tanason jin a inda take din "Algeria" "Yaushe zamuje daddy?,tanason ta ganni nima inason na ganta" ta tambayeshi a shagwabe. Ido ya zuba mata sosai,shi kansa a yanzu bazai iya kai kasa kai tsaye inda maji take ba,tun haihuwarsa har girmansa bai taba zuwa,a baya yana da kwadayin zuwan,amma a yanzun kwata kwata babu wannan cikin ransa,baisan kuma yaushe hakan ta faru ba,kawai dai ya tashi ne dare daya yaji yayi loosing interest akan dukkan abinda ya shafeta,kafin daga bisani kuma ya yakan yawaita samun mantuwa akan komai daga danganceta. "Zamuje angel" "Daddy yaushe?" Ta sake tambayarsa tana kafeshi da idanu,idanunsa ya janye daga kanta,murmushi kadan yana subuce masa,ya fuskanci rigima takeji "Wata rana" ya bata amsa yana sanya hannuwansa ya dauketa cak hadi da cewa "Muje muci dinner" zata sake magana ya dora yatsansa akan lips dinsa gami da cewa "Shshshsh,ya isa" duk da qanqantarta amma tana gudun abinda zai bata masa rai,tana matuqar jin maganarsa fiye da tunani,saita kwantar da kanta a kafadarsa,a haka suka qarasa dining room din. Sallamar cook din nasa dake jiran ya iso yayi serving nashi yayi,da kansa ya zuba musu iya abinda zasu iya ci shi da fadeelan yabar sauran. *********Karfe daya na rana ne,lokacin da kowanne ma'aikaci dake qarqashin company din yake morewa lokuttansa na break. Dai dai lokacin da sãahar a cikin nata office din ta duqufa wajen ganin ta gama hada dukka bayanan data samu daga financial team na company,tana duba yiwuwar yin magana akan document dinta dake office na CEO,batason tayi aikin banza,tanaso ta aiwatar da dukka tsare tsaren da tayi,don ta tabbatar zai kawo gagarumin ci gaba da kuma sauyi cikin company din. Buda qofar da akayi ya sakata daga fararen idanunta tana kallon bakin qofar,mr sameera ce,ta bata izinin qarasowa bayan ta janye hannuwanta daga kan system din "Ranki ya dade,sir hamza ne ya sake dawowa" idanunta da suka dan daure saboda kallon allon system din tadan juya kadan,qaramin tsaki taja,hamzan yanason shiga rayuwarta,kaf fadin company din a yanzu bata da wata matsala saishi,yaqi fahimtar inda tasa gaba,gaba daya sake shige mata yakeyi a kowanne lokaci,don kawai office dinta yana da alaqa da department dinsa,don ko yanzu report din da take dubawa daga office dinsa ya fito,banda haka da tuni ta yanke dukkan wata alaqa da zaya bashi damar ganinta "Ki gaya masa ba yanzu ba,aiki nakeyi,ya tura kowanne saqo ta email din office,zan duba sanda na zama available" jinjina kai sameera tayi,ta juya ta fice. Cak ta tsaya da aikin da takeyi tana sake jan wani dogon tsakin da yafi na farko,saita tura kujerarta baya tana dan fidda iska daga bakinta,da alama wani tunani ne ya darsu a ranta lokaci daya. Yatsunta tasa tana murza goshinta dasu,tana tuna shigowarta company a safiyar dazu,yadda ta tadda employee a dan hautsine,sakamakon korar wasu ma'aikatan guda uku da ceo yayi a safiyar "wanne irin mutum ne shi?,me izza da dagawa?,he doesn't give excuse to anyone?,abu kadan kora?,kowa ma yana iya kora ko yayi masa fada?" Tayi maganar can qasan zuciyarta,haushinsa da kuma tsanarsa suna huda zuciyar tata,abinda ta lura dashi ma,gaba daya yafi zafafa al'amuransa akan mata. Sake jan wani dogon tsakin tayi karo na uku,gaba daya tuna abin da ya farun yasa tayo loosing interest akan aikin,ta duba baqin agogon dake daure a tsintsaye hannunta qirar kamfanin Casio,akwai ragowar mintuna talatin kafin lokacin komawa bakin aiki yayi,coffe take da buqata,amma batason takura mr sameera,don haka ta tsugunna a hankali ta daura igiyoyin baqon takalaminta daya mugun haska farar qafarta me dauke da dogayen yatsu,ta miqe a nutse ta dauki iya wayarta ta fita a office din. A nutse take takawa a farfajiyar gurin,cikin girmamawa ma'aikatan ke gaidata,saboda Suna respecting nata sosai,duk wanda yayi mu'alama da ita kuma kusan sai ya fadi halinta ya kuma yi mata shaida me kyau. Ko kusa ko alama bata ga koda inuwarsa ba,saijin maganarsa tayi a bayanta "Ranki ya dade,barka sa fitowa" mr hamza kenan,wanda ke biye da takunta yana son ya cimmata cikin zumudin da katarin ganin fitowarta da yayi. Kadan ta waiwaya ta aje masa kallo daya "Ya kake?" Ta fada a daqile,hamza na daya daga cikin mutanen dakeson zame mata barazana cikin company din,tare da yi mata kutse cikin walwalarta da al'amuranta,duk wani hanya da zatayi avoiding nasa tayi,amma ta karanci kamar baya fahimta,da alama yana sahun mazan dake da shegen naci da kafiya ne "Lafiya amma ba qalau ba,please ki taimaka ki gayawa secretary dinki,ta daina min shamaki da ganinki,wallahi it really hurts me" sunzo bakin qofar kitchen din,kuma bata da buqatar yaci gaba da binta,don haka ta dakata,ta juyo gaba daya tana dubansa "Excuse me mr hamza.....ko zaka taimaka ka juya,saboda banason ka shigarmin lokacin nawa hutun,na gaya maka idan maganar office ce ka tura ta email zan duba,idan kuma bata office bane, please i beg you,banason wani abu da bashi ya taramu a nan ba ya hadani da kai,bama kai ba,koma waye bana buqatar wata hulda ko alaqa" da hanzari ya buda baki zai maida mata da martani,amma sai taji yayi dif,batasan dalilin daukewar wutarsa haka lokaci guda ba,amma koma meye sanadi ita ba damuwarta bane,don dama tafi buqatar shirunsa akan amsarsa,don haka ta juya ta shige kitchen din kanta tsaye. Wayam din data gani a kitchen din babu kowa da kuma qarancin haskensa bai sanya ta zaci akwai wani abu ba,saboda wannan shine karon farko data taba shigowa kitchen din. Coffe dama kadai tazo nema,don haka ta nufi mini coffee maker din data gani a jone,data duba sai taga akwai saura a ciki,don haka ta ciri mug guda daya,ta cikashi dashi,yawunta yana tsinkewa,saboda wani qamshi da taji yanayi na musamman,uwa uba kuma kana kallonsa zakasan ya hadu iya kwadayinka da shan coffee. Dan qaramin murmushi ta sauke,saita gyata tsaiwarta tana kai mug din bakinta,dai dai sanda ta juyo. Babu zato ta saki mug din,cikin razana taja baya,fararen idanunta suna sake girma hadi da fitowa waje. Tsoratar da tayi yasa bata iya tsaiwa ta tantance waye ba tayi qofar waje da sassarfa,saidai kuma tana dab da isa ya rigata isa gurin,ya saka hannu ya tura qofar ya rufeta bam,taja birki a mugun hautsine tana sauke dubanta a kansa,sai a lokacinne ta gane waye. MT jarma ne da kansa,cikin shigar suit dinsa ta ko yaushe,saidai kuma a yau din babu suit jacket din a jikinsa,alamu suna nuna ya barota a office,hannun rigar ciki da ya kasance dogo ya tattareshi ya barshi iya gwiwar hannunsa,wannan ya bawa murdadden hannunsa dake cike da gargasa da wasu irin jijiyoyin da yawan shiga gym ya haifar dasu. Kwantacciyar sumarsa me santsi a dan hargitse take kadan,lips dinsa sundan sake yin jaa saboda zazzafan coffee din da yake sipping a hankali. Ko a yanzun ma da yake tsaye ci gaba yayi da sipping abinsa cikin nutsuwarsa da kamewarsa,kamar bashi ya tsorata ta ba,sanann yasa hannu ya garqame musu qofa haka kawai ana zaune qalau. Ranta ne taji yayi mummunan baci,tadan motsa fuskarta kadan saboda yadda zafin coffee din data saki ya dan taba qafarta yake mata zafi kadan kadan,wannan wacce irin dabi'a ce zai samu guri ya zauna a kitchen,a corner din da ba lallai kai ka iya ganinsa ba?,saita janye idanunta ta taka zuwa qofar don ta bude ta fice,don bata qaunar hada rufi daya dashi bare taci gaba da zuqar qamshin turarenta da yake neman sanyaya dukkan wani zafi data dauka akan abinda yayin. Table din dake daura dashi ya matsa kadan ya dora cup din,cikin zuzzurfar muryarsa dake cakude da wani irin amo me ya soma magana "You must learn saying salam a duk wajen da zaki shiga,saboda nan din mudai musulmai sunfi yawa......sannan bari na taimakeki na tuna miki wani abu daya,nan masana'anta ce,kayi aiki a biyaka da gwargwadon wahalarka na wata daya,ba waje bane da aka bude saboda soyayya ba,saboda haka ki kiyayi bawa wani damar ganinki a office da kebantacciyar buqatarku wadda bata da alaqa da company,idan ba haka ba,you will loose your job" ya qarasa maganar yana dora hannunsa a mariqin qofar,ya budeta sannan yace "Dont try to do this again......inda kin fita a yadda kikaso fita,wani ya ganki me kike tunani zai zata" bai jira amsarta ba ya taka zai fita, zuciyarta tazo mata iya wuya sosai. Yama gama raina mata hankali,yaso qona mata qafafuwa,sannan kuma ya bita da wasu sharuddansa marasa amfani a gurinta,tunda dai ai ita ba yarinya bace,tasan meye ya dace da ita. Ji tayi idan ya fita ba tare datace masa komai ba tabbas yaci bulus,duk da zuicyarta na qoqarin tuna mata maganganun yaa Saifullahi da yaa zaid na ta girmamashi,gaba yake da ita "Shi kuma wannan kullemu da kayi fa?,idan wanin ya gani yace me?" Ta fada tana jin takaicin yadda tayi dogon zama a guri daya dashi,harta shaqi turarensa da kyau,ya shiga kowacce kafa ta hanci da kwanyarta. Waiwayowa yayi ya zube mata manyan kewayayyun idanun nasa dake da wani irin magnet da kwarjini,har sai dataji kamar zata zube,yayo taku biyu ya dawo baya kadan "Kina iya gayawa duk wanda ya tambayeki..... nayi raping naki ne,don wanann din kadanne daga aikinku". "Ya salam" ta fada can qasan zuciyarta hade da wani mugun bugawa da zuciyar tata tayi,ba kuma tare data shirya ba ta koma da baya ta zauna saman kujerar dake kusa da ita,wanda tayi yaqinin banda taimakon Allah kujerar tana kusa da ita lallai zata iya faduwa qasa. Kamar baice komai ba ya juya a nutsensa ya fita a kitchen din. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/17, 6:49 PM] +234 806 578 4295: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 25 Wasu hawaye masu zafi taji sun cika mata idanu,qarshen cin zarafi yayi mata shi,FYADE ai ba qanqanuwar kalma bace da furtata zai zama abu me sauqi har haka ba,kadan daga aikinsu me yake nufi kenan da ita?,kawai saita kasa riqe hawayenta,ta barsu suka silalo ko zata samu ganin gabanta da kyau,tun bayan abinda adam yayi mata.....ba wani mahaluqin daya taba mata kalma me tsananin daci zafi da qasqantarwa irin haka ba,sai ta miqe kawai a gaggauce tana fita a kitchen din,har ranta tana jin tsanar shi kansa kitchen din,da kuma dalilin daya kawota. Tana fitowa a hanya suka hadu da sameera,ta tareta da yanayi ya dan rudani kadan "Ance kitchen kika tafi,inata qoqarin tsaidaki saboda time ne na shigan sir kitchen din yayi lunch,karkije a samu matsala" "Ba'a samu ba,gashi na dawo" ta bawa sameera amsa a taqaice tana wuceta. Toilet dinta ta fada tana sake rage qwallar takaicinsa data sake taruwar mata,sai data kusan minti goma kafin tayi controlling kanta,ta daura alwala ta fito ta tayar da sallah,tana sake jin tsanarsa qwarai a ranta,tana kuma sake tabbatarwa da kanta shi din wani irin mutum ne mara iya mu'amala da gautsin harshe. Ko bayan ta idar zamanta taci gaba dayi saman abun sallar,duk da akwai sauran ayyukan da takeson gamasu a yau din,a haka miss sameera ta nemi izinin shigowa. "Boss ne yake neman izinin ganinki" tunda tace boss ta gama fahimtar waye,abun sai ya girmame mata,dr Ahmed da kansa yafi qarfin neman izini wai don zai shigo office dinta,da sauri ta tashi saman abun sallar tana dubanta "Yafi qarfin neman izini miss sameera,maza bude masa qofa" saita juya a gaggauce tana murmushi,tabbas sãhaar din batasan waye boss ba,da batayi mamaki ba don ya nemi izinin shigowa ba. Cike da tarin haiba kwarjini da kuma kamalarsa yayi sallama,saita miqe tsaye tana masa sannu da zuwa tare da nuna masa gurin zama,da kanta ta bude qawataccen fridge din dake office din ta ciro masa ruwa da lemo masu matsakaitan sanyi,kasancewar ita dinma ba mai yawan shan abu me sanyi bace "Na gode sosai diyata" ya fada yana yaba dattakonta,da yadda take da girmama manya tare da sanin kimarsu. Ita kunyar godiyar ne ya kamata,tana neman gurin zama yace da ita "Ya ayyukan?,ina fatan kina jin dadin aiki da yayan naki?" Qaramin murmushi ta kuma saki,kanta a qasa tace "Alhamdulillah abba" "Ma sha Allah,na sanshi sarai,wasu lokutan bashi da kirki,yana da zafin zuciya,amma kuma yana da tausayi" kai ta jinjina tana kokwanton tausayin da Dr yace toufeeq yana dashi. Ruwa kadan yasha,sanann suka fara tattaunawa kan sabbin ci gaban da aka samu cikin company din,daga bisani yace "Sajjad ya gayamin,akwai kundin da kika bayar,ya gamsu da ayyukan ciki,ya kuma yimin bayani,amma har yanzu banga an aiwatar da komai ba" "Tuni na miqa su ga office din ceo muna jiran sign dinsa" "Kina da copy dinsa a gurinki?" Miqewa tayi a nutse,ta buda computer ta kawo masa gabansa. A nutse ya dinga karanta komai, "Ma sha Allah,ma sha Allah" kawai bakinsa yake furtawa,baiko kai ga qarasawa ba ya dago kai "Akwai ideas masu kyau da muhimmanci a nan,zaifi kyau a saka hannun da wuri,inaji a jikina za'a samu cimma gaci yadda akeso" sosai taji dadin yadda ya yaba mata din,har ta rakashi yana mata addu'a gami da sanya mata albarka. Lokacin tashi yana cika ta baro office dinta,kai tsaye ta sauka zuwa qasa,tana daga cikin sahun farko na ma'aikatan da suka baro office dinsu,don haka gurin ba cikowar masu daukan ababen hawansu. Hakan dama takeso,tayi ta fice kafin wancan mayataccen ya isketa,sam baya yin fushi ko kuma zuciya game da dukkan abinda zata gaya masa. Sau uku tana qoqarin kunna motar amma taqi kawo wuta gaba daya,abun ya bata mamaki ya kuma daure mata kai,tunda dai tasan lafiya lafiya ta tafi ta barta. Ta gwada dukkan wata dabara amma taqi,dole ta fito ta rufe motar,ta fidda wayarta tana gwada kiran mechanic dinsu,tana masa bayanin abinda ya faru,tare da kwatanta masa kamfanin,kamfanin ba wani boyayye bane,don haka yace yana zuwa nan da minti arba'in zuwa awa daya. Sauya akalar kiran nata tayi zuwa ga number afifa,bugu biyu ta daga "Bestie,kin tashi daga aiki ne?" "A'ah,sai sixs,wani abu ne?" Lumshe idanunta tayi cikin damuwa "Motana yaqi tashi,baisan meye damuwarta ba,kuma banason fita neman abun hawa na haya" "Subhanallahi,to ba damuwa,bari zan iso kamar nan da awa daya saina daukeki,kinga na rage time din tashin kada ya zamana na fito da wuri" "Okay,thanks" ta fada tana tsinke kiran. Da isowar mechanic din dana afifa tana sanya ran yayi lokaci daya,ta dubi agogon hannunta sannan ta sauke tana duban building din,ma'aikata sunata fitowa kowa yana kama gabansa,batason komawa can saman nan,don haka ta yanke ta wuce executive garden dake kamfanin ta zauna ta jirasu a can,da wannan shawarar ta karkata akalarta zuwa can din. A nutse ta durfafi gurin,yanayin wajen yana sake burgeta,da alama yana samun kyakkyawar kulawa. Sanya qafafunta kenan sautin muryarsa shine abu na farko daya fara ziyartar kunnenta,kafin daga bisani idanunta su sauka a kansa,dai dai lokacin da shima dan motsin da yaji ya sakashi daga kai,idanunsu suka sarqe waje daya,yana daga tsaye hannunsa guda daya cikin aljihunsa yana magana da wasu mutum biyu da bata gane ko su waye ba,saboda suna dan gaba kadan dashi. Qaramin tsakin da batasan meye dalilin yinsa ba ta saki,kawai dai tasan taji haushin ganinsa a wajen,ya kuma bata mata budget din da tayi na sakewa ta zauna a wajen ta jirayi afifa,saita juya a nutse tana fita a wajen. Dif maganar da yakeyi ta dauke,ya lumshe idanunsa a nutse yana jin wani irin bacin rai na taso masa,idan har dai dai kunnuwansa suka jiye masa,sautin tsaki ya jiyo,wanda yaga alamun fitarsa daga dan qaramin bakinta data turoshi gaba lokacin da take hada sautukan tsakin. Ransa ne yaji yayi wani mugun baci,tunda yake zai iya cewa ba wata diya mace data taba masa tsaki,tsakinma mara dalili,haka siddan saboda ganin araharsa?,nan take yaji bazai iya tolerating ba,don ya gama fahimtar kamar tana daukan kanta wani abu,tana da ji da kanta over. Sam basu lura da barin wajen yakeyi ba har sai da yakai qofar fita,cikin daga murya sajjad yace "Hi man......ya kamata mu gama kafin mu wuce fa" "One minute" kawai ya iya ce masa,idanunsa na biye da ita,duk da cewa ta danyi masa nisa kadan. Sai ya qara yawan takunsa,mutum ne ingarma me yawan kuzari,ga kuma tsaho da yake dashi,wannan ya taimaka masa nan da nan ya rage tazarar dake tsakaninsu,wanda sam bata sani ba,ta yanke shawarar ta buda office dinta kawai ta zauna ta jirayesu acan,ko hawa na nawa ne ta gwammace ta koma ta jirasu,akan dai ta sake ganin fuskarsa. Hankali kwance elevator ta bude mata ta shige,tana shirin komawa ta rufe shima ya shigo,ta koma ruf ta rufe sannan ta fara aikin haurawa dasu zuwa saman. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 26 Haka kawai taji gabanta yayi mummunar faduwa,kowanne sashe na jikinta yayi sanyi saboda yadda ya zuba mata mayatattun idanunsa,yana jifanta da kallon tsana. Tayi tunanin zata iya jurewa kallonsa kamar yadda ya ritsata da nasa idanun,amma tun ba'a yi nisan zango ba taji ta gaza dauke nauyin zagayyun idanunsan nan masu tsananin haske,kamar ba idanun namiji ba. Gaba daya sai ta jita kamar wadda aka nannade aka jefa cikin wani keji,kamar an sanya igiya an daureta,ta dinga fatan na'urar ta sauketa da inda ta umarceta tayi ta fice ta bashi guri. Saidai kuma suna isa floor din ya matsa gurin madannan ya sake bata direction na dawowa dasu floor din qasa,a sannan ta waiwayo ta sake dubansa da fararen idanunta karo na biyu,still har yanzu ita yake kalla,kallon dake sake bayyana fushin dake kwance a zuciyarsa. Sake janye idanun nata tayi ta maida dubanta wani wajen,gaba daya kallon da yake mata ya wuce qa'idar da jarumtarta zata iya dauka,uwa uba kuma shirin rikicewa takeyi gaba daya,saboda yadda qamshinsa yake sake cika elevator din. Tattara hankalinta tayi tana jiran jin sun isa,ta riga ta gama ayyanawa a ranta suna isa zatayi hanzarin ficewa,don ta fuskanci kamar ya shirya tayita yawo dasu daga sama zuwa qasa,can can qasan ranta tana tuna tsakin data sakar masa. Da wani irin hanzari ta nufi qofar da zummar fita,amma kuma kafin ta isa har ya maida qofar ya rufe,ya kuma sake sakata ta lula sama dasu. Wannan karon tsaiwa tayi daga bakin qofar yana lumshe idonta,ranta itama ya soma baci da rainin hankalinsa,ta yaya zayazo ya sameta a waje ya kuma dinga mata wasa hankali?,na meye?,zata tsaya gab da qofa,zataga gudun ruwansa,idan ta fita yasa qarin tuwo ya dawo da ita. Duk yadda taci buri kuwa suna isa sai gashi tsaye bakin qofar,abun yayi matuqar bata mamaki,batasan wanne irin zafin nama gareshi ba "Excuse me mana,fita zanyi" ta fada da siririyar lallausar muryarta "Wa kika yiwa tsaki?" Ya jefe mata tambayar kansa tsaye cikin izza da qasaitarsa kamar wani basarake,duk da yadda yayi mata matuqar kwarjini,amma motsawar tata izzar ta bata qwarin gwiwar amsashi "Da wanda ya tsargu" ta amsa masa tana qoqarin kaucewa qwayar idanunsa,don har yanzu tana cike da takaicin abinda yayi mata dazu a kitchen. "Ko?" Ya fadi wani miskilin murmushin gefen baki na subuce masa,duk da cewa ba murmushi bane na kyautatawa ko jin dadi,amma wani irin sirrin taccen kyau ya bayyana muraran kan fuskarsa,fuskarta yake duba,yanason gano daga inda ta samo wannan qwarin gwiwar tsaiwa ta gwada masa rashin kunya,yayi imanin batasan wane shi ba,amma a yadda ya lura akwai quruciya sosai tattare da ita,qaramin abu kawai zaiyi da zai bata zazzafan warning,ta yadda ba zata sake marmarin maida masa martanin magana ba. Bata taba kawowa ba ko kusa ko alama,kamar a mafarki taji an take dogayen yatsunta da qarfi,sosai zafi ya ziyarceta,ya kuma ratsata tun daga saman qafarta zuwa qwaqwalwarta "Wayyo Allah na" ta fada a jigace "Wa kika yiwa tsaki nace?" Ya sake maimaita mata tambayar wannan karon da wani irin zafin rai,har hakan na bayyana kan fuskarsa "Sa'anki ne ni?" Ya kuma jefa mata tambayar,duk da bata samu damar amsa masa tambayar farko ba "Ko don kinga Dr ya baki damarmaki da yawa kike tunanin kanmu daya dake?" Ya kuma fadi a mugun tsawace,sautin tsawar tasa tana ratsa mata kunne "Bakizan tsaki zagi bane a gurin wanda ya girmeka?" Still dai ya tambayeta yana kallon fuskarta,wadda zufa ta fara wanke goshinta dake lullube da wasu irin gashi masu matuqar santsi "Lemme warn you......daga yau,duk randa kika kuskura kika qara yimin tsaki ko......." Sai ya murza yatsunsa akan fuskarta "Bazan koreki ba,bare kisa Dr yaga baqina,amma sai na ɓarka bakin tsakin,ki zama me d'a'a ga wanda yake sama dake" yana qarasa fada ya dage mata qafar,ya kuma kauce ya bata hanya yana jira ta fita. A wahalce ta tashi daga tsugunnawar da tayi,hawaye sun jiqa mata fuska,wannan shine qarshen cin zarafi da tozarcin da zaiyi mata,ba tare data kalleshi ba ta juya ta fita daga elevator din tana jan qafarta da tayi mata nauyi. Floor din qasa ya sanyata ta maidashi,yana tsaye yana kallon yadda take sauka qasa dashi,sai furzar da iska yake daga bakinsa,yana son ya fifita zuciyarsa daga zafin data dauka. A wajensa wannan din zallar raini ne,ba abinda ya tsana a duniya sama da tsaki,tsakinma a rasa daga gurin wanda zai fito sai mace?,macenma yarinya qarama wadda ya girmewa da shekaru masu dan dama,kuma ma ma'aikaciyarsu dake qarqashinsu,wanda kaf rayuwarsa ba yarinyar data taba masa irin hakan,kawai don ta samu dama daga gurin Dr,ko don tana ganin tana da kyau?, abinda ya gani dazu tsakaninta da hamza ya fado masa a rai,ya dunqule hannu ya kaiwa iska naushi,yana jin tsanar mata na nikuwa a ransa. Ya tsani mata totally, especially masu kyau irin haka,tabbas koda yaushe basu rabuwa da shaidan,babu wani alkhairi sam a tattare dasu sai tarin sharri,bazai bar mr hamza yaci gaba da barar musu da mutunci ba. Har ya saka dayan qafar zai fita yaji ya taka wani abu,sai ya dawo da baya yana duban qasa,wani abu me qyalli ne ruwan azurfa,ya duqa a hankali yasa hannu ya dauke,ya wulla a aljihunsa ya fice. A daddafe ta samu ta isa office dinta,tana budewa ta zube saman sofa ta saki wani nannauyan kuka me cin zuciya,tunda take apart from abinda adam ya aikata mata,ba'a taba tozartata irin wannan ba,saita koma ta kwanta sosai saman sofa din,tana jin zama yayi mata kadan,ta saki kukanta sosai tana share qwalla. A qalla ta kusan minti ashirin a haka sannan taji zuciyarta tayi sanyi,ta miqe ta zauna,dai dai lokacin kiran mahmud ya sake shigo mata,wanda wannan shine kira na biyar da yayi mata. Bata ko saurari wayar ba,ta miqe ta nufi toilet,ta wanke fuskarta da kyau,sannan ta dawo ta tsaya cikin office din ta dauki wasu qananun abubuwa nata ta zuba a jaka,da zummar har abada tabar aiki da kamfanin MT JARMA GROUP OF COMPANY,dama can sunci darajar yaa muhyi da bazata taba iya cewa a'ah ba. Tana shirin jefa wayar a jaka kiran nasa ya sake shigo mata,tuna tayi cewa a yanzun yanayin komai ne bisa iznin daya samu daga gurin mutumin da yafi kowa kima da martaba a wajenta,wanan ya sanya ta daga wayar,ta kuma mara a kunnenta ba tare da tace komai ba "I hope kina lafiya ko?,ko zaki turomin full address na companyn,zan qaraso sai nayi dropping naki a gida idan an bani dama" bacin rai kan bacin rai,tadan cije lebanta tana jin sha'awar sakeyin wani kukan bayan wanda tayi,ita afifa zata yiwa haka?,haka sukayi da ita?,salon kawai ta zubda mata qima da mutunci zata kira wani mahmud wai yayi dropping nata "Karka damu,ina hanyar gida,thanks" tayi maganar a gajarce,saboda batason tayi tsaho har bacin rai da fushin da bashi ya haddasashi ba ya shafeshi. Yau gaba daya sai takejin kamar ba ranar saarta bane,ranta a mugun jagule ta iso farfajiyar company din,kiran mechanic din ya shigo a dai dai,yace mata yana bakin gate din farko,sai tace ya qaraso ciki,ya sameta parking lot na company din. Tun daga nesa ta fahimci motocinsa da motarta ne kawai ya rage a gurin, zuciyarta na sake motsa mata da bacin ransa tana danneta har ta qarasa gurin. Ta matsa kusa da motarta tana amsa kiran wayar musa mechanic,ta gama ta jefa wayar a jakarta tana qunquni. Gaba daya guards dinsa sunyi carko carko a gurin kamar zasuci babu,kowannesu cikin shigar baqar suit ya qame,suna jiransa sanda yake tsaye yana sallama da baqin da ya gama ganawa dasu cikin garden din company din. A gaggauce ta yiwa musa bayani,don ta matsu taga ta fice daga companyn "Idan ka gama ka kaimin ita gida,saika fadamin kudin gyaran" "To idan ba damuwa,bari na fita na taro miki abun hawa mana" ya fada cikin girmamawa "Meye ya samu abun hawan diyar tawa?" Dattijuwar muryarsa ta bayyana a gurin. Waiwayawa sãahar din tayi tana dubansa sanda ya tsaya daura dasu,masu tsaron lafiyarsa na tsaye daga bayansa,hannunsa dauke da mini laptop,yana dubanta cikin kulawa. Har abada yana da wata kima da martaba a gurinta, saboda dattakonsa da kuma girmama dan adam da yake dashi,cikin mutuntawa irin ta uba da d'ansa tace "Yadan baci ne abba,amma yanzun in sha Allah nasan zai gyara" "Subhanallah,ashshsha,to yayi,ammm.....amma ame zaki koma gida?" "Zan qarasa titi,zan samu abun hawa" kai ya girgiza,sannan ya yafito daya daga cikin guards dinsa ya masa magana qasa qasa,ya zabura da hanzari don cika umarnin ogansa yayi gaba. Rusunawa yayi daga bayan toufeeq daketa amsa waya,ba tare daya katse wayar ba ya waiwayo yana dubansa,tsaf har ya gama gaya masa saqon BOSS "Okay" ya fada yana sauke wayar,ya taka a hankali don amsa kiran mahaifin nasa,masu tsaron lafiyarsa suka motsa da zummar binsa,ya tsaidasu ta hanyar umarni da hannu. Yana takawa zuwa inda suke tsayen ita da Dr ahmad jarma,idanunsa zube fes a kanta,can qasan ransa yana mamakin dalilin tsauwarsu haka shi da ita,dr din kuma na magana da ita cikin kulawa,tamkar yadda zaiyi magana da shi ko NADEEYA. "Abba....akwai wani damuwa?" Toufeeq din ya fada a girmame yana duban fuskar mahaifinsa. Waiwayawa yayi ya dubi sãahar,wadda a sannan takejin kamar ta rufe ido ta bude ta ganta a gida,ta samu nasarar tsere musu sannan ya mayar da dubansa gareshi "Ta yaya matsalar mota zata samu president dinka sannan ka tayar da dukka motocinka ku tafi ba tare da an kula da buqatarta ba?" Hannunsa ya murza kamar kadan,yana jifanta da wani irin bahagon kallo,dr din bai jira amsarsa ba yace "Ka dauketa ku sauketa a gida,ka tabbatar kun ajeta har cikin gida kamar yadda muka karbo amanarta" "In sha Allah " ya fada da lallausar muryarsa dake cike da bacin rai,shi yarinyar zata yankema schedules kawai saboda buqatar qashin kanta?. Dai dai lokacin sajjad ya qaraso gurin,akwai banbancin halaye masu yawa tsakaninsa da toufeeq,don shi din cikin sakin fuska yake tambayarta akwai matsala ne tayi late na komawa gida?. "Dole haka wataran dama ta faru,tunda kunyi sakacin kula da buqatun ma'aikata,maza a sanyata a mota a kaita gida, motarta ce ta samu matsala" "Yanzun nan abba" sajjad din ya fada gami da ce mata bismillah bayan yayi gaba,tabi bayansa. Tun isowar sajjad taoufeeq din ya wuce mota ya zauna abinsa,yasan tunda har ya iso wajen,abinda abban ma baice ayi ba sajjad din zai sake ruruta abun,ya fuskanci yana wani mugun bata girma na musamman,abinda ya kasa ganewa mene shi?. Kansa tsaye ya bude motar da toufeeq din kadai take dauka,saikumma shi idan tafiya ta hadosu tare "Bismillah ko?" Ya sake fada cikin girmamawa fuskarsa a sake.a nutse ta fara sanya qugunta a motar,sannan ta dauke qafafunta a hankali saboda ciwon da 'yan yatsunta sukeyi mata. Tun bata waiwaya gefanta ba,qamshin turarensa shine abu na farko daya sanar mata da wanzuwarsa a gurin,sanann dukka jikinta ma ya bata. Ya hakimce a owners corner yana danna wayarsa hankali kwance,tamkar baiga shigowarta ba,amma can qasan ransa yana tsara yadda zai cimma sajjad ne,don ya qona masa rai matuqa. Muryar dr ta sake wanzuwa a gurin,ya tako da kansa ya qaraso bakin motar "Akwai ciwo a qafarta fa .....taoufeeq,ka sauketa asibiti a dubata da kyau kafin ku wuce gida,kai kuma sajjad muje ka tayani ganin baqin can,Allah ya sawwaqe,ki miqamin gaisuwa gurin girema" "Zaiji" ta fada softly,tana mamakin shin yasan abbanta ne dama?. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/18, 5:38 PM] +234 816 440 5958: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 27 Shuru motar ta dauka,sai sanyin ac da qamshin turarensa daya cika motar,ko sau daya bai motsa ba,sai aikin danna wayarsa da yakeyi,har zuwa sanda motar ta motsa tana fita daga cikin company din,cikin wani irin yanayi da ba lallai ka fahimci ma tafiya motar takeyi ba,iya wannan kadai ya isa shaida maka zunzurutun kudin da aka narka kafin a siya motar. Wani qaramin sassanyan ringin wayarsa tayi,ya dauke manyan idanunsa daga wayar hannun nasa ya maida ga qaramar wayar dake gefansa,sai ya ajiiye dayar ya daga wancan kiran bayan ya sanya earpiece a kunnensa. Tuni ta lumshe idanunta ta hade jikinta tsam a waje daya,duk da tazarar dake tsakaninsu,amma sai takejin kamar idan tayi qwaqwaqwaran motsi jikinta zai taba nasa,kamammiyar muryarsa me wani iri amo dake da taushi da dadin sauraro ce ke fita cikin nutsuwa,har kamar baka tantance abinda yake fada cikin wayar. Bai jima sosai ba ya ajiiye kiran,ba dadewa wani kiran ya sake shigowa,tadan gyara zamanta tana sake jin yadda ta takura a zamanta tare dashi cikin motar,tana son taja tsaki amma karon farko zuciyarta ta tuna mata abinda ya faru da ita dazun sanadin hakan,duk da haka bata haqura ba,cikin zuciyarta tayita mita gami da tura baki gaba,kamar ta bude idonta ta ganta a gida. Ringing wayarta ta fara yi,sai a sannan ta bude idanunta,ta zaro wayar daga jaka,afifa ce ke kiranta,wani haushin afifan ya kamata,kamar itace tayi mata laifin,sai tayi rejecting ta dora wayar saman cinyarta. Sake kira tayi,amma harta katse bata daga ba,a karo na uku yayi magana cikin izza "whether you answer your phone call or turn it off, I don't want noise" yayi maganar kamar ba da ita yake ba,don bai kalli inda take zaune ba. Tanason ce masa ya sauketa kawai,amma tana tuna idan ta aikata hakan kamar bata girmama tsohon daya tako da qafafunsa don kawai a bata kulawa ba,sai ta zabi kawai ta shareshi,tayi kamar bata jishi ba. Ci gaba da kira afifan tayi,mahmud yana tayata,a qalla sai da suka kira sau bibbiyu,ba zato ba tsammani taji ya saka hannu ya suri wayar dake ajjiye saman jakarta data dora kan cinyoyinta,yayi switching nata off,ya jefota saman wani dan abu me kama da akwati dake a tsakaninsu. "Wannan shine karo na qarshe da zan gaya miki dole ki dinga yimin biyayya,you must remember that i am your boss" "And then what?!,zamowana ma'aikaciyarku bawai yana nufin zamana baiwarku bane!" "What's the difference?,kina aiki ne domin kudi,kina kuma aiki domin a biyaki" murmushin takaici ne ya qwace mata "You are too proud mr jarma,sannan fahimtarka bata baka dai dai ba,am not one of the women who can lose their dignity saboda kudi ko qyale qyalen duniya,drop me please" ta fadi wani abu na zabalbala daga cikin zuciyarta,tsanarsa na ninkuwa a ranta,tana jin a duniya bayan adam,shine namijin da tafi tsana a rayuwarta" "you can say whatever you want,but.....babu abinda zai canzaku daga yadda kuke.....and bazan saukeki ba,don baki isa bani umarni ba,amma doing it for the sake of Dr jarma,umarninsa ne" tamkar ya watsa mata wuta a fuskarta haka taji, hawaye suka cika idanunta fal,to amma batason ya gansu har ya fuskanci rauninta,don ta rantse ta daina gwadawa kowanne d'a namiji rauninta,bare ya samu hanyar takata tare da illata rayuwarta. Titi ta zubawa ido tana jin kamar ta balle murfin motar ta fice abinta,to amma kwata kwata komai na motar ba irin wanda ta saba gani bane,tilas taci gaba da rintse idanunta,don bata qaunar ganin koda shatin inuwarsa,idan kuma tace zata ci gaba da bashi amsa,may be ta amsa masa da maganar da zata zunda kimar yaa muhyi a idanunsu,dama familyn Dr mamman girema gaba daya. Tana daga cikin motar amma tana iya hangen tsaruwar asibitin da suka shiga,umarni yayi a duba masa likitan da yake on duty,cikin gaggawa da son cika umarni suka fita,yadda baice mata ci kanki ba,haka bata motsa ba,har zuwa sanda suka dawo suka shaida masa "Dr raheema ce" kai kawai ya gyada musu,ya musu wani sign da batasan na meye ba,sai taga daha driver har security din nasa sun fita daga motar. Hannu ya sanya ya dauki suit jacket dinsa ya zura,ya daidaita zamanta a jikinsa,ya danna Lock password na qofofin,suka bada 'yar qara alamun sun bude,ya tura ya zura qafarsa sanann yayi magana a qasaice "Follow me" "Allah ya kiyaye na jera da kai" maganar dake qasan zuciyarta kenan,tsananin yadda ya bata mata rai ya kuma cikata maganar ta fito ba tare data shirya ba. Cak ya dakata daga nufin fitar da yakeyi,ya maido qafafunsa ciki,ya kuma sake maida lock din ya rufe,maida jikinsa yayi makarin kujerar yana furzar da iska me zafi daga bakinsa,for the first time da wata mace tayi disgracing dinsa,why?,me yasa yarinyar taketa karya masa record?,who is she?,ya qare da tambayar da bashi da amsarta. Banda darajar Dr jarma,banda shi din ubane a gareshi da bai taba saba umarninsa ba,yarinyar sam bata isa ya hada koda hanyar wucewa da ita ba,bare ta samu daman maida masa magana. Bluetooth din kunnensa yadan taba da dan yatsansa manuni,sannan yace "Tell dr raheema to meet me in the car,ina tare da patient" abinda ya fada kenan a taqaice,ya bude tafukan hannayensa yana kalla hadi da murzasu guri daya. Me zaiyi mata wanda zaiyi matuqar bata mata rai?,ya kuma kashe wannan bakin me kama da gidan tsutsa na rashin kunya da rashin ganin girman na gaba da ita?. Knocking glass din akayi,hakan ya tabbatar masa da isowar dr raheema din,qasa yadan sauke glass din,muryarta me cike da fara'a da matuqar kirki tace "You are welcome sir,kaine yau da kanka?" Ta qarasa maganar tana sauke dubanta akan kyakkyawar balarabiyar fuskar sãahar dake cike da fushi. "Yes,please come in" ya fada yana dage glass din window sama ya rufesu ruf kaman dazun. Daya daga cikin guard dinne ya shigo,ya juyo ma dr raheema da kujerar gaban sãahar,ta zamana tana facing dinta,ya qara mata fadi da zurfi yadda dr zataji dadin zama. "Gud evening madam" dr raheema ta fada da fuskarta da bata rabo da murmushi. Idanu sãahar ta daga ta kalleta,saita gaza tankwabar da gaisuwar tata,ta maida mata a taqaice "good evening dr" abinka da likita,nan da nan ta fahimci ba meson dogon magana bane,don haka ta maida dubanta ga jarma "Sir,i hope ba wani babban abu bane ya faru ba,naji kace na taho da kayan aikina" gyara zamansa yayi bayan ya cire suit jacket din nasa "Yes,yau car service zakiyi,ga patient din nan,ta gaya miki damuwarta" daga haka ya maida hankalinsa ga dan qaramin computer din dake maqale da seat din yana ci gaba da duba aikinsa na dazu daya katse. "Sannu madam,meye damuwar?" Ta sake tambayarta da dakakkiyar fuska. Qafarta ta daga mata,dr raheema ta kalli qafan,sai ta kalleta cikin sauri,abinka da farar fata,fatar wajen tayi jajur "Sir,me ya samu qafarta hakanan" "Ask her" ya amsa mata carelessness. Wannan karon batasan sanda ta jefa masa wata muguwar harara ba,tana jin tabbas inda tana da dama sai tayi masa mugun duka. Dr raheema data gani sai murmushi ya qwace mata,abun ya burgeta sosai,har ta kasa yin shuru "Baka kyauta ba sir......you must show your care and concern,kasan mu mata bamason rashin nuna kulawa" "Do your job dr.....am in hurry please,banason jira" "Okay sir"ta fada cikin girmamawa tana ajjiye maganar a gefe. Saida tayi mata allurar anti tetanus saboda batasan dame taji ciwon ba,sannan ta bata pain killers,tace kuma zata iya gasa gurin da lukewarm water,sannan ta hada kayan aikin nata ta fito. Tana fita suka dawo,dukka motocin suka dauki saiti suka sake fita a asibitin. Ko sau daya bai tambayeta address dinsu ba,tadaiji yana magana a waya,amma zugin da qafarta keyi bai barta taji abinda yake fada bama,daga bisani taji yana basu umarnin yin amfani da map dake jikin motar. Sanda motar ta tsaya data bude idonta sai gata qofar gidansu,ta boye mamakinta ta dauki jakarta cikin kamewa da takatsantsan da qafafunta ta fice daga motar,tana jin kamar an zareta daga cikin tarin qayoyi. Afifa dake tsaye jikin motar mahmud ta nufota da hanzari,wanda sam bata lura dasu ba,saboda Allah Allah take ta isa gida ta sake rage kukan dake cin zuciyarta karo na biyu. Gwanar kuka ce sosai,duk wanda ya santa ya santa da wannan dabi'ar,kuka baya mata wuya "Bestie,lafiya?" Afifa ta fada tana qoqarin riqeta,hannu ta daga mata "Ki barni don Allah,koma meye ke kika jawomin" "Da nayi me?, Ta tambayeta cikin mamakin bacin ran data gani a fuskarta "Mahmud yaje har kamfanin akace boss yasa a kawoki,sai musa ya samu yana gyaran motarki,tare muke dashi tun dazun a nan muna jiran isowarki,ganin kinyi delay yasa muka fara kiranki,kuma daga qarshe wayar a kashe, hankalinmu ya tashi" dai dai sanda takai qarshen maganar mahmud shima ya iso,dukka jikinsa a sanyaye,bayan ya gama kallon motocin da suka sauke sãahar din yanzu,wadanda suke dauke da number MT JARMA tun daga 01 har zuwa 05 "I hope she's fine" ya tambayi afifa,don tuni ita ta soma shigewa gidan ma "I don't think so,naga yanayinta kamar akwai damuwa" idanunsa ya sake mayarwa kan shacin tayoyin motocin,kamar a nan zaiga amsar tambaya da kokwanton da suka cika masa zuciya,tun daga dannowar motocin street din nasu,har zuwa fitarsu "Don't bother,zan shiga naji me ya faru,koma meye i will let you know" "Thank you afifa" ya fada yana zube hannayensa a aljihun rigarsa. Yana yabawa gudunmawar da take bashi wajen samun soyayyar sãahar din "No worries" ta bashi amsa tana gaggawar cimma sãahar din,sauqin abunma daya,anty farheen na ciki,koma meye tasan zata tari matsalar,tunda tasan halin 'yan kayanta sosai. Da sallama ta shiga parlor din,ba kowa sai maama dake gyarawa aleena socks dinta,khalipha kuma ya gaggwafe a qasa yanata qoqarin hada wani maths puzzles,tun dazun ya fara,har yanzun kuma bai hadasu dai dai ba "Maama,sãahar fa?" Dan tabe baki kadan tayi "Suna ciki ita da uwarta" juya akalarta tayi zuwa dakin,tana cewa khalipha dake kiran tazo ta duba masa ya kasa hadawa "Drop it aside son,i will be back". A hankali ta tura qofar dakin nasu,daidai lokacin da sãahar din ke zaune gefan gadonsu,ta zuba hannayenta saman fuskarta tana sheshsheqar kuka,anty farheen na zaune saman stool tana fuskantarta,tana tallafe da bayan hannunta tana dubanta kawai ba tare data hanata kukanta ba. Tun daga sanda adam yayi breaking heart dinta,yayi breaking dukka wani trust nata akan kowa,saita zama me raunin zuciya,wanda a times kuka ne kawai yake sanyawa ta samu tayi controlling anger dinta. Ko yanzun ma ta fara gaya mata amma ta kasa ci gaba ta fashe da kuka,farheen tasan crying is the one way to calm her self,wannan ya sanya batayi qoqarin hanata ba. Taji motsin shigowar afifa,saita bude fuskarta wadda harta hada jaaa "Me kika shigo kiyimin?" "Afifa fita please" anty farheen ta fada. Harara afifan ta watsawa sãahar "Ba inda zani,inkinso ki hadiye zuciya,duk wanna fushin nasan kawai don kinganni da mahmud ne,to zama daram a dakin nan" tasan halin afifa da kafiya wani lokacin,batason suyi ja'inja da ita alhalin tana cikin irin wannan bacin ran,afifa means alort to her,ba zata taba iya bata mata rai ba,wata sashe ce ta rayuwarta,don haka ta wuce toilet,ta qarasa matse hawayenta ta dauro alwala. Tun kafin ma ta gama alwalar taji sanyi yana sauka a zuciyarta,ita kanta wannan tsananin fushin bata sonshi,to amma yata iya?,wata qaqqarfar qaddara ta keto tsakiyar rayuwarta ta sauya mata abubuwa da dama. Ta sake yarda afifa da anty farheen din wasu mutane ne na musamman Allah ya ajiye mata,duk cikinsu babu wadda ta tashi,idan ta lura kamar damuwa ce saman fuskar kowannensu,duk da afifa ta maze tanata danne danne a wayarta,kamar komai bai sha mata kai ba. Wannan caring din data gani tattare dasu yasa ta kasa sauya kayan jikinta da tayi niyya,ta koma inda ta tashi dazu ta zauna,anty farheen na ankare da qafarta da tayi jazur "Daga yau na ajjiye aiki da companyn MT JARMA,don Allah anty ki tayani fahimtar da yaa muhyi" ta fada a raunane,tana jin dacin abubuwan da yayi mata a yau. Furucinta dukkansu yaja hankalinsu,har afifa tabar danna wayar da takeyi,ta miqe ta zauna sosai tana kallon sãahar din. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/18, 5:38 PM] +234 816 440 5958: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 28 Dif dakin yayi na wasu mintuna,kafin anty farheen ta tattara hankalinta sannan tace "Me ya faru daya kawo wannan ajjiye aikin rana tsaka haka?" Qwalla idanunta suka kawo,tayi qoqarin maidasu ta kuma kawo dakiya ta azawa ranta,sannan ta fara basu labari daki daki,daga qarshe ta qarqare da fadin "I can't take it anymore anty,how can he humiliate me like that?yana tunanin ina da interest ne akan dukiyarsu?,ya dauka ni na kawo kaina nayi begging a bani aiki,kamar yadda sauran wulaqantattun matan dake mutuwar masa soyayya sukayi aka basu gurbin aiki yanzu haka a company din ba,baisan tilastani yaa muhyi yayi ba shima don kawai yayi alfarma wa mahaifinsa?" Shuruu anty farheen tayi tana jinjina kai,sosai taga zallar bacin rai saman fuskarta,afifa zatayi magana tayi saurin dakatar da ido,sannan ta fara magana "Gaskiya bai kyauta ba,baisan mace 'yar tarairaya bace?,so amma duk da haka,ina roqar masa afuwa ummin abba,sannan on my own view akwai dalilin da yasa yake behaving haka.....but kafin sannan,dole na gaya miki gaskiya ummin abba,kema kina da naki laifin" "Yes" afifa data kasa jure rashin saka bakinta ta fada,har sai da sãahar ta waiwaya ta dalla mata harara da fararen idanunta dake da raguwar danshin hawaye. Juyawa farheen tayi "Afifa,i beg you..." Yatsunta tasa ta kame bakinta,sanann ta koma ta kwanta,saidai duk da haka kunnuwanta da hankalinta yana kansu din tana ci gaba da sauraron abinda anty farheen din taci gaba da gaya matan. Mai da kai farheen tayi ga sãahar tana dubanta cikin kulawa "Don ba dai dai ba anyi miki,ya bata miki rai na yarda,kuma ya miki laifi,tunda har abun yakai ga taba lafiyarki......to amma abinda nakeson ki sani,shi babba duk inda yake babbane,koda babban nan ba musulmi bane Christian ne,abu na biyu ko babu komai ai ya girme miki ya kuma baki shekaru sãahar,ina cewa ma zaid ya miki magana akan kiyi haquri kiyi aikinki?,ki kuma bashi girma ko don daddyn aleena?,sannan karki mata,namiji ako yaushe sarki ne,ke macace dole ko yaushe a qasansu kike....." "Ni ba a qasan wanan nake ba anty,ni a qasan abba dasu ya muhyi kawai nake a yanzun,amma babu wani namiji a samana" ta fada da sauri,da alama an tabo mata bangaren da tafi adawa dashi. Karamun murmushi ta saki "To shikenan,amma dai kamata yayi ace,tunda kinsan halinsa kici maganin zama dashi ,magana ta Allah kuma babu namijin da yasan abinda yakeyi wanda zai yarda da wannan,kina qasa da shekarunsa,sannan kina qasa dashi a aiki sannan kuma ya dauki rani?,bazai yiwu ba,kiyi tunani da kyau,a yanzun kina cikin fushi,yanke hukunci ba naki bane" taji duka maganganun farheen,amma batajin akwai wata sauran shawara data rage,gaba daya ta gama tsanarsa da dukkan wani abu da ya shafeshi,ajjiye aikin shine kawai maslaha a wajenta saboda muddin zasu ci gaba da haduwa,zaici gaba da yi mata haka,ita kuwa ba zata taba jura ba,saita maida masa dai dai da abinda yayi matan. ***********Tun washegarin ranar da abun ya faru bata sake batu ko yunqurin zuwa aiki ba,sunyi waya da miss sameera,tana tambayar lafiyarta jin shuru bata shigo ba,tace mata bata jin dadi ne. Cikin alhini tayi mata sannu,tare da shaida mata zata shigar da report "Da kin barsu ma sameera,basai kinyi reporting ba". A kan hakan suka rabu,amma duk da haka bata fasa yin report din ba,duk sai taji ba dadi rashin zuwan sãahar din,kirkinta yana da yawa,tana kyautata mu'amala sosai a tsakaninsu. Tun daga ranar har zuwa satin gaba gaba daya tayi qaura daga zuwa aiki,duk da cewa zuwa lokacin ma qafar ta warke sumul,koda maama ta tambayeta dalili ce mata kawai tayi hutu ta dauka,sai bata sake yi mata zancan ba. **********Karfe hudu na yammacin ranar litinin ne,wanda ya kama shigarta sati na biyu rabonta da MT JARMA GROUP OF COMPANY. Tana zaune cikin farfajiyar gidan,guri na musamman da aka kebe saboda hutawa. IG ta shiga tana duba hotunan styles na dinkuna da takeso takai,tayi scrolling down kenan hotonsa ya mamaye fuskar laptop din nata. Faduwa gabanta yayi,cikin sauri ta furta "A'uzubillahi minash shaidanir rajim" ta sake maimaitawa kusan sau uku,kafin daga bisani ta bude idanun nata a hankali tana jan tsaki,ji take kamar ta fasa computer din gaba daya,sam bata qaunar ganinsa har can cikin zuciyarta,ko yanzun data aje aikin ta daina zuwa ji takeyi kamar tayi nesa da wani baqin maciji. Tana shirin sauka daga IG din gaba daya idanunta ya fada kan sunan me account din MEENAL YA'AQOUB AJI(AJI). "Banzaye marasa kishin kansu" ta furta tana qoqarin karanta rubutun dake qasan hoton nasa. Kamar dai wancan karon,itace wadda ta wlafa hoton nasa tare da kalmomi na yabo tare da nuna zallar madarar soyayya da qauna a gareshi,sauran 'yammatan da suka zube comment sama da dubu uku suna sake yaba kyanshi haiba da kamalarsa,tare da sake kodashi. Baki sãahar ta tabe "Ko meye abunso a nan?,a green snake under green grass kenan" "To tunda bakison kalla ki sauka mana,naga kema kallon nasa kikeyi" muryar afifa taji daga bayanta. Wani irin fatali tayi da system din kafin takai ga waiwayowa ga afifa wadda ta rugo tana fadin "Subhanallahi" ta daga system din tana fatan batayi komai ba,saboda tasan nawa ta sanya ta siyeta,system ce me tsada ta kamfanin apple,kuma ko shekara batayi ba sukayi order dinta ita da afifan. Sai data tabbatar ba abinda ya sametan sannan ta fita ta kashe mata ita gaba daya,kafin ta maida hankalinta akan sãahar din. Manyan idanunta ta kafeta dasu,bacin ranta yana bayyana sosai saman fuskarta,suna hada ido tadan kauda idon don ta samu damar gayawa afifan abinda yake ranta "Bestie...." "Me yasa kika tsaneshi har haka sãahar?" Afifan fa katsi numfashin sãahar din daga abinda tayi niyyar gaya mata,ba tare da ta barta ta bata amsa ba ta sake cewa "Ina jiye miki tsoron hadisin ma'aiki yayi aiki a kanki fa?,yace kada ku zurfafa soyayya don tana iya juyewa qiyayya,kamar dai tsakaninki da adam,sannan kuma yace kada ku zurafaf qiyayya saboda watarana zata iya juyewa zuwa soyayya". "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,bestie bansan bakya qaunata ba sai yau" sãahar ta fada da muryarta data canza saboda tsananin bacin rai,duk duniya afifa dince kawai take zata iya gaya mata hakan ta qyaleta. Kowanne yana shirin sake magana qarara wayar sãahar dake kan cinyoyinta ta katseta,maida dubanta tayi ga wayar tana tsammanin mahmud ne,amma sai taga mutumin da bata taba zaton kiransa ba,Dr mahmud JARMA. Cikin matuqar mamaki da kuma girmamawa ta daga kiran hadi da yin sallama "Waalaikumus salam diyata" "Barka da yammaci abba" "Barka kadai,kin yini lafiya?" "Alhamdulillah abba" "Ayimin afuwa,inata son na kirayeki naji ya qafar taki,sai kuma sabgogi suka riqeni,to amma shekaran jiya munyi waya da muhyiddeen,yace kin warke tun cikin wancan satin ma" cikin jin nauyin afuwar da yake bida a wajenta tace "Na warke abba,alhamdulillah" "To ma sha Allah,nayi zaton ciwon ne ya hanaki komawa aiki,ina fatan za'a daure a koma din" "In sha Allah" ta samu kanta da furtawa saboda yadda yayi mata kwarjini take kuma jin nauyinsa,duk da cewa babu plan na komawarta aikin kwata kwata. Addu'a sosai yayi mata,cikin jin dadin irin girman da take bashi,qaunarta da kimarta data iyayenta suna sake qaruwa a ran Dr mahmud JARMA. A sanyaye ta sauke wayar daga kunnenta tana tuhumar kanta dalilin da yasa ta amsawa dr jarma cewa zata koma bakin aiki?,me yasa bata gaya masa cewa tabar aiki ba?. "Yanzun nan ya zaid ya shigo,nayi masa zancan ankon bikin fatima,yace cikin week din nan container dinsa da yayi order laces daga china zata iso,akwai wasu colors guda goma na musamman da su kadai ne a ciki,zai cire mana" "Yayi,amma duk wani event da tasan akwai maza a ciki a cireni" ta fada tana gyara zamanta,can qasan ranta alqawarin komawa bakin aikin da tayi ba tare data shirya bane yake damunta. Sanye yake da yadin lallausan yadi da aka saqa da ainihin zaren guanaco me taushi da tsada,an shirya masa dinkin da yayi masifar dacewa da darajar yadin da martabarsa,ya kuma dace da jikin mamallakin yadin. Rufaffen takalmin qasar italy ne a qafarsa me asalin kyau da tsada,wanann kusan al'adarsa ne,komai nashi designer ne,komai nasa na musamman ne. Kansa babu hula,sai sassalkar sumarsa daketa qyalli,da wani irin gyara dake nuna tana samun kulawa,hakanan yana amfani da tsaftatattun tsadaddun mayukan gyaran gashi na maza. Zallar kyau da kwarjinin dake shimfide a fuskarsa dake da qarancin fara'a a bayyane yake muraran,kwarjinin da yake hanawa mata da yawa kallon fuskarsa kai tsaye. Shi da angel din nasa suke takowa zuwa inda motocinsa suke jiransa,akwai baqi da sukazo daga qasar tokyo da zasu karbesu shida daddyn nasa,wanda a yanzun haka suke bristol suna jiransu. Daga daya bangaren nasa kuma hajiya qarama ce,riqe da wata doguwar takarda "Zaki bani aron lokacin daddyn naki muyi magana kuwa?" Hajiya qarama ta fada tana duban fadeela. Siririyar dariya yarinyar tayi tana dora kanta saman hannun daddyn nata da yake riqe da nata hannun,sai ya saka hannunsa ya dauketa cak ya a zata saman kafadarsa,wani miskilin murmushi na fita daga labbansa. "Wannan sune list na mutane cikin dangi da za'a bawa zakkar wannan shekarar" hajiya qarama ta fada tana duban takardar. Kadan ya waiwaya ya kalleta,sannan yace "Mu qarasa ki bawa jibril ko elyas" "To yayi" ta fada tana ninke takardar. Dukkanin motocin an shiryasu kamar yadda aka saba,ya qare musu kallo a nutse sanann yace "Da mota biyu kawai zamu fita yau" "Me yasa?,baka tsoron lafiyarka?, idan baka qara guards ba ai ba zaka rage ba,yadda yanzun duniyar nan ba amana ba gaskiya" kai ya kada,shi dukka guards da yake fita dasu badon komai bane,don kawai ya samu sauqin tafiyar da aikinsa ne,bashi da wata alaqar gaba da kowa, hakanan dukiyarsa da guminsa ya tara,halas dinsa ce,so bayajin akwai wata barazana da zaiji tsoron fuskantarta "Ba komai,fi amanillah" ya furta calmly,baki tadan kyabe kadan,yana da wani irin tauhidi da wani lokaci yakan bata tsoro,zata sake magana cook dinsa ya iso,yadan tsaya daga nesa nesa yana jiran izinin qarasowarsa,sai yasa hannu ya yafitoshi,wannan ya bashi damar qarasowar yana cire zungureriyar hular chief dake kansa "Sir,you didn't choose what you want to eat" yayi maganar yana miqawa jibril takardar dake dauke da jadawalin abincin wata guda. "Bashi takardan mu wuce,i want something lite,banason abu me nauyi yau,coz zan dawo gida late" yayi maganar yana sauke fadeela. Dai dai sanda wayarsa ta dauki tsuwwa. Sunan Dr mahmud din da ya gani ya sanyashi daga wayar da hanzari "Ka taho ne?" "On my way dad" "Good,ka tsaya ta gidan Dr Mamman girema,ka duba jikin president dinka,ya kamata ka dinga kyautata mu'amala da employee dinka toufeeq" "Alright dad" ya amsa masa yana sauke wayar daga kunnensa. Zazzafar iska ya furzar daga bakinsa yana zube hannayensa cikin aljuhun wandonsa,me yasa dad zaiyi masa haka?,wannan umarnin da ya bashi dai dai yake da yace masa yabi jirgin sama ya kamo masa shi,wannan yarinyar maras kunya?,me dagawa da izza zai taka ya sake zuwa gidansu a karo na biyu da sunan dubata?,bayan wancan karon dad din ya sakashi kaita asibiti ya kuma kaita har gida ya sauketa?. Duk yadda yaso ya qirqiri wani uzuri da zai hanashi wannan zuwan amma abun ya faskara,sun riga sunyi magana da dad din yace masa ya gama komai yana hanyar zuwa,so babu wani excuse ya tabbatar da zai bashi ya karba. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/22, 7:41 AM] Maman Aslam: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 29 Duqawa yayi yayi kissing goshin fadeelan,ita kuma tayi masa addu'a kamar kowanne lokaci "A dawo lafiya abby,Allah ya tsareka ya bada sa'a" wannan addu'ar yana ji da ita,yakanji kamar ta fita ne daga bakin mahaifiyarsa sometimes "Wannan yarinya akwai iyayi,ko iyayin waye kika kwaso haka oho" hajiya qarama dake kallonta tana qaramar dariya ta fada,shima yana jinsu,sun saba irin wanann wasan dake kama da wasan jika da kaka,do haka ko waiwayosu baiyi ba ya wuce ya shige motar da tuni jason ya bude masa. A ciki ya samu sajjad yana jiransa,ya kalli agogonsa sannan ya dubeshi "Dr yace muje shagari quaters tukunna ko?,nasan zamu kashe kamar awa daya a can din" wani kallo ya watsawa sajjad din bayan ya zauna sosai cikin kujerar "Awa dari zamuyi" fashewa da dariya sajjad yayi har yana duqawa,yadda yayi maganar ya tabbatar masa a wuya yake "To ai shikenan,ba laifi,saina gayawa Dr kana buqatar awanni dari,ayi postponing meeting din zuwa wasu kwanakin a gaba" "Will you keep quiet sajjad?" Ya fada a nutse yana lumshe idanunsa hadi da budesu "Afwan" ya fada yana dariya,sannan ya maida kansa ga google da ya shiga,yana duba sabbin kayayyaki da sauran companies suka saki a satin,gudun kada suyo kaya iri daya,amma can qasan ransa cike fal yake da dariya da kuma annashuwar abinda Dr ya yiwa toufeeq din,bayan shekaru kusan biyar,yau dr ya karyawa toufeeq record,abinda yasan cewa duk duniya banda shi ba wanda ya isa ya masa hakan. Ko cikin motar shuru yayi kamar wanda ke tunani,bini bini ya duba agogon hannunsa,shi ko hanyar unguwar bayason bi bare ya isa ga gidan,ya danna wani madanni daga gefansa,wanda saqo zai kaiwa driver din dake gaba na buqatar ya qara speed na motar. Cikin mintuna qalilan suka isa qofar tafkeken gate din gidan, driver din yana shirin dannan hon don a basu damar shiga farfajiyar gidan toufeeq ya dakatar dashi "Inaga ta fito kawai mu dubata,no need sai mun shiga har cikin gidan" waiwayowa sajjad yayi ya kalleshi "What kind of dubiya is this?,ka taba jin ance wanda za'a duba shi zai fito?" Kafin yayi wani yunquri sajjad ya bawa driver din umarnin shiga ciki. Hon biyu kacal me tsoron qofar ya buda gate din yanason ganin su waye,Dr mamman dake zaune daura dasu yana duba jarida yace ya bude,kosu waye da alama sanannu ne. Wanann din dabi'arsa ce,lokaci bayan lokaci yakan zauna a bakin gate din da kansa tare da me gadin,ya girmi baaba habu,amma shi dinma dattijone kamar shi,zaman nasa a wajen lokaci lokaci yana yiwa baaba habu din dadi,akwai kyakkyawar mu'amala da fahimtar juna a tsakaninsu,sannan hakan yana sake baiwa dr girema damar fahimtar matsaloli da kusakurai da za'a iya gyarawa. Rufe news paper din yayi sanda motar ta gama tsayawa,toufeeq da sajjad suka fito,miqewa yayi sanda suke sajjad ya nufoshi toufeeq na biye dashi a baya. "Barka da yamma" shi da sajjad din suka fada kusan lokaci guda "Barka kadai yan samari daga ina?" "Daga kamfanin MT JARMA muke,munzo duba jikin daya daga cikin ma'aikatan mu ne Khadija" "Ma sha Allah,amma kai din yaron Dr ne?" Abba ya fada cikin sakin fuska yana duban sajjad, murmushi sajjad yayi ya juya yana dubam toufeeq "Ga dansa nan" matsowa taoufeeq din yayi,abba ya miqa masa hannu sukayi musabaha,sannan ya waiwaya ga jamilu wanda ke aikace aikace a gidan "Yi musu jan gora zuwa setting room,sai ka yiwa ita sãahar din magana" "Muna kan hanya ne abba,ko zamu samu ganinta?" Toufeeq ya datsi hanzarinsa,kai ya jinjina "Babu damuwa,rakasu ta can baya,naga wucewar 'yar uwarta gurin,na tabbatar suna tare" godiya sajjad yayi sannan sukabi bayan wanda aka kira da jamilu. Sake zurfafa ganinta afifa dake zaune tana fuskantar sãahar tayi tare da son tantance abinda idanunta ke gane mata,a youngest handsome millionaire,a business tycoon Muhammad toufeeq jarma. Yana takowa majestically,takun da ya banbanta dana sauran maza,koda a yanzun yanayin tafiyarsa daban da tasu sajjad da kuma jamilu. Sãahar ta bada baya,ta tabbatar ba zata iya ganin meke faruwa a bayanta ba muddin ba ita ta tabota ba,so amma tana gudun reaction dinta,kada taje tayi misbehaving,don haka ta maze,taci gaba da kurbar mamakinta ita kadai,har zuwa sanda suka qaraso gurin. Sallamar jamilu ta saka sãahar waiwayawa,abinda ya bata damar ganin abinda ya sanqarar da tunaninta,lokaci guda idanunsu suka gauraya cikin na juna,a take kowa izzarsa ta motsa,haushin dan uwansa kuma ya sake motsa musu. Me wannan dan izzar yakeyi cikin gidansu? "Alhaji ne yace a rakosu" jamilu ya fada cikin rusunawa,gamar fadar tashi kuma tayi dai dai da miqewar sãahar,ta fara dauke wayarta headphone da sauran tarkacen da tazo gurin dasu,don ba zata iya hada numfashi da mutumin nan ba,bare har magana ya shiga tsakaninsu. Tana gama debewa ba tare data waiwaya ba tayi gaba da zummar dauke system dinta a inda afifa ta ajjiye mata,ta duqa takai hannu,saidai kafin hannun nata yakai ga sauka a kai wani hannun ya dauketa ya aje gefe. A nutse ta dago da fusatattun idanunta,ta zubesu cikin nasa sanda yake tsaye a gabanta,hannunsa guda daya zube a aljihun wandonsa,shima ita yake kalla "Nan fa ba MT JARMA COMPANY bane,bare kace zaka sakamin doka ko iyaka daga yin duk abinda nayi niyya" gyara tsaiwarsa yayi,yana jinjina qarfin halin yarinyar,da qwarewa wajen rashin kunya da tsiwa "Koda ba MT COMPANY bane,amma anan din,cikin tsakiyar gidan naku ina iya ladabtar dake iya yadda naso......tunda qafafun naki sun warke,ina tunanin wani sabon tabon kike da buqata daga wajena.......Me kike a gida bayan kin warke?" Ya jefa mata tambayar cikin izza yana kafeta da ido. Mamaki ne ya cikata,tayi kasaqe tana kallon qarfin hali irin nasa,ya tsareta da tuhuma kamar wani ubanta. Zare idanunsa yayi daga kallonta,ya duba agogon hannunsa minti goma sha biyar kacal yayi niyyar qonawa a dubiyar da Dr ya tirsasa masa yayita,kuma ta cika,dago idonsa yayi ya sanya hannunsa a aljihun rigarsa,ya fiddo wayarta data bari a mota ya cilla mata "Ki tabbatar kin dawo aiki ranar Monday,ko kuma ki rasa aikinki" abinda ya fada kenan,ya zagayeta ya wuce. Da kallo ta bishi cikin tsananin bacin rai,ya isheta ya kaita maqura,ita ba yarinyarshi bace da zai dinga yi mata irin wannan izzar,tabbas a yau dai baici bulus ba,zata koma aiki amma kuma saita rama abinda yayi mata,tabbas zai biya da farashi me tsada. Ta qofar baya ta wuce ta bulla sassansu,a parlor ta samu afifa da maama a zaune,bata tsaya ba sai tayi wucewarta ciki,tana kuma shiga daki ta maida muqulli ta rufe qofar,ta zauna tana fidda zazzafan huci daga bakinta,tsanarsa na sake ratsa mata jininta. Sai da suka daidaita akan hanya sajjad ya dubeshi "Da ka sanya muka bar gurin,ina fata ba wani abu mara kyau ka yiwa yarinyar mutane ba" "Kanta na yanke zan siyar" ya amsa masa a taqaice "A yadda kake da zafin rannan,idan ka fara yankan kai an mata sun shiga uku,kafin shekara 'yammatan garinku sun qare inaga" maganar sajjad din taso bashi dariya,sai kawai yadan murmusa kadan da iya labbansa yana girgiza kai,sajjad din yana ci masa tuwo aka yadda yaga dama,amma ba komai,shi da shi kar tasan kar ne. ***********Cikin karsashi da tare da maido dukka azamarta gangar jikinta ta shiga company din ranar monday,abu na farko data fara yi shine hada dukkan documents da report data fara aiki a kansu,ta tattara dukkan wasi bayanai,harda hardcopie data aikawa office din ceo din bai saka hannu ba,ta zauna cikin kwanaki hudu ta tura zuwa email din Dr ahmad jarma,tace ya duba musu,idan komai yayi,suna buqatar sanya hannunsa zasu fara aiwatar da komai. A dare daya ya duba dukkan bayanan,bai samu gamawa ba sai kusan qarfe uku na dare. Sosai ya jinjinawa kaifin basira da qwaqwalwa irin na sãahar din,yayi saluting nata sosai,tunanukanta da yadda ta iya tsara abubuwa sai yake masa yanayi da tsari da ra'ayin toufeeq dinsa,tsarikan nata sunyi bala'in burgeshi,don haka baiyi jinkiri ba ya sanya mata hannu a gaba daya guraben da ake buqatar sahalewarsa,don aiwatar da ayyukan da kuma fidda kudade daga asusun kamfanin. Sanda documents din suka isketa murmushi ta saki,sai taji kanta sakayau,kamar Dr din ya share mata wani fage da zata aiwatar da dukka ayyukanta hankali kwance ba tare data bi ta office dinsa ba har ya samu damar da zai bata mata rai,taci alwashi!,kuma tana da yaqinin wannan itace hanya guda daya da zata qona masa rai. Sati na gaba ta fara gudanar da komai,aka fitar da kudade akayi hiring mutanen da zasu bada gudunmawar farfado da kamfanin,cikin sati guda ta sauya komai ta kuma fara gudanar da al'amuranta hankali kwance. Wata guda kacal company ya fara ci gaba,kawo yanzu kusa duk wanda ya kwana ya tashi cikin company din yasan da zamanta,ta maida kanta busy sosai ta yadda zatayi abinda ya dace,wanda zai faranta ran Dr,ya kuma daga kima da martabar yayanta, she's very hard worker,wannan ya qarawa ma'aikatan qwazo da karsashin aiki,ta kuma samu soyayya sosai daga garesu hadi da martabawa,wannan ya fara sanya mata so da qaunar aikin cikin ranta kadan kadan ba tare data farga ba. ********Cikin satittikan da suka biyo baya gaba daya aiki takeyi tuquru cikin kamfanin,duk wani abu daya zama nauyinta ne akafadarta yake tayi qoqarin ganin ya tafi dai dai,gaba daya bata sake bi takan abinda ya danganci office din CEO ba,duk da tana sane da file dinta dake gurinsu,ta zuba idanu ne taga ko zata samu saqo daga gurinsu,yau ne ko gobe ne,shuru dai. Ba jimawa ta fara samun soyayya daga wajen employees sosai,duk wanda yaga yadda take tafi da aikinta yasan cewa tasan abinda takeyi,da yawa ta tafi da zukatansu,mafi yawansu sun fada a soyayyarta,saidai kwarjininta da yadda bata sakewa mutane fuska musamman maza ya sanya suke shakkar tunkararta. Ta kame kanta sosai,ta kuma sake shata layi ga duk wanda ta fuskanci dan rawar kaine. A hankali sai aikin nata ya fara shiga jikinta,ta fara jin qaunar aikin,saita samu kanta da daura damarar yin dukkan wani abu da zai kawoma kamfanin ci gaba,ko don albarkacin Dr mahmud da ya dauketa kamar diyar cikinsa,don cikin watanni biyun da tayi sai hudu yana kiranta,ya shaida mata yana samun bayanin yadda aketa samun ci gaba daga bakin sajjad. Ba wani sanin sajjad din tayi cancan ba,amma zata iya shaida fuskarsa da kuma nasa muqamin. Ta bangaren toufeeq aikinne yaso hadar masa,nasa company din da yake shirin kafawa daya baro ana processing budeshi abubuwa sunyi nisa,ana da buqatarsa,dole yayi wani irin busy sosai,yake kasa hankalinsa gida biyu yayi aikin MT JARMA GROUP OF COMPANY sannan yayi na MAHFAD FACTORY,kwata kwata baya samun kansa sai dare,nan ma lokutan baccin nasa bame yawa bane sosai,yana qoqarin yakicewa ya dawo gida ne kadai saboda fadeela bayason abinda zai sanya ta dinga jin kewa,ko ta nemi wani abun ta rasa bata samu ba. *_RAI DANGIN GORO_*👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽 FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/22, 7:41 AM] Maman Aslam: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 30 *_RAI DANGIN GORO_* Yadda ayyuka suka dauki zafi cikin company din,da yadda hadin kai ke samuwa daga dukka ma'aikatan ya sanya cikin satin basu damar samar samar da wasu games don nishadi a kowanne department. Ranar Monday bata wuce awa daya da shigowa office ba,miss sameera ta shigo,fuskarta dauke da murmushi tace "Kin samu gayyata daga CSO Chief security officer na MT JARMA COMPANY,yau zasu gabatar da nasu game din na hack day,during break hours". Hannu ta miqa ta karba mini computer din da miss sameera ke duba saqonni irin wannan tana duba saqon da aka aiko din. Kai ta gyada kadan sannan tace "Babu matsala,ki tunamin idan time yayi" "In sha Allah" ta fada tana dan russunawa cikin girmamawa,sannan ta juya ta fita. Fitar tata da yayi dai dai da shigowar kiran ahmad gana wayarta. Har ta dauke kai taci daga da aikinta kamar ba zata daga ba,sai kuma wata zuciyar ta nuna mata kamatuwar yin hakan,koda batason tayi wayar dashi a qalla ta bashi uzurin da zai sanya ta zamewa amsa wayar tasa,tun ranar da yazo gidansun har yau bata sake daga wayarshi ba bare ya sanya ran samun damar sake ziyartar. Lokacin data daga wayar a zaune yake,amma sai gashi ya miqe tsaye saboda farinciki,maganar gaskiya ya kira ne kawai,bawai don yana da wani tabbacin na zata daga ba, sassanyar muryarta ta saukar masa da kasala lokaci daya,ya koma ya zauna yana dafe wayar qamqam a kunnensa "Am so sorry,na katse miki aiki ko?,nasan yanzu lokacin aiki ne" ya katsi hanzarinta tun kafin ma tace komai "Ayimin afuwa,na kasa daina kiranki ne,amma ko iya haka Am really grateful " "Why did you call me?" Ta tambayeshi kai tsaye "I want hear you,i missed your sweet voice" ko kadan maganar tasa bata burgeta ba,saima bata mata rai da tayi,ko kadan bata jiran jin yabo daga bakin kowanne namiji a yanzu "Okay,It's working hours now,can you turn off the phone?" "Can i call you later please?" Ya fadi cikin kwantar da murya,hakanan taji yau din ta kasa musa masa,sai kawai tace masa "Allah ya kaimu" daga haka bata tsaya jiran jin amsarsa ba ta datse kiran. Tana ci gaba da aikin amma rabin hankalinta yana kan hanyar da zata bi ta yakice mahmud daga rayuwarta,ta fuskanci wani banzatar da lamuransa da takeyi sam baya damunsa,kamar ma ko a jikinta wai an tsikari kakkausa,qara qaimi kawai abinsa yakeyi. Duk kuma yadda yakai ga sonta bata jin ko kusa ko alama zata iya aurensa,bama shi kadai ba,ta tattara al'amarin aure gaba daya ta rufe shafinsa,bata sani ba ko sai a qiyama. Sanda miss sameera ta shigo ta gaya mata lokaci yayi saita duba agogo,ta tsaya tayi sallar azahar,duk da cewa akwai sauran lokaci,farkon muhtarinta ne a sannan. Coffee tasha rabin cup,sannan ta gyara yafen mayafinta daya zauna sosai a kanta,ya dace kuma da doguwar rigar atamfar jikinta,wadda dinkin yabi jikinta kamar domin ita aka halicci atamfar da dinkin gaba daya,jikinta sai fidda sirrintaccen qamshin nan nata yakeyi,saika dauka yanzu yanzu ta gama fesa turarukan nata,kabbasa ce me dan karen qamshi data dade da bin jikinta,bayan body mist da sauran turaren kaya da take using dasu masu dan karen tsada da kyau,tana iya kashe ko nawa ne ta siya turare,ba kamar sauran tarkacen makeup ba da har yau saidai a siya mata,don ba wani damunta sukayi ba,gwara gwara powder ma. Tare suka taho da miss sameera,suna dan tattaunawa akan abinda ya shafi aikinsu. Dab da zasu gifta office dinsa idanunta ya sauka a kansu,can qasan ranta tayi qwafa gami da duke kanta,don ko ta qofar office din bason gifatawa takeyi ba bare wani abu ya kaita,har ya hadata mu'alama da mamallakinsa. Babban hall din company a nan ta taras da ma'aikata masu yawa,kowa yana saman kujerarun da aka warwatsa a gurin, gurin sama na musamman aka bata ta zauna tana maida hankalinta ga babban allon majigin dake iya nuna yadda kowanne abokin aiki ke qoqarin yin kutse a na'urar dan uwansa amma wancan yana tosheshi. Tun bata jima da zama ba wasan ya dauki hankalinta sosai,bama ita kadai ba,kusan duk wanda yake wajen abun ya matuqar qayatar dashi,mayun na'ura aka hada team dinsu guda kowa yana qoqarin baje fasaharsa. Sosai wasan ya dauki zafi,ya kuma dauki hankula,har haka ya sabbaba tashin 'yar hayaniya a hall din saboda ana gab da gangara a wasan. Ba zato ba tsammani sai gashi ya bayyana a gurin,da yawa basu lura da shigowar sa ba,har sai daya fara zuwa tsakiyar hall din,sannan kowa ya fara shiga taitayinsa,cikin girmamawa kowa ya fara duqar da kansa yana miqa masa gaisuwa. Ko gaisuwar mutum daya bai amsa ba,yaci gaba da takowa ciki,cikin izza da qasaitarsa,hannayensa zube a aljihun suit dinsa,fuskarnan a dinke tsaf kamar ko yaushe,murtukewar kuma da bata taba hana bayyanuwar kyansa. Bai tsaya ba har ya isa ga kujerar da CSO yake tsaye a gabanta,yadan russuna cikin girmamawa "You are welcome sir" ya fada a ladabce,yana mamakin yadda akayi yasan da game din,bayan basu tura takardar gayyata office dinsa ba. An rasa zaququrin da zai tura ne saboda zallar shakkarsa da sukeyi,dukkansu jikkinansu sun basu bazai dauki wannan da muhimmanci ba bare ya halarta. Idanunsa masu kaifi ya zube masa yana jifansa da kallon da ya sanyashi qas da kansa,cikin husky voice dinsa data qara wani zurfi da bacin rai a cikinta yace "what nonsense are you doing here?" Kadan ya dago ya saci kallonsa,yadan sosa kansa sannan yace a ladabce "Ba shirme bane sir,and It's not a joke, it's a game to strengthen the security team" "Who gave you permission to do it?,a tsakiyar ranakun aiki saboda rashin sanin muhimmancin ayyukanku?" "Sorry sir,munyi requesting wa office din president,da muka samu tabbacin zuwanta munyi tunanin wannan ya wadatar......". Ambatar sunanta yasa ya gama fahimtar inda komai ya dosa,tunda ya shigo da safen yaci karo da sabbbin ma'aikatan da baisan da zamansu ba dama,yaga kuma aikace aikace masu yawa da shi yasan bai sanya hannu don a gabatar dasu ba,saboda yana da nashi plan din da yakeson ya kammala a qaddamar dasu duka a tare kuma lokaci daya. Waiwaya yayi yana duban sashen da take,tana zaune akan seat dinta,har zuwa yanzu bata tashi ba,hakanan bata motsa ba,tana ci gaba da latsa system din gabanta,duk da cewa an dakatar da komai amma ta shiga wani sashe daban,zakayi tsammanin batasan me yake faruwa cikin hall din ba. Kafeta yayi da idanu,ransa yana sake baci,wato she doesn't care?,me yasa Dr zai saurin aminta da ita ne ma wai?,meye dalili?,baisan sharrin mata ba,they can do whatever don suga sun shiga jikinka,sun samu aminci da yardarka,sannan daga bisani su cutar da kai,bayan dogon lokacin da suka dauka tare da kai,bazai sake barin haka ta faru ba!,har abada!!. Matsawa yayi gaba kadan yana fuskantarta,cikin izza ya motsa bakinsa yana magana da ita da wani irin zafi "Where did you get all this courage mr president?,me yasa kikeson ki dinga yin gaban kanki bayan baki cancanci hakan ba?" Cikin matuqar mamaki ta daga kai,kanta tsaye ta saka idanunta cikin nasa birkitattun idanuwan wadanda ke cike fal da memories masu zafi dake sake zafafa kansa "What are you trying to say?" Ta tambayeshi itama kai tsaye "Kin fahimci komai,dukka wadan nan abubuwan da kike gudanarwa me hakan yake nufi?,baqin fuskar ma'aikata da kika kwaso babu cikakken bincike tantancewa ko tattaunawa da wadanda suke da haqqi da abun,me hakan yake nufi?" Wani irin kallo ta jefa masa,zuwa lokacin tana jin takai geji,ta kuma gaji da sauraron maganganunsa masu kama da ya shirya ci mata mutunci,saita miqe tana fuskantarsa kai tsaye cikin rashin tsoro da kuma rashin shakka,saidai kafin tace komai muryar sajjad ta mamaye gurin. Tun sanda ya shiga office dinsa saima data tura masa information na cewa ana can ana game din,a nufinta na b'ata sãahar da kuma kawo rigima a tsakaninsu,tace masa ya fita zuwa hall din yaji hankalinsa bai kwanta ba da fitar tasa ba,saboda tun daren jiya yasan cikin mugun bacin rai yake,saboda kiransa da NADEEYA tayi ta gaya masa saqo daga AMEESHA,ita kanta nadeeyan tayi nadamar kiran,ta dauka komai yana zuwa ya wuce,ta zaci zuciyarsa ta sassauto ashe ba haka bane,ta tafka kuskuren daya dami zuicyarta,tun jiya kuma take kiransa amma har zuwa yanzun bai daga wayar ba,abinda yasa ko kamfanin da zafi zafinsa ya iso yau,sai Allah kuma ya kade azal bata sauka kan kowa ba har ya isa office dinsa,shi yasa yanzun da yaji ya fita sai yabi bayansa,don shi yasan da game din,ya jima ma zaune cikin hall din yana kallon yadda suke abun cikin gwaninta sa qayatarwa. "everybody outside please!" Nan da nan employees din kawunansu ke a qasa cikin d'ari d'ari da rashin jin dadin maganganun da yake gayawa president din tasu suka fara qoqarin fita cikin gaggawa,kamar basu da buqatar dama gani da jin abinda yakeyi matan,banda wasu tsiraru cikin mata da basu so hakan ba,dama su din ta shige musu hanci da qudundune,tako ina ta sha gabansu,sun rasa yadda zasu fatota,ciki harda saima dake lafe a bakin qofa. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/23, 6:15 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 31 Da hanzari sajjad ya tari numfashinsa,don bayason yace komai kada al'amuran su qarasa jagulewa "Please toufeeq Calm down,don't make harsh words" bai ko waiwayo ba ko ya saurareshi ba ya tako zuwa gabanta,ya bada kusanci sosai a tsakaninsu irin wanda bai taba yi ba. Ranqwafawa yayi yayi mata rumfa saman kanta yana dubanta "Nawa ne kasonki?!" Ya fada da wata irin kakkausar murya. A birkice take kallonsa,sosai maganarsa ta daketa,sai yanzu ta fahimci inda ya sanya gaba ma gaba daya,yana nufin wani ha'inci ta qulla ko ko meye?,kamar yasan me take tunani saiya sauqaqe mata ta hanyar sake bayyana mata abinda yake nufi "Nace nawa ne share dinki?,tsakanin kawo ma'aikata da sauran ayyukan!,nawa kika tsara samu!,nawa kika samu!,ki gayamin zan ninka miki,amma ki fita daga rayuwarmu!" Duk da cewa bata shirya zubda hawayenta ba amma ta gagara riqesa,a take ya zarto daga idanunta ya sauka saman lallausan fuskarta da bata iya riqe komai ma ballantana ruwan hawaye saboda santsi da sulbinta,ta kafeshi sosai da ido kamar wadda ta warke daga ciwon makanta,cikin matsanancin fushi tace "wanne irin mutum ne kai mara kirki?,mara iya mu'amala?,wanda baisan kima da martabar dan adam ba?,me yasa dukka zancanka kudi!,me yasa kake hangen kudi sune gaba da komai?,kana tunanin aiki daku na nufin in zama baiwa?,ko mara 'yanci?,ko kuma aiki daku na nufin zan mallaki wata dukiya?saboda kun mallaki yanke talauci?,Mr Muhammad.........idan baka sani ba yau ka sani,banyi aiki daku bisa radin kaina ko kuma don ina nema ba.....nayi aiki daku ne bisa dole da kuma takura neman alfarma da kuma ganin kimar yaaya na, karamcin mahaifinka kuma ya zama silar wanzuwata a nan gurin......baka da matsayin da zan nema sa hannunka akan ayyukan kamfanin nan,duk abinda kake tunanin na aikata.....yes na aikata din,na samu kaso me tsoka wanda hankali bazai dauka ba,na tara arziqin da yafi na mansa musaa dukka a jikinku,do your worst,I don't care or fear......ba dai dukka taqamarka kora ga ma'aikaci ba?,zaka iske resigning letter dinku a wajen sameera,ka riqe tsiyarka ka bawa wanda kaga dama" ta qarasa fada kuka sosai yana qwace mata,sannan ta soma fita daga hall din da sassarfa kuka na sake qwace mata. Da sassarfa sajjad yabi bayanta shi da mr hamza,saidai cikin rashin sa'a ta rufe office din,a yanayin da take sun tabbatar ba zata sauraresu ba,sai suka barwa miss sameera dake tsaye saqon idan fa bude ko tazo fita don Allah kar ta barta,ta tsaidata ta sanar dasu. A office ya sameshi yana kai kawo,ya cika ya batse kamar zai fashe "Burinka ya cika,hankalinka kuma ya kwanta" sajjad ya fadi shima cikin bacin rai "Stop sajjad,don't aggravate my anger,bakaji me ta fada bane?,I will surely punish her" ya qarasa fada yana dukan bayan kujera da hannunsa a zafafe. Kallonsa kawai sajjad yakeyi,yama rasa abun fada,wanne irin tashin hankali ne haka suka tashi dashi yau,sai kawai ya zaro wayarsa ya fara dialing number Dr. Tana kuka tana rubuta resigning letter din,bawai tana kuka kan barinta aiki bane, a'ah,tozartata da yayi a gaban mutanen da suke ganinta da kima da mutunci,maganganun daya gaya mata,wanda shine mutum na biyu a duniya daya taba gaya mata magana masu zafi irin haka. Ta kammala rubutawa kai tsaye ta turawa sameera,tace bayan ta tura musu a rubuce tayi printing as hard copy,ta riga ta yanke har abada ita da companyn,bama iya kamfanin kadai ba,duk wani aiki da yayi kamanceceniya da wanann ta barshi har abada. Da hanzari take tattara dukka wasu kaya da suke da alaqa da ita tana hadasu a wata jaka,ta taka zata cire wata calendar dinta kanta yayi mummunan sarawa,ta koma da baya babu shiri ta dafe kanta da hannayenta biyu tana kiran sunan Allah,idan batayi wasa ba alamu sun nuna ciwon kan da taketa gujewa motsawarsa a yau zai motsa din. Batason ciwon ya sameta a nan,don haka ta bude qofar,ta leqa ta kira sameera. Yanayin da taga uwargidan nata ya sanya hankalinta tashi,nuni tayi mata da iya kayan data samu cirewa ta miqa mata key tace ta saka mata a mota. Sameeran na fita ta miqe da qyar,ta yafa mayafinta ta zura takalminta ta taka a hankali tana ficewa daga office din,zuciyarta na karyewa,wani sashen na zuciyar tata tana ban kwana da dukka abinda ya shafi MT JARMA,bankwana na har abada. _uhmmm,ko shin da gaske bankwanar ne?,ko kuma akwai sauran kallo?,masu karatu,ku gyara zama da kyau,akwai fa sauran kallo,zamu shiga gaba ta biyu na labarin,gaba me matuqar muhimmanci,muje zuwa_🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️ Da kallon mamaki maama kin bita sanda ta shiga gidan "Ke kuma me ya faru na ganki a gida a irin wannan lokacin?" Idanunta fal da hawaye da taketa qoqarin shanyewa tace "Ba komai maama" "Qarya kike ban yarda ba" ta fada tana tattara hankalinta a kanta tare da barin duk abinda takeyi. Hawaye ne ya zarto a fuskar sãahar din,tasa bayan hannunta ta share "Na ajjiye aiki maama" fuska tadan baata kadan "Dalili dame?" Kai kawai ta shiga girgizawa,bakinta ya kasa furta komai,tana jin daci da ciwon abinda yayi mata har saman harshenta,ga kanta da yake sara mata sosai kamar zai rabe gida biyu "Jeki,Allah ya kyauta" maama ta fadi saboda yadda taga ta gaza furta komai,koma meye tasan zataji idan yayunta ko afifa sukazo. Komai ta zube a qasan daki ta isa gado ta kwanta rub da ciki tana fashewa da kukan da takeson saki tun dazun, idanunta a lumshe tana bitar maganganun daya yayyaba mata,tayi nadama da dana sanin sanin kamfanin ma gaba daya bare wasu mutane dake da alaqa dashi. Sai data shafe kusan awa daya sanann ta laluba magani tasha, tayi kuma sallar azahar don tasan zaiyi wuya batayi bacci ba,idan kuma tayin lokacin yana iya kubce mata. Kamar yadda ta zata din kuwa,lokaci kadan baccin yayi awan gaba da ita,saidai dukka cikin barcin ba komai sai mafarkai,wadanda dukka toufeeq ne a ciki da tarin cin mutunci da cin zarafinsa a gareta. Knocking din baaba rabi ne ya tayar da ita "Hajiya tace ki fito hakanan kici abincin rana" "To" ta amsa mata,ta sa hannu ta shafi fuskarta,tana tuna yadda ya zabga mata mari a mafarki,kwatan kwacin marin da ta taba ji ya zabgawa wata,kai ta girgiza ta miqe a hankali ta wuce bandaki. Alwala ta dauro,sannan ta dawo ta cire kayan jikinta. Wata sof cotton shirt ta saka me gajeran hannu royal blue,me adon furanni da gold colour,sai spaghetti skirt daya dace da rigar,tasa comb ta sake gyara gashinta daya hargitse saboda baccin da tayi,ta qara turare a jikinta ta dauki wayarta dake da tarin miscall ta kashe ba tare data tsaya duba kiran waye da waye ba,ta tabbatar dai harda kiran dan anace mahmud a ciki. A parlor ta samesu,maama da baaba rabi dake gyara freezer din parlor din "Barka da fitowa farar d'iya" ta fada tana murmushi "Barka baaba rabi,ya aikin? "Alhamdulillah " "Ma sha Allah " ta fadi tana qarasawa kusa maama ta zauna,wadda har yanzun binta take da kallo "Me za'a kawo miki?" Baaba rabi ta tambaya "Barshi baaba,zan dan huta ne kadan sannan naci abincin,zan zuba da kaina" ta amsa mata tana daukar remote ta canza channel. Bayan wucewar baaba rabin kallonta maama tayi "Kunyi waya da yayanki ne?" Saida gabanta yadan fadi,tasan yaaya muhyiddeen take magana a kai tabbas,batason ko sau daya ya roqeta ta koma aikin nan,don ba zata iya ba muddin wannan mutumin yana a cikin kamfanin "Bamuyi ba,ko ya kira din inajin bacci nake a sannan" kai ta kada "Me ya sanya kika ajjiye aiki sãahar?" Shuru ne ya biyo baya na 'yan sakanni,tanata qoqarin hadiye bacin ranta sannan ta motsa bakinta "Bazan iya ba maama,dansa bashi da kirki sam,baya ganin kima da girman kowa,duk wata mace dake aiki a kamfanin kallon baiwa yake mata,ko wata mara daraja da batasan martabar kanta ba" shuru maama ta danyi sanann ta numfasa "Amma dai kinsan qarfe daya baya amo ko?,kuma ko meye halin mutum sai k........." Qarar wayarta ya katse mata maganar,sai t maida hankalinta a kai ta daga wayar ta sanyata a free. Dr mamman girema ne,wanda kafin su gama wayar sun sanya sãahar din cikin tunani,tabbas inda dukka maza irin mahaifinta ne,su kuma mata duka zasu kasance kamar mahaifiyarta ba ko tantama da ba'a samu mutuwar aure ba,koda an samu din ma saboda sabanin da baya wucewa tsakanin bayi,to zaiyi matuqar qaranci. Tuwon alkama yace yanaso miyar danyar kubewa,batason ta zauna tayita zaman tuna mutumin da a wajenta bashi da wani amfani sam,banza ma ta fishi,don haka sai ta wuce ta debi abincinta taci,tana kammalawa ta shiga kitchen da kanta ta dorawa abban nata tuwon. Tunda akayi sallar magariba taji yaa muhyi din tare da abba suka shigo gidan ta qule a daki taqi yarda ta fito,saidai ana gama sallar isha'i saiga maama da kanta "Ki dauki abincin can ki kaiwa abbanku,zan shiga wanka" hakanan ta miqe jiki a sabule,ta fidda hijabinta ta maida gurbinsa da dan qarami ta fito ta debi kayan abincin ta wuce sassan Dr mamman. A ladabce ta zauna ta gaidasu dukkansu,don yau kafin ta fita basu hadu da abban ba,ta zauna sosai ta fara serving nasu duka su biyun da suketa tattaunawa akan harkokin da suka shafi kasuwancin da suke na hadin gwiwa a tsakaninsu. Ta ajjiye musu komai tana shirin miqewa abba daya gama wanke hannunsa yace "Dawo ki zauna mana ummin abba" murmushi kadan tayi,ta dawo ta zauna din,sai da ya fara cin abincin sannan yace "Me ya faru ne yau a MT JARMA?" Kanta ta sunkuyar tana jin rauninta yana dawowa,kamar yanzun abun yake faruwa,amma dole ta bude baki tayi magana da harshen da zasu fahimceta "Na ajiiye aiki yau abba,ku yimin afuwa abba kai da yaa muhyi na rashin neman sahalewarku kafin aiwatar da hakan,abun yazo a gaggauce ne,sannan kuma a gabar da bazai bada damar yin hakan ba" "Me ya faru?" Abban ya sake jefa mata tambayar. Bata rufe komai ba ta zayyane musu,tun haduwarsu ta farko har zuwa abinda ya wakana yau din. Ta qarashe maganar tana hawayen takaici. Ga mamakinta sai taga abban ya saki murmushi yana girgiza kai "Dake dashi dukka quruciya ce take damunku da kuma zafin kai,tare da wasu memories da suketa hunting rayuwarku,shikenan dai,bakin alqalami ya riga ya bushe,dr jarma ya kirani da kansa,yace bazai tilastaki ba akan ajjiye aiki da kikayi,yace a baki haquri a madadinsa da dukka ma'aikatan,sannan ya tura kudi a baki saboda hobbasar da kikayi kika daga kamfaninsa zuwa matakin gaba,kika gyara matsalar da suke fuskanta kaso sittin cikin d'ari" ya qarashe fadi yana duban fuskarta. Batace komai ba sai kai data girgiza,taji dadi da bai nema alfarmar lallai ta koma ba,don bataso ya roqeta abinda ba zata sake iyayi masa shi ba. "Dama aiki ba dole bane,aure ne dole" abban ya sake fadi,maganar data bugeta sosai,ta kuma sakata dago kanta da sauri ta kalli abban,shima idanunsa yana kanta,ya jinjina kai alamun tabbatar mata da hakan "Tunda taqi tsayawa ta fahimci kowa abba bazaiyiwu taci gaba da zama babu auren kuma ba aikin ba,Allah baya barin bawa babu aikin yi,akwai irin aikin da takeso din abba,idan na dawo daga tafiyar nan ta wata daya zuwa biyun nan zan applying mata" kai ya sake jinjinawa yana tsame hannunsa daga tuwon "Banqi ta taka ba,amma duk da haka ta maida kai ta fidda miji,saboda lokaci tafiya yakeyi,kuma har yanzu ke din yarinya ce qanqanuwa ballantana kice kin girmi yin aure a yanzu". Gaba daya babu abinda maganganunsu sukayi sai dagula mata lissafi,dan ciwon kan data samu ya ragu sosai ya dinga qoqarin dawowa saboda damuwa,ga gidan babu kowa bare ta samu me debe mata kewa,tanaso tayi magana da anty farheen to amma tasan tabbas yaa muhyi yana gidan,don tafiyar tasa sai zuwa wani satin,sai kawai ta hada kayanta a washegari tabi afifan nata zooroad. Ranar da taje qin cewa afifan komai tayi,itama bata matsanta ba sukaci gaba da hutunsu,har sai data huce,ranar suna ta raka afifa gyaran farce da fuskarta,suna hanya tana driving ta bata labari. Sosai afifa bataji dadin ajjiye aikin ba,duk da itama taji ba dadi akan yadda abun ya faru tsakaninta da toufeeq din,saidai itama ta gaya mata "Ba kowanne namiji ke iya fuskantar mace ya bata uzuri ba,ya kuma banbance rashin kunya da tsaiwa akan haqqinta ba,bare mutum irin MT da Allah ya yiwa baiwar kyau kudi da ilimi da kwarjini....." "To hell with his kudi da kwarjinin,ya dauka ina cikin shirgin wawayen 'yammatansa ne da zan dauki irin wannan?,ki daina yabonsa please kina batamin rai afifa.....bakisan wayeshi bane,saboda baki taba mu'amala dashi ba,he was arrogant beyond belief,good look don't always signal kindness" dariya afifa tayi "Wato kin fahimci kyansa ya janye hankalina sosai ko?" "chapter close a beg" yatsunta biyu ta sanya tayi signal na zipping bakinta,bata kuma sake cewa komai din ba,sai suka shiga wata hirar ta daban. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/23, 6:15 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 32 *********K'arfe kusan takwas ne na dare,saman titin dake wadace da fitilu yake tuqin yau da kansa,kuma shi daya,abinda ba kasafai yake faruwa ba. Sanye yake da wata maroon and golden hoodie captan abaya na maza saqar qasa turkiyya,dogon hannu gareta,ya saki hular a bayansa,hakan ya bawa kyakkyawar fuskarsa damar fitowa sosai,cike da wannan turbunewar da kuma rashin fara'a daya zame masa dabi'a. Kiran dr jarma ne ya fito dashi,don yana zaune shida fadeela a part dinsa suna buga game data tubure itakam yau tare zasuyi,da qyar ya lallabata ya maidata gurin nanny dinta sannan ya fito,tare da alqawarin zai dawo da wuri su qarasa. Baisan kiran na meye ba,amma alamu sun nuna a gaggauce yake neman nasa. Cikin rukunin gidajen dake sharada NNDC QUARTER,mayalwacin layin dake shimfide da kwalta da kuma fitilu a jere reras,kowanne gini dake layin abun kallo ne,wannan yana wane wancan,a haka yaci gaba da tafiya bayan ya ragewa motar gudu,da alama ya kusa isowa gidan daya nufaci zuwa. K'ofar wani mansion house dake dauke da ginin bene hawa biyu ya tsaya,ya danna hon na farko, kafin yayi na biyu security din dake sanye da baqaqen uniform da suke kama dana police ya buda masa qofar,a nutse ya sanya hancin motar zuwa cikin makekiyar harabar gidan. Biyu daga cikin security dinne suka bude masa qofar cikin girmamawa da qauna me tarin yawa suke gaidashi,ya amsa musu yana rufe motar,ya jefa key din a aljihun rigar tasa,ba tare daya ciro hannuwan nasa ba yaci gaba da takawa zuwa cikin kamar maijin sanyi. Bawai sanyi yakeji ba,kawai yana jin wani iri ne da yanayin yadda dr din ya kirashi. Kai tsaye ya kutsa zuwa hanyar da zata sadashi da falon gidan,ya tsaya yayi knocking,duk da cewa gidan mahaifinsa ne,amma hakan ba sakashi shiga kai tsaye ba,duk sanda yazo gidan sai ya tsaya ya nemi izini don cikar dokar addinin musulunci. K'ofar aka bude,labiba ce,sanye da wata doguwar riga da tasha tattara daga qirji,ta bude daga qasa sosai,kanta cike da qananun kitso da gashin doki,sao farata zaqo zaqo data sanyawa hannayenta tamkar wata dabbar daji,amma ita a gurinta hakan ado ne na wayayyun mata masu aji(wallahi wallahi wallahi muddin kinsan daya daga cikin wadan nan abubuwan dabi'unki ne to kiyi gaggawar dainawa tun kina raye kina da lafiya,qarin gashi haramunne koda mijinki zaki yiwa,ko meye zaki sanyashi a kitsonki a qara miki tsahon gashinki haramunne,hakanan saka farce shima haramunne,haramunne haramunne,koda faratan hannunki bai halasta ki tarasu ki barsu baki yanke ba,haramunne barin farce yayi zaqo zaqo bare har kije ki biya kudi a dora miki shi,kina 'yar adam amma kinason kiyi kamanceceniya da dabba?,suke da wanann siffa ta akaifa ko qumba masu tsaho,acikin tsarki na addinin musulunci,bansa aske gashin maara dana hammata harda yankan farce sai yiwa yara shayi(kaciya), ma'aiki baya taba fadar magana wallahi wallahi ta tashi a banza,idan yace abu haramunne mu yarda mubi,ba wani kwaskwarima da malaman zamani masu son zuciya zasuyi ma maganarsa ta koma halak,haram haram ce,halal halal ce,Allah yasa mufi qarfin zakatanmu👏🏽👏🏽). Sau daya tak ya kalleta ya kauda idanunsa,sannan ya gewayeta ya sanya jikinsa zuwa falon "Sannu da zuwa yaa toufeeq" ta furta tana bin bayansa hadi da binsa da wani mayen kallo,bai amsa mata ba yaci gaba da kutsa kai,masu aikin dake kai kawo a parlor din suka yi masa barka da zuwa sannan suka kauce daga gurin. "Abban yana samansa" ta fada cikin yauqi da kwarkwasa,wanda sau tari wani lokaci ita kanta batasan hakan tana faruwa ba,tsabar yadda zuciyarta ne ta afu ason samun soyayyarsa. "Ya toufeeq" ta kira sunansa,waiwayowa yayi ya watsa mata wani irin kallo daya takura zuciyarta guri guda ya sanyata harbawa,saita duqar da kanta qasa tana wasa da yatsunta "Yaa toufeeq,am sorry for what happened last time,tsautsayi ne in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba" qaramin tsaki yaja,yayi gaba ya fara takawa zuwa stairs din dake cikin falon. Binsa tayi da kallo har ya bacewa ganinta,hannuwanta ta yarfar kamar zata saki kuka,ta tsani wanann miskilancin nasa,yana matuqar dafaata da dagula mata lissafi,sai ta koma ta zauna saman daya daga cikin qayatattun kujerun falon tana dafe da kanta,dai dai sanda daya daga cikin masu aikin gidan ta qaraso cikin rusunawa "Ranki ya dade,abincin daren,na kammala fa" "Dalla matsa ki ban guri" ta fada mata cikin tsawa tana jan tsaki "Allah ya baki haquri" ta fadi tana janye jikinta daga gurin tunda ragowar mutuncinta,tasan tsaf zata iya ci mata zarafi,ta juya ta koma cikin kitchen din,cikin ranta tana Allah ya qara da yadda toufeeq din yake wajiga rayuwarta. Sake daga kai tayi ta dubi stairs din,gurin mommynta takeson zuwa,to amma ta sani,tunda ya iso ko ruwan giya tasha bata isa hawa saman ba har sai ya sauko,saita kwashe qafafunta ta mayar saman kujerar ta kwanta tana dakon fitowarsa,a ranta tana tsara yadda zasu kebe ita dashi ko na minti talatin ne kacal. Da sallama a bakinsa ya shiga falon bayan dr yayi masa izini,tana duqe tana zuba masa lemo a cup,kakkaurar mace wankan tarwada me tsaho da jiki,wanda kana dubanta zakasan ba hausa fulani bace. Da fara'a a fuskarta ta dago tana cewa "Wata sabon gani,kaine yau a gidan namu?" Dan binta yayi kadan da kallo yana mamakin furucinta,A GIDAN NAMU,sai baice mata komai ba,ya taka a nutse ya isa daura da mahaifinsa,kwata kwata baisan me yasa bai taba jin matar ko daukarta da wani daraja ba,duk da tsahon shekarun data kwashe tana amsa sunan MATAR MAHAIFINSA,sannan dai dai da rana daya bata taba gwada masa wani hali ba,amma haka kawai take takenta baiyi masa ba. "Ina ka baromin kishiyata?" Ta sake fada cikin fadada fara'arta,maimaikon ya amsa mata tambayarta sai ya buge da fadin "Barka da dare"yayi furucin kamar ba da ita yake ba,yana maida dubansa ga mahaifinsa,cike da kulawa tace "Barka kadai Muhammad,ya ayyuka,ya akaji da kacaniyar jama'a" ta tambayeshi cikin nuna kulawa. "Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice,sam bata damu ba,don ta saba da irin wanna halayyar tasa,saita fara kwashe kayan abincin dake gurin tana dubansa "Me za'a kawo maka?" Kai ya girgiza,baisan sai yaushe zatayi fushi ba ta daina tambayarsa abinda zaici ba duk sanda yazo gidan,bayan tafi kowa sanin baya cin abinci daga hannun kowa kuma a ko ina ba,sai a wasu kebantattun hannuwa da gurare. "Alhamdulillah,basai na saki hidima ba" murmushi ta kumayi "A'ah kace dai ba zakaci ba kamar kullum" "Yi tafiyarki ki rabu dashi,kada Allah yasa yaci din" Dr ahmad ya fada,wanda tunda ya shigo lemonsa yake kurba yana kuma kallon labarai daga NTA network news. "Zaici ne wataran ai" ta fada da dariyarta tana yin gaba. Sau daya tak kalmar ta shiga kunnensa amma ya gama fahimtar abinda take nufi ba tare da ita tayi zaton zai fahimta din ba. "Barka da warhaka" ya fada cikin girmamawa,sauke qafafunsa dr ahmad yayi qasa yana ajiye cup din hannunsa gami da bashi amsa duka lokaci guda "Kai ya kamata a yiwa barka ai,irin wannan aikin da kayi na cin zarafin yarinyar dana nema alfarmar a bani aronta,ka kuma sanya tabar aiki lokaci guda,to kaga kai ka cancanci a yiwa barka" bai barshi yace komai ba dr din ya tsinke da fada,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,daga qarshe yace "Ka ajjiyemin komai daya shafi company dina kaima na sallameka,na gode da iya taimakon daka bani,ka koma bakin taka dukiyar" daga haka ya miqe ya wuce bedroom dinsa yana bar masa falon. Kasa motsawa yayi daga gurin,yanajin tamkar ya hadiyi zuciya ya mutu,tsahon tasowarsa bayan shudewar matsalolin da suka sanyo kai a rayuwarsu tun zamanin quruciyarsa,bazaice ga lokacin daya zauna yayi masa fada me zafi irin haka ba,sai yanzu?,a dalilin yarinyar?,ya jima a gurin sannan ya miqe a nutse yana sauka qasan,fuskarsa cike fal da fushi da kuma bacin rai,ta zama silar gurbata kyakkyawar alaqar dake tsakaninsa kenan da mahifinsa lokaci guda?. Suna zaune a falon,hajiya mansura(matar dr ahmad jarma) tare da labiba,ganin yazo zai wucesu ba tare daya kalli kowa a cikinsu ba,kamar ma baisan da zamansu ba hajiya mansura ta magantu "Harka sauko?,kun gama kenan?" Da so samu ne yayi wucewarsa,to amma ko babu komai ita din mata ce ga mahaifinsa,zata iya cin darajar mahaifin nasa koda qanqani ne "Eh" ya amsa bayan ya waiwayo yana dubanta hannayensa zube a aljihun rigarsa. Kwarjini ya mata sosai,tadan daburce amma saita maze ta hanyar sakin murmushi "Ammm,tafiyarku daya da qanwarka,nace ko ta bika saiku tafi tare?" Ido kawai ya lumshe wanda ke nuna ya amsa kenan,ya juya ya fita a falon. Da mugun gudu ta sauko daga saman kujerar,ko ina na jikinta yana rawa "Mommy,ki bada kayana gobe usaina ta kaimin" "Ki tsaya ki tafi da kayarki,goben akwai inda zan aiketa" "Tsaf zai tafi ya barni idan na tsaya jiran hada kaya" tayi maganar a lokacin ma takai bakin qofa. Lokacin data isa tuni ya tayar da motar,abinda ya tabbatar mata inda ta qara wasu mintuna saidai tazo ta tarar da wajen wayam. Gaba ta bude zata shiga,cikin kaushin murya yace "Koma baya!" Jiki a sanyaye ta maida murfin ta rufe,ta koma bayan ta zauna,ranta ba haka yaso ba,taso zaman kusa dashi,ta yadda duk maganar da zatayi masa ta tafi cikin kissa da kuma jan hankali. "Yaa toufeeq" ta kira sunansa sanda suka dauki hanya sosai "I don't want to hear anything from you har mu qarasa gida,if not kuma,i will drop you" kallonta ta maida ga titunan da suke wucewar,yadda suka dauki shuru saboda daukewar qafa da ababen hawa sakamakon dare daya fara yi,marufar asirinta yin shurun,don tasan kadan ne daga aikinsa ya sauketan kamar yadda ya furta. Ranta ya quntata sosai,dukka wani plan nata ya rushe,manufar da yasa tacewa Mommy tayi masa magana ya sauketa ma ya tashi a banza. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 33 Shuru ne ya wanzu cikin motar,sai satar kallonsa da take tayi ta cikin madubin motar a duk sanda zasu gifta wani guri dake da wadatar haske,ji takeyi kamar taje ta rungumeshi tsam tsam ko zata ji sassaucin yadda zuciyarta ke azalzala da qaunarsa,burinta da fatanta a yanzu shine Allah ya mallaka mata toufeeq din kota halin yaya ne ma. A nasa sashen kuwa hadiyar wani abu ke tauri kawai yakeyi daya tsaya masa a wuya,tabbas ya sake amanna da kaidin mata babba ne,babu abinda ba zasu iya aiwatarwa ba,fada da kalmomin da Dr ya gaggaya masa kawai ke yawo a kunnensa,yayi qwafa can qasa yadan daki sitiyarin motar kadan yana jinjina kai,ji yake dama ya buda idanu ya ganta yanzun a gabansa. Dan qara speed na motar yayi saboda wani faduwar gaba da yaji ya ziyarceshi,wani yanayi ne da yakan samu kansa a ciki muddin wani abu zai afku ga fadeela,sai duka ya samu kansa tunaninsa ya koma gida. Tun kafi ya kammala parking yace mata ta sauka,ta fidda ido tana ganin yadda motar ke slow bata qarasa tsaiwa ba,saita langabe kai zatayi masa salo "Yaa toufeeq idan na karye fa?" "Keep quiet,will you drop ko sai na fiddaki da kaina?" Jin haka ya sanya ba shiri ta tattare ta tsallake,Allah yasa motar a sannan ta kammala tsaiwa, zuciyarta kamar zata fashe saboda baqinciki,batasan me yasa yake tozartata haka ba,tanason tayi zuciya ta kuma yi fushi dashi amma ta kasa,shi din fushinka banza ne,rashinsa banza a wajensa,wannan bacin ran ya sanya tayi wucewarta ba tare data tsaya ta kalli inda baaba ramatu ke zaune ita da fadeela ba,wadda ta damu baaba ramatun ta rakota su fito su jira dad dinta,dole ta taso suka bar nanny dinta a ciki. Yana fitowa daga motar fadeela din ta miqe da sassarfa tayi gurinsa cikin murnar ganin ya dawo da wuri "Daddy......dadddd......." Maganar ta kasa fitowa gaba daya,saboda yadda harshenta ya lanqwashe,haruffan suka sarqe cikin na juna,a take kuma kowanne sashe na jikinta ya fara wani irin kakkarwa ta soma lanqwashewa zata kai qasa,kafin takai qasan har ya risketa,ya kuma tallafota ta fada jikinsa ta zube gaba daya,ta fara wata irin jijjiga me qarfin gaske. Duk da cewa ba yau ne ciwonta irin haka ya fara tashi ba,amma har yau har kwanan gobe ya kasa sabawa da irin wannan tashin hankalin da yake tsintar kansa a ciki a duk lokacin da EPILEPSY din fadeela ke fuskanta a rayuwarta ta motsa,komai qwace masa yakeyi,kamar yanzun daya rude gaba daya yana kiran sunanta,wanda zuwa sannan ta zama unconscious. Tuni baaba ramatu dake qwalla ta kirayi hajiya qarama,ganin dosowarta gurin yasa yayi hanzarin yiwa kansa saiti tare da qoqarin dawowa da kansa dai dai,bai jira isowarsu ba ya dauketa don ya sama mata gurin da zata zama comfortable ya wuce sassansa da ita da wani irin sassarfa yana monitoring numfashinta yadda yake kai kawo yana wani irin riqewa. Sosai ya kwantar da ita saman lallausar sofa,ya kuma tallafi kanta da pillow me laushi yana kallon numfashinta,a duk sanda take irin wannan abun,sai ya dinga ganin kamar zai rasata,kamar zata tafi ta barshi,hannunsa ya sanya ya juyata barin hannunta na dama don daidaituwar numfashinta da yakeyi kamar zai dauke,yaci gaba da kallonta,yana jin inama ace yana da qarfi ko wata dama da zai iya fidda wannan ciwon daga jikinta?,a ko yaushe saidai ya zauna ya kalleta helpless,har sai ta gama ta dawo hayyacinta. Maida dubansa ga agogo yayi bayan shudewar wasu mintuna,dai dai sanda hajiya qarama data iso tace "Ta tashi?" Kai ya girgiza ya jawo wayarsa a gaggauce yana neman number Dr anwar,har yanzu idanunsa nakan agogo yana irga mintunan,bata taba daukar mintuna irin haka ba tare data dawo dai dai ba,abun ya fara daga masa hankali. Kira daya tak ya daga "Fadeela ce?" Dr anwar ya fada,saboda layi ne da yasa aka tanadar masa saboda matsala irin wannan "Gani nan" ya fada kawai "Kada ka matsa daga inda take,ka barta a right side dinta kaci gaba da monitoring dinta da kuma mintunan" "Alright" ya fada yana ajjiye wayar da sauri,zuwa lokacin hajiya qarama ta koma kujerar kusa dasu ta zauna,ta hada tagumi hannu bibbiyu tana maimaita kiran sunan Allah cikin nuna tsananin tashin hankali,kauda hankalinsa yayi daga maganganun da takeyi,saboda qara masa tashin hankali da kuma karaya kawai sukeyi. Mintuna biyar kacal Dr anwar ya iso,saboda basu da nisa,layi biyu ne kadai ya rabasu. Shi ya dauketa zuwa clinic na cikin gidan,dab da zasu shiga ta motsa tana bude idanunta a hankali bakinta dauke da sunan "Daddy" miqa masa ita yayi yace ya qarasa masa da ita ciki,suna hada ido ta saki ajiyar zuciya ta qanqameshi sosai,sai taji zuciyarsa na karyewa,tausayinta da tausayin rayuwarta da kuma tsanar mahaifiyarta data jefata a wannan mummunan yanayin yana sake ratsa kowanne sashe na gangar jikinsa. Sosai Dr anwar yayi checking dinta don gano abinda yasa jijjigar tata ta dauki lokaci fiye da yadda ta saba,ya ajjiye kayan aikinsa gaba daya yana duban toufeeq,hajiya qarama na zaune daga gefe,baaba ramatu kuma na tsaye daga saman kan fadeelan "Ya kamata gaskiya a qara ninka kulawar da ake bata,akwai factor's da zasu iya ta'azzara epilepsy din,ta qaru daga adadin mintunan da aka saba yinta" idanunsa da suka sauya launi ya mayar kan baaba ramatu "Ina fatan nanny dinta tana aikinta?" Dan sunkuyar da kanta tayi,ta fahimci me tambayar tasa take nufi,idan ta bayyana masa gaskiya zai kori yarinyar ne daga bakin aikinta,idan kuma ta boye masa taci amanar mutanen da suka bata yarda,har yanzu batajin yarinyar ta samu kulawa dai dai da wadda Dr anwar ke magana akai,ita din ba komai take iya aiwatarwa ba,kamar kula da magungunan yarinyar da sauran wasu kayan qarin lafiyar,abune na wadanda sukayi karatu,ita kuma bata taba halarta boko ba,iya bakin qoqarinta tanayi wajen kula da fadeela tamkar jikar data fito daga jininta,kowa ya shaida hakan,wasu abubuwan hajiya qaraman ne ya kamata tayisu,to amma ita din ba mazauniya bace,koda mazauniyar ce ma,bata ganin alamun......... "Ko yaushe ciwon zai iya worsening,me zai hana kayi haquri a jarraba yi mata aiki?" Maganar dr anwar ta katse tunanin baaba rabi. Yayi susa ne a inda yake mata qaiqayi,kullum cikin sallolinta na dare addu'arta tafi qarfi akan ciwon fadeela,Allah ya yanke mata,idan da alkhairi Allah ya fahimtar da mahaifinta mahimmancin aikin nan ayi mata ta huta ta rabu da wannan ciwon,tana matuqar qaunar yarinyar kamar jininta. "Haba likita?,ya zaka ce haka?" "Hajiya" baaba ramatu a wannan karon ta sanya baki "Nima ina ganin abarwa Allah a gwada jarrabawa din,ba'a san inda za'a dace ba" "Dakata ramatu,ashe baki da hankali kema?" Ta fada cikin fushi "Ke kinsan ma me ake nufi da yiwa mutum aiki a qwaqwalwa?" Shuru baaba ramatu tayi tana sadda kanta qasa "Allah ya baki haquri" ta fada a sanyaye tana jin ciwon maganar data yaba mata,shi yasa sai ayi abu dubu cikin gidan bata tofa tata ba,wannan shi ya siya mata kima ya kuma sanya ta dade sosai cikin gidan. "Relax please" toufeeq dake riqe da hannun fadeela ya fada yana rage girman idonsa,dole hajiya qarama ta koma ta zauna tana huci harda qwafa "Dr,banason azo ayi abinda zai zama nadama a garemu,kaso mafi rinjaye a aikin nan bashi da tabbas na dawowarta normal,if akayi rashin dace ma abun yana iya qaruwa ko kuma a sake samun wata matsalar bayan ya qarun haka ne?" "Yes,duka akwai probability na samun hakan" "Mubar zancan" "Is ok" kansa ya mayar ga takardar ya sake rubuta mata qarin wasu magungunan ya miqa masa "Aci gaba da kula da magungunanta da muhallinta,and someone who is very knowledgeable is the one who can takes care of her" "Thanks" ya furta yana bawa dr anwar din hannu sukayi musabaha sannan yayi musu sallama ya fice. Matsowa hajiya qarama tayi tana shafa kanta a nutse "Sannu uktie" daga kai yarinyar tayi ta kalleta,saita sakar mata wani dan malalacin murmushi wanda zai nuna maka jikinta duka ba dadi,qarasowa toufeeq yayi ya bata hannu,ta kama hannunsa ya dagota,ya dauketa cak ya azata a kafadarsa "Ka bani ita mu wuce sashena ta kwana gurina mana?" Hajiya qarama ta fada "I can take care of her, don't mind it" "Okay,ke ramatu,ki tattaro magungunanta ki kawo su,a hado mata da kayan baccinta,ki cewa nanny dinta tazo part dina ta fara mata wanka ta shiryata saina miqo maka ita" "No,tell her to pack her things,gobe driver ya sauketa a inda aka daukota,she's no longer needed,zan canzata with someone better" yana gama fada ya fara takawa a hankali yana fita daga clinic din,yana jin zuciyarsa kamar zatayi melting down,wani irin yanayi na tsananin kewa da tausayin kawunansu yana tsarga masa. Shi yayi mata komai kamar yadda yace,ya shiryata cikin fararen kayan bacci masu taushi,ya bata abinci taci,tana ci ta kalleshi da fararen idanunta "Dad,kaima kaci" kai ya girgiza yana qoqarin sauke murmushi akan fuskarsa "I can't eat" sai ta bata fuska ta rufe nata bakin,ya fahimci me take nufi don haka yace "Later angel" "Sure?" Sai ya gyada mata kai yana lumshe ido. Ci gaba yayi da kula da ita,har bacci yayi awon gaba da ita,ya zauna a gefanta yana qare mata kallo cike da tausayi,zuciyarsa na gaya masa ya ajjiye komai da komai,ya zauna yayita kula da ita tsahon rayuwarsu. Qarar wayarsa ta katse masa tunanin daya zurfafa a ciki,yanzun yake shirin kasheta, saboda baya buqatar wata hayaniya kuma,ajiyar zuciya ce ta qwace masa sansa yaga sunan MAJI yana yawo saman screen dinsa,sai ya daga wayar a sanyaye ya kaarata a kunne hadi da yin sallama da muryarsa da tayi laushi qwarai "Bakayi bacci ba?" Ta tambayeshi bayan sun gaisa da hausarta da ta gauraya da sirkin larabci,cikin wani yanayi na nauyin qirji da kuma tausayi dake can qasan zuciyarta yana cinta "Yanzu nake shiri" "Ina fadeela?" "Tayi bacci" shuru na rashin sabo ya gifta a tsakaninsu sannan tace "Ka yawaita addu'a tare da miqawa Allah al'amuranka,kana buqatar matar aure ta gari kamar yadda fadeela take buqatar UWA" shuru yayi yana saurarenta,ta saba yi masa wannan maganar dake kama da wasiyya,amma kuma a yaudin tayi masa maganar da bata taba yi masa irinta ba. Shurun da yaji yasa ya gane kiran ya yanke sai kawai ya ajjiye wayar gefe,ya zame daga gefan fadeelan ya kwanta rub da ciki yana sauke idanunsa akan innocent baby face dinta. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/24, 2:11 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 34 ******Tamkar wadda aka yiwa dukan tsiya haka take dawowa cikin dakin,duk wani karsashi data fita dashi babu shi afifa sam bata lura da sauyin yanayinta ba,saboda lokacin da ta dawo din tana amsa waya ne,tana gamawa kuma ta dora mata da hirar da sukeyi dazun kafin ya fita "Epilepsy duk bahaushen asali yana mata kallon farfadiya,ciwon da aka dangantashi da aljanu,amma kuma mu a likitance ba aikin aljanu bane,aikin daga gazawar qwaqwalwa ne,na gaya miki dalilan dazu da irin yadda akeson a basu kulawa.....yanzu kuma bari kiga w......" Maqale mata maganar tayi,saboda waiwayowa da tayi taga sãahar din dafe da kanta hannu bibbiyu. Da sauri ta ajjiye system din hannunta dake dauke da zanen qwaqwalwa ta nufi sãahar din "Me yake faruwa?,kin fita lafiya kuma saiki dawomin a haka?" Ta fada tana dafa kafadarta. Kanta ta dago da idanunta da suka cika da qwalla,cikin matuqar sarewa da mutuwar jiki tace "Inajin kamar na fara gajiya da rayuwar nan" "Me kuma ya faru haka ana zaune qalau?,ko yaa muhyi dinne?" Kai ta gyada tana sharce qwallar data ziraro mata "Shine,yana maganar na sake duba akan hukuncin ajjiye aikina,ni kuma wallahi Allah afifa bazan taba iya sake taka kamfanin MT jarma da sunan ma'aikaciya ba,bazan iya daukan cin fuska ko cin kashi daga gurin kowanne d'a namiji ba a yanzu,na fuskanci iya abinda zan iya dauka,ina buqatar nutsuwa,inason nayi nesa daga dukkan wani namiji da abinda ya danganceshi,wai har kun manta da irin abinda na fuskanta ne?" Kai afifa ta girgiza,ta kama hannuwan sãahar din dukka biyun "Cool down mana bestie,taya zamu manta da wadan nan baqaqen ranakun a rayuwarmu?,yaa muhyi ba cewa yayi ki koma ba lallai,cewa yayi kiyi tunani, kina iya cewa ba zaki iya komawa ba ya baki uzuri,na tabbatar bazai sake cewa komai ba,please kada ki ja ciwon kanki ya tashi,calm down bestie" kai ta jinjina tana jin sassauci natsuwa na saukar mata kadan kadan,sai ta lumshe ido ta dafa hannun afifa "Thank you for always being with me afifa" murmushi ta saki tana jin tausayi da qaunar 'yar uwarta "Ba buqatar ki godemin,domin kamar na aikata dole na ne.....yanzu ki kwanta kawai,dare ya farayi,gobe zan qarasa miki bayanin" bata musawa afifan ba,don a yanzun itama ba abinda take buqata irin ta zauna silent ko hayaqin da takeji cikin kanta zai sauka. Ta kwanta ne kawai ta kuma rufe ido,amma duk wani motsi na afifa tana jinsa,har afifan ta gama abinda zatayi ta rage musu hasken fitilar dakin zuwa kala me duhu ta kwanta. Cikin duhun dakin idanunta keta walainiya,ba abinda ke gilmawa qwaqwalwata irin abinda ya faru da ita,rayuwarta ta baya data shude kamar zuwa da tafiyar ruwan sama,ta runtse idanunta da kyau tana girgiza kai,saboda bata shirya tuna irin wannan abun ba cikin daren daya fara nisa,saidai duk yadda takai ga toshe tunanin sai daya fara dawo mata da kansa. *_WACECE SÃAHAR?,ME YA FARU DA ITA?,ku biyoni muje mu gani_* *NAMIJI tabarmar k'ashi* Madaidaicin gida ne dake dauke da dakunan bacci manya guda biyu a qasa,da kuma mayalwacin parlor dake dauke da dukkan wani nau'i na kayayyakin da rayuwa ke buqata ga masu qarfi da kuma wadatar abun hannu. Qawataccen dining area da aka zubawa dining me kyau da daukar idanu na gilashi,da kuma qofar qawataccen kitchen din mamallakiyar gidan, kitchen din daya tara dukkan wani abu daya kamata ace akwaishi ga kitchen din diya mace. Tun daga manyan hotunan masu gidan dake manne a bango hudu na gidan kadai ya isa ya gaya maka irin gidan daka shigo,hotunane da aka daukesu bisa tsari da burgewa,gogewa da kuma sanin ilimin zamani,hotunan dake fallasa zallar soyayya qauna kulawa da kuma shaquwa tsantsa daga idanun mutanen da siffofinsu ke manne jikin taswirar. Duk da akwao banbancin siffa da kyau daga barayin mutumin dake jikin hoton zuwa ga matar dake tare dashi,amma wannan bazai zama cikas zuwa ga burgewar da zasu yiwa zuciyarka ba,hakanan bai zama cikas ga bayyanuwar soyayyar dake idanun kowannensu ba. Komai na falon a kammale yake a tsaftace hakanan a kintse,cikin wata irin tsafta kulawa da kuma sassanyan qamshin dake gauraye da sanyin ac din dake karakina cikin falon da kuma kewayensa,wani irin yanayi daka iya karyar da zuciyar dake da rauni,ya kuma bawa kowacce irin rai nutsuwa da gamsuwa. Daga saman gidan shima Parlor ne dauke da bedroom guda daya,saidai yafi dukka bedrooms din gidan girma da yalwa,shine kuma yake a mazaunin master bedroom,saidai shi parlor din baikai girman na qasa ba,saidai yana da jan hankali da alatu sosai har kamar ma yaso yafi falon qasan,hakan kuma baya rasa nasaba da kasancewarsa falon me gidan,wanda daga shi sai matarsa ke mu'amalantar sa. Cikin daya daga cikin bedrooms na gidan,dakin baccin dake da wani irin tsari da aka shiryashi cikin unique colors,qofa guda daya tal dake cikin dakin baccin ta bude a hankali. Sambaleliyar matashiya ce ta fito,doguwa mai matsakaicin tsaho,murjajjen jikin da ya hana bayyanuwar tsahonta,ya sanya tsahon ya zamana ado a gareta,fara ce sol farin dake da surki surkin ja a cakude dashi. Sassalkar sumar kanta mai tsaho santsi da kuma cika kadai ta isa ta gaya maka cewa ita din ba BAHAUSHIYA bace,saidai wani yaren daga cikin yarukan da Allah ya albarkaci qasata nigeria dasu. Kai tsaye zaka iya kiranta da KYAKKYAWA cikin mata dake da kyau a ajin farko,wani baiwar kyau da Allah ya bata tun tana ciki zuwa isowarta duniya,kyan dake iya zama barazana ga rayuwar diya macen da bata samu kyakkyawar tarbiyya ba,ko bata hadu da iyayen qwarai ba,wani irin kyau mai sanyi da tsayawa a rai,wanda ya cakuda da tsafta iya kulawa da kai da kuma gayu sannan ilimi ya hada dukkansu yayi masa ado na musamman. Towel ne kawai daure a qirjinta,cikin wata irin nutsuwa take takowa har ta iso gaban makeken mudubinta,har ta miqa hannu zata dauki daya daga cikin tsadaddun mayukan shafawarta saita fasa,ta daga kai tana kallon agogon bangon dake manne saman mudubin wanda yayi wata qaramar qara dake nuna awa guda cif ta cika. Zagayayyun fararen idanunta ta janye daga kan agogon cike da mamaki,saita dauki man ta bude,ta dan tsaya tana dubansa kamar yaune rana ta farko data fara ganinsa,ba zata iya tuna when last da ta bari man shafawarta ya qare ba,hakan yana nufin dole gobe taje shopping kenan,saita lakaci man ta fara shafe lafiyayyar fatarta cikin hanzari,tana yi tana duban wayarta dake ajjiye a gefe. Kasa daurewa tayi,gani takeyi kamar ta kasa saurin da ya kamata ace tayin,ta jawo wayar tana loda wasu numbers dake alamta ta jima da haddace su,suka cika cif ta danna kira,SOULMATE sunan ya bayyana baro baro kan screen din wayar tata. User busy ta saka mata,mamaki ya kamata,ta sake maimaita kiran aka sake sanar mata ana amfani da layin,saita aje wayar kawai ta mayar da hankalinta kacokam akan shiryawar da takeyi din,saidai can qasan zuciyarta bata daina mamakin wasu abubuwa da take gani cikin satin nan ba,wanda kai tsaye zata iya kiransu da BAƘIN ABUBUWA. Kamar ko yaushe ta shirya tsaf cikin wata lafiyayyar rigar bacci da ta saka kudi masu nauyi ta siya duk don saboda ta burge mijin nata,masoyin da duk duniya idan ka dauke iyaye da kuma AFIFA bata da kamarshi,tayi checking kanta da kanta ta tabbatar komai yayi fiye da yadda ADAM keson ganinta a kowanne dare,saita saki qaramin murmushin da ya sanya dimple din dake dukka kumatunta lobawa,ta kawo qaramin baby hijab ta saka,sannan ta dauki wayarta laptop da sauran wasu tarkace da takeson dubawa na sauran aikin office da bata qarasa ba,ta zura slippers a qafarta ta fito. Sai data kashe kowanne qwai da sauran kayan electronics dake aiki a qasan sannan ta haura saman cikin takun nan nata kamar tafiyar wahainiya,wanda ya zame mata halitta cikin jininta yake. Ba kowa a falon,sai butar shayin data barshi yana sha a dazun da sautan cups da suka bata,dukka sai data killacesu sannan ta dawo zuwa babbar qofar da zaga sadata da bedroom din nasa,tana mamakin yadda akayi duk motsinta na yau baiji ba. Da sallama a bakinta ta tura qofar,yana zaune sosai saman lafiyayyen gadon,ya jingina bayansa da fuskar gadon,saman cinyarsa kuwa na'urar laptop ce daya zubawa dukkanin idanunsa,yakuma bata hankalinsa dari bisa dari,koma me yakeyi da alama yaja hankalinsa matuqa. Sautin muryarta ya sanyashi daga kai a hankali ya watsa mata manyan idanunsa,sai ya fidda qaramin murmushi daga labbansa idanunsa nadan lumshewa saboda yadda ta dauki hankalinsa,har yaji ma komai ya fita daga kansa,shi kansa yasan Allah yayi masa baiwar kyakkyawar mace,Allah ya bashi macen da yasan qarfin ikonsa ko wani qoqarinsa.... dukiyarsa ko iliminsa,wayo da dabara dukka basu isa su bashi SÃAHAR ba face tsananin rabo da kuma irin sa'arsa,wadda tunda ya fara gwagwarmaya a rayuwarsa ya fahimci shi din me sa'ar ne. Kyawawan idanunta masu zubin gold ta narke masa tana kallonsa cikin salon kallon tuhuma,takuma maqale kafadarta tana kebe baki,sai ya daga hannayensa dukka biyun sama "Am sorry baby" saita sake kafadarta ta fara takowar saidai har yanzu bata saki fuskarta ba. Kai tsaye tayi qoqarin shigewa jikinsa sanda ta iso abinda zai zata ba,tana shigewar ne tare da qoqarin kai idanunta kan allon computer dinsa,saidai tun kafin kwanyarta ta gama tantance komai ya saka daya hannun ya rufe system din ba tare daya kasheta ba,yasa daya hannun kuma ya riqota cikin jikinsa sosai yana jifanta da wani irin kallo "Bansan lokaci ya tafi har haka ba baby" ya qarasa maganar yana kissing goshinta,a shagwabe tace dashi da muryarta dake da wani irin zaqi da taushi "Duka cikin satin nan haka kake mun,bansan yaushe na koyi bata lokaci akan computer da waya ba...... nidai ka gayamin,ko wata ka samo?". Tsam ya janyeta daga jikinsa yana duban qwayar idanunta,yanayin fuskarsa ya canza daga walwala zuwa wani yanayi na daban,idanunsu suka sarqe waje daya,sai ya girgiza mata kai "Banason na qara jin wannan kalmar daga bakinki,ina dake ta yaya idanuwana zasu iya ganomin wata macen?,kinsan matsayinki a raina kuwa?,kinsan yadda kike a zuciyata?,beside ma.....mu da muke qoqarin ganin munkai rayuwarmu wani mataki na kwatance......ina nake da lokacin da zan kalli wata diya mace?,wai kina tunanin a duniya ma akwai macen data kai kyanki kuwa?" Kanta ta cusa a qirjinsa dariya tana subuce mata,a duk sanda adam yake gaya mata irin wadan nan kalaman,tana jin kanta acan qololuwar sama,tana jin duk duniya babu macen da ta kaita sa'a,babu macen da tayi dacen mijin qwarai kamarta,tana jin cewa zata iya tsayawa takarar macen da tafi kowacce mace sa'ar miji a duk fadin duniya,zuciyarta kuma na sake nutsewa cikin shauqin son adam da kuma qara amincewa dashi da kuma sallama masa rayuwarta gangar jikinta dama komai data mallaka. Saman kanta ya dora nasa kan yana shafa sumarta da yake matuqar so yana kuma sake fito mata da abinda yake zuciyarsa a kanta,tayi shuru tana saurarensa,kowacce gaba ta jikinta tana saki cikin zallar shauqin so. Sun jima a haka kafin ya umarceta ta bashi ruwa a parlor,ta sauka a hankali ta fice tana takawa tana jinta kamar tana yawo a gajimare,yayin da shi kuma ya bita da kallo,yana jin sha'awarta na sake fusgarsa da wani irin shauqi a kanta. Kafin ta dawo ya kashe system din yama yi ready din kwanciya,ta hauro gadon ta tsiyaya ruwan ta miqa masa. Sai daya kammala sha sannan ya bata cup din yana cewa "Wannan watan ya akayi salary dinku yayi delay?" Maida cup din tayi ta ajjiye,sanna ta juyo gunsa "Sun shigo fa tun kwana uku,kawai na dan ari kudin ne na siya wasu abubuwa dasu,amma gobe nake sa ran zan tura main account din gaba daya". FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 [8/24, 2:11 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 35 Fuskarsa tadan canza kadan har hakan ya bayyana qarara "Me kikayi dasu da yafi abinda yake gabanmu muhimmanci baby?" Kai ta yada gefe tana dan murmushi kadan,adam da gaske yake,so yake yaga tabbatuwar mafarkinsu,ya bawa abin muhimmanci qwarai da gaske fiye da yadda ita din ta bashi,kodon akwai banbancin muhalli gidaje da yanayin rayuwa da dukkaninsu suka fito daga ciki ne?,batason gaya masa Afifa ta arawa,don babu jituwa ko kadan tsakaninsu,don haka tace "Wasu gyare gyare namu na mata nayi dasu" a tausashe ya kamo hannunta ya sanya cikin nashi yana duban qwayar idanunta "Idan kikaji ana batun ready made to kece,ke din baki buqatar wata kwaskwarima ko sauran gyara,ko yaushe cikin kyau da daukan hankali kike baby,so please mu maida hankali mu tara abinda muka tara mu gabatar da qudurinmu kafin cikar shekarun da muka dibawa kanmu" kai ta gyada tana dubansa,zuciyarta na qara aminta dashi,ci gabansu yakeso da gasken gaske ita da dukkan abinda zasu zo nan gaba ta tsatsonta,akwai masoyi sama da haka a rayuwa?. "In sha Allah,hakan bazai kuma faruwa ba" kai ya jinjina yana sakar mata murmushin nan nasa gami da gyada kansa. Suna shirin kwanciya ya saka hannunsa da sauri ya jawo locker din bedside dinsu ya ciro wani dan kati,sai ya fiddo idanunsa duka waje "Kaiiiii!" Ya fada yana dafe kai,ta daga idanu tana dubansa sanda take zura santala santalan qafafunta cikin duvet "Me?" Ta jefa masa tambayar tana kallon yadda ya dafe kai "Yau ya kamata ace kinje allura,ni dake duka mun sha'afa" ya qarasa maganar yana ritsata da idanu jikinsa adan sanyaye,ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi,tadan juya qwayar idanunta sannan tace "Shine duka hankalinka ya tashi haka?" Fuskarsa yadan sake hadi da qaramin murmushi sannan yace "Banaso a samu matsalane baby" "Matsala kuma?,kamar ba miji da mata ba?,kana tunanin duk babyn da zamu samu a yanzu ba zamu iya daukan nauyinsa ba?" Kansa ya girgixa a nutse ya maida katin saman drower din ya ajjiye yana duban idanunta "Ba haka nake nufi ba.....amma kinsan komai yana da lokaci,kuma komai idan aka tsarashi yafi zuwa ta dadin rai" iska ta furzar daga bakinta tana dubansa,duk cikin tsarukan adam wannan ne kadai baiyi mata ba,wannan ne kadai takejin rawar zuciya da rashin tsaiwar hankalinta a kansa,har yau har kwanan gobe ta gaza sabawa,ta kasa jin gamsuwa da nutsuwa da hukuncin,duk kuwa da cewa ta gaza musanta masa ko qalubalantarsa,tasan koda tayi yunqurin hakan yana da tarin hujjojin da zai bata da zasu mamaye tunaninta "Ko baka da wanann halin na tabbatar ina da gatan da bazan rasa komai ba" kansa ya fara girgizawa da sauri "Noooo.....Allah ya kiyaye,ta yaya hakanma zata faru?,ya za'a yi nabarwa wasu hidimarki?,har abada,meye amfanina baby?,karki qara fadin hakan,inason na nunawa duniya ne i can make it happen,i can do it,we shall live happily,wannan din akwai lokaci na musamman dana tanadarwa zuwansa" kyawawan idanunta na saman fuskarsa tana dan lumshesu da budesu, zuciyar ta na bata mabanbantan ra'ayi,ta yaya zaka tsarawa kanka abinda Allah ne kadai yake da ikon tsarawa bawa?,ta buda baki a hankali zatace wani abu,sai yasa tafin hannunsa ya rufe tausasan labbanta yana girgiza kai,sannan daga bisani ya birkitota jikinsa yana lullubeta da soyayyarsa. *_W A S H E G A R I_* Shirye take tsaf cikin wata lafiyayyar lafaya wadda ta kusan zame mata al'ada sanyatan,a duk sanda ta sakata din kuma sai kamanninta su canza,ka rasa fahimtar da wanne yare zata dangantata,wani irin kyau shigar take mata mai daukan hankali. Golden yellow ce da aka yiwa ado da brown color,dukkan takalmi jaka da dan kunne zuwa sarqa da tayi amfani dasu sunyi matuqar dacewa da shigar tata. A nutse suke takowa ita da adam din suna hira qasa qasa,sanye yake da joggers pants dogo har qasa da kuma wata shirt me gajeran hannu,hannunsa yana riqe da hand bag dinta,daya hannun nasa kuma yana riqe da key din motarta,cikin kulawa tamkar wani bodyguard dinta. Da kansa ya bude mata motar ta shiga ta zauna,sannan ya zagaya ya ajjiye mata hand bag din a kujerar me zaman banza,ya kuma durqusa saitin window din yana jifanta da wani narkakken kallo "Karfe nawa zaki dawo?" Murmushin nan dake qarawa fuskarta kyau da daraja ta saki "Zan iya kaiwa yammaci,inason na biya ta gidan momee" kai ya jinjina "Banjin yau zan fita,inaso na huta,naso mu kasance tare,amma ba damuwa,da yammar ki zauna zan shigo gidan saimu wuce tare" kai ta jinjina masa,yayi kissing hannunsa ya hura mata iskar sannan yaja da baya,ta saki murmushi ta maida masa martani,ta kunna motar yaja baya ta tasheta ta fice a gidan a hankali. Ajiyar zuciya ta saki idanunta nakan titi,kwanya da zuciyarta gaba daya ba abinda take bita sai kyakkyawan xaman dake tsakaninta da adam,wani irin zama me cike da fahimtar juna qauna tausayi da zallar soyayya,iyakar zamansu na shekara biyu ba zata iya tuna ranar data bata masa rai ko ya bata mata ba,kullum ita dashi cikin tattalin junansu suke. Lallausan sautin wayarta ya katse mata tunaninta,ta dan dubi wayar kadan dake gefanta,sunan BESTIE A ya bayyana kan screen din wayar,ta saki murmushi har qaramin bakinta yana motsawa,ta miqa hannu ta daga wayar ta sakata a handsfree. "Zaki shigo kuwa?,ko oga adam ya hanaki?" Murmushi ya qwacewa Saahar "Hooo afifa ta adam....." "A'ah.....adam dai na saahar,bar wannan zancan" ta katsi numfashinta,da alamu batason zancan "To shi kam baice komai ba,infact ma ina kan hanya,ina fatan kina gida baki wuce zoo road din ba" "Eh bankai ga tafiya ba,daman yau sai dare nake da niyyar tafiya" "Okay saina qaraso" daga haka ta gimtse wayar ta ajeta a gefe tana dora dukka hannuwanta kan sitiyarin ta dafeshi,ta sauke ajiyar zuciya sosai,tana mamakin irin wannan rashin jituwa tsakanin adam da afifan,ta sani adam yana tsananin sonta,yana kuma yin komai don ita da kuma girman qaunar da yake mata,yayin da afifa take challenging duk wani tsari ko shiri na adam din,komai nasa baiyi mata ba,bai kuma dace da tsari da kuma hasashen da takewa rayuwar saahar din ba,saidai dukkaninsu ta yiwa kowa uzuri,ta tabbatar dukkaninsu qaunarta a zukatansu ne ta kawo wannan sabanin a junansu. Tafiyar mintuna talatin kacal ta sadar da ita da shagari quaters,ta gangara layin dake shimfide da kwalta,gidajensa bisa tsarin da kana kallo kasan kusan dukka mazauna wajen suna da sukuni na rayuwa. Gida me lamba 0009 ta tsaida motarta ta danna horn,babu jimawa mai gadin gidan ya bayyana,ya kuma dage qofar gidan cikin gaggawa sakamakon gane motar da yayi,ya maida qofar ya rufe bayan shigewarta da sauri yabi bayanta. Duk da kasancewarsa ya fara manyanta amma hakan bai hanashi bude mata qofa ba yana fadin "Barka da zuwa uwar dakina" yayi maganar yana dariya,ita dimma murmushi takeyi "Baaba habu barka kadai,lallai yau nazo a sa'a,kamar kowa yana gidan ko?" Ta fada tana bin rumfar adana motocin dake gidan da kallo,wadda ke dauke da motocin uku na baqi,sauran kuma duka motar mai gidan da matar gidan ne "Aikuwa duka basu jima da shigowa ba,sunzo alhaji dr ne" idanu ta fiddo adan rude "Me ya samu abban?" "Ba komai fa,jiya ne yadan kwana da zazzabi" da sauri ta fita a motar baaba habu ya kulle mata,ta bude jakarta ta cire kudi ta miqa masa "Ayiwa iyali cefane" hannu biyu yasa ya karba yana kwarara mata godiya,bata tsaya saurarensa ba,don idan da sabo ta saba da godiyar baaba habu da bata qarewa. "Allah ya tsareki ya kareki daga dukkan abunqi da kuma sharrin me sharri" ya furta yana juya kudin a hannunsa,ya jima baiga mutane masu kirki da karamci ba irin ahalin gidan Dr Mamman girema ba. "maama" ta fada da hanzarinta sanda take shiga falon,saika dauka sun dauki wasu shekaru basu hadu ba,zallar kewa da kuma qaunar ganin mahaifiyarta ya bayyana muraran a muryarta,kiran kuwa ya iske matar har cikin kitchen dinta dake falon,tayi hanzarin daukar butar shayin data cika da zazzafan baqin tea wanda yasha hadin kayan qamshi masu kwantar da hankali ta fito tana cewa. Fara tasss kamar diyarta saahar din,doguwa ce itama,amma shekaru da girma sun sanyata tayi jiki,duk da bamai yawa bane amma ya hadiye tsahon nata kaf,saita shiga jerin sahun mata masu matsaikatan tsaho kamar saahar din,kallo daya zakayi mata kasan cewa ta zuba tashen kyau qwarai da gaske zamanin quruciya kamar yadda diyarta a yanzu take. "Eheeennn....aifa saike saahar,bansan ranar girmanki ba" ta fada murmushi na fita a fuskarta. ƙanƙameta tayi sosai kamar zata koma cikinta "I miss you maama" "Sakeni saahar,kayan ruwan zafi ne a hannuna" sakin nata tayi tana gaidata,sannan ta karbi kayan hannun nata suka jera zuwa falon Dr,cikin sakalci take qorafi "Yanzun abba baiji dadi ba amma maama a rasa me gayamin,banda Allah ya kawoni?" "Bafa wani ciwo bane,zazzabi ne da ciwon kai,kuma hakan baya rasa nasaba da stress da rashin hutu" "Amma ya kamata zuwa yanzu abba ya zauna ya huta,me yake nema Allah yayi masa komai" dan kyabe baki maama tayi "Naji su yasir na magana akai,ban sani ba ko yanzun zai yarda ya huta din" daidai lokacin da suke isowa qofar falon,maama na gaba saahar din tana biye da ita. Dattijon da duka duka shekarunsa ba zasu haura hamsin da takwas ba,zaune saman luntsuma luntsuman sofa's dake zagaye da qawataccen falon. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 36 Daga gefansa Aafiya ce durqushe saman qafafunta,matashiyar da suke sa'anni ita da sahar din,baqar fata mai haske gareta sabanin saahar dake fara tasss,saidai komai nasu kusan daya ne,kama daga tsahon da girman jiki,sanye cikin wasu gray material da aka yiwa dinkin riga da skert budaddu,tarkacen takardun abban take hadawa,daga daya hannun nasa kuma yaaya saifullah ne yake zare abun auna bugun zuciyar daya cusa qasan abun awon jinin daya nada a hannun abban,wannan kusan ba sabon abu bane,kusan duk bayan wani lokaci yana yima abban irin wannan gwajin,na hawan jini dana suger saboda kula da lafiyar abban,duk da bashi da komai daga jinin har sugar din,Allah ya bashi cikakkiyar lafiya. Daga saman daya sofa din kuma yaaya muhyiddeen ne zaune,gefansa yaaya zainul-abideen da suke kira da yaa zain,dukansu hira suke a tsakaninsu,fuskar kowa qunshe cikin walwala da farincikin dake nuna zallar sukunin rayuwa da kwanciyar hankali daya samu matsugunni cikin rayuwar kowannensu. Hawaye taji yadan tsatstsafo cikin idanunta,sai taji tayi missing gidan dama kowa da kowa,harda rayuwarta ta baya,ada ita keda wannan matsayin,ko yaushe tana daga gefan abban tana kula da buqatunsa,yanzu kuwa aure ya nesantata da komai dama kowa. A shagwabe ta qarasa shigowa falon,ta kuma isa gaban abban daya tarbeta da dukkan kulawa,abu na farko ta fara qorafi akan rashin sanin rashin lafiyarsa "Jiya ne kawai amma kinga yadda suka sanyani gaba" "Me zakizo kiyi to,bayan gamu duk munxo?" Yaaya zain ya fadi,duk da ya girmeta,infact itacema qarama,amma time to time sai ya dan xungureta sunyi fadan sako da sako. Baki ta tabe ashagwabe "Ni kaina na sani da abbana kawai" "Gaskiyarki auta ina bayanki" yaaya muhyiddeen ya fada yana murmushi,ta waiwaya tana sake masa murmushi "Yauwa yaaya na na kaina" yaaya saifullah ne baice komai ba kasancewarsa shine babba,sai ta waiwaya tana gaidashi bayan ta gaida abban tayi masa sannu da jiki,ta gaida kowa ta waiwaya ga Aafiya "Babu ko maraba bestie" "Goyaki kawai zanyi yanzun nan,shine abinda ya rage ki gane nayi murna da zuwanki" dariya duka falon aka saki,don tsakanin Aafiya da saahar babu me shiga. Shigowar saahar ya sake jinkirta tafiyar yayun nata,a nan suka sake sabon breakfast gaba dayansu,duk kowa ya cika cikinsa a gidansa kafin fitowarsa,basu watse sunbar falon ba sai kusan qarfe daya saura bayan abba Dr yasha maganinsa yadan kwanta. Suna isa dakin aafiya dake gidan ta fara warware lafayar jikinta gami da warware agogon dake daure a tsintsiyar hannunta "Bestie....bari nayi alwala nazo ki gyaramin kaina don Allah,ya dameni wallahi kwana biyun nan" idanu Aafiya ta fiddo "Hala kin manta santsi da tsahon gashinki,sai yaushe zamu gama aikinsa" karyar da wuya tayi "Haba mana bestie....."ta fada a karye "Ya na iya dake,ina hutun sallah,idan kin fito sai muyi" Aafiya tayi maganar tana nutsewa cikin sofa din dakin gami da jan wayarta ta soma dannawa. Tana idar da sallah Aafiya ta fara gyara matan,tanayi suna taba hira,abunda ya daukesu mai tsaho,sanda suka gama data duba agogo saita fidda idanu waje,ita da zataje asibiti allura?,lokaci ya qure tasan yanzun haka nurse din dake mata allurar ta tashi,batason kuma yauma su sake missing allurar kamar jiya,ta fuskanci hankalin adam bazai kwanta ba sai ta tabbatar masa tayin "Bestie taimaka kiyimin allura mana" sosai ta waiwayo tana duban saahar "Allura?,baki da lafiya ne?" Aafiya ta jefa mata tambayar dai dai sanda take amsar allurar daga hannun saahar. Juya allurar ta fara yi tana kuma qoqarin karantar allurar meye,dukka idanunta ta fitar waje,cikin mugun gigita ta watsasu kan fuskar saahar "Wannan allurar kice?,ko acan pharmacy din sukayi mistake din baki ita?" Janye idanunta saahar din tayi daga kallon tuhumar da Aafiya keyi mata,bayan ta tsareta da dukkan kallo na idanu da kuma kunnuwanta,sam ta sha'afa cewa wani babban sirri ne,sirri ne da suka tsarashi tsakaninta da adam,bata tunani duk duniya akwai mahaluqin da yasan da wannan babban sirrin idan ka dauke mommee din adam din "Allurar planning bestie?,tun yaushe kika fara?" Aafiya ta jefawa saahar tambayar tana tsareta da dukkan wani kallo dazai nunawa dan adam tsantsar tuhumar da ake masa mai tsananin qarfi da kaifi. Shuru saahar tayiwa Aafiya ba tare data amsa mata ba,yayin da Aafiya taci gaba da tsareta da kallon tana jin wani daci yana ratsata har saman harshenta,kwanyarta ta cika da nau'ikan tani iri daban daban,zuciya nata yi mata hasashe kala kala. Tasan saahar sosai har fiye da yunwar cikinta,shurun da tayi yana tabbatar mata da cewa batayi shirin amsa mata tambayarta ba,kuma muddin ta kafe akan abu,la shakka bata isa ya juyata kota sauya mata ra'ayi ba,don haka ta kwantanta yin barazana gareta ko zata samu taji bayanan da zuciyarta keda muradin ji daga bakin 'yar uwartata. Wannan ya sanya ta miqe tsam da allurar a hannunta tayi qofar fita a dakin. Cikin wani irin zafin nama da dukkaninsu basusan saahar din tana dashi ba ta miqe,cikin matuqar sa'a ta samu nasarar cafkar hannun Aafiya "Ina zaki?" Waiwayowa tayi ta watsa mata wani kallo "Zanje na nunawa maama da abba abinda kike aikatawa kanki" "Baki da hankali ne?" "Nice bani da hankali ko kuma kece saahar?" Ta kirayi sunanta kai tsaye abinda ba kasafai take yinsa ba. Ta fahimci Aafiya takai qololuwar fushi,kuma bata da sauran zabi illa ta gaya mata abinda take da buqatar ji din "Zauna sai muyi magana a nutse" "Bazan zauna ba har saikin gayan komai,yaushe kika fara wannan allurar,keda ko bari baki taba yiba tsahon shekara biyu da aurenki,muna nan munata addu'ar ganin qwanki a duniya?" "Satin farko na aurena" sosai maganar ta daki Aafiya,har sai data dan ja baya kadan,to amma tana buqatar samun cikakken qarin bayani daga bakin saahar din don ta samu makama "Satin farko kuma?,shi adam din ya sani ko munafuntarsa kike?" Gyara zama tayi tana jin tambayoyin Aafiya sunkai mata ko ina,ta gaji da jera mata tambayoyin da taketa faman yi "Kin fiya takura da zaqule zaqule,xama mukayi mukayi shawara muka yanke hakan ni dashi,duka duka saura watanni kadan watannin da muka diba su cika na dainayin allurar gaba daya,so please don Allah banason kowa yaji zancan nan,tunda dai mun kusa kammalawa". Tashin hankali sosai ya shigi Aafiya,ita da tayi karatun lafiya tasan illar da hakan zai iya haifarwa da saahar,ta sani.....saahar ta saya ne kawai,ba zancan tare da adam sukayi shawarar aikata hakan,tunda duk mahaluqin daya kwana ya tashi yasan saahar din mada mugun son yara kamar me,tana iya yin komai saboda yara,tana kuma iya barin komai saboda yara,naturally ma akan ce dukka wani ko wata auta suna da son yara,to na saahar har ya wuce misali,abun kamar cikin jininta ne,ada maama ta dauka iya na quruciya ne,saidai har girmanta har zuwa aurenta abun yana nan tare da ita,to ta yaya koda dukka jikinta kunne ne zata amince saahar zatayi planning bisa radin kanta?. To amma koma meye a yanzun tashin hankali ba nata bane,idan illa take gudarwa saahar kome meye zuwa yanzu allurar ta dade dayi mata,fada tashin hankali da masifa ta tabbatar ba zasuyi tasirin komai ba,ta sauke ajiyar zuciya bayan dabara ta fado mata,ta dawo a hankali jiki a sanyaye ta zauna daga gefan saahar,ta kamo dukka hannuwanta ta sanya a nata "Idan wani ya fahimceku bestie wani bazai fahimceku ba,idan wani bai zagi adam ba wani zai zageshi,don me kina da buqatar irin wannan allurar kinsan zan iya yi miki amma baki nemana nayi miki asirinku a rufe basai sun fallasa sirrinku ba?" Sosai maganar ta bawa saahar mamaki a yadda tasan hali da dabi'ar Aafiyan tata,ta kafeta da idanu,wani sashe na zuciyarta ta gaza gasgata zancan afiyan,wani bangaren kuma na gasgatata,tunda ita din kaifi daya ce,bata qarya don a sota,hakanan duk yadda magana takai ga rashin yi maka dadi zata gayamaka ita muddin dai gaskiya ce. Hannuwanta ta kamo cikin son gamsar da saahar din tayi yadda takeso "Wannan din sirrinku ne,kuma sai amintaccenku ya kamata ya sani,tashi nayi miki" ta qarashe maganar tana sakin hannayen saahar din,ta soma zuqe ruwan allurar cikin syringe tana mita "Shekara biyu amma bestie ace kina da wani sirri da kike boyemin,duk yadda muke dake,na sake yarda adam ya shiga tsakaninmu" sai zuwa sannan tadan saki murmushi,idan da sabo ta saba jin wannan tababar da suke akan juna,aafiya na qorafi akan adam koda yaushe,kamar yadda adam ke qorafi akan aafiya,batasan yadda zata hada kawunansu su fuskanci juna ba. "Next month idan kin tashi zuwa ki sameni a asibiti,don banason maama ta gani ta tambayi ba'asin yin allurar" "Wai meye ya sanyaki saukowa haka da wuri bestie?" Saahar ta jefawa aafiya tambayar da tun dazun take cin zuciyarta,ta kuma shiga cikin kokwanto "Saboda inason abinda bestie na takeso,kinason adam,kinason duk abinda yakeso,ni kuma inason bestie na,kuma dole na tayata son duk abinda takeso muddin da gasken ina sonta"ta amsa mata kai tsaye idanunta cikin qwayar idanun saahar. Janye idanunta tayi daga na Aafiyan tana son gamsar da kanta da gasken aafiya take,don ita din kaifi daya ce,dadi ko wuya basa sakata canza ra'ayinta. Tana jin kamar kada ta tafi tabar gidan saboda tsananin sabo da kuma soyayyar dake tsakaninta da familyn ta,amma dole qarfe uku da rabi ta yiwa maama sallama "Da wuri haka bestie?" Aafiya ta tambayeta sanda ta isketa tsaye a falo bayan shigarta kitchen kenan ta hada musu banana smoothie "Munyi da adam zai sameni gidan momee da yammar nan,daga can saimu wuce gida" tabe baki Aafiyan tayi "Ya kamata,muje na taka miki" "To bani smoothie din na shanye mana kafin na tafi,kinsan akwai amana tsakanina dashi" "Na zaci ai sauri bazai barki kisha ba" qaramin murmushi kawai saahar din ta saki,batasan me yasa duk Wani abu daya shafi adam ba aafiya bata maraba dashi,zuwanta daya tsahon shekara biyun nan gidansu adam din,ta kuma yimata rakiya da qyar,bayan sun fito kuma tayi shuru cikin mota kamar wadda ruwa ya shanye "Yadai bestie?" "Mamar adam din nan sam bata yimin ba,wai yaushe ta fara sonki ne bestie?" Aafiyan ta jefawa saahar dake driving tambaya. Dan qaramin bakinta ta bude cikin alamun mamaki sannan ta bushe da dariya,ta san halin Aafiya ba kowanne mutum bane yake mata a karon farko "Ni banga aibun momee ba,bata da matsala,tana daukata kamar wata qawarta,bata taba takuramin ba,hasalima bata iya boyen duk wata damuwarta,so kuma ni dama bata taba nunamin qiyayya ba" "K'nnnnn,haka ne" Aafiya ta fada a taqaice tana jawo wasu takardu dake ajjiye gaban motar sahar din ta tara dubawa,shuru ya ratsa motar kafin ta sake dago kai "Waye zai bude joint account kuma?" "Adam ne ya karbosu,bai gayan na waye ba yace na ajjiye masa kawai" saita gyada kai ta maida takardun da ba'a kai ga cikewa ba inda ta daukosu,ta gyara zamanta tana dauko wata hirar daban. Har bakin mota Aafiya ta rakota,saahar tanata mita "Wallahi wallahi kin bani mamaki,ban taba zaton aure zai nesantamu ba,tsahon shekara biyu cur amma zan iya irga zuwanki gidana da yatsun hannuna?,wanne laifi mukayi miki?,tun adam na min qorafi har ya koma gorantamin kan cewa baki damu dani ba,ni daya na damu dake,ko yaa zain da yake namiji ya fiki zuwa gida na fa" qaramin murmushi Aafiya ta sake "Ke kuma sai kika yarda da zancan adam?,ki rabu dashi so yake ya hadamu,aiki bestie kema kin sani,amma na miki alqawarin zuwa in sha Allah ending next month" hannu kawai saahar ta sanya tana rufe qofar motarta "Kice kawai baki shirya zuwa ba,basai kin fitomin ta haka ba" "Seriouse,Allah da gaske nake miki" ta fada tana dariya bayan taja ta bata hanya,tana nan tsaye har saahar dake galla mata harara ta mirror din motar ta fice daga gidan,Aafiya ta saki ajiyar zuciya sannan ta juya a hankali tana komawa cikin gidan. Minti ashirin kacal suka kaita unguwar sharada. Saboda ta danyi gudu ba laifi,bataso taje ta samu adam ya isa yana jiranta. A farfajiyar gidan ta tsaida motarta ta kasheta ta fito,ta fara takawa cikin nutsuwa da takuntan nan zuwa cikin gidan tana gyara laffayarta. Gab da zata qarasa qofar da zata sadata da ainihin falon gidan mata biyu suka fito,daya a gaba daya a baya,sai tadanja da baya ta tsaya don basu damar wucewa. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 : *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 37 Ta farkon macace da aqalla ta doshi shekara hamsin da biyar,saidai a ido ba zakace haka ba,saboda yanayin yadda take,kallo daya zakayi mata ka fuskanci gogaggiyar macace wadda tasan kan rayuwa sosai,idanunta fes suke,akwai wayewa mai tsanani a tattare da ita,gajeriya ce mai gogaggiyar baqar fata,tana da manyan idanuwa da dogon hanci,wannan ya qawata mata fuska sosai,ta bayan nata kuwa doguwa ce,wannan itace momee din adam,wadda suke kama sosai ta fuska. "Kina hanya ashe?,har na fidda rai?" Ta fada cikin madaukakiyar fara'a,cikin kunya da kara irin wadda kowacce diya keji ga surukarta saahar tadan duqar dakai "Ina hanya momee.....barka da yamma,ina wuni?" Ta gaida baquwar dake tare da momee din wadda ta kafeta da idanu cikin wani irin kallo na qurilla,har saahar din na jinsa har cikin jininta. Da sauri ta murmusa cikin nuna kulawa "Lafiya lou,kina lafiya?" Ta amsa da hausarta data dan baci kadan,da alama su momee din sun fita qwarewa nesa ba kusa ba "Lafiya lau alhmdlh" "Ki shiga ciki bari na rakata na dawo" momee ta fada suna juyawa da baquwar "Ina mamakin yadda adam ya samu kyakkyawar yarinya haka,kyanta na bani tsoro k......" Saahar ta jiyo muryar baquwar,wadda bata qarasa jin abinda take fadi din ba,katsewa tayi ko nisan data fara yi mata ne bata sani ba,ta sanya kai cikin parlor din momee din,wanda a yanzun ya zama abun sha'awa cike da kayan alatu. 'yar budurwar da ake kira da raihanatu ta amsa sallamar saahar din cikin mayalwacin murmushi da kuma tarin kirki da girmamawar da takewa saahar,ta qaraso da sauri tana karbar ledar hannunta hannu bibbiyu har kamar zata kai qasa tana cewa "Sannu da zuwa anty" cikin fara'a Sahar din itama ta maida mata "Sannu raiha sarkin aiki,ya gida ya aiki?" "Alhamdulillah anty,bari na kawo miki ruwa" ta yiwa ledar guri a wajen,ta juya da sauri ta doshi kitchen dinsu dake manne da parlor din,saahar ta bita da kallo. Yarinyar diya ce ga qanwar momee,momee din ta dauko riqonta,itake mata komai,kamar yadda yarinyar itama itace komai na gidan,yarinyar nada wani irin hankali kirki da kuma nutsuwa,bata da surutu sam,hakanan bata da shiga shirgin da ba nata ba. Cikin mintin da bai gaza daya ba raiha ta gabatar ma da saahar drinks masu sanyi hade da ruwa,tana murmushi tace "Mun cinye abincin rana anty,bamu gama kuma na dare ba kiyi haquri" murmushi ya subuce mata "Ni ba baquwa bace raihana,kada ki damu" ta girgiza kai tana murmushi itama,har cikin zuciyarta tana jin qaunar anty saahar din,saboda sauqin kai kirkinta kyauta da kuma kyautatawarta,matsayinta dana mahaifinta,kyawunta ko iliminta sam bai sanya mata girman kai ba ko jin ita din wata bace,uwa uba kuma yadda ta dauki momee din a matsayinta na surukarta. Bata taba komai a ciki ba,don ta fito gida a qoshe,har zuwa sanda momee ta dawo parlon ta zauna tana cewa "Sannu da zuwa,har na cire rai ai" a kunyace saahar ta saki murmushi,tadan sunkui da kai tana murza zoben hannunta "Ina sane momee,ga saqon nan" sosai ta washe baki cikin fara'a,ta miqe tsam ta dauko ledar da kanta tana budawa. Manyan kaji ne broilers da suka qanqare saboda dadewa cikin freezer,cikin ma'aikata gidansu ta sanya wata cikinsu ta ciro mata "Allah dai yayi miki albarka,ai baqi nayi,duka naman gidan ya qare,gashi ni kuma banason girki babu nama ko kadan" saita qwalawa raiha kira,cikin minti daya ta iso gurin,harara ta jefa mata "Kina abu kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,dauki wannan naman,ki cire wani daga ciki kiyimin farfesu" "Tom momee" ta amsa a ladance,ta sukunya ta dauki ledar ta wuce kitchen din. Kamar ko yaushe hira sosai momee ke janta da ita,harda abinda saahar ke ganin bai shafeta ba,to amma tana baiwa momee din uzurin banbacin al'ada da yare dake tsakaninsu,sannan kuma irin wayewarta daban da wayewar sauran surukai data sani. Mafi yawa saidai ta amsa da eh ko a'ah,ko kuma tayi murmushi wani lokacin,tun tana zuba idon ganin adam har aka kirayi sallar magariba,a sannan raiha tayi mata jagora zuwa dakinta,duk da momee din tayi mata tayin shiga nata dakin tayi sallar amma sai tace a'ah,don ba zata iya sakewa ba. Sai a sannan ta samu sukunin kiran adam din,amma harta qaraci ringing dinta bai daga ba,ta haqura ta ajjiye wayar zuciyarta na gaya mata yana sallah ne hala. Tana idarwa ta sake gwada kirannasa,cikin sa'a ta shiga,ta bada dukkan hankalinta ga wayar tana jira ya daga. Dab da zata tsinke ya daga din,muryarsa can qasa yayi sallama,ta amsa masa cikin kulawa "Nayita jiranka dear.....kuma baka shigo ba" dan gyaran murya yayi kadan "Ban samu na fita din bama,throughout yau ina gida" hankalinta ya sake kaiwa ga muryarsa "Lafiya kake?" "Me kika gani?" "Muryanka was so cool.....kaman jikinka ba qwari" "Yeah.....bacci nayi ban tashi ba har yamma,shi ya kashemin jiki" "Alright,na taho kenan?" "No,ai nayi alqawari,zan shigo saimu dawo tare" "Okay" "I missed you" ya fada cikin tsananin kulawa, murmushi ya subuce mata "I missed you too,saika qaraso" daga haka sukayi sallama ta ajjiye wayar taci gaba da lazuminta,lokaci lokaci tunani yana waftar hankalinta ya kaishi ga wani abu na daban,bata bar dakin ba har sai datayi sallar isha'i. A falo ta samu momee,ta baje dabgen kajin tana kaiwa ciki,tayi d'ai d'ai saman kujera kamar ita daya ta rage a duniyar. Raihana ta qwala kira har kusan sau uku a jere "Maza hadawa diyata abinci taci" ta amsa a aladabce,ba jima ta dawo da babban tray ta ajjiye gabanta "Zauna mana muci" saahar ta yiwa yarinyar tayi,saita girgiza kai,tamkar taga hararar da momee din ke watsa mata ta gefan ido "Zanci nawa yanzu anty,wannan naki ne". Batayi nisa dacin abincin ba ta qoshi,dama ita tun tale tale bata cikin sahun mutanen da abinci ya dama,tana rufe warmers din adam na shigowa. Hannayensa zube a aljihun wandonsa,cikin wasu shirt da trouser yake sanye,shi din gwanin wanka ne,akwai iya daukan ado me jan hankali,idanunsa a kanta,haka yake mata irin wannan kallon ko gaban waye. Kallo daya tayi masa ta dauke kanta daga sashensa,yayi mata kyau amma jikinsa babu kuzari kamar yadda taji dazu a waya,sai daya iso cikin Parlor din sannan yayi sallama yana laluben wajen zama,saahar din ta miqe tsam da tray din bayan tayi masa sannu da zuwa ta nufi kitchen dasu,duk da yadda momee ke cewa ta zauna raiha tazo ta kwashe. A kitchen din ta sameta ta gama cin abincin tana wanke plates din,da hanzari ta karba kwanukan tana mata sannu, murmushi saahar din tayi ganin yadda ta tarbeta kamar wadda tayi wani aiki me yawa "Aike za'a yiwa sannu"sai kawai taja kujerar plastic ta zauna tana bin yadda raiha ke gudanar da aikin nata cikin nutsuwa,batabar kitchen din ba har sai da adam ya leqo yayi mata magana. Sunyi gaba shida momee din,ta tsaya tana tattara jakarta data gani a bude,ta danyi mamaki,don tasan a zuge tabar jakar,to amma sai wata zuciyar ta bata may be ta manta ne,a buden ta barta,tunda babu wani baqo cikin gidan bare parlor din bare ta zargi wani abun. "C'mon momee,please kibar maganar nan" muryar adam kenan dake fita a kasalance idanunsa nakan saahar dake fitowa,waiwayowa momee din tayi kafin ta maida dubanta ga adam "Okay,amma kayi tunani akai ka gani,think twice kafin yanke hukunci" "Nasan abinda nakeyi fa" ya amsa mata kai tsaye yana dosar motar saahar da key din ke hannunsa,ya buda mazaunin mai zaman banza yana jira isowarta. Sai data yiwa momee saida safe,ta rakata da addu'o'i kamar zata rusuna mata har qofar motar,saahar din ta shige a kunyace kan yadda momee din ke mata,sannan ya zagaya shima ya shiga seat dinsa,ya tayar da motar suka fice a gidan. Shuru ne ya ratsa motar,tunanin saahar ya dauketa ya wulwula da ita can baya,wasu watanni masu dan dama da suka shude cikin rayuwar aurenta da adam,koda cikin tarin mafarkai,bata taba tsammanin zatayi mafarki guda daya da zai nuna mata nan gaba momee zata sota ba,zata amsheta hannun bibbiyu a matsayin suruka ba,sai gashi a yanzun......cikin wani hali da yafi kama da juyin juyi momee ta amsheta har fiye ma da yadda take nunawa adam qauna da kulawa,duk da kasancewarsa tilon d'a a gareta. Saukar hannun adam saman nata hannun ya fargar da ita,ta waiwayo ta zube masa kyawawan idanunta da suka tilasta masa lumshe nasa idanun "Yaadai?,akwai matsala ne?" Tattausan murmushi ta sakar masa tana girgiza kai "Babu" sai yaja hannun nata zuwa bakinsa a tausashe yayi kissing bayan hannun,wani abu ya sauka a zuciyarta,ko yaushe adam baya gajiya da ita,hakanan baya gajiya da bayyana zallar soyayyarsa a gareta. ********Misalin qarfe shida ne na yamma,dai dai lokacin babu abinda gidan yake fitarwa sai daddadan qamshin turaren wuta daya wadaci kowanne lungu da saqo na gidan,sai sauran burbushin qamshin daddadan abincinta da tuni ya gama zama ready saman dining table. Saahar din irin matan nan ne da suka kai sunan mata ta kowanne fanni na rayuwa,suka kai qololuwa gurin iya zamantakewar gidan aure,suka kuma qware tare da ci gaba da neman sani cikin kowacce rana ta ubangiji ga dukkan macen data amsa sunanta,ta kuma qware gami da sanin dukka hanyoyin kyautatama miji,tare da zama tauraruwarsa. Tun daga abinda ya shafi kyan sura,gayu dake cakude da ilimi da kuma tsantsar tsafta,kawaici haquri da iya mu'amala,uwa uba iya girki da kuma gyaran kai kowanne lokaci lungu da saqo,ta yadda zata dace da muradin adam,tasan yadda zata hadawa kanta nau'in dukkan wani abu da zai daga martabarta da darajarta na diya mace awajen miji. Idan ka shigo gidan ka sameta kaga yadda take tafiyar da gidanta cikin tsari da nutsuwa ba tare da ta buqaci me aiki ba zakiyi matuqar mamaki,duk da tarin gata da dukiyar da mahaifinta keda ita,amma wannan sam bai sanya ta dauki kanta takai wani bigire ba,tana ganin cewa cinyewar rayuwar mace a gidan aurenta shine ta bautatawa mijinta,tayi hidima cikin gidanta da dukka jikinta da hannuwanta. Kamar yanxun data kammala komai,tana sanye da wata gown ta wani farin material me santsi qal dashi,ta daure sassalkan gashinta cikin farin ribbom daya dace da rigar jikinta,jikinta na fidda wani sihirtaccen qamshi da babu lallai ka iya tantance ainihin turaren da tayi amfani dashi kai tsaye,qamshine mai tafi da zuciya da tsayawa arai,tana qaunar qamshi har batasan iyaka ba,zata iya saka ko nawa ne ta siyi turare muddin qamshinsa ya dace da tsarinta. Tana shirin zama ta tuna bata hada ruwan wankan adam din ba,saita aje wayar hannunta,ta juya cikin tafiyarta me kama da na me tausayin qasa ta wuce dakinsa sannan ta zarce toilet dinsa. Daga ciki ta jiyo qarar sautin wayarta,ta goge hannunta jikin rowels din dake rataye a bandakin cikin tsari,wanda da kanta ta zabarwa kanta tsarin duka toilets dinsu,take kuma kula dasu kamar ba muhallin qazanta ba saboda yadda suke samun kulawa. Special tone ta sanya masa,don haka kafin ta qaraso ta fahimci wanda yake kiran, murmushi ya subuce mata,ta juya qwayar idanunta sannan ta daga wayar ta kara a kunnenta "Amincin Allah ya tabbata a gareka" "Tare dake mace daya tamkar da dubu.....nazo wuce wani fish park ne naga suna gashin kifi,kina da buqata ne?" Take taji yawunta ya tsinke,ta tuna wanda taci shekaran jiya kamar ta tsinke harshenta,tunda take bata tana craving na kifi irin wannan karon ba "Na gode qwarai da gaske dear,ina buqata idan har zan samu" "Kin samu ma matar aljanna,kinfi gaba haka,kinfi qarfin ki nema abu ki rasa" ya fada a tausashe,sautin murmushinsa yana isa kunnuwanta,idanunta ta juya dadi yana dada ratsata,idan tace duk duniya babu miji kamar nata to ba shakka batayi kuskure ba,batajin a wannan lokacin akwai miji kamar nata,ko yaushe soyayyarsa a gareta sabuwa ce,kulawar data tabbatar mata da yawa sun rasata,wasu kuma suna kewarta,batasan dame zata amsa masa ba,saidai farincikin da takeji wanda a kullum baya gajiya da sanyata a cikinsa,a haka ya barta da waya a hannu tanata smiling,kafin daga bisani ta zame wayar daga kunnenta,ta koma ta zauna saman kujerar ta zauna,sannan taja wani english novel tana dubawa qafarta daya saman daya tana jiran qarasowarsa. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 38 Horn dinsa kadai ya isar mata da saqon dawowarsa,ta ajjiye littafin a gefanta ta miqe a nutse tana takawa zuwa farfajiyar gidan. A tsakiya suka hade, yasa dukka hannayensa biyu ya tarbeta,ya dagata sama cak yana dariya "Na jima banga macen da bata da nauyi kamarki ba" dubansa tayi sosai da dukka idanunta,saiya lumshe idanunsa yana jinjina mata kai "Ka jima kuma?,akwai wata ne bayan ni?" Idanunsa dukka ya ware yana dubanta gami da girgiza kai "Babu,har abada kuma ba za'a samu ba,idan mutane na cewa kada ki yarda da mijinki muddin zaice miki bayanke babu qari,banda adam a ciki,ki rubuta ki ajjiye,ina miki magana ne kan qanne na da nake dasu wanda momee ta riqesu kafin daga baya ta aurar dasu tun a ghana" murmushi ta saki tana saqalo wuyansa "Nima nafison na zauna a haka,don banason ka daina daukata" ta fada tana langabe kai. Dariya ya saki yana duban idanunta "Kina tunanin akwai qibar da zatayi sanadin da zan daina daukan matata masoyiyata?,babu ita,muje ciki na baki kifinki" daga haka ya taka da ita zuwa ciki suna hira qasa qasa. Tun hankalinsa baikai kan yadda take cin kifin hannu baka hannu qwarya ba har ya ankara,ya tsaya da abinda yakeyi yana kallonta,sai ya kama hannunta da take qoqarin kaiwa baki ya riqe yana dubanta cikin kokwanto,suka hada idanu saita sakar masa murmushi "Please dear,don Allah ka barni na qarasa mana" "Yaushe kika zama hadamammiya ne?" Wuyanta ta langabe tana kallonsa "Nima ban sani ba,kawai dai na wayi gari inason kifi fiye da komai" hannun ya sakar mata,sannan ya koma da baya ya zauna yana fuskantarta,yanayin fuskarsa yana dan canzawa kadan bada wani alamu me yawa ba "Tun yaushe?" Ya jefa mata tambayar,wanda ita tuni taci gaba da cin kifinta,ta daga kai suka hada ido "Dearrrr.....ka bari na gama tukunna,ban qoshi ba Allah" shuru ya danyi yana ci gaba da kallonta,kafin ya miqe yana zare kayan jikinsa saboda wanka da yakeson shiga. Tun daga shirinsa zuwa zaman cin abincinsa da shirin kwanciya baccin da sukayi ta lura kamar kuzarinsa ya ragu,da tayi complain sai yace "Yau nayi overwork baby,jikina duka ciwo yakemin" tsam ta miqe,ta shiga kitchen ta hada masa ruwa me dumi,daga gefansa ta zauna ta miqa masa mug din "Ga wannan kasha,yana sauke gajiya" kurba daya yayi ya miqa mata,saita langabe kai tana kallon fuskarsa "Ai baka sha ba dear" kansa ya girgixa yana dan qaramin murmushi "Cikina ya cika fa,ko kin manta abinci na gama ci yanzu?,ba space,hakanma is okay,thank you". A sanyaye ta sauka daga saman gadon,yadan bita da kallo sannan ya gyara zamansa sosai saman gadon yana dubanta "Yauwa kafin ki fita kiban wancan briefcase din,ki dawo a kitchen din kizo ki gani" miqa masan tayi taje ta ajjiye mug din a kitchen din sannan ta dawo,ta zauna daga gefansa tana kallon takardun daya fito dasu. Biyu daga ciki ya zaro ya miqa mata,ta karba amma tana masa duban neman qarin bayani "Wadan nan filayen ne da mukayi zamu siya ni dake,an gama cinikinsu kamar sauran,ga takardun ki saka hannu" a nutse ta karanta rubutun dake jikin takardan,kamar kullum kamar kuma ko wanne lokaci,duk sadda suka siya wata kadara tare dashi,maimakon sunansu su biyun sunanta yake sanyawa,tasha masa qorafin shi da ita duk daya ne,koda sunansa ya saka dinma ai babu laifi. Motsa bakinta tayi,yasan qorafin data saba zatayi masa,sai ya saki murmushi ya daga mata hannu "Bazan fasa saka sunanki ba fa,karkiyi ma magana,don na saka sunanki sai meye?,komai dana mallaka naki ne fa,bare ni dake din mun riga mun zama abu daya,saka hannu kawai" ya fada yana miqa mata biro,cikin sanyin jiki tare da jinjina qauna soyayya da kuma fahimtar juna me zurfi dake tsakaninta da adam din ta yi signing da signature dinta,wata irin sign me matuqar kyau da tsari,ta miqa masa takardun tana cewa "Allah yasa musu albarka.....ina alfahari da irin tunaninka da qoqarinka" ta fada tana jinjina kai,tsarin daya kawo musu naci gaba ita sam bata taba kawowa ranta tayi hakan ba,daga aurensu zuwa yanzu suna da filaye masu suna filaye da suka hada kudi suka siya masu yawan gaske,hakanan zunzurutun kudin dake join account dinsu dake maqare da kudin da suke zubawa duk wata daga cikin albashin kowannensu,wanda dashi suke saka ran amfani da filinsu da yafi kowanne girma su tayar da ginin katafaren kamfani. Murmushi yayi bayan ya mayar da takardan cikin takardunss,ya sanya hannunsa ya rungumeta tsam cikin jikinsa yana shaqar lallausan qamshinsa "Ni yafi dacewa nayi wannan godiyar" saita kwantar da kanta saman qirjinsa tana sakin murmushi,zuciyarta fes,cike da zallar farinciki hadi da samun nutsuwa da cikakkiyar gamsuwa da kalar mijin da take da. ***********Tsaye tayi bayan gama wanke mata kan tana goge ruwan kan nata da qaramin towel don dake saman kanta wanda ke dauke da tambarin katafaren gurin gyaran kai da jiki na mata Thairaphy saloon and spa,zare towel din tayi ta ajjiye,afifa dake zaune tana duba wani magazine ta daga kai tana dubanta "Ya dai" "Kifi zanje nemowa,nan haka nasan ba za'a rasa ba" ta fada tana maida rolling Vail dinta saman gown din jikinta da hanzari, rufe magazine din afifa tayi tana kallonta "Amma kinsan ba'a yi gyaran jikin ba ko?,karmu bata lokaci fa" "Manta kawai,yanzu zan dawo" ta fada tana zaro key din motarta daga jakar,cikin sauri ta nufi qofa "Bansan qaunar data shiga tsakaninki da kifi ba" "Nima haka"ta bata amsa a qagauce,sai afifan ta bita da kallo,wani abu ya darsu a ranta, murmushi ya qwace mata tana jinjina kai "Allah ameen"ta fada tana ci gaba da gyada kai kamar qadangaruwa,kafin muryar daya daga cikin ma'aikatan dake wajen ta katse mata tunani,ta miqe tana zare nata dankwalin,gashinta me cika da tsaho ya bayyana,ma'aikaciyar taja mata kujera ta zauna aka fara gyara mata nata gashin. Afifa na zaune daga saman kujerar tana karantar yadda saahar kema kifin wani irin ci,zargin dake ranta yana sake tabbatuwa,iya saninta da asaahar bame ciye ciye bace,hasalima ko yunwa zatayi mata meye bata yarda taci abinci a waje, especially idan wajen na jama'a ne kamar haka,tana da wani irin halayya dda dabi'a ta daban data banbanta data koww,batace mata komai ba har sai data gama,ta wanke hannunta da kyau ta sauke ajiyar zuciya hadi da murmushi tana kallon afifa,sai afifan ta tabe baki tana kau da kai "Wanda yaci shi kadai dai shi kadai zai mutu" murmushi mai sauti ya kufcewa saahar,tasa hannu tana rufe bakinta "Am sorry bestie,na manta gaba daya,gaskiya ban kyauta ba,but zan fanshi kaina,zan siyo miki wani harfa sai kinci kin ture" "Banso" ta fada tana jefa mata hararar wasa,cikin zuciyarta cike fal da wani irin farinciki kyakkyawa fata da kuma zato me qarfi akan saahar din. Awa biyu suka gama abinda sukeyi sukabar wajen suka wuce zoo road gidansu afifa,tun cikin mota ta fara jin jikinta yayi laushi,kasala duka ta rufeta,ga wani yanayi da yake saukar mata kamar zazzabin cikin qashi. Afifa dake tuqi ta waiwayo ta kalli saahar din "Anci kifi anyi dam baki ya mutu" ta fada cikin salon tsokana,wannan ya bawa saahar damar muskutawa tana yatsina fuska "Jikina me a mace kaman fever keson kamani" "Ya salam......aiko mu qarasa gida nayi miki test na gani,amma me zai hada madam adam da maleria ma?" Fuska ta yatsina tana jin jikinta sosai babu dadi "Ba wani test fa,kusan last two weeks ina jin hakan,ko aiki ma daurewa kawai nakeyi,nafi zaton maleria din na kwaso,kinsan munje wata ziyara da momee munyi kwana daya" tsaki afifa taja cikin ranta,yadda bata qaunar d'an matar haka uwarma,saidai ba yadda zatayi sun riga sun zama daya a yanzun,tunda suna auren 'yar uwarta kuma aminiyarta tun daga quruciya har zuwa girma,sai bata sake cewa saahar din komai ba,har zuwa sanda suka qaraso gidan. A harabar gidansu ta tsaida motar,saahar ta rigata fita ta wuce ciki,sai data kashe motar ta kulleta sannan tabi bayanta. Saman kujerar falo ta sami saahar din a zaune,ummi mahaifiyar afifa tsaye a kanta suna magana,matar data debo dukka kamannin Dr mamman girema,wanda ko ba'a gaya maka ba zaka fuskanci JINI DAYA ne ke yawo a jikinsu,ba zaka kirata da yayarsa ba,saboda shekarun dake kwance a jiki da fuskarta basu kai na dr mamman din ba,don haka zaifi dacewa ka bata matsayi na qanwarsa. "Ki duba saahar afifa kafin ku shiga shiriritar taku" abinda ummi ta fada kenan tana wucewa kitchen. Dakin afifan da bashi da maraba dana saahar suka kwasa suka wuce,dukkansu tun kafin auren saahar ba zaka banbance dakin waccar da waccar cikin gidansu ba,kowacce tana iya amfani da dakin 'yar uwarta,ta kuma yi tasarrufi dashi yadda taga dama,har zuwa yanzun da duka dakunan afifa ke amfani dasu,duk da ita dinma ta kusa kaucewa tabar gaban iyayenta,don akwai kudin khalifa idress a kanta,akwai abinda ya kawo tsaikon sanya rana da mahaifin afifa ya roqa a daga masa,yanason kammaluwarsa kafin saka ranar. Kan yalwataccen gadon afifan saahar ta zube tana fidda iska daga bakinta,tana daga kwancen tana kallon afifa ta gama hada komai da zata buqata sannan ta kalleta "Taso mu gani" miqewa tayi tana cire dankwalin kanta da takejin ya mata nauyi ta ajjiye a gefe "Amma da ki fara da yimin allura ta ko?" "Waime?,allurar planning?" Kai ta gyada mata a kasalance,wani abu mai tauri yazo ya tsayawa afifa a wuya,ta allura ma take ana batun duba lafiyarta?,duk da hakan afifa ta shanye bacin ranta,don tasan zaiyi wuya idan ramin data ginawa adam din baiyi zuruf ya afka ba,don ba zatace ramin data ginawa saahar ba,domin a gareta ba rami bane wannan,abinda tayin dai dai yake da tudun muntsira data ja hannun saahar din ta kaita ba tare da ita kanta ta sani ba "To madam biyayya vice's qauna,taso na fara duba lafiyarki tukunna,tunda itace gaba da komai" duk da jikinta ba dadi sai data saki qaramin murmushi ta girgiza kai,tabi qaramar robar da afifa ke miqa mata da kallo "Me zanyi da wannan?" "Fitsarinki nake buqata" dan kafe afifa tayi da kallo kamar me tunani,sai kuma tasa hannu ta karba ta shige toilet din afifan. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 VIP🔥💯 Zafin kai 3k Furar danko 3k Tabarmar kashi 3k Bakon munafuki 3k *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 39 Bata jima ba ta fito da fitsarin,ta miqawa afifan ta koma ta zauna tana lumshe idanunta,tana jin yadda jikinta yake qara zama weak,ita kanta tana mamakin wanann sauyin da bata taba jin irinsa ba. "Yes!!!!" Afifa ta fada da wani irin madaukakin sauti "Alhamdulillah Alhamdulillah" ta maye gurbin furucin nata da sauri tana murza tafukan hannayenta waje daya. Sai a sannan saahar ta bude idanunta a hankali ta zubesu akan afifa dake tsaye tana ta faman buga murmushi,dukka hankalinta da idanunta nakan saahar "Me wai?" Ta tambayeta a gajarce,sai fuskar afifan ta sake fadada da farinciki,abinda ke nuni da cewa farincikin dake danqare a zuciyarta ba kadan bane a wannan lokacin "Congratulations mrs adam,congratulations" ido saahar ta fidda tana duban afifa "Meye a kanki bestie,da ciwon kikemun murna ko kuwa?" Dariya ta saki a nishadance "Wannan ciwon ai irinsa muka dade muna nema miki,you are pregnant bestie" cak komai ya tsayawa saahar saboda yadda maganar tazo mata a bazata na farko,na biyu kuma yanayin yadda cikin yazo,murna zatayi ko akasin hakan?,duk da tana da tsananin buqatarsa,tana cikin kewa da qishirwar samun yaro a kusa,tana qaunar yara qwarai da gaske har batasan iyaka ba,to amma kuma har yanzu basu cimma plan dinsu da adam ba,hakan na nufin cikin yazo a lokacin da basu shiryama zuwansa ba ko kuwa?. "Bestie banason wasa,kina magana ne akan rayuwata fa" batace mata komai ba sai dauko strip din datayi mata test din dashi ta ajjiye mata a gabanta,layuka biyu gasunan sun bayyana radau kamar ma sunfi fitowa a jikin nata tsinken fiye da yadda suka saba fitowa,hakan yana nufin cikin ba na satin jiya ko yau bane. Kanta ta dago jikinta a sanyaye ta kalli afifa "How comes afifa?" "Min indillah" ta amsa mata kai tsaye tana goye da hannyenta a qirji,tana qarewa saahar nazari da karantar yadda ta karbi cikin a ranta. Akwai farinciki shinfide can qasan fuska da zuciyarta,amma ta karanci kamar akwai wani abu mai nauyi dake tasowa yana danne wannan,wanda jikinta yake bata koma meye baya rasa nasaba da adam "Ciki dama yana iya samuwa ana tsaka da yi maka injection na planning?" Dukka girarta ta daga kafin ta amsa mata "Yes mana saahar,akwai wanda ya isa halittar Allah wanzuwa aduk sanda yaso?,allura fa just wani qaramin garkuwa ne da bai isa ya hana Allah yin yadda yaga dama da bayinsa a duk sadda yaso ba" "That's absolutely true" ta furta a hankali tana gyada kai,bata iya sake cewa komai ba saahar din,sai ta samu kanta da cika da farinciki,dukkan wani kwadayinta da son haihuwarta yana dawowa sabo fil cikin ranta,farinciki takeji yana mamayarta irin wanda bata taba tsammanin zata tsinciki kanta a ciki ba,lallai haihuwa ni'ima ce,'ya'ya kuma rahama ce da babu kamarta(Allah ya azurta masu nema da samu,ya bayar dame albarka ya albarkaci diyoyin musulmai gaba daya). "Ni ya kamata na yiwa mr adam wannan albishir din,ki kwanciyarki,zan prescribing maki wasu magunguna idan yazo zaku wuce sai ya tsaya ya siya miki,don't mind any changes da zakiji a jikinki,you will be alright in sha Allah soon" kai ta gyada tana lumshe idanunta,afifa ta dauki wayar saahar din da zummar kiran adam din yazo ya dauketa,tabar saahar da ido a lumshe,hannunta saman plate tummy dinta tana shafawa a hankali,tunani fal kwanyarta,wai ita din itace zata zama uwa,itace wata halitta yanzun haka ke rayuwa a jikinta,murmushi ya subuce mata,wata qaqqarfar soyayyar abinda duk ke kwance a marar tata ya fara sauka cikin zuciyarta. Afifa bata sanar da saahar zuwan adam ba,ta sanya an saukeshi a Parlor din baqi na gidan,ta sanya me aikin gidan takai masa ruwa da lemo,sannan ta shiga daki ta zura dogon hijabi ta fito. Ta iskeshi zaune a falon,cikin shigar qananun kaya,ya cika falon da turarensa,hannunsa riqe da wayarsa yana chart. Baki afifa ta tabe sannan tayi sallama,ya daga kai yana amsa mata sallamar,fuskarsa kadaran kadaham,haka kawai jininsa bai taba zuwa daya da yarinyar ba ko sau daya,kamar yadda itama nata jinin da nasa bai haduwa sam,kawai dai kowa yana dakewa ne saboda darajar saahar dake a tsakaninsu. Hannun kujerar dake daura da qofar fita ta zauna tana cewa "Sannu da zuwa mr adam" zamansa ya gyara,ya maida wayar aljihunsa,ba tare da ya amsa mata ba ya jefa mata tambayar "Ina baby?" "Babynka tana ciki,yanzu zata fito....." Sai tadan dakata,ta fidda iska kadan daga bakinta,bayan ta sake canzawa fuskarta yanayi,babu sauran sassaucin data shigo dashi "Na fara iskeka ne don nayi miki kyakkyawan albishir din cewa ka kusa zama uba,babyn naka na dauke da wani babyn naku......i mean matarka nada juna biyu" ta qarashe maganar tana zube dukka idanunta akan fuskarsa,tana fatan ko yaya ta fusgi wani reaction nasa,wanda shi zai bata kowacce irin dama da takeson samu daga gareshi. Cak komai ya tsaya a falon tsakaninta da adam din,kafin daga bisani ya sakar mata murmushi yana juya key din motar dake hannunsa "Ban taba zaton ke mutuniyar kirki bace irin yau,kin iya kawo kyakkyawan albishir,duk da naso na fara jin hakan daga bakin baby...... anyways.....ke da ita duk daya ne,ina taya junanmu murna" ya qarashe maganar yana tsareta shima da nasa kallon. Murmushi ta saki tana murza hannunta "Haka ne abinda ya kamata ya fito daga bakin kowanne magidanci na qwarai.....shikenan daga yau allurar planning ta qare,saika maida hankali ga kula da abinda yake cikin nata,yadda kake kula da duk wani kudi da zai shigo ko ya fita ta account dinta,da yadda kake kiyaye lokuttan yin salary dinta da sauran komai nata.....ina fatan yaron da ba'a shirya zuwansa duniya ba..... ubangiji ya qaddari zuwan nasa ta silar innarsa afifa......zai samu kulawa matuqa da qauna hadi da soyayya,kwatankwacin wadda ake iqirarin ana yiwa mamansa......yanzu zan turo maka babyn naka,ku sauka lafiya" daga haka ta miqe tana ficewa daga falon,yayin da adam ya miqe tsaye yana rakata da ido,zuciyarsa na suya sosai. Ya akayi yarinyar ta rainashi har haka?, waye ya gaya mata sirrin rayuwarsu da yadda suka tsara zasu tafi da ita tsakaninsa da matarsa mallakinsa?,me yarinyar ke nufi akansa?,wanne kallo takeyi masa?,akwai maganganu da yawa da yakeson gaya mata don tasan shi din ba sa'anta bane,to amma kuma ta riga tayi nisa ba ta yadda zai iya amayar mata da dukkan abinda yakeson fada din. Sosai Zuciyarsa ke quna,ransa yayi matuqar baci da maganganun afifan,a zafafe ya fita a falon,ya bude motarsa ya zauna yana jiran fitowar saahar,ya tabbatar banda saahar na sonshi so na gasken gaske,yayi amannar da tuni afifa ta dade da tarwatsa kyakkyawar mu'amala ta fahimtar juna kyautatawa da girmamawar dake tsakaninsa da ita. Sallamar saahar din kawai ya iya amsawa,ba tare daya waiwayo ya dubeta ba ya tayar da motar ya figeta suka fice daga gidan,saahar da batasan abinda ke faruwa ba ta bishi da kallo galala cike da mamaki "Na dauka zaka shiga ka gaida ummi ne ai" ta fadi a sanyaye tana mamakin abinda ya canjashi da matsanancin fushi haka lokaci guda. Shuru baice mata komai ba,sai mamaki ya sake kamata,ta gaza dannewa saboda bata saba ganin irin wannan yanayin a tare dashi ba "Dear......lafiya kuwa?,ko wani abu ya faru?" Da wani irin gudu ya gangara gefan titi ya tsaida motar,cikin tsawa da hargagi ya soma magana "Saboda zallar rainin hankali ma ni kike tambaya lafiya?,bayan kinsan komai?,kinsan abinda ya farun?,ki aiko 'yaruwarki ta cikin mutunci ta wulaqantani,ashe yawo kike dani kina bayar da labarin ina karbar dukiyarki,kina gayawa duniya nidin makwadaici ne?,to ki sani ba abinda zanyi da dukiyarki,ki kuma gayawa wannan banzar 'yar uwarki taki afifa ta fit......." "Ya isa!!" Ta fada da qarfi zuciyarta na wata irin suya,mamakin adam yana cikata,ta dinga kallonsa sosai waiko zataga wani sign na fara shaye shaye a tare dashi,tunda take dashi ko kallon banza bai taba hadata dashi ba bare tsawa har irin haka ba, zata iya jure komai amma banda zagin afifa,don ita din Wani sashe ce ta jikinta "Ta yaya zaka zo kana hukuntani akan al'amarin da bansan dashi ba?,har kana qoqarin zagin afifa,afifan da bata nufinmu da komai sai alkhairi?" "Kedai!,amma banda ni,yadda ta tsaneni nima haka na tsaneta,i hate her with passion,idiot....." Saiya finciki motar da kyau,har saahar nayin gaba zata daki gaban motar ta kare da hannayenta, hankalinta ya tashi sosai,bata saba ganin tashin hankali ba,kamar yadda bata taba ganin bacin rai makamancin haka daga gurin adam ba,duk da tasan yana da fushi amma bai taba kwatanta mata ba. Kuka ta fashe dashi tana dora kanta saman cinyarta,wanne abu afifa dinta ta yiwa adam da zai dauki irin wannan mugun fushin?. Suna isa gidan yaci burki,ya fita yabarta a motar bayan ya kashe. Da hanzari itama ta fita a motar tabi bayansa,saidai bata cimmasa cikin falo ba,tana niyyar binsa daki da take jiyo motsinsa da qarfi sai gashi ya fito,hannunsa dauke da wani file. *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 40 Yana daga tsayi ya wurgoshi kusa da ita,abinda ya baiwa dukka takardun ciki damar fitowa suka warwatsu a falon "Ga komai naki nan,ki duba dukka abinda babu a ciki ki rubuta zan biyaki,sauran abinda mukayi hadaka kuma ki lissafa nawa ne na cire miki naki" ya qarashe maganar cikin fushi. Iya wuya zuciya tazo mata,sai taji ba zata iya jurewa wannan abun nasa ba,bayan batasan me tayi masa ba,ta miqe a fusace karo na farko a tarihin zamansu data taba maida masa magana "Basai ka fake da abinda afifa tayi maka ba,zaka iya cin mutuncina duk ta yadda kaso adam,na gode" kuka ya qwace mata ta juya da hanzari ta nufi bedroom dinta. Sautin kukanta bai hanashi wucewa dakinsa ba yana jan mugun tsaki,amma tsakanin awa daya zuwa biyu sai wayarsa tayi qara,ya kalli wayar yaja tsaki,banda me kiran nada muhimmanci a wajensa ba abinda zai sanyashi daga wata waya a yanzu,shi daya yasan iya adadin yadda ransa yake a bace da kuma irin rudanin daya samu kansa a ciki a iya ranar yau,komai yazo masa a bazata,ya miqa hannu ya daga wayar yana maqaleta a kunnensa. *_BAYAN AWA DAYA_* Ajjiye wayar yayi,ya shiga toilet dinsa ya fidda kayan jikinsa yayi wanka,ya dawo ya shirya cikin armless riga da boxer dinta,ya feshe kansa da turare sannan ya wuce dakinta. Yayi mamakin tarar da ita tana kuka har sannan,yayi tsaye a kanta yana kallonta,sai yaji zuciyarsa ta karyo,ya qarasa kusa da ita ya dora hannunsa saman bayanta "Awa nawa kikayi kina wannan kukan da bashi da amfani?,bayan kinsan bake kadai bace?" Maganar tasa tazo mata a bazata,sai kukan nata ya tsaya cak,yadda yayi maganar juna biyun dake jikinta kadai ya tabbatar mata shima yana maraba dashi,sabanin yadda tayita tunanin da yadda zata fahimtar dashi. Bata gama wannan tunanin ba taji ya sanya hannunsa duka biyun ya dagota ya rungumeta yana fadin "Am sorry,raina ne a bace" ajiyar zuciya ta saki tana narkewa a qirjinsa,cikin lokaci qalilan komai ya wuce a tsakaninsu kamar komai bai faru ba,kasancewar basu saba samun sabani a tsakaninsu irin haka ba,sai ya bude sabon shafin tattalinta tare da nunawa abinda ke cikinta zallar qauna muraran,wannan ya wanke komai daga zukatansu. *********Cikin kwanakin da suka biyo baya komai ya koma normal,hankalin saahar ya sake kwanciya sosai da yadda adam ke tattalinta yana nunawa cikin jikinta qauna,har excuse ya nema mata daga wajen aiki saboda laulayin da take fama dashi,laulayi takeyi sosai,yau lafiya gobe babu lafiya,gaba daya hankalin 'yan gidansu yana kanta,tun daga kan abba har ya zaid da take bi,kowa tattalinta da kuma riritata yakeyi,kamar itace zata haifa musu jikan farko. Saidai duk irin riritar da suke nuna mata bata kai rabin wadda adam ke mata ba. ********Zaune take saman couche,ta miqe qafafunta sosai yadda zata sake,chiffon armless short gown ce a jikinta,wanda rashin tsahonta ya bawa sambala sambalan kyawawan qafafunta damar bayyana. Waya suke da momee,wadda kullum kwanan duniya sai ta kirata tayi mata sannu da jiki,tun abun yana sata jin kunya da nauyi harta fara sabawa,sukayi sallama da ita dai dai sanda adam ke fitowa daga kitchen,hannuwansa duka biyun riqe da mug dake dan fitar da tururi,qamshin kayan qamshi na tashi a ciki. Tun kafin ya qaraso ta miqe ta zauna sosai,shima ita yake kallo fuskarsa tana fitar da murmushi,ya soma takowa a hankali saita maqale kafada a shagwabe "Jan rai ko?" "Yes" ya amsa mata kai tsaye yana dariya qasa qasa. Kunnuwanta ta kama tana dariya kadan kadan "Na tuba,don Allah a bani nasha" idanu yadan zubata,yadda tayin tayi masifar burgeshi,kyanta kuma ya sake fita muraran,sai yaji jikinsa yadan saki amma kuma ta wani sashen wata zuciyar ta qara masa qaimi tare da karsashi,ya qarasa gabanta yadan russuna ya miqa mata cup din "Thanks dear" ta furta da sassanyar muryarta bayan ta saka dukka hannuwanta guda biyun ta karbi mug din cikin zallar kwadayin shan tea din,ta sanya bakinta ta kurba,saita lumshe ido tana sakin murmushi saboda dadin da ya ratsa ta sosai "Na yarda yau kadai.....ka fini iya hada black tea" murmushi ya sakar mata ba tare da yace komai ba,ba kuma tare da ya dauke kallonsa daga kan fuskarta ba,ta sake kai cup din bakinta ta sake sipping,dai dai lokacin da qaramar wayarsa dake kan wani dan teburin gilashi tare da babbar wayarsa dake charge ta dauki qara,ya qarasa a hankali,ya zareta daga charging ya karata a kunnensa idanunsa har yanzu akan fuskar saahar "Yanzu?....kamar dai gobe...... alright on my way" ya fada a hankali,saiya cire wayar daga kunnensa ya tako inda saahar take. Rusunawa yayi yayi kissing goshinta "Ayimin afwa baby,fita ce ta kamani yanzu,just one hour zanyi zuwan da dawowar...... I hope ba damuwa?" Kai ta jinjina masa tana lumshe kyawawan fararen idanunta "Babu dear" ciki ya wuce,ba jimawa ya fito,ya canza kaya zuwa qananun kaya,sai zabga qamshi yakeyi,ya mata kyau sosai,ya sunkuya ya sake kissing dinta,har ya wuce ta kira sunansa "Kayi kyau da yawa,Allah yasa ba zance zaka je ba" ta fada tana langabar da kai. Dariya sosai ya saki,sai ya dawo ya tsugunna a gabanta "Bayan ke babu wata,idan akwai ma Allah yasa ta makance ta gurgunce koma ta mutu....."baki ta kama tana dariya "Nidai ba ruwa na,irin wannan mummunan fata haka" "Eh kuma har zuciyata na fada ba,bazan wuce hour dayan ba zan dawo in sha Allah" ya fada yana miqewa da dan hanzari sanda wayarsa ta qara yin qara alamun ana sake kiransa. Hakanan ta samu kanta da binsa da kallo har ya fice. A nan falon taci gaba da zama tana kallon wani film da mbc2 suke haskawa,film ne daya shafi soldiers battle,tana son irin films din sosai. Kamar daga sama taji qarar waya,a mamakance ta waiwaya tana duban daga inda sound din ke fita. Wayar adam ce a wajen,tadan zubawa wayar ido tana mamakin yadda akayi yau ya manta wayarsa,shi da kwana biyun nan baya sake da waya,ko yaushe tana hannunsa,bini bini ya dauka ya duba,har wani sabon suna ta saka masa saboda maitar riqe waya daya koya,ko cikin dare idan ta farka da yake a kwanakin nan bata fiya kwana da qoshin lafiya ba sai ta ganshi riqe da waya,tun tana daukan abun da wasa har taga ya zama gaske,tayi masa complain sai yace akwai wata sabuwar harka ne da yakeson ya gwada shiga,so ana wayar masa dakai ne yadda business din yake,wanda kuma yake masa bayanin ba qasar nan yake ba,yana china, akwai tazarar 7hrs tsakaninmu,darensu shine ranarmu,lokacin shi kuma yana office bazaiyu ya maida hankali ba akan waya ya ajiye aiki,ranarsu kuma shine darenmu,a sannan shi yana da chance nayin chart,shi yasa yake tashi a daren. Ta gamsu,saboda ya yarda da adam din,bata taba kamashi da wani laifi da zai sanya zuciyarta tayi ɗar ko rawa a kansa ba. Kira bayan kira haka ya dinga shigowa,hakanan taji qarar wayar ta dameta,saita yanke shawarar sanyata a silent,don ita din ba gwanar daga masa waya bace,koda za'a kira wayarsa sau dubu bazata waiwaya ta kalleta ba,ada har qorafin hakan yake mata "Idan kirane mai muhimmanci ko kuma samuwa ce kinga shikenan ta wucemu" dariya kawai takeyi,saboda bata jin zata iya,tana da dabi'a na tsame kai daga abinda ba huruminta bane bai kuma shafeta ba. Da sauri ta koma ta zauna sanda ta miqe da nufin cimma inda wayar take saboda wani hadadden ciwon mara na tashin hankali da taji ya soketa,ta runtse idanunta ta kuma dafe mararta da kyau tana kiran sunan Allah tana jujjuya kanta saboda azaba. Akalla ta kusa kwashe minti biyar a haka tana juya kanta hagu da dama,gefe guda kuma qarar wayar naci gaba da cika mata kunnuwa. Ta bude idanunta a hankali bayan ciwon ya lafa tana share gumin daya tsatstsafo mata a goshi,qafafunta babu cikakken qwari ta miqe ta nufi wayar. Tana isa wayar ta danyi blinking light alamun shigowar saqo,ba inda idanunta suka sauka sai kan fuskar wayar. Da sauri ta zare idanunta daga fuskar wayar tana lumshe su,gabanta na wani irin dokawa labbanta na furta "Ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagis" tana fatan ta bude idanunta taga ba abinda suka gane mata bane da farko. Saidai a wannan karon data sake bude idanun nata abinda ta gani ya zarta wanda ta gani da farko,dukkan jikinta ya dauki rawa,taji a sannan bata da sauran zabi da ya wuce ta dauki wayar. Tana daukan wayar qafafunta suka gaza daukarta,dole ta zame ta koma da baya ta zauna saman kujera, hannuwanta kamar ba zasu iya riqe wayar da kyau ba,ta fara qoqarin gwada password din dake kan wayar. Duk password din da ta saka sai yace mata wrong,daga qarshe ta gwada saka qarshen number wayarsa,a take ta bude,saqon da bai gama fitowa ba ya bayyana muraran. K'azaman kalmomi masu munin gani bare kuma kunnuwa su iya jumurin sauraronsu,wani gumi mai zafi ya shiga tsatstsafo mata ta kowacce kafar gashi dake jikinta,zuciyarta ta ninka bugunta kamar zatayi tsalle ta fito daga qirjinta,kanta yayi wata irin sarawa ta fara gani dishi dishi sanda ta fara bin charts din dake inbox din da number wayar da babu suna a kanta. Wasu irin qazaman saqonni da ko ita da take halalin adam bata tunanin sun taba musayar irinsu a tsakaninsu,hotuna na kowanne sashe na jikin yarinyar,harda muhallin da ko mahaifiyar yarinyar tana tunanin zaiyi wuya ta sake katarin ganinsa tun bayan da shari'a ta hau kanta. Ganin abun take kamar al'mara,ganin abun takeyi kamar ba adam dinta bane,kamar ma ba wayarsa bace,ba abinda ke kaikawo cikin kwanya da zuciyarta da sunan adam din da kuma fuskarsa. Video na qarshe da idanunta suka gaza kalla wayar ta sulale a hannunta ta fadi tare da wani hadadden ciwon mara da bata taba jin makamancinsa ba,sai kawai ta cure a wajen tana jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta. Wannan yayi dai dai da bude qofar falon da adam din yayi cikin gaggawa,har yayi nisa ya tuna yabar wayarsa,duk da yasan baida matsala,kuma bashi da haufi matarsa bata taba wayarsa,amma haka kawai yau din yaji ya kasa samun nutsuwa,yaji bashi da gamsuwar tafiya,dole ya juyo da kan motarsa ya dawo ya dauki wayar sannan ya koma. Sam bai lura da inda ya aje wayar ba,idanunsa akan saahar dake cure guri daya kamar alkaki suka fara sauka. Da hanzari ya qaraso yana kiran sunanta,duk da azabar ciwon da takeji a mararta amma hakan bai hanata daga kai ta watsa masa wani kallo da jajayen idanunta ba. Sosai yasha jinin jikinsa amma zuciyarsa na gaya masa komai normal ne,ya miqa hannu gareta,ta tattara dukka ragowar qarfinta ta miqe tana jin mararta kamar zata rabe biyu "Kada ka yarda ka tabani,karka qaraso inda nake......" Bata kai ga qarasawa ba numfashinta ya soma sarqewa,tana jin wani abu me dumi ya ratso ta jikinta ya soma bin qafafunta yana gangarowa,duk da yanayin gushewar hankali da take kan gabar yi,amma hakan bai hanata qoqarin ganin abinda ke faruwa da ita ba,idanunsu shi da ita suka sauka lokaci daya akan jinin dake malala saman tiles din falon,bai jira cewarta ba ya qarasa gareta da hanzari yana riqeta,zuwa lokacin itama tuni ta qarasa ficewa daga hayyacinta,saboda qarin tashin hankalin fitar jinin da ta gani daga jikinta.[8/29, 2:05 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 41 *******Daga lokacin data fahimci cewa ta farka,ta dawo cikin duniyar da batayi tsammanin dawowarta ciki ba,sai ta fara qoqarin bude idanunta don ta tabbatar da inda take din. A lokacin da kwanyarta ta fara yi mata bitar al'amari na qarshe daya faru da ita saita rasa dukka qwarin gwiwa karsashi da kuma sha'awar bude idanun nata,ta sake runtse idanun nata cikin jin zafi,wani abu me tsini na sukar qirjinta kamar an fiddo zuciyarta an shanyata tsakiyar qwalleliyar rana. Hannunta data daga a hankali takai saman cikinta ta shafa bayan ta tuna yadda taga jini yana bin qafafunta a kallo na qarshe data yiwa jikinta. "Saahar,kin farka ne,sannu" muryar anty labiba matar yaa saif dake zaune a gabanta ya ratsa kunnuwanta,bayan zuwa yin salla da maama ita da afifa suka fita yi. "Sannu saahar" anty labiba ta fada tana riqe hannunta dake saman cikin "Ki daina motsa hannun, cannula din dake hannunki zata goce" ta fada cikin matsanancin jin tausayinta,daga yadda taga tana shafa cikin lallai shine abu na farko daya fara zuwa mata kenan a rai bayan ta farfado din,wanda tuni ya fice daga jikinta ta cikin jinin data dinga fitarwa me yawan gaske. Tare maama suka shigo ita da afifa,dukkansu rige rigen isowa gareta sukeyi "Menene abun kukan kuma?,Allahn daya baki shi zai sake baki wani" abinda maama ta fada kenan cikin muryar lallashi,a nata zaton saahar din ta fuskanci babu cikin a jikinta. A mugun karye ta daga kai ta kalli maaman,xancan yayi mugun dukanta,wasu tawagar hawayen masu zafi suka kunno kai,saita maida idanunta kawai ta lumshe,abinda ya bawa hawayen damar saukowa da kyau. Tsahon zaman da sukayi tare da ita suna lallashinta idanunta na a rufe ba tare data iya budesu ba,taji ciwo sosai na rasa gudan jininta da tayi,amma a yanzun hankalinta yafi karkata ga mummunan ganin data yi a wayar adam din. Ciki tasan ubangijin da ya bata shi zai sake bata wani,ko a kusa ko a nesa kamar yadda ya kawo mata wannan,to amma kuma wannan baqon al'amari daya shigo rayuwar adam fa?,wanda kai tsaye zata iya kiransa da neman mace koda bata ce neman mata kai tsaye ba,iya maganganunsu kawai ya gama gaya mata adam ya jima da yarinyar,sunyi mugun sabo,kuma sun saba kasancewa da juna da irin mu'amalar dake iya wakana tsakanin ma'aurata "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta har ta fito fili ba tare data ankara ba,sai sautin muryar maama da tace "Yauwa,ita zakiyita maimaitawa" sake motsa bakinta tayi a karo na biyu tana sake maimaita kalmar,hawayen na sake bin kuncinta. A matuqar sanyaye afifa ke sanya tissue tana dauke mata hawayen,saahar dinta jaruma ce da take da wani irin juriya dakiya da kuma cinye abu,irin tashin hankalin da take gani dimuwa da halin qunci sai take ganin kamar ya zarta yadda ya kamata ace an gani a fuskar macen data jima bata samu haihuwa ba ta hadu da miscarriage,saidai bata ga wani abu guda daya da zai dasa mata kowanne irin zargi a zuciyarta ba bare ta sanya ayar tambaya. Dai dai lokacin likitan yayi knocking qofar ya kuma tura ya shigo shida wata nurse dake riqe da file na saahar din "Yauwa ta farka?" "Ta farka dr" anty labiba ta amsa masa "Ma sha Allah" ya fada yana tsaiwa daga gefan saahar din "Sannu ko?" Ya sake fada yana duban fuskarta,sai a sannan ta bude idanunta a hankali da suka tasa saboda hawayen daketa fita daga cikinsu akai akai "Ya da kuka kuma madam?,sorry for the lost.....kiyi addu'a,next year kamar war haka sai kiganki saman gadon nan rungume da babynki alive and healthier" idanunta ta mayar kawai ta lumshe,abinda takeji cikin zuciya da qirjinta ta tabbatar babu me iya fahimta,da rufaffun idanuwan nata ta amsawa likita dukka tambayoyin sa,sai ya rufe file din nata yadan dubi afifa "Idan me gidanta ya shigo a turomin shi,inason magana dashi kafin na fita duty" "Okay,in sha Allah" ta amsawa likitan bayan ta daga kanta daga wayar da take dannawa, zuciyarta duka babu dadi,duk sanda daya daga cikinsu ya shiga damuwa ko tashin hankali,kusan su biyu suke raba wannan damuwar da dukka sakamakon da zai biyo baya. Yanayin yadda taga kukanta yana tabasu tare da sake sanyasu damuwa ya saka dole ta tattara abinta ta cinye ta hadiye tana kiran sunayen Allah can qasan ranta,don ita kadai tasan qunci da bala'in da zuciyarta take ciki,dukkansu sun sanyata a gaba kowanne tambayarta yake me takeso?,me yake damunta?,bisa taimakon afifa da anty labiba ta shiga bandaki ta gyara jikinta tayi wanka,ta fito afifa ta shiryata sannan ta zauna yaa zaid yana ajjiye mata plate din abinci a gefanta "Banason naga komai a cikinsa" wani marayan busashen murmushi ta saki,ta karyar dakai zuciyarta na karyewa,bata jin a yau maqogoranta zaiyi wani amfani,don bata tsammanin akwai wani abu me tauri kamar abinci da zai iya wucewa ta gurin saboda tsabar quntacewa da gurin yayi. Ganin da gaske ba zata iya cin abincin ba dole suka haqura,afifa ta hada mata kakkauran tea,ita da yaa zaid suka sanyata a gaba,aka samu tasha rabin cup,ta buqaci zata kwanta,shuru take da buqata,kadaici takeson samu ko zatayi wani tunani me amfani kan bala'in dake tunkaro rayuwar aurenta koma kai tsaye tace ya tunkarota,tashin hankali da musibar da ko wanne lokaci hankalinta ke tashi, tsigar jikinta ke zubawa idan taga wata mace cikin irinsa,yau gashi AKAN KANTA.....tamkar almara......tamkar cikin tarikicen tarkacen mafarkai,saidai kash......wannan din a zahiri ne,gaskiya ne,ba mafarki hikaya ko tatsuniya ko almara bace. Dukkaninsu sun dauka bacci ne ya sake dauketa,don haka yaa saif da yaa muhyi suka dauki iyalansu suka wuce gida,ya zaid shima ya wuce bayan maama ta sanyashi ya dauki masu aikin gidan biyu da suke tare anan tace su tsaya su karbo abincin dare,hamisu driver ya dawo dasu zuwa magrib. Shuru dakin yayi,daga afifa dake faman research a wani website sai maama dake jan carbi counter,sallamar adam dake gaba momee na biye dashi shi ya ratsa shurun da dakin yayi. Har tsakiyar kanta taji saukar muryar adam din,bata motsa daga yadda take ba har suka qarasa shigowa,tana jin sanda maama ke gaisawa da momee cikin surukuta tare da bata kujerar zama,yayin da adam ya matso dab da gadonta,ya miqa hannunsa a hankali ya sanya shi cikin nata yana kallon kyakkyawar fuskarta data fada tayi wani fayau da ita. Ji tayi kamar ya manna mata wuta,da da hali abinda tafiso a yanzun shine ta zare hannunta daga cikin nasa,to amma bata son tayi wani abu da zai fuskanci idanunta biyu,don bata shirya kallon fuskarsa ba a yanzu. Kamar afifa ta shiga zuciyarta sai kuwa ta isarwa da adam din saqon likita,ya zame hannunsa ya juya ya fita zuwa office din likitan. Ya sameshi yana shirin fita daga duty,to amma shigowar adam din ya sanyashi tsayawa da hada takardunsa da yakeyi ya masa izinin zama,ya zauna kujerar da take fuskantar dr,ya bashi hannu sukayi musabaha. Gyaran murya kadan yayi sannan yace "Kaine me gidan saahar girema ko?" Kai ya jinjina yana dubansa "Ma sha Allah,kasan cewa zubewar cikinta nada alaqa da shan tablet na zubda ciki?" Sosai fuskar adam din ta nuna zallar mamaki da alhini "Tablet kuma dr?,haka kuka gani?" Kai ya jinjina masa cikin yanayi na tabbatarwa "Yes,and after that ma.....mahaifarta ta dan samu rauni gaskiya sanadiyyar injection na planning da kuma wannan tablet din masu qarfi da tasha" "Nasan da zancan injection,infact ma da yardarta aka fara" "But haihuwarta nawa?" Likitan ya jefa masa tambayar yana kallonsa cikin mamaki "Ko daya,duka duka ba bamu cika two years da aure ba until now" mamaki qarara ya bayyana kan fuskar likitan "Amma....sorry mr adam,waye ya baku wannan shawarar?,bakusan allurar planning koda ka haihu bata masu haihuwa daya ko biyu bane?" Iska adam ya furzar daga bakinsa,dr yadan lumshe ido sannan yace "Am sorry kada na zaqe da yawa,duk da cikin aikinmu ne mu bada shawara ga hanyar da zata bulle ma mara lafiyarmu don samun ingantacciyar lafiya kuma cikakkiya......a likitance kada ta sake ta'ammali da wani qwaya ko allura na zubda ciki ko hana haihuwa,don a yanzu haka mahaifarta ta samu rauni sosai,koda a gaba fa sake samun ciki sai an bashi special care matuqar inason juna biyunta yayi surviving har zuwa haihuwa" shuru adam yayi yana gyada kai,kafin ya sauke ajiyar zuciya yana kallon likitan "Akwai wanda yasan dukka wadan nan bayanan?" Kansa ya girgixa cikin halin ko in kula "Babu,but sister dinta taso taji wani abu daga gareni,so amma kuma tunda kaine ka kawota kuma kaine mijinta, that's why bance komai ba,coz kaine kafi cancanta mu tattauna maganar da kai" "Okay dr,na gode,inason please kada wanda yasan da wannan,zanyi qoqari in sha Allah na kiyaye lafiyarta,zan kuma bincika abinda ya kawo wadan nan matsalolin" "Hakan yayi kyau" daga haka sukayi sallama da likitan ya baro office din. Tsahon zaman da sukayi a dakin shida momee din taqi koda bude idanunta bare su gaisa,har suka gama zamansu sukayi sallama suka wuce gida ita da adam din. Wata irin jinya saahar takeyi me wahala tare da qoqarin danne abinda ke cikin zuciyarta,jinyar ta zame mata guda biyu,ta zuciya data gangar jikinta,tayi masifar kewa tare da rashin jin dadin rasa abinda ke cikinta,saboda yadda ta qwallafa rai a kansa,ta kuma aza dukka burinta a kansa,sai gashi rana daya sanadin kuskuren adam tazo ta rasashi,abu na biyu mummunan ganin da tayi a wayar adam din,wanda ya zama silar tarwatsa wani sashe mai girma na farinciki da walwalar rayuwarta,banda Allah yasa kota ina tana da matallafa,da family me qarfi dake tattalin farincikinta. Da farko baccin qarya ya tsira duk sanda adam yazo har kuwa ya tafi koda awa nawa zaiyi,daga bisani ta fahimci abun yayi yawa,kuma har kamar an fara fahimtar ta,wannan yasa ta canza salo,zaizo kuma har ya tafi bata barin kowacce kalma ta hadata dashi,koda kuwa kallon fuskarsa batayi,rabon data dora qwayar idanunta akan fuskarsa tun randa fa kalli fuskar wayarta,duk sanda tayi yunqurin kallon nasa saita hangeshi cikin qazamin hoton da ya dauka shida yarinyar da bata gama tantance kamanninta ba cikin wani qazantaccen yanayi da ko a mafarki bata taba tunanin ganin hakan akan adam ba,dukka wani yarda da aminci daya samu daga zuciyarta sai taji a hankali a hankali yana sulalewa. Yanayin da yaga saahar din ta koma yayi matuqar girgiza adam din hadi da sanyashi cikin matuqar tashin hankali,yanason ko yaya ne ta bashi dama da zasuyi magana amma ta hana hakan faruwa,har zuwa randa aka basu sallama. Kai tsaye ta wuce motar yaa Saifullahi,yaa saif din ya ranqwafo yana kallonta "Ki koma matar mijinki mana,ina cewa ke ya budewa motar yana jiranki ki shiga?". Kanta ta langabe,idanunta nason kawo ruwa amma kuma tana hana hakan faruwa,su dukka basu sani ba,sam a yanzun bata da sha'awar komawarta gidan adam,to amma kuma idan tace ma ba zata koma din ba tasan bata isa ba,dole saita bada gamsashshiyar hujjar da zata zame mata garkuwa,ta kuma zama silar da zasu karbi uzurinta suyi mata yadda takeso,su barta a gida ta gama warkewa,ta kuma yi nazari a tsanake kan makomar zamanta da adam,ta gano daga ina kuskuren yake?,sakacinta ne ko nasa?,amma hakan dukka ba zata samu ba,don duk da yadda suke gatantata,suke kuma shagwabata ba shakka basa lamuntar wasa da harkar aure,ba kanta farau ba,ta gani daga kan yayarta wadda ya zaid yake bi Anty ANUUM. Tana fita a motar yaa Saifullahi adam ya nufo gurin da sassarfa,yamatso da nufin tallafa mata ta isa motar duk da tana takawa sosai amma saita zame,ta matsa gefe kadan dashi tayi gaba ta barshi. Bai sare ba ya bita,ya kuma cimmata tana kici kicin bude motar,sai ya bude mata front seat,sabanin ita dake qoqarin bude back seat. Karon farko ta daga manyan fararen idanunta ta zube masa su ba tare da tace komai ba. Wani abu yaji ya dakeshi sosai,kwarjini tayi masa sosai,haryaji yana shirin narkewa a wajen,saiya kauda nasa idanun,bai sake dubanta ba har zuwa sanda tashige ya maida qofar ya rufe ya zagaya ya tashi motar suka fice daga harabar asibitin. Shuru ne kawai ya baqunci motar,kaiba zaka ce akwai mai rai a cikinta ba,karo nafarko tun aurensu da irin hakan ta faru. Saahar din wata irin macace ta daban da take da matuqar qoqari wajen iya kula da miji,taka tsantsan tare da qoqarin barin dukkan wani abu da adam bayaso,bata daukan fushi dashi koda ya bata mata,tafi gane ta sanar masa su tattauna su yiwa kansu sulhu,a tsahon zamansu na wannan shekarun babu wanda ya taba jin kansu,sun zama wadansu irin ababen koyi da kwatance ga kowa. [8/29, 2:05 PM] KYAUTA: *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 42 "Saahar" adam din ya kira sunanta kai tsaye da wata irin murya dake shaking,sarai ta jishi amma saita lumshe idanu kawai batare data amsa ba. Sake kiran sunanta yayi amma kamar dazun,ya fahimci ba zata amsashi ba koda zai kwana yana kiran sunanta,a duk sanda take cikin maquracin bacin rai, dabi'ar miskilanci itace abokiyarta a sannan. Samun tabbacin ba zata amsa masa ba sai ya fada jero mata kalamai na kare kai da kaifin harshe da kuma zaqin iya tsara kalamai da Allah ya bashi. Wata irin baiwa ce dashi kansa yake alfahari da ita,baiwar da yasan cewa ta siyo masa abubuwa masu yawa masu tsada da daraja.....cikinsu kuwa harda ita saahar din. Dukka wata kalma da yasan zata iya tasiri a zuciyar saahar din a lokacin ya arota yayi amfani da ita,to amma ko gezau,kamar ma bata wajen,abinda yayi matuqar karyashi,don bata taba gwada masa irin wannan dabi'ar ba. Har suka isa gida,bata tada kai koda sau daya ta kalleshi ba,ta sani muddin ma tace zata kalleshi to ba abinda zata hango tattare da adam din face baqinsa da zuciya da idanuwanta zasu dinga gani,hakanan matuqar tace zata bude baki tayi wata magana.....to lallai kalmar da dukka zata fita a bakinta muninta zaiyi yawan da zata iya haifar da faruwar komai. Yana tsaida motar ta budeta ta fice a gaggauce,cikin zafin nama shima ya bude bangarensa ya take mata baya,yakuma yi nasarar cimmata a tsakiyar falon gidan,ya sha gabanta yana kallon fusatattun idanuwanta da suka tashi daga ainihin launinsu na fari qal da baqi sidik din qwayar idanuwa,zuwa pink da surkin red. Wani mugun kwarjini tayi masa da ya qarasa karyashi gaba daya,sai yayi qasa da qwayar idanuwansa yana cewa "Dukkan laifin da kike tuhumata dashi saahar na yarda na aikata.....amma ban aikata babban laifin da zuciyarki ke miki hasashen na aikata din ba,ban taba yi ba na rantse miki da girman Allah" "Ka bani guri na wuce adam!" Furucin ya fita daga bakinta da wani irin madaukakin sauti daya canza tone na muryarta,karo nafarko data taba tanka masa tun daga waccar ranar da abun ya faru "Bazan matsa ba saahar,kiyimin dukka kalar hukuncin da kikeso muddin zaki tsaya muyi magana koda ba zaki fahimceni ba". Juyawa tayi kawai ta doshi hanyar fita ba tare data sake koda motsa bakinta da nufin tankawa maganarsa ba. Yayi wata muguwar zabura yabi bayanta,don ya tabbatar tana nufin ficewa daga gidansa,wanda faruwar hakan yana nufin faruwar komai da komai,yana nufin tonuwar asirinsa,yana kuma nufin subucewarsa daga kafatanin rayuwarsa,abinda a yanzun bai shirya masa ba. Hannu yasa ya maida qofar parlor din ya rufe,ya kuma murza key ya zare key din ya jefa a aljihun rigarsa,sai yasa dukka hannuwansa ya hade a nasa,ya kuma sulale a wajen ya tsugunna bisa gwiwoyinsa,sannan ya buda tafukan hannayen nata ya saka fuskarsa a ciki ya rufe ruf tare da kubcewar kuka. Duk da a yanzun batajin adam din bisa kowanne matsayi a zuciyarta,bata jinsa kwata kwata daga guraben da a baya yakai,amma kukansa yazo mata a bazata,ya kuma bata mamaki,kuka koda ga qaramin yaro abune me cin rai da zuciya gaba daya,bare ga babban mutum da yakai munzalin magidanci kamar adam,saidai wannan ko daya bai kashe wutar dake ruruwa cikin zuciyarta ba. "Na roqeki kiyimin alfarma ki yafemin,kiyi haquri kiyimin dukka kalar hukuncin da kikaga dama,amma karki nesanceni,kada ki gujemin,ina mai hadaki da girman Allah......ki yafemin,na miki alqawari ba zaki sake samuna da wani laifi kwatankwacin wannan ba,sharrin zuciya da na shaidan ne,duk sanda kika sake kamani da laifi mai shigen wanan bama wannan din ba,na amince na kuma lamunce miki kiyimin dukka irin hukuncin da kikaga dama" duk yadda taso ya sakar mata hannu ya barta da abinda takeji a zuciyarta amma yaqi bata wannan damar,yaci gaba da amfani da baiwar iya sarrafa kalamai da yake da ita,ya dinga zaftare tsananin fushi da bacin ran da suka kafa sansani mai girma da qarfi a zuciyarta,har sai da yayi nasarar ture kaso mai girma daga cikinsa "Ka sakarmin hannu.......har yanzu bansan makomar zamana ni dakai ba...." "Har sai yaushe saahar?,me kikeso nayi miki wanda zai wanke wannan mummunan laifin da na aikata?" "Sai nayi tunani" ta fada kanta tsaye. Da gaske tana buqatar nutsuwa,tana buqatar tayi tunani me kyau,tana buqatar su zauna ita dashi su tattauna,tana kuma da buqatar lalubar daga inda matsalar take. Lamarin babban abun tashin hankali ne daga gurin diya mace,ba kowa ke iya jurewa ta fuskanci irin wannan babban qalubalen ba. Ya qyaletan kamar yadda taso,ba kuma wai ya qyaleta bane dukka yadda ta buqata,yayi kane kane tsakanin dakinta da nasa,wunin ranar gaba daya bai zauna guri daya ba,dukka hidimar gidan ya dauka ya aza a wuyansa,dukka wani abu da saahar din keda buqata shi ya dinga yi mata,duk da bata buqaci komai daga wajensa ba,daga bisani da taga bashi da niyyar bata space kamar yadda ta buqata,sai ta murza key ta rufe dakin. Tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi,tayi addu'a da dukkan iyawarta da nau'ikan addu'o'in data sani,ta nema ubangiji ya shiga lamarinta ya kuma bata juriya,taji ta muzanta da yawa ta kuma qasqanta,ta kalli kanta a madubi har sau babu adadi,tanason zaqulo abinda ta rasa,tanason zaqulo inda ta gaza,tana kuma son gano wanne GURBI ne da bata cikewa adam ba har ya tsinciki kansa cikin irin wannan qazamin sahun?. Saidai a dukka hasashe da dogon nazarin da tayi,bata tsinkayi abu daya da ta kasa cikawa adam ba. Babu wanda yasan halin da take ciki,babu kuma wanda tayi niyyar gayawa koda afifa kuwa,tanaji har cikin zuciyarta ba zata iya tonawa adam asiri ba,sun fara hawa matakin fara samun zuri'a,ko taqi ko taso,a yau ko kuma gobe ana iya kiransa da uban 'ya'yanta,shike da matsala ita ke zaune dashi,su tattauna a tsakaninsu su kamo bakin zaren tare tana ganin shine hanyar da zasu samu mafita. Tun washegarin ranar data dawo momee ta bata aron rahina a cewarta har sai jikinta ya warware tunda ita din bata da ra'ayin me aiki,yarinyar itake komai na gidan tamkar saahar ba a kwance take ba,ita din bata iya hassala komai,daga kwanciya sai kwanciya,damuwa ta farmaketa ta cimmata a lokacin da bata taba hasashen wata matsala ko damuwa cikin rayuwarta ba,tana ganin komai nata ya cika cif cif,gibi guda daya daya ragema rayuwarta na rashin haihuwa shima ya cikashe!,ashe qalubalen yana gaba!. Sati guda bata ko yarda sun sake hada hanya da adam ba,har sai zuwa ranar data gamsu a karan kanta lokaci yayi daya kamata ta fuskanceshi da dukka tarin tambayoyi da tuhume tuhumenta. Ranar tun da safe bayan ya fita itama ta fito ta qwarara jikinta,rahina nata murnar ganin fitowar saahar din,kusan wunin ranar tare sukayi komai da ita,har zuwa magrib inda saahar ta wuce dakinta. Qarfe takwas da wani abu na dare tana gaban madubi tana daure dogon gashinta mai santsi da baya rabo da gyara adam ya turo qofar dakin ya shigo,idanu suka hada saita janye nata idanun ta maida kan mudubin,yayin da shi kuma ya kafeta da kallonsa cike da kewarta,jikinsa fes da alama tun daxun ya shigo,yayi wanka ya canza kayansa cikin wasu qananun kaya da suka amsheshi qwarai. Hannunsa ya cire daga aljihunsa,yaji bazai iya ci gaba da jurewa shariyarta ba,ya tako zuwa inda take,ya tsaya dab da bayanta yana kallon kyakkyawar fuskarta ta madubin,ta sake haske,fuskarta tayi fayau. Jikinta ta zame daga wajen,ya bita da kallo,ya motsa bakinsa zaiyi magana,ta rigashi ta hanyar masa nuni da wajen zama,sannan itama ta koma daga gefan gadonta ta zauna. Dukka idanunta ta zuba masa,wani bacin rai yana motsawa daga qasan zuciyarta zuwa saman fuskarta,idan tace ta taba jin tashin hankali mai gauraye da bacin rai irin wannan tayi qarya,tayi namijin qoqari qwarai,ta tattare dukkan abinda ke taso matan,ta jefa masa tambayar data dade tana son amayar da ita,ko zata samu sauqin radadin dake yankar naman zuciyarta kowanne dare zuwa rana "Yaushe ka fara neman mata adam?" A hargitse ya kalleta,don tambayar ta dakeshi qwarai,yanayin fuskarsa ta sauya yayi wani mugun laushi "Idan kikace neman mata.....kina nufin zina fa kenan?" Kai ta jinjina kai masa "Qwarai kuwa,domin abinda idanuwa suka karanto kenan,qwaqwalwata kuma ta fahimta" "Subhanallah,wa'iyazubillah" ya fada fuskarsa na nuna girman yadda furucin yayi masa radadi a zuciya,tsahon wasu sakanni sannan ya iya daga kai ya dubeta "Ba neman mata nakeyi ba,duk da tarayyar da mukeyi akwai sabon Allah a ciki,tunda zataga tsiraici na zanga nata..... Ta rudeni watanni uku baya da suka shude,banda ita na rantse da Allah ban taba neman kowa ba,ban taba tarayya da kowacce mace ba,kuma tun daga ranar ban sake kulata ba,ban sake bi ta kanta ba" "Ta ina na gaza maka adam?,ko akwai wani waje da na gaza maka daka rufeni ka kasa gayamin?" Kai ya girgiza da sauri "Ke din ta kowacce fuska kin kerewa kowacce mace,idan nace kowacce mace.....ina nufin nau'in kowacce mace daga kowanne jinsi da yare na duniya ni a wajena" wayarsa dake aljihunsa ya ciro,ya kuma fidda layukansa gaba daya ya lanqwashesu suka karye,sannan ya qarasa gabanta ya ajjiye mata wayar "Idan kinso daga yau ni adam na ajjiye wayatama gaba daya sai sanda kika lamunce min,kiyi haquri ki yafemin,kici gaba da zama dani,sannan ki lullube sirrina,na miki alqawari saahar,muddin na sauya ko naci amana,na yarda amanar Allah ta cini nima" kalmarsa ta qarshe tayi masifar yi mata nauyin da har sai data tilasta mata rufe idanuwanta,amanar Allah ta cishi?,lallai da gaske yake mata,ba shakka ya canza ya kuma shiryu da gasken gaske. Ta dauki wannan kalmar ta azata bisa babban ma'auni,ta bata matsayi me girma,irin matsayin daya zarta ta qiyasceshi,a nata dabi'ar da kuma kyakkyawar tarbiyyar data samu,girman ubangiji ya wuce wani dan adam yayi wasa dashi,ko ya fake a bayansa ya aiwatar da dukka abinda son zuciya da qaawar duniya zai sawwarawa mutum. Ta dauki wannan kalmar a matsayin madogara,ta fifitata ta karbi nadamar adam,cikin sati guda ta fara qoqarin daidaita kanta tare da daidaita dukka lamuranta,ta dinga kokawa da kanta da yaqi da kanta tana son komawa ainihin saahar,tare da qoqarin maida komai a tsakaninsu ya koma bisa mizanin daidaito. Cikin lokaci qalilan ya sake canza mata,ya zame mata tamkar bawa dake qarqashin ikon uban gidansa,sai abinda tace shi zai aiwatar,sai abinda ta zaba,ya ninka dukka kyautatawa da kuma soyayyar da yake nuna mata,kulawa da tattali marasa misali,cikin wata guda kacal ya mantar da ita komai,ya kuma sake amintar da ita,ya nisanci dukka abinda zai kawo zargi da kokwanto a tsakaninsu shi da ita. Rayuwa taci gaba da tafiya sannu a hankali,wannan amincin.....wannan yardar.....wannan hadakar da wannan gamayyar dake a tsakaninsu tana ci gaba da wanzuwa. *_WASA FARIN GIRKI_*😭 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 43 *_WASA FARIN GIRKI_* Totally adam ya sauya mata,ya sake zama wani me mugun sanyi tare da takatsantsan da damuwarta da duk wani buqata tata,a tsakiyar wannnan,watanni biyar da rasa wancan cikin wani cikin ya sake samuwa. A wannan karonma itama hankalinta baikai kai ba,tana dai yawan jin jikinta babu dadi sam,adam ne ya fara ganowa,ya kuma kaita asibiti da kansa don tabbatarwa. Irin girman farincikin data gani a idanu da fuskarsa ya ninka nata ya shanye,harda qwallarsa,ya rasa inda zai sakata. Lokacin da take gayawa afifa cikin murnar yadda adam ya karbi cikin,haka kawai jikinta ya sanyaya,amma ta hadiye abunta,cikin farinciki ta taya sãahar din murna. Komai adam ya hanata yi a gidan,shike komai,yayi hidimarta yayi tasa,ya kuma shirya ya fita aiki,bashi ma da wani cikakken lokacin kansa,ya dawo dakinta gaba daya ya tare,yabar nasa bedroom din,sai kuma ya fara bata tausayi,tayi qoqarin komawa dai dai itama,tare da sake saisaita tsarin gidanta,saidai duk da haka bai fasa yi mata hidima ba. *******K'arfe sha daya na safe ta fito daga wanka,daure da babban towel daya rufe jikinta sosai,tana a tsaye gaban madubi tana ware gashinta daya jiqe don busar dashi da hand drayer,tana ware gashin tana kallon fuskarta,tayi fresh sosai ta kuma fara dan cikowa. Cikinta ya shiga wata na uku har ya fara nisa,wannan ya sanya ta fara samun sauqin laulaye laulayen da take fama dashi,taji jiki iya jin jiki,ta gasu,don kusan yafi cikinta na baya bata wahala. A nutse aka turo qofar dakin nata,ta maida dubanta ga qofar,adam ne ke shigowa da innocent face din nan nashi,yana sanye da shirt turtle neck me dogon hannu da trouser dinta data zauna masa a jiki sosai tayi masa kyau,idanunsa akan sãahar,yana jifanta da wani iri kallo dake cike da tarin soyayya,kamar zai cinyeta. Har ya iso ya ajjiye madaidaicin tray din hannunsa idanunsa na a kanta,sai daya daidaita zaman tray din saman madubin sannan ya sanya hannuwansa ya jawota jikinsa yana dora kansa a gefan kafadarta "Qara kyau kike kullum my heart" dan qaramin murmushi ta saki "Shine kaketa wani kallo na kamar zaka cinyeni?" Ta fada shagwabe sosai,sai ya saki dariya me qaramin sauti "Bakisan matsayinki bane a zuciyata,da ba zakiyi mamakin irin kallon da nake miki ba" shuru tayi tana jin saukar numfashinsa a wuyanta,kowacce rana sake jinjina soyayyarta dake ninkuwa a zuciyar adam takeyi,a duk sanda kuma ta tuna da incident dinsu na watannin baya sai taji tana sake gayawa kanta tabbas sharrin shaidanne da kowacce irin zuciya bata iya tsallake masa idan yazo da qaddara. Dan janye jikinta tayi daga gareshi jin shurun nasa yayi yawa,ta waiwayo tana duban fuskarsa,damuwar da take hanga tun jiya ta sake ganinta muraran kwance saman fuskarsa,duk sai taji babu dadi,don ta tabbatar inda shine da tuni ya sakata a gaba da tambaya,har sai yaji menene?,ya kuma tayata sun magance abun koda da shawara ne "Damuwa naketa gani fa a fuskarka" murmushi ya sake saki yana girgiza kai,tare da saka hannu ya maida gashinta dake son tsole mata ido baya "Ba wani damuwa fa,kawai sauyin yanayi ne" fuska tadan bata "Amma ko da ban cika mace ba,mata na rako duniya,almost three years amma ace na kasa gane damuwa a fuskar mijina?, c'mon,tell me kawai,ba'a boyewa abokin kuka mutuwa" ajiyar zuciya ya saki me nauyi dake alamta lallai akwai damuwar sosai a ransa,ya koma gefan gado ya zauna yana goye da hannayensa,idanunsan nan dake cike da wani irin kallo a kanta,sannan ya fara magana "Momee ce......" Sai yayi shuru yana duban wani gurin "Uhmmm,me tayi momee din?" Kansa ya girgixa sannan cikin damuwa yaci gaba da magana "Wai lallai saina canza mota motar da take hawa,jarinta kuma yayi qasa,saboda ta tana kudinta sosai wanna zuwan da tayi Ghana,tana buqatar wasu kudi ta dora jarinta" qaramin murmushi sãahar ta saki,duk da taji maganar wani iri,saboda motar momee din ba wani dadewa tayi ba,hasalima tata ce adam din yake hawa,momee ta nuna sha'awarta,sãahar din tace yabar mata,gif ne ya Saifullahi ya bata. Bataji komai ba,don iyakar kirki matar tana dashi,hakanan soyayyar da take nuna mata ko adam data haifa baya samun ire irenta ma,bata qaunar bacin ranta ko dis!. Uwa uba kuma ita din tana comparing momee da maama dinta,ta tabbatar yadda adam yake sonta yake kuma girmama iyayenta......ba shakka zai iya yiwa abba da maama komai muddin yana da dama "To meye abun damuwa a ciki dear?,uwa ce fa?,ko ranka tana ce kana so ba zaka iya cirewa ka bata ba?" Kai ya girgiza da sauri "No heart.....ba haka bane,kinsan a yanzu babu agenda na taba kudaden dake hannuna....infact ma ni banason taba abinda yake ba mallakina bane ni kadai" ido tadan fidda tana kallonsa,sai kuma ta bata fuska tayi kicin kicin "Kanason gayamin momee bata haifeni ba,kai kadaine danta" dariya sosai ya saki "Nidai bance ba,kawai dai banason taba kudin ya kawo delay wajen cikar burinmu,inason kafin babymu ya iso duniya,yazo ya samu mahaifinsa wanda yake tsaye saman qafafunsa,sai raɓi inuwa ko alfarmar kowa ba" ya qarashe maganar bayan ya iso gabanta,ya dora hannunsa plate tummy dinta da har yau yake mamaki da kuma tantamar tabbatuwar samuwarsa. K'awataccen murmushi ta saki,ta dora nata hannun saman nasa,wannan ya bashi damar dago fuskarta yana kalla "An soso miki inda yake miki qaiqayi ko?,na lura kafuwar kamfanin ma bata dameki ba kamar yadda kika damu da zuwan babyn nan" kai ta jinjina "Allah ya jarabceni da son yara,inajin ranar dana haihu bazan iya bacci ba,har ina rayawa a raina,wannan tsananin son yaran kada ya zama tawa jarrabawar kenan,na mutu ban haihu ba" "Komai lokaci ne,gashi yanzu yana hanya?" "In sha Allah" ta fada tana jin wani farinciki yana lullubeta,ta jarabtu da son wannan cikin fiye da cikinta na baya. Zame jikinta tayi daga nasa,ta matsa zuwa side bed drawer dinta,ta budeta,sannan ta jawo safe dinta,ta ciro wani bangul guda biyu me kyan gaske daketa daukar ido,ta qaraso wajen adam dake tsaye daga bayanta, hannayensa cikin aljihun wandonsa yana kallonta. Miqa masa tayi "Abun hannun nan yana da matuqar muhimmanci a wajena,amma duk muhimmancinsa baikai na miji na gari irinka ba,na amince ka siyar dashi,ka siyawa momee duk abinda takeso,idan da saura a zuba a kudaden da suka rage mana na gininmu,koda foundation a fara sakawa na ginin" baya yaja yana zare idanu "What?, a'ah,ba za'a yi haka dani ba,Allah ya sawwaqe"ya fada yana yarfar da hannu,fuska ta bata tana kallonsa,sai shima ya tsaya ya zuba mata ido yana kallon yadda rashin jin dadi ya ratsa har cikin zuicyarta "Ni ba kyauta na baka ba,ka rubuta idan komai na kamfani ya kammala zaka biyani" dariya ya saki sosai "Matata me wayo,to godiya nake" ya fada yasa hannu biyu ya karba yana juya abun hannun,wanda ya tabbatar idan aka kaishi kasuwa kudade ne masu nauyi za'a karba. Ya sani yayi kuma imani sãahar ta dabance ko cikin mata,tana cikin sahun mutanen da idan suka soka qaramin abu bai sanyawa su gujeka,zasu iya sadaukar maka da dukkan farincikinsu muddin zasu samu soyayya da kulawa daga gareka,hakanan idan suka qika,zaiyi wuya wani abu yasa su soka. Da hannunsa ya dinga bata breakfast din har taci ta qoshi,ya tattare plates din zai fita dasu yana cewa "Bari na watsa ruwa,inason zan dan fita,sai naga waya kamata ya siya banguls din" miqewa tayi a nutse tana daure lallausan gashinta da wani qaramin scarf kalar english wears din jikinta "Yaukam ko ladan hada maka ruwan wanka ka barni na samu please" ta fada a shagwabe,kai ya girgiza "Indai nine na yafe" tsaiwa tayi tana dubansa,kamar me tuna wani abu "Amma,yau kusan two weeks kana hanani shiga dakinka,why?" Ta fada tana bata fuska, murmushi ya sakar mata,ya kama kumatunta yaja "Banason kiyi dukkan wani aiki bare ki wahala,idan kika shiga da zummar hadamin ruwan wanka,zakice zakimin gyaran daki ne,don dakin yayi qazanta da yawa,abinda ni kuma bana so kenan" kanta ta kawar gefe cikin nuna tata rigimar "Wannan gatan yayi yawa,ba'a kaina aka fara samun ciki ba,gidanmu cike yake da 'yan aikin da idan na buqata za'a kawomin,amma banason,saboda me?,aure nazo bautar Allah,ba zaman jin dadi da baiwa zuciya da rayuka abinda sukeso ba,ina fatan samun dacewa" ta qarasa maganar tana zube idanunta a kansa. Kai ya jinjina,shi kansa shaida ne,gata kyau ko wani matsayi na rayuwa bai sanyata ta dakaki kanta a gidan aurenta ba "Shikenan,let's go" ya fadi yana bata hanya,saita miqe tana harararshi "Da ladan kakemin buqulu?" "Ban isa ba" ya fada yana daga hannu sama alamun surrender. Koda suka shiga dakin bataga wani datti me yawa da yake magana a kai ba,ta hada masa ruwan yayi wankan a gurguje ya fito ya shirya,tana zaune daga gefan gadonsa suna hira har ya kammala,sannan suka fito tare,sai taga yana saka key yana kulle dakin,abinda ya maidashi dabi'a kenan a kwanakin,to amma da yake tana da nata bedroom din,kuma ba wani abu take ajjiyewa cikin dakin ba,sai bata taba damuwa ba,yayi kissing nata lightly a forehead dinta sannan ya wuce. Ba abinda zatayi,yau ko aiki ba zata fita ba,don haka tayi zamanta a Parlor,ta kunna kallo,jita jifa tana taba chart a wayarta. Sallar azahar ce kadai ta tasheta,tayi sallar ta duba fridge ta dauko fresh samosa da adam din ya mata order ya cika mata fridge dashi wai saboda yunwar dare,ta soyata,ta hado da hollandia me sanyi ta dawo ta zauna. Tana tsaka daci kiran afifa ya shigo wayarta "Uwar biyu" ta fada cikin salon tsokana "Allah yasa,tabbas da kin samu kyautar kujerar umra daga adam" zuciyar afifa daga can ta tsinke,batasan wanne suna zata bawa adam ba,har yanzu zuciyarta bata taba nutsuwa da komai na adam ba,ta rasa me yasa?,duk da cewa ya bada dalilai masu yawa da yaci ace kowa ya gamsu ya kuma aminta dashi,amma ta nata bangaren hakan ya gaza samuwa "Allah yasa" ta amsawa sãahar din "Kudaden nan sunzo ko?" Kai ta girgiza tana sipping madarar "A'ah,anya?,banga alert ba" "Haba?,amma tun jiya da dare fa,kuma sunyi debiting dina,receipt din na manta banyi generating ba" "Karki damu,zan duba balance,nasan sunzo ma" "A'ah,duba dai yanzu ki gayamin,amana ce ya zaid ya bani kuma kafin na gaya masa na saka sai nayi confirming ya shiga Account dinki" qaramin murmushin dake qara mata kyau tayi "Bestie koni kika siyar kikaci kudin kinci halak" "Na sani,amma yanzun ki duba tukunna" ta fada tana katse kiran,ta ajiye wayar a gefe tana jiran kiran sãahar,akwai abinda takeson takai sãahar din gashi,addu'a kuma take takai gano. Tana murmushi ta soma checking balance dinsu ta USSD CODE,tayi na farko yayi cancelling,ta sake gwadawa har sau uku yana cancelling,tayi duk wami qoqari na checking din amma yaqi yiwuwa,abinka dame ciki,haka kawai abun ya zafafeta,sai ta soma trying number wani ma'aikacin banking da suke ajiyar. Sanda ta gama masa bayanin cewa yayi "It seems like anyi disconnecting duk wani details naki daga Account din,to amma kuma ina doubting,saboda indai za'a yi hakan saida saninki da yardarki,anyway,gobe zan shiga bankin,zan duba miki komai in sha Allah" godiya tayi masa ta sauke wayar,duk da cewa wani bangare na zuciyarta cike yake da mamaki,amma wani sashen kuma cikin tantama yake,kanta ya kulle dason gane gaskiya da kuma meye dai dai?,ganin zata batawa kanta lokaci saita ajiye komai,don bata da tabbacin gaskiyar ko rashinta akan duk abinda zuciyarta zata raya mata,taci gaba da cin samosa dinta. Takai plates din kitchen kenan ta fito taji ana knocking,ta fasa zaman da tayi niyya,ta isa qofar falon ta budeta. Mamaki ne sosai ya kamata ganin raihanatu,don tsahon aurensu da adam batajin yarinyar tazo gidan yakai sau uku,duk da yadda takeson yarinyar saboda hankali da nutsuwarta,da kuma yadda take girmamata. *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 44 Ta taba yiwa momee din complain akan hakan,tabe baki tayi "Na rabaki da wannan,wannan me baqin halin,sumumu kasau" murmushi ta danyi kadan,can qasan zuciyarta cike da mamaki,bata taba ganin wani abu na rashin kyautawa raihanatu tayi ba,duk tsahon zuwanta gidan kullum cikin hidima takewa momee,bata tana tsallake umarninta,tausayi da nutsuwarta yake qarawa sãahar qaunarta,wannan ya sanya koda kayan bayarwa zata fitar,raihanan take baiwa,ko yanzu kayan jikinta na sãahar dinne,don ba kasafai momee ke mata dinki ba,takance tana yi mata, yarinyar ce kamar ba mace ba,batason kwalliya bata sawa, sãahar dai bata taba ganinta cikin qazanta ba,ko yaushe fess take da tsaftatattun kaya. "Shigo ciki mana" sãahar ta fada ganin wani abu me kama da tsoro a fuskar raihana dake tsaye daga bakin qofa,hannunta dauke da ledar dake nuna aikenta momee tayi ta biyo nan,sau biyu tana waigawa tana kallon bayanta kafin ta fado falon. A qasa ta zauna, sãahar ta tasheta tace ta koma saman kujera "Ya gida yasu momee?" Ta fara tambayarta ganin har yanzu batace komai ba tana nufar qofar kitchen,hannunta taji an riqo,saita juyo,fuskarta ta sauka akan raihanatu. K'walla ta gani cike fal da idanun nata,yanayinta ya sake sauyawa qwarai,kowanne lokaci zata iya sakin kuka "Ki zauna anty don Allah,magana nakeson zamuyi,gida nakeson komawa da sauri,kada momee ta fahimci na biya wani gurin" kai ta jinjina,saita dawo da baya ta zauna dab da raihanatu ta zuba mata ido,jikinta yayi wani mugun sanyi da kuma mutuwa,wanda batasan dalilin hakan ba,sai taji gabanta yana faduwa kadan kadan lokacin da taga raihana ta sad da kanta qasa,qwalla tana diga. Tsahon zamanta da yarinyar bata taba zama irin haka da ita ba,zuciyarta ta shiga fargaba da taraddadi,kafin tace wani abu raihanatu cikin rawar murya ta fara magana "Kafin rasuwar mamana ta gayamin duniya a yanzu cike take da mutane azzalumai,marasa amana,marasa kuma saka alkhairi da alkhairi,na sake tabbatarwa a yanzu akan yayar mahaifiyata,na kuma sake tabbatarwa a yanzu a zamanki da yaya adam da momee. Bazan taba nutsuwa ba,bazan taba samun kwanciyar hankali ba idan har na bari akayo miki wannan zaluncin,bayan kunnuwa na sunji amma na gagara gaya miki" sai tayi shuru hawayen naci gaba da zuba tana hadiyar zuciya "Na baro yaya adam a gida yanzu suna shirya yadda zasu qarasa murqushe dukiyarki" ta tsaya da zancan tana kallon sãahar. Ido sosai sãahar din ta zuba mata,maganar tana neman matsugunni a kunnuwanta sannan ta isa ga kwanyarta,tsahon wasu sakanni sannan ta danyi murmushi tace "Ba murqushewa zaiyi ba ba raihanatu,nina dauka da kaina na bashi,ba bangula guda biyu ba?" Kai ta girgiza alamun a'ah "Duk wata dukiya dake hannunki da wadda take hannunsa,bama wannan ba anty.....kinsan yaa adam yana da wata matar bayan ke?" Wani irin mugun hautsinawa kanta yayi,mararta kuma ta damqe guri guda kamar curarren alkaki,amai ya taso masa me bala'in zafi tare da tashin hankalin daya daki zuciyarta,saita miqe da mugun gudu ta nufi kitchen wanda shine yafi kusa da ita. Sosai ta dinga kwarara amai,har sai dan samosa da madarar da tasha babu jimawa suka fice gaba daya,a sannan raihanatu tana tsaye a bayanta tanayi mata sannu cikin tashin hankali,a wahalce sãahar ta gama kuskure bakinta tana maida numfashi ta juyo tana duban raihanatu data gama tsurewa gaba daya,zuciyarta kuma ta fara shiga tsoro da nadamar abinda yasa ta gaya mata wannan babban sirrin "Kiyi haquri anty,ban gaya miki don na daga hankalinki ba,na gaya miki ne saboda kina da kirki,ke din mutuniyar arziqi ce,barin wasu mutane masu mummunar zuciya su cutar daku babban zunubi ne" hannu ta dora a kafadar raihanatu "Karki damu raihanatu,jikina yana bani da dukkan gaskiyarki kikayi maganar nan" saita jawo yarinyar jikinta tana jin zuciyarta tana karyewa,duk da a yanzu tana gayawa kanta ba rauni take buqata ba,tana buqatar qarfin hali da dauriya me tarin yawa don ta gano ainihin gaskiyar maganar,duk da wani sashe na zuciyar yana mata tantama,anya adam?,adam da momee?,zasu aikata?. "Na gode raihanatu" ta fada sannan ta janyeta daga jikinta,hannuwan sãahar duka biyun raihanatu ta kamo ta riqe,abinda bata taba yi ba,cikin rawar murya tace "Amma don Allah anty kiyimin alqawarin ba wanda zaisan ni na gaya miki maganar nan" "Komai rintsi komai tsanani raihanatu,na miki wannan alqawarin" tana nan tsaye kamar statue har raihanatu ta fice a gidan. Gaba daya ji tayi kamar an yashe komai daga cikin kanta,ta rasa dukkan wata idea da matakin daya kamata ta fara dauka,babu abinda yake mata amsa kuwwa a kunne sai YAYA ADAM YANA DA WATA MATAR BAYAN KE,ta yaya hakan zata kasance?,ta yaya hakan zata yiwu?,bayan ko yaushe suna tare da dam?,shiba matafiyi ba ba komai ba bare tace yayi amfani da wannan damar yayi auren a wani garin bata sani ba?,sai ta sulale ta zauna a wajen,tasa hannunta guda biyun ta dafe kanta wanda taji yana sara mata,kanta taji yana cushewa,zai buga da kalar tunanin da take takurawa kanta dashi,saita fara karanto sunayen Allah,da haka ta samu taja jikinta ta koma falon ta zube saman kujera. Tunda ta kwanta bata tashi ba sai da akayi sallar la'asar,kana kallonta zakace bata da lafiya,dab da kiran magariba adam ya shigo,tana daga kwancen ta daga kanta tana kallonsa,fuskarsa cike da walwala da wani irin nishadi wanda batasan daga ina ya samo asali ba,saita samu kanta da qarewa fuskarka kallo da kyau,zuciyarta tana nazartarsa,nazarin da bata taba yinsa a kan adam ba. Ganinta a kwance yasa ya sauke hannayensa daya ware mata yana jiran ta shigo ya rungumeta,duka sai walwalarsa ta koma,ya tako da sassarfa cikin nuna damuwa me yawa ya iso gareta "Heart,what happened?" Yayi maganar yana dagota zuwa jikinsa 'banajin dadi" ta bashi amsa a taqaice "What?,kada dai ace a kwance kika wuni?"kai ta sake gyada masa "Ya salam,me yasa baki kirani ba?,amma baki kyautamin ba, please please karki qara yimin haka,idan wani abu ya sameki fa?" Yayi maganar kamar zai fashe da kuka,sai ya kwantar da ita,ya ciro waya,saiji tayi yana kiran wani likitansa. Drip yasa aka daura mata,wai tafijin qwarin jikinta,ya kasa zaune ya kasa tsaye,bayan fitar likitan ya shiga kitchen ya dora abincin dare,yayi yayi ta fada me takeson ci tace masa babu komai. Wanzuwarsa a kitchen din ya bata damar sake zurfafa cikin tunaninta,ta dinga hango mode dinsa tun daga shigowarsa gidan kawo yanzu,tarin qauna kulawa da kuma riritawa ce zallah,sai zuciyarta ta cika da kokwanto,amma kuma ta rasa meye yake bata qwarin gwiwa da tabbaci. Karin ruwan babu abinda ya qara mata,saboda wata irin narkakkiyar damuwa ce dake kwance qasan a zuciya,a haka suka kwana. Washegari tunda wuri ya hada mata breakfast ya shirya yace mata zai fita,amma azahar ko la'asar zai dawo. Har ya fita saita miqe ta bishi,a qofar dakinsa sukaci karo,yasa hannu ya jawo qofar yana kullewa da dan sauri,yayin da idanunsa ke a kanta yana kasheta da murmushi. "Akwai wani abu ne?,ko kinaso na taho miki da wani abun?" Kai ta girgiza "A'ah,zan dan fita strolling ne idan na gaji da kwanciyar" "Ba damuwa,amma ko nasa momee ta kawo miki raihanatu?"kiran sunan kawai yasa gabanta ya fadi,saboda tuna gagarumin abun da muddin ta samu tabbacin afkuwarsa,zai zama sila ta guntulewar alaqar auratayya tsakaninta da adam,duk yadda take da kai, muddin kai din maha'inci ko maciyin amana ne.....to tana shata layi me girma a tsakaninka da ita. "Ka barta,na danji dadin jikin ai" ta amsa masa. Kasa komawa dakinta tayi bayan fitarsa,taja jiki ta zauna saman kujera,kamar kuma wadda aka mintsina saita miqe da sauri,kai tsaye ta doshi dakin adam. Tambayar kanta takeyi me zataje tayi a dakin?,tunda ta tabbatar ya rufe dakin a gabanta,kuma bata da sauran spare key da zai bata damar shiga?,amma duk da wannan tunanin sai ta gaza tsaida kanta daga dosar dakin da takeyi. Sau daya ta murda dakin bawai don tana tantama ko tana da masaniyar bai rufe ba,amma cikin iko da qudurar ubangiji taji ya bude,mamaki ya cikata,ta tsaya tana duban qofar bayan ta bude,ta leqa sai ta fahimci yana sauri ne bai murza key din da kyau ba,lock din bai gama shiga ba ya zare ya dauka ya shige. Sakin wannan tunanin tayi ta wuce dakin da gaggawa. Cak ta tsaya tana qarewa dakin kallo,tana nazarin ta ina zata fara binciken da zai bata shaida ko tabbacin abinda take zargi?,shikam adam ma bashi da safe irin nata,saboda yasha gaya mata ya yarda da ita. Wani tunani ya fado mata,a dazu da suka shiga dakin taga yanata kaffa kaffa da wardrobe dinsa,tun bata ankara ba har hankalinta yakai kai,amma bata kawo komai a ranta ba ko kadan,saboda tasan zuwa yanzu ya wanke dukkan wani zarginsa a ranta. Cike da fargaba ta buda wardrobe din,cikin ranta tana addu'ar Allah yasa komai ya zama hasashe ne,Allah yasa komai ya zama tunani ne,muddin ta samu adam da cin amanarta,batasan ta yadda zuciyarta zata iya dauka ba. Tsaf ta bincike wardrobe din,saidai bataga komai ba,tasa hannu tana shirin rufewa idanunta ya sauka daga can qasanta,wani abu me kama da jaka ta gani a jingine daga can gefe,saita tsugunna ta jawo,jakace baqa mai cike da zips kala kala,tunda take da adam bata taba ganin jakar ba,wannan ya qara mata qaimi da karsashi,ta fara bude zips din,take kudade masu tarin yawa daure cikin kyauraye da kuma takardu masu yawa suka fado. *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 45 Kafafunta ne taji sunyi wani irin sanyi suna kamar zasu lanqwashe da kansu kai kace narkakkiyar roba ce,sai ta zame ta zauna sosai a qasa,ta ajjiye kudaden da suka kasance dollars masu tarin yawa bandir bandir gefe guda,ta zube takardun da kyau,ta soma dauka tana dubawa. Wani irin gumi ne ya fara yanko mata,tun daga tsakiyar kanta zuwa tafin qafafunta,kowacce takarda da original copy dinta,da kuma wadda aka sauya a manne da 'yar uwarta,indai idanunta dai dai suke gane mata......takardun dukka filayenta da sauran kadarorinta ne dake wajensa aka sauyasu da wasu sunaye na wasu mutane da batasansu ba,affidavit na court dake bada tabbacin sunayen da kuma mallakar dake jikin takardun na asali,takardun withdrawal da akayi daga joint account dinsu,statement of account gaba daya,dama rufe account din da akayi kwata kwata. Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana,komai ya canza,ya tashi daga mallakinta zuwa mallakar ADAM ADAM,FAINUSA ADAM da kuma WARISHA KHADIRI,mutanen da batasan su waye ba banda sunan adam din dake maqale a jikin sunan kowannensu. Kamar wadda aka tsinkawa jijiyar hannu ta zaro takardar gaba, certificate of birth ne me dauke da sunayen dake a sama,FAINUSA ADAM da ADAM ADAM,kanta ya sake kullewa da kyau,wani irin tashin hankali ya dira a tsakiyar zuciya dama kwanyarta tunanin da ya darsu a ranta ya sanyata ci gaba da birkita takardun gabanta cikin hanzari,caraf hannunta ya sauka akan takardar shaidar zama ma'aurata ADAM/WARISHA. Sosai hannuwanta suka fara rawa,da gaske ne ashe?, abinda raihanatu ta gaya mata da gaske ne?,adam yana da wata matar bayan ita?,da gaske ne adam ya shirya cin amanarta?,indai waccan matarsa ce su kuma yaran fa na waye?, tambayar data sanyata surar passport din data gani guda hudu a gabanta,wanda budeshi ya zame mata tamkar madubi ko amsa na dukka tambayoyin dake karakaina a tsakiyar kwanyarta zuwa zuciyarta,suna barazanar fasa mata tunani. Fes kamannin yaran suka bayyana kansu da kansu,adam sak!,kamar yayi kaki ya ajjiye,ko kamar karan da aka samu gwanin iya rabo ya tsagashi gida biyu. Dif komai ya tsaya mata,ta dinga jujjuya korayen fasfunan da suka kasance baqaqe wuluk a idanunta,fasfunan dake dauke da visa ta qasar england,visa din da zata basu damar zama a qasar na shekaru ɗai ɗai har shekaru biyar cif!. Da qyar ta qwaci kanta ta fusgi harshenta ta kawowa kanta da kanta dauki ta hanyar furta "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, la'ilaha illa anta subhanaka inji kuntu minazzalimin" ta fara maimaitawa wasu hawaye masu zafi suna malala daga idanun nata. Qoqarin hanawa kanta tashin hankalin kanta takeyi da gasken gaske,saboda yadda taji mararta tana qullewa,bata shirya asarar abinda yake cikinta ba,don haka tayita kokawa da numfashinta tana jansa tare da fitar dashi da sunan Allah,wata 'yar qaramar nutsuwa ta sauko mata,saidai zuciyarta na mata wani irin ciwo da zafi tana jin inda za'a dubata a yanzu qila a tarar ta kumbura. Miqewa tayi jiri yana dibarta ta wuce toilet dinsa,ta tsaya gaban sink ta kunna famfo ta daura alwala tana fatan tiririn yaji da zafin dake fita a fuskarta ya tsagaita,ta kusa kashe minti goma tana daura alwalar tana kuma maimaitawa,ita kadai tasan dimuwa da razanar da zuciyarta take ciki,daga bisani tilas ta daure famfon ta fito zuwa bedroom din. Gefe guda ta zauna,ta zubawa takardun da kudaden da fiye da rabinsu haqqinta ne ido,shi yasa ta daina jin alert?,ya zare duk wani kudi data nema da guminta?,ya yiwa matarsa da yaransa wadanda batasan da zamansu ba visa na barin qasar?,ya dauke duk wata dukiya tata ya maidata mallakinsa?,ya hanata haihuwa,ya hanata morar komai nata,ya yaudareta yaudara mafi muni,ya shiga rayuwarta a lokacin da taqi baiwa kowanne namiji fuska,yayi amfani da iya kalamansa, kyakkyawar mu'amala da kulawa mai matuqar nauyi da zurfi,irin kulawar da komai taurin kai da kafiyarki dole ki amshi soyayyar mutum,ya hada da wayo da dabara irin wanda itadin qarancin shekarunta basukai kansu ba,ya cusa mata soyayyarsa ya mallaketa yake kuma neman sanyata cikin musiba mara misali,me ta yiwa adam haka na cutarwa tsahon rayuwarsu da zaiyi mata wannan mummunar sakayyar?. Ji tayi kamar zuciyarta tana narkewa,kukanta yanason fitowa fili ta yishi sosai,amma zuciyartata tana tunasar da ita "Lokacine daya kamata ace kinyi abinda ya dace,ba lokacin kuka bane yanzu" maganar data fito daga can qarqashin zuciyarta kenan,ta kuma zaburar da ita,ta barota daga inda take zaunen,ta dawo ta tattara takardun da kudin,passport din da komai da komai yadda suke a tsare a jakar,bayan ta gama ta zuge jakar,ta daukota ta fita daga dakin,bayan taja kowacce qofa ta maidata yadda take,tamkar ma bata shiga dakin ba. Doguwar riga me sulbi ta zura saman kayan jikinta,ta yane kanta da mayafin rigar,bayan ta shafa fuskarta da hoda ta zizara kwalli daya qarawa idanunta haske,duk da yawan kukan da tasha,sannan ta wuce zuwa farfajiyar gidan,ta bude motarta ta jefa jakar a ciki,ta tashi motar ta fice a gidan da gudun tsiya. Kai tsaye gidansu ta nufa,tanason ta yiwa jakar ajiya a muhalli me kyau,tanason taga iya gudun ruwan adam,tanason ya kama kanshi da kanshi ta hanya mafi sauqi da dacewa. Qasa da mintinan data saba isa gida a yau ta isa,don gudu tayi sosai saman titi,tanason ta riga adam komawa gida,batason yasan cewa ma tafita kwata kwata daga gidan. Biyu cikin ma'aikatan gidansu ne suka taso suna mata sannu da zuwa,a yau din bata cikin dukkan wani yanayi na walwala ko sakewar data saba yi musu,don haka sama sama ta amsa musu,ta bude baya ta dauki jakar,saita barwa marwa key din motar tace ta rufe mata,ta wuce gidan dauke da jakar. Gidan babu kowa sai masu aikin daketa kaikawo,ko maama ma a sannan tana daki a kwance tana hutawa,da kallo ta bita lokacin data shiga dakin,ta miqe ta zauna tana ci gaba da nazartarta "Ajiya na kawo miki maama,wasu kaya ne masu muhimmanci,don Allah karki barsu nan kusa,nima ajiya aka ban,ina tsoron tabasu ko kuma nayi sakaci wajen ajiyarsu" abinda tace da maama din kenan,sai tabi jakar da kallo sannan ta sake maida dubanta ga sãahar "To shikenan,amma dai,kedin lafiya lau kike kuwa?" Wani abu me nauyi ya sauka a qirjinta,tana jin kamar ta budewa maama zuciyarta taga tsantsar damuwa da kuma tashin hankalin da take ciki,to amma idan ta aikata hakan tasan zata jefata ne a damuwar data ninka tata. Dukkaninsu wani irin so suke mata,sam basu ajeta nan kusa ba a zukatansu "Ba komai,kawai yau inajin weakness ne,gida ma zan wuce nadan kwanta,zan samu relief in sha Allah idan na tashi" kai tadan jinjina tana dan jin tantama,amma dai bata sake hango komai dazai bata hujja ba "Allah ya qara lafiya,ya raba lafiya,kinqi bari a kawo miki me tayaki hidimar gida,ke kadai a family kin fita zakka sãahar,ba wanda babu me aiki a gidansa sai ke" murmushin da yafi kama da yaqe ta saki "Maama saina haihu in sha Allah" "Dolenki ai" ta fada tana miqewa da jakar a hannunta. Kamar a zuwa haka a komawa ta dinga tsala gudu,cikin mintuna qalilan ta isa gidan,ta qarasa da motarta parking lot ta kasheta ta fito zuwa cikin gidan. A parlor ta zube,dauriyarta tana nan qarewa,ba abinda ke mata yawo a idanu sai hotunan yaran dake jikin passport din,da sunan ADAM a matsayin ubansu,da kuma matar dake a mazaunin matarsa, kuma mahaifiya ga yaran kamar yadda ta gani a sauran takardun dake dauke da gurbin da ake buqatar sunan mahaifiya. To hakan me yake nufi?,tun asali adam baya sonta kenan?, auren jari yaso yayi da ita?,ko cin amana ne zallah ya sauka zuwa zuciyarsa?,mummunar zuciya suka hadu da iblis sukayi masa muguwar kururuwa?,adam da d'a?,wanda ba ita ta haifa ba?,adam da mata bayan ita da duniya ta gama sani?,ya maye gurbin kowacce kadara tata da dukiyarta da sunan 'ya'yansa?,wanann wacce irin azzalumar duniya ce muke rayuwa a cikinta?. Duk yadda taso ci gaba da jurewa abun ya faskara,kuka ta zauna tanayi wiwiwi a falon,tafukan hannayenta shinfide saman fuskarta. Karar shigowar motarsa harabar gidan ya sanyata miqewa,kai tsaye ta wuce dakinta,ta kuma zarce bedroom ta fara hada ruwan wanka tana zare kayan jikinta,sam batason adam ya fuskanci komai bare wani abu ya darsu a ransa,don haka ta hada ruwa me dumi sosai,wanda tana gab da fara wankan ya Murda qofar dakin ya shigo, muryarsa cike da wani irin nishadi da a karon farko sãahar ta fassarashi,cikin muryar shauqi da nuna zallar soyayya yake kiranta "Heart!,heart kina ina?" Lamarin da ya sakata lumshe idanuwa,wasu hawaye masu dumin gaske suka sulalo mata "Har tsahon yaushe zai dauka yana yaudararta kafin ya gaya mata gaskiya?,ko kuma har sai lokacin da zata bude ido ta laluba sama da qasa babushi?,ya tattara komai nasa da ba nasa ba sun bar qasar shida iyalinsa?. Gyaran murya tayi masa,saiya murda qofar bandakin "Budemin nayi joining dinki mana" bata iya furta komai ba saboda ta tabbatar muryarta ta shaqe,saita sakeyi masa gyaran murya,dai dai sanda kira ya shigo wayarsa,saiya maida hankali kan kiran ya juya yana ficewa daga dakin tare da daga wayar duk a lokaci guda. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 46 Sake fashewa tayi da kuka cikin bathtub din,tanajin kamar ana matsa zuciyarta,ta jima a hakan sannan ta fito daga bandakin,tana takawa a hankali saboda yadda mararta ta riqe, idanunta suka sauka akan ledar daya shigo da ita ya ajjiye mata,wadda kullum yake kawo mata dukka abinda ta zabi ci kafin fitarsa,a yau sai taji ta tsani ledar da kuma tsani wanda ya kawo ledar,ta matsa gaban madubi tana goge ruwan jikinta,bata da karsashi ko sha'awar komai,kawai zata daure tayi komai ne don batason ya fuskanci wani abu,batason bashi qofar da zai dago akwai wani abu daya faru bayan fitarsa,tanason ta kamashi ne red handed,tana son ya kawo kanshi da kanshi,a dole ta shafa mai,ta zaro wata doguwar rigar ta zura,dai dai sanda taji an budo qofar da qarfi,har sai data hadu da bango ta bada wani bammm!. Da sauri ta daga kai tana dubansa,shima ita yake kallo,ta tsirashi da idanu,wani lafiyayyen tashin hankali ne a kwance saman fuskarsa,ta hadiye wani abu me daci da tauri,nata bacin ran yana son yin tasirin da taketa danne masa tun awannin dazu,amma kuma sai tayi wani qaqqarfan yunquri ta kauda shi gefe,ta maye gurbinsa da lallausan murmushin da idan kayi masa nazari me kyau zakasan cewa zallar yaqe ne takeyi me masifar ciwo "Sannu da zuwa,ka dade kuma cemin kayi da wuri zaka dawo" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba. Wani abu me matuqar girma ya hadiye a maqoshinsa,wanda ita kanta dake tsaye tana iya ganin yadda maqwallatonsa maqogaronsa yayi sama sannan yayi qasa,mummunar faduwar gaba da kokwanto suka lullubeshi,yayi namijin qoqarin qaqaro murmushin da yafi kama da kuka,cikin sanyin murya yace "Eh......na dan tsaya ne,momee na raka wani guri" murmushi ta kuma saki tana gyada kai,amma kuma zuciyarta na wani irin qonewa,ba zata iya ci gaba dayi masa wannan murmushin tana kallon fuskar da take da mugun baqi a idanunta ba,don haka ta waske ta hanyar juyawa zuwa ga ledar tana cewa "Let me see me aka kawomin" baice komai ba sai cika qofar da yayi ya juya ya fita a dakin,ta daga kanta a hankali tana sakin ledar ta fadi qasa,tabi qofar daya bar mata a bude da kallo,ruwan hawaye suna cika idanunta,dukkan wani tabbaci da yaqini yana sake samuwa a tatttare da ita. A daren babu wani abu data iya ci,hakanan bata sake ganin adam ba,sai sintiri da motsinsa me qarfi data dinga jiyowa daga dakinsa zuwa parlor,haka ta duqunquna cikin duvet,idanunta a runtse zazzabi yanason kamata. Sai wajen sha biyu saura sannan ya shigo dakin,har a sannan tana kwance ne kawai idanunta sun soye,babu wani alamun bacci,tana ga monitoring motsin adam din. Yana kunna fitilar dakin ta miqe tana hamma tamkar daga bacci ta tashi,ta kalleshi suka hada idanu tana mutstsuka ido "Kada kacemin sai yanzu ka shigo?,har nayi baccin farko?" Ta fada tana qare masa kallo,daga shigowarsa gida zuwa yanzu har wata rama taga yayi,fuskarsa ta fada,ya firgice gaba daya "Eh sai yanzu......ina wani aiki ne" "Maimakon ka kirani na tayaka saika barni nayi bacci ni kadai?" Ta saje fada a shagwabe,kamar amma gasa zuciyarta,bata iya jin amsar daya bata ba,sai kansa daya shafa. Saukowa tayi da niyyar zuwa tayi fitsari sannan ta daura alwala ko zataji sauqin zuciyarta,amma mararta ta riqe gam,saita zauna daga bakin gadon tana cije lebe,kanta a qasa tana ambaton sunan Allah "Yau su waye da waye sukazo gidan nan kam?" A hankali ta daga kai ta kalleshi,yana zaune gefan gadon ko kayan jikinsa baiyi nufin cirewa ba,kai ta girgiza "Ai yau ni kadai ka bari a gidan na wuni kamar tsohuwar mayya" ta amsa masa tana kafeshi da ido,sai ya danyi jim sannan ya zame ya kwanta kamar wanda zazzabi ke shirin saukar masa. Koda ta dawo kwanciyar ta tayi,ta kuma saki jiki sosai kamar wadda ke bacci,tana jinsa yanata juyi,ta kwanta ya tashi ya miqe ya fita ya dawo,har zuwa sanda addu'a taci qarfin idanunta baccin da takewa kanta fata yazo. Washegari bayan ta farka daga baccin daya dauketa bayan sallar asuba baya dakin,data fito falo sai taji motsinsa a bedroom dinsa,koda fa leqa ya yiwa komai na dakin filla filla "Halan furniture zaka sake mana?" Ta fada tana dariya,ba fara'a ko daya a fuskarsa,sai kai daya girgiza "Sanitation nakeyi" ya amsa mata a taqaice "Ya kamata, shikenan yau bari na fansheka na hada mana breakfast" bata jira cewarsa ba ta juya ta fice. Tana girkin tunani fal zuciyarta da ranta, sauqinta daya tun jiya bata fasa kiran sunan Allah a baki da zuci ba,tana samun raguwar quncin sosai da sukunin zuciya,tanason gayawa afifa,to amma ta tabbatar yadda afifa keda haushin adam komai ma zata dagulashi,ashe akwai abinda 'yaruwarta keji a jikinta shi yasa ta tsani adam har haka?,me yasa ita bata taba jin komai a kansa ba?,sai tarin yarda da aminci?,ko don ita za'a jarraba?,shi yasa komai nasa yayi tasiri a kanta?,bata taba manta yadda haduwarsu da adam ta samo asali,a b u k,yana level 400 gab dasu fara final exam,tana level 200. Sam adam ba ajinta bane,hasali ma sãahar din tun a sannan da take da shekaru qanana she has a CHARISMA that attract many people to her,ba kowanne namiji ke iya tararta da sunan soyayya ba,amma adam din ya daukarma ransa saiya siya soyayyarta,yana da baiwar BAKI da IYA TSARA MAGANA(abubuwa biyun dake cutar 'yammatan wannan zamanin kenan game da maza),tun daga randa ya bayyana mata soyayyarsa tayi gaba a wajen ta barshi kamar sauran samarin dake yawo a kanta,ya shiga ya fita yasan komai a kanta,ya zaqulo dukkan wani abu dake burge sãahar,abinda tafiso da wanda bataso,ya maida kansa irin wannan mutumin sak,a duk inda yasan zasu hadu,sai yayi wani abu daya tabbatar zai burgeta ko kuma yana cikin likes dinta. Ya jima yana bibiyarta da rayuwarta kafin ta daina ganinsa tsaf,abinka da zuciya da akace tanason me kyautata mata,tana kuma qin me munana mata,tun bata damu ba har ta fara jin babu dadi,basa makaranta daya da afifa,afifa na northwest a sannan,a b u k din da take kuma ita bamai kule kulen qawaye bace,tana da mugun miskilanci sosai,idan kaga sakewarta to irin iyayen nan masu zuwa da qananun yara,a nan ne zaka ga jerarrun fararen haqoranta,wannan din kuma sai ya sanya mata farinjini sosai gurin matan,gefe guda ga mazan dakeson miqa soyayyarsu a gareta,wadanda sukasan ita din me ajice kuma tafi qarfin ajin ajinsi,suna fatan koda abota ko qawance tayi dasu uwa uba tana da wata irin basira,tana da brain qwarai da gaske,wadan nan su suka sanyata zama sananniya sosai. Sai bayan wani lokaci sannan ya dawo,ko a sannan bata sake masa yadda yakeso ba,saidai an samu improvement akan yadda suke a baya,da wannan ya samu qofa ya kuma baje duk wata basirarsa,wadda sai data kusa qarewa tasss kafin ya samu dasa qaqqarfar soyayyarsa a zuciyarta. Bai mata qarya ba ya gaya mata wayeshi,su din ba masu shi bane,yana rayuwa ne da mamansa wadda ita ke daukar nauyin karatunsa da komai nasa,yana fargabar gidansu kamar ba zasu bashi aurenta ba,amma da yake Dr mamman girema dattijone,duk da yadda ya muhyi da yaa Saifullahi sundan nuna basaso,abinda ya tsayawa adam a rai kenan,amma dr mamman ya tsaya akayi komai,ba takurawa ba tsawwalawa,abinda ya girgiza kowa ya bawa kowa mamaki. A irin zallar kyau tsarin halitta gata da kuma aji na sãahar,ba wanda ya taba kawowa zata auri mutum me qaramin matsayi da matakin wadata a rayuwa irin ADAM. Sam ita ba wannan take dubawa ba,mutum ce da bata dauki rayuwarta da zafi can can ba, soyayya da kulawar da momee din adam ke nuna mata kawai ta isa ka kalla ka qara kalla,duk da cewa farko farkon aurensu,wata irin tsana ta yiwa afifan,qiri qiri ta nuna bata sonta,wanda ba wanda yasan meye dalili,amma dare daya komai ya canza,ta sata a jikinta da soyayyar da ko adam din bai sameta ba. Tun asali haka kawai wata irin rashin jituwa ke a tsakanin afifa da adam,wanda sai a wanann lokacin sãahar din wasu abubuwan suka fara zuwa kanta,ta fara tariyar dalilin da abubuwan daka iya jawo haka,ciki harda wannan yanayin data tsinci kanta a ciki a yanzu. A sauqaqe ta hada simple breakfast,ta samu ta durawa cikinta tea da chips ta miqa masa ta wuce nata dakin. Wanka tayi ta shirya kanta cikin sauqaqan kaya,tana cikin hutu ne data dauka a gurin aiki saboda yanayin laulayinta me dauke da ciwo,don haka ta shirya kanta cikin wata simple gown,ta koma saman gado tayi kwanciyarta ba tare data sake koma masa ba,zuciyarta cike da tunanuka iri daban daban,duk da yadda taketa qoqarin hana kanta,ko don lafiyar abinda yake cikinta. Tana jinsa yana waya sama sama amma bata iya tantance ainihin abinda yake fada,sai kai kawonsa lokaci zuwa lokaci,kusan awa biyu cikakku sannan ya tura qofar dakin nata,tana daga kwancen ta daga kai ta kalleshi,gaba daya yayi wani hajaran majaran dashi,suka hada ido,yau ko yaqen da yake ta qoqarin mata tun daga jiya zuwa yau ya kasa,sai haqora daya bude mata kawai "Ko zaki tashi kema ayi miki sanitation din?" Idanunta tadan juya kadan,baqincikinsa yana sake cikata,ta gama fahimtar inda ya dosa tsaf,don haka hankali kwance tace masa "Ka manta kowanne wata daga gida ina kiran masu aiki suyimin irin wannan gyaran?" "Na sani,yau ni nake sha'awar nayi miki" ya fada adan diririce da kuma alamun zaquwa,bata sake ce masa komai ba,ta miqe tsam ta kwashe duvet dinta tayi hanyar falo,don wani sanyo sanyi takeji dake nuna alamun zazzabi yana tafe. Tun idanunta suna kan tv tana sauraren motsinsa daga dakinta har baccin da bata samu isashe ba daren jiya yazo ya sureta,baccin da babu komai cikinsa sai takura da mafarkai marasa dadi,wannan ya sanya batayi nisa ba ta farka,mararta ta cika da fitsari,ta yaye duvet din ta sauke qafafunta qasa ta nufi bedroom dinta. Yana zaune saman bedside drawer dinta,ya aza dukka hannayensa guda biyu saman kansa ya dafe,kamar wanda mummunan ciwon kai ya cimma,ya maida komai inda ya jawoshi,saidai dakin ba abinda yayi face hargitsewa,ta san za'a rina,don bashi da cikakkiyar nutsuwar maida mata dakinta yadda yake,kawai ta barshi ne don taga iyakacin gudun nasa ruwan,ta kuma sake badda tunaninsa. FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 47 Toilet din ta wuce abinta,sai da tayi fitsarin ta sake daura alwala sannan ta fito,zuwa sannan ya sauke dafe kan nasa da yayi,ya goge hannuwansa a qirjinsa,suka hada ido,ta janye nata idanun tana bin dakin da kallo kafin ta sauke a kansa "Wannan ai wani aikin kawai ka bani,ka sake hautsinamin daki" iska ya furzar daga bakinsa yana ritsata da idanu,yana jin kamar ya yaye duk wani hijabi dake tsakanin kowanne dan adam da abokin maganarsa,ya gano inda ta ajiiye masa jakar,yana jin wani irin tashin hankali yana saukar masa,fargaba da wani irin firgici,wani sashen zuciyar tasa kuma tana cike ne da tantama,don yasan tabbas sai daya kulle dakinsa kafin ya fita,kuma tuntuni ya kwashe dukka spare keys din,suna gurinsa,kowanne kuma a cike yake babu guda daya daya bata,to amma ai jakar bata da qafafu,zata tafi da kanta ne?,ko kuwa fiffike tayi?. "kasala ce ta saukarmin" abinda ya fada kenan ya miqe yana jan qafafunsa ya fice,ta rakashi da kallo,taja tsaki hawaye nabin idanunta,mutum har mutum,amma yaudara ha'inci gami da cin amana sun ratsashi,itakam me zatayi da adam?,batajin har abada zata sake yarda dashi. Cikin kwanakin gaba daya ya gama zama wani iri,babu cikakken kuzari kwata kwata a tattare dashi,tuni dafa abinci ya zama tarihi a gidan,don dama shine yakeyi,ita bata iyawa sai jifa jifa,to daga ita har shi din a yanzu babu wanda yake da nutsuwar da zai tsaya yaci abincin ma gaba daya. Saidia yayita sintiri a kanta,ita kam koda wasa taqi nuna masa tasan komai kota gane abinda yake wakana,ta kawo idanu ta zuba masa,ta rungumi addu'a kawai,tana jiran ganin abinda hali zaiyi,murje idanunsa ne zai kawo kansa ko kuwa?. Shi da ita gaba daya sukayi rama cikin kwanakin,basa wata doguwar magana a tsakaninsu,duk da tana ta qoqarin yin komai kamar yadda ta saba,saidai yadda zuciyarta ke mata ciwo,wani lokacin tana buqatar kebewa,sai tayi masa qaryar batajin dadin jikinta,baya cewa komai shima,saidai hakan na sake dulmiyashi cikin kogin kokwanton ita ta dauke jakar koba ita bace. *_K A C I Ɓ U S (M U G U N G A M O)_* Wai bahaushe yace kaciɓus mugun gamo,sau da dama akwai zazzafar jarrabawar da zata fado rayuwarka,har wasu lokutan idan bakayi da gaske ba ta kusan zama silar rabuwarka da imaninka(wa'iyazubillah)amma kuma sai ta zamewa rayuwarka MABUDIN ALKHAIRI,sanin gaibu sai Allah,tabbas haka yake,batuna kuma da bashi canzawa. A cikin wannan yanayin da rayuwarsu ke tafiya a kai,cikin huwacewa ta ubangiji Allah ya qaddara tafiya aikin hajji ga dukka familyn Dr mamman girema,matarsa,yaransa harma da jikokinsa,da 'yan uwa na kusa da sukan biyawa,ciki harda afifa. Tun asali an tsara za'a yi tafiyar harda sãahar,amma samuwar cikin jikinta ya kawo zare sunanta daga cikin masu tafiyar. Taji ba dadi sosai,saboda tafiya ce da sau daya suka taba yinta wannan shine karo na biyu,ko wancan karon da akayi tafiyar gab da bikinta ne,taji dadin aikin hajji qwarai cikin familynta,kuma abune dama da yakan yiwa kowa dadi idan ka gudanar dashi cikin tawagar iyalinka. Tun ranar da sukayi waya da maama ta sanar mata tafiyarsu zata iya kamawa next week taji gana daya jikinta ya sanyaya,sai takejin kamar idan sun tafi ba zasu dawo ba,ko kuma ba zasu dawo su tarar da ita ba,cikin jikinta ta dinga jin kamar akwai wani babban abu mara dadi dake tunkarar rayuwarta,don haka cikin satin ta dinga ziryan zuwa gida. Wuni take a jikin maamanta,afifa na gefe suna hira,dukkansu sunga yanayinta ya canza,ga ramewar sa tayi,maama ta fara tambayarta "Ko akwai matsala ne tattare da cikin?" Kai ta girgiza "Nima bansan me yake sakani ramar nan ba maama" saita jinjina kai "Allah ya raba lafiya,karki dinga zama haka,ki kula da kanki da kyau don Allah" "In sha Allah" ta amsa tana maida kanta ta kwantar,tana jin kamar kada ta koma gidanta,kamar tayi zamanta tare dasu. Afifa dai tana gefe batace komai,har maama ta gama abinda takeyi ta fita ta barsu a dakin,afifa ta ajiiye nail cutter din hannunta ta kira sunan sãahar,tana daga kwancen ta kalleta "Ban yarda da cewar babu abinda yake damunki ba,kamar yadda maama ma na tabbatar bata gamsu da xancanki ba,kawai don ita din me kawaici ce,wadda kuma bata cika takurawa sai taji sirrin da mutum ya yanke ya barwa cikinsa ba" shuru sãahar tayi idanunta a runtse tana jin heart beat dinta har cikin kunnuwanta,hawaye masu dumi suka ciko idanunta da suke runtse amma taqi basu damar zubowa,tsahon wasu mintuna,batace komai ba itama afifa bata sake magana ba,ta buda bakinta a hankali "Tabbas akwai abinda yake damuna,babbar matsala ce da take gab da rabani da gidan aurena,idan har shuru yaci gaba da wanzuwa a bakinsa ba tare da kowanne irin sauyi na bayani ko bayyana kai daga gareshi ba,to komai zai bayyana,zan bayyana komai da kaina da kuma bakina" ta qarashe zancan tana bude idanunta akan afifa. Sosai afifa ke kallonta kamar meson karanto matsalar data kira din "Amma kinsan barin kashi a ciki baya maganin yunwa?" Ta fadi bayan ta rasa wacce kalma zata fada din,don gabanta wani irin faduwa kawai yakeyi da yadda taga fararen idanun saahar din sun canza launi. Wani malalacin murmushi ta saki,ta saukar da kanta qasa "Na sani,amma komai yana da lokaci" shuru ya sake ratsa dakin,afifa ta jima tana karantar fuskar sãahar din,sanann taja numfashi ta sauke "Allah yasa muji alkhairi" bata amsa mata ba,tadai maida kanta ne kawai ta kwantar, Allah ne kadai yasan me gobe zata haifar,Allah ne kuma kadai yasan ya rayuwa zatayi da ita a gobenta. Randa ake sanya ran tashinsu tayi niyyar kwana a gida ne,don haka da shirin kwana ta taho,cikin ikon Allah wajen sha daya na dare saiga kira mahajjatan qaramar hukumarsu su fito,cikin qanqanin lokaci gidan nasu yadan cika da masu sallama da kuma wasu daga cikin wadanda za'a yi tafiyar dasu,wasu kuma daga gidajensu sun wuce airport din,ba jinkiri suka fito,motarsu daya da maama da kuma afifa,jikinta a sanyaye tana kwance jikin maaman "Ni ina ganin idan ba dama ku koma asibiti ayi miki checkup,hankalina ba'a kwance yake ba sãahar tun ranar nan,bana ganin alamun lafiya a tattare dake,idan mukaje muka dawo still babu sauyi,zan yiwa yayanku magana ya siya mana ticket muje Egypt ko india a dubaki da kyau,jiya jiya abbanku ma yakemin qorafi" kamar maama din ta xungureta,saita sake lafewa a jikinta tana sakin siririn kuka, zuciyarta sam ba dadi,rayuwarma jinta take kawai gata nan gata nan,kukan da ya tashi hankalin maama din sosai "Anya ba damuwa?,anya zan tafi na barki a haka?,me yake damunki?" Yadda taga hankalin maama ya tashi ya sanya ta sassauta kukan,tana kuma qoqarin daidaita kanta,batason tayi asarar aikin hajji guda saboda ita,wataqila dukka ayyukan hajjinta a wannan ne zata samu cikakken karbabbe me cike da da cewa da rahamar Allah,ba zatayi mata wannan asarar ba "Lafiyata qalau maama,zanyi kewarku ne,duk kun hada baki kun tafi kun barni" ta fada tana kebe fuska "Ba zamuso wani abu ya sake samun abinda yake cikinki ba,idan Allah ya saukeki lafiya zakuje umra keda adam din,hajj kuwa zagayowar shekara kamar yaune,zuwa sannan ma zaki iya yayemin jikana saiki ajjiyemin abina ku tafi" kiran sunan adam da tayi kamar wani fami ne akan ciwon dake danqare cikin zuciyarta,saita sake lafewa jikin maaman ba tare da ta sake cewa komai ba. Tana tsaye ita da sauran ma'aikatan gidansu da ba dasu za'a je ba wannan karon har jirginsu ya tashi,zuwa lokacin qarfe sha biyu dai dai na dare,kubra daya daga cikin masu aikin biye da ita suka koma inda motocin gidansu ke fake,ta shige daya daga ciki,drivern yaja suka bar airport din. Tun a motar ta hada kai da gwiwa cike da damuwa,tana jin kamar ita daya tayi saura cikin duniyar,suna isa gidan ta wuce dakin maama,gadonta ta haye ta lulluba da duvet dinta tana jin wata matsananciyar kewarta da bata taba jin irinta ba tunda suke tafiye tafiye,saboda akwai adam a gefanta,a lokuttan qauna da soyayya da kuka tsantsar kulawar da take kashe mata kewar duk wani makusancinta,a lokacin da yake nagartaccen miji tsayayye da baya gajiya da nuna mata zallar soyayya da kulawa,amma ayanzun daya zame mata tamkar wani shirgegen maciji dake dauke da uban dafi a bakinsa,dafin da takejin taqin dake tsakaninta dashi bashi da yawa,wanda da ace ya kai ga tsarta mata shi da wani zancen ake ba wannan ba. Cikin daren tayi wani irin kuka da yafi dukka sauran kukan da tayi a baya ciwo da yawa,ta tabbatar a rayuwa babu abinda yafi maraici d'aci da kuma ciwo,irin ciwon dake da tsananin wahala,kamar tasan qarin MUMMUNAR QADDARAR da take sake jiranta a washegari. Wannan kukan ya sanya tun asuba taji jikinta ba dadi,ta laluba magungunanta na anti natal ta barsu a gida,ba yanzun ta shirya komawa gida ba,to amma ya zama dole,don tana buqatar magungunan,don haka da safe bayan ta karya da abincin da take samu tana sanyawa cikinta da qyar saboda dan tayin bawan Allahn dake cikinta,tayi wanka ta shirya cikin doguwar rigar da a yanzun kusan suta maida kayan sawarta,kamar wata me takaba,kyakkyawar fuskar nan ta kode saboda kukan data kwana tanayi,saidai har a lokacin wannan sassanyan kyan bai gushe ba,ta karba key na daya daga cikin motocin,a yau fushin dake cinta a zuciya da tashin hankalin da rayuwarta ke ciki ya gaza boyuwa,ba fara'a ko alamun sukuni sam a fuskarta,wannan yanayin yasa cikin kulawa kubra tace tazo ta rakata?,kai kawai ta girgiza mata ta fice a gidan. *_Turqashi!!!!,shin me zata tarar?_*😭😭😭😭 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 https://arewabooks.com/u/huguma Page 48 A qofar gidan ta tsaida motar,da nufin ta fita ta bude gidan,tunda ta sani,ya gaya mata shima zaiyi tafiya ta kwanaki uku. A hankali take takawa zuwa qofar gate din,saboda yadda mararta ta sake qullewa,ta saka key ta buda qofar,ta tura qaramar qofar dake maqale jikin gate din ta shige. Bata ankara da motarsa dake ajjiye a farfajiyar gidan ba har sai data kawo tsakiyar gidan,mamaki yadan bayyana saman fuskarta,batayi tsammanin ganin motarsa ba,to amma sai zuciyarta ta bata wataqila tafiya ce ta team,a abun hawar ma'aikata suka tafi,ko kuma yabi jirgi ne ohon masa,duk da cewa tana tsammani zaiyi wuya indai ba biya masa akayi ba ya iya samun kudin biyan kudin ticket da sauransu. Tun daga sanda ya tattara komai ya kammale,idanuwanta suka kai ta kwashe,alamu da yawa suna nuna mata sauyin al'amura da yawa a tattare dashi,akwai abubuwa da yawansu da a yanzu baya iya aiwatarwa,hakan kuma yana nuni da cewa,dama can cikin kudadensu yake dukka birgima da facakarsa. Yage wannan tunanin tayi taci gaba da shiga cikin gidan. Mamakinta ya sake qaruwa lokacin data bude qofar falon,kaya ne a warwatse a qasan falon,ba watsewar kayan bace abun mamakin,gamayyar kalolin sutturar mace da namiji,daya dai tabbas kayan adam ne,yadin data siya masa a dinke a matsayin gift ranar zagayowar shekarar haihuwarsa,sauran kuma ba zata iya tantance suturar waye ba,tasan dai ba tata bace. Wani abune ya daki zuciyarta,amma saita matse zuciyar tata daga zarge zarge da tunane tunanen data fara debo mata,koma meye a yanzun bata rayuwar adam take ba,ta kanta da tata rayuwar da rayuwar abinda yake cikinta takeyi,koda tana buqatar sanin wani abu akai,tasha maganinta a yanzu shine abinda yafi zame mata me muhimmanci,tanajin mummunar fargabar da kuma mugun bugun zuciya,amma haka ta dauke idanunta daga kan kayan,ta kuma dauke idanunta daga kan sashen dakin adam dinma gaba daya ta nufi dakinta,saidai tana zura key da nufin budewa qofar ta tura kanta da kanta. Wani irin gurnani da sautin nishi ne abu na farko daya fara kaiwa ga idanunta,kafin daga bisani idanun nata su iya dauko mata hoton abinda ke wakana a tsakiyar gadonta na Sunnah,tare da mijinta na sunnah,cikin gidan aurenta na sunnah. Ba qaramin dan gajeran yaqi akayi tsakanin ido da kwanyarta kafin qwaqwalwar ta yarda ta kuma tantance mata gaskiyar abinda idanun suka hango mata. ADAM mijinta,tare da wata mace da ba zata iya gane ko wacece ba,suna aikata fasiqanci akan tsakiyar gadonta,dukkansu haihuwar iyayensu,dagashi har ita,ko duvet basu kaarantawa kansu sun rabawa jikinsu ba bare akai ga batun sutura. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta fada da qarfi sanadiyyar fusgota tayi daga cikin bakinta qarfi da yaji lokacin da numfashinta ke niyyar katsewa daga gangar jikinta. Dif taji sautuka marasa dadin dake tashi sun katse,ta daga kanta da yayi mata wani mugun nauyi tana sake qoqarin bude idanunta a karo na biyu. Tayi zaton ganin kowannensu a wani muhallin na daban yana neman sutura ko maboya,a'ah.......sabanin haka sai ta sake ganinsu a tare da juna,suna ci gaba da aikata alfasharsu hankali kwance,kamar ma basusan ta shigo ba. "ADAM!!!" Ta kira sunansa da wani irin sauti kamar na mutuwa,waiwayowa yayi yana duban tsakiyar qwayar idanunta da rinannun idanunsa,ba kuma tare da ya fasa aiwatar da abinda yakeyi din ba. Wani irin mummunan fushi da tashin hankali ya rifto mata,ta daga qafarta da zummar kaiwa cikin dakin don ta dakatar dasu,saidai taku biyu kacal tayi!,wani abu me dumi taji ya tsarga daga mararta yana bin qafafunta,abinda ya sanya mata waigi,ta dakata a firgice tana binsa da kallo. Jini ne jajir yake saukar mata, shigen jinin data gani a wancan lokacin na baya,wanda ganinsa ya tabbatar mata da zuwan qarshen zaminin cikinta,a yanzun kuma me yake shirin alamta mata?. Da wacce jarrabawar zubarsa zaizo mata?, qwaqwalwarta batayi nisan kiwon da zata lalubo mata amsar tambayarta ta fara kokawa da numfashinta,a hankali ta soma gani dishi dishi,dukkan wani jarumta ta gabban jikinta ta fara zagwanyewa,saita fara sulalewa tana yin qasa,inda daga bisani ta kife kif a akan fuskarta kuma saman cikinta. *******Ba zata iya cewa ga iya adadin awannin data dauka kafin dawowarta duniya ba,iya abinda zata iya tunawa kokawa data fara yi da zuciya da ruhinta,kokawar da batasan a gaske take yinta ba,har sai lokacin da taji ana bada umarnin riqeta,ba jimawa taji an daddanneta,bawai iya hannuwanta kadai ba,harda qafafunta,ta kasa motsa koda yatsarta,a sannan ta yanke shawarar buda idanuwanta taga ko cikin kabari take wannan al'amarin yake faruwa da ita?. Ba cikin kabari bane,cikin dakinta take,saman gadonta data tabbatar an gama yamutsashi da qazantaccen al'amarin da idanunta suka gani a dazu,hannunta guda daya qarin ruwa akeyi mata,wani dogon baqin mutum dake sanye da lab coat yana tsaye kusa ruwan yana qoqarin zuba wasu allaurai,daga daya bangaren kuma adam ne,wanda ya haye fiye da rabon gadon,kuma shike daddanne da ita. Wani azababben bacin rai tsana da kuma mummunar qiyayyarsa ce ta zarto tun daga asalin qasan zuciyarta har zuwa saman fuskarta,wani irin qarfi yazo mata,tayi yunquri me qarfi sai gashi tayi nasarar ture adam din gaba daya gefe,saboda ya saki jikinsa,bai dauka zata iya aiwatar da hakan ba. K'arin ruwan da ake mata tasa hannu ta fincike,take ruwan ya soma zuba a qasa,jini kuma ya ballewa hannun nata,kafin takai ga miqewa adam din ya miqe tsaye yana dosowa inda take "Karka sake ka matso inda nake,karka kuskure ka qaraso kusa dani,mugu azzalumi,macuci fasiqi,na gama zama dakai har abada wallahi,nayi nadamar saninka a rayuwata,nayi nadamar hada jikina da nayi da naka qazantaccen jikin" tana gama fada ta diro qafafunta qasa cikin fushi qasa,saidai tana miqewa ta jita fayau,kamar iska zata kayar da ita,jini me dumi ya sake zarto mata,amma duk da haka bata dakata daga fita da take niyyar yi ba. Ta tsani ganin koda inuwar adam bare ta hada daki daya dashi,ballantana kuma har suyi musayar numfashi,burinta kawai ta ganta ba a cikin gidan ba kota wanne hali,saidai tana kaiwa bakin qofa taji an fincikota an watsar,kafin ta gama gane ainihin abinda yake faruwa,an saukewa kyakkyawar fuskarta lafiyayyun mari guda biyu,wanda saida kunnenta ya dauke ya daina ji na wucin gadi,idanunta kuwa wasu irin taurari ta gani sun gifta,bata dawo hayyacinta ba adam ya bayyana a gabanta. Wata irin tsaiwa yayi a kanta,ya raba qafafunsa biyu a tsakiyarta yana duban qwayar idanunta da kyau "Ina zakije da?,ai yanzu aka fara wasan,wasa ne me kyau dake nuni da kyakkyawan shirin bugashi da kikayi,wanda inda kinsan true color din abokin buga wasan naki da baki tarki yin irin wannan wasan dashi ba" mamaki ya sanya ta daga fararen idanunta da suka taruwar jini a gefe tana kallonsa "Eh,idan kuma har baki shirya ci gaba da buga wasan ba........hanya guda daya ce gareki,ki fiddomin jakata da kika dauke" kai tsaye babu wani bata lokaci ko dogon ta fahimci abinda yakeson fada "Jakarka?" Ta fada bawai don tanason musawa ko kokwanto ba "Yes jakata,wannan ne zai sanya na baki damar tafiya salin alin,ina tsananin sonki sãahar,don ban taba samun mace me zallar madarar kyau da cikakkiyar ni'imar da take iya gamsar dani,da wani irin dandano da dadi na musamman kamarki ba,amma wallahi wallahi nafison kudi fiye dake,kuma nayi imanin su zasu sake samarmin wata macen wadda ta fiki ma wala'alla a wata nahiyar duniyar,matata ba zata taba hanani yin duk harkokin da nakeso ba,saboda itama bai hanata tayi tata rayuwar ba,amma ke muddin zanci gaba da zama dake,duk wata shaqatawata da jin dadina saidai na ajjiyeshi a gefe saboda wai kiyaye mutuncin addini da kuma samun dorewar soyayyarki da zaman lafiya a tsakaninmu,kamar yadda nayi tsahon uku babu kadan a zaman da mukayi......wanda nikam bazan iya ba,inason rayuwa" ya qarashe maganganun nasa yana sakin wani mugun murmushi. Saita zama speechless,ta narke a wajen tana kallon adam din cikin tsantsar mamakin daya gama daskarar da ita a gurin "Me kike kallo?,zaki ban jakata na sallameki ko saimun ci gaba da buga game din?" "Da kudadena halalina zakayi wannan shaqatawar?" Ta jefa masa tambayar da tafi qona mata rai,tafi kuma yi mata ciwo a ranta "Really,kin fini tarawa da yawa ai,sannan acan gida ma an tara miki wasu ana kan tara mikin ma kinga ya kamata naci gadonki tun kina raye,tunda na taqaita miki wahala ban bari kin haihu dani ba,wancan cikin na saka miki tablet yabi rariya salin alin,wannan ma yana fara girgidi na sanya aka zaquleshi aka watsar,don haka ina binki ladan aiki ma" sosai ta sake razana da bayanansa,ta miqa hannu ya shafo jinin dake bin qafafunta har yanzu ta kawoshi dai dai fuskarta tana kalla,wasu zafafan hawaye suka fara bin kuncinta,shikenan,shima ta rasashi. Wata irin dakiya taurin rai da zafin zuciya ne suka saukar mata a lokaci guda,ta daga fararen idanunta da a yanzun suka rine zuwa jajaye ta kalleshi da muryarta data qara kauri ta kuma cakude da sautin kuka "Yadda idan mutum yabar duniya sunyi bankwana da ita kenan har gaban abada.......haka nan wannan jakar tabar hannunka har abada,koda hakan yana nufin rasa numfashina ne" miqewa yayi zumbur yana dubanta saboda girgiza da yayi da jin furucinta,yasan halinta tsaf fiye da kima,KHADIJA tana da matuqar taurin kai a wasu lokutan,hakanan ita din kaifi daya ce,idan tace YES tofa YES dinne,hakanan idan tace NO zaiyi wahala ta dawo tace YES. Da qyar ya tattara qwarin gwiwarsa,ya saki dariya ya qara taku biyu zuwa gabanta kamar zai take yatsun qafarta "Nasan halinki fa,shi yasa na shiryawa dukkan wani taurin kan da zakizo min dashi,wuya da kuma azaba babu abinda bata sanyawa a barshi ko a aikatashi,idan ke qwararriyar 'yar wasa ce to kin hadu da qwararren me buga wasan" FURAR DANKO Billyn Abdul -ZAFIN KAI Mamuhgee -TABARMAR ‘KASHI Safiyya Huguma -BAKON MUNAFIKI Miss xoxo Duka hudu 1k Uku 800 Biyu 600 Daya 400 Pay at👇 1487616276 Access Bank Bilkisa Ibrahim Sai katura shedar biyanka anan👇 09032345899 Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇 09033181070 *Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din* +22799643131 *_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_* *THANKS FOR CHOOSING US*🥰 Zafafa🫶🔥 Page 49 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 49 Juyawa yayi ga likitan dake tsaye a gefe abinsa kamar ma baisan abinda yake wakana ba "Me kake jira likita?,ci gaba da aikinka" sai ya waiwaya gareta "Kika musanta ko kikace zakiyi taurin kai.....zakici gaba da shan baqar wahala ne a hannuna,babu kuma wanda ya isa ya qwaceki". Zumbur ta sake miqewa ganin likitan ua dosota,har batajin ciwo da zubar jinin jikinta,da gudu ta doshi qofa,amma kafin ta isa adam din ya rigata,ya kankane qofar,daga bayanta kuma likitan yana tsaye yana jiranta,ta duba hagu dama babu ba wani gurin tsira sai qofar toilet,don haka ta kwasa ta nufa can da gudu. Harta wuce drawer dinsa ta hangi wayarta akai,ta dawo da baya ta finciki wayar ta qara gudu zuwa toilet din,idanun adam suka kai kai,ya baro bakin qofar da wani irin mugun sauri ya biyo bayanta,kafin ya iso ta samu nasarar shigewa bandakin,ta tura qofar,ta kuma danneta da bayanta. Hannunta na rawa ta kunna wayar,ta fara laluben wanda zata kira,zuciyarta tayi mugun karyewa sanda ta tuna a yanzun kusan dukka wanda take saka ran samun daukinsa baya qasar baya tare da ita,daga qarshe ta yanke shawarar kiran ummin afifa. Wayar tana ringing adam dake bakin qofa yana dannota iya qarfinsa tare da qoqarin bankadeta ya bude qofar,ta runtse ido tana sakin kuka,bakinta fal addu'ar kada Allah ya bashi ikon cimmata har sai ummin ta dauka,muddin bata dauka da wuri ba tasan cewa kashinta ya bushe,a yadda ta zubar da jinin nan,babu wani cikakken qarfi yanzu haka a jikinta da zata iya ci gaba da tare qofar. Ringing din ya tsaya,muryar ummin ta bayyana radau tare da yin sallama "Zasu kasheni,zai kasheni" abinda ta fada kenan cikin qaraji,saboda nasarar bankado qofar da adam din ya samuyi,dalilin da ya sanyata faduwa gefe qasa warwas,taku biyu ya isa gabanta,yasa hannunsa ya damqe bakinta da kyau,ta inda babu damar da zatayi magana,ya zubamata ido da wani irin kallo na zallar rashin imani yana duban fuskarta tare da ja mata zazzafan gargadi da idanun nasa,sannan ya miqa hannu ya dauki wayar da har zuwa lokacin ummi ke fama cewa hello hello jin shuru ba'a sake magana ba. Kiran ya kashe sannan ya sakar mata baki,ya koma saman toilet ya zauna yana maida numfashi,ransa a matuqar bace "Kin ginawa kanki da kanki rami,zakisan cewa bani da imani" yana fadin hakan ya kamata,saidai taqi miqewa tsaye sam,bai damu ba ya riqe hannunta da kyau ya fara janta a qasa kamar kayan wanki,bai ajjiyeta ko a ina ba sai a gaban likitan "Kayi mata allurar bacci,ka hada mata data 'yan shaye shaye me qarfin" tana ji tana gani ya danneta aka hada ruguntsumin alluran aka dirka mata,a hankali jikinta ya fara saki,saidai idanuwanta basu daina zubar da ruwan hawaye ba,hakanan bakinta bai fasa fadin "Allah ya isa,Allah ya sakamin,Allah ka yimin sakayya". Bai ko dubeta ba ya jawo stool gabanta ya zauna,yayi kiran ummi. Bugu daya ta daga a matuqar rikice "Me yake faruwa da sãahar din?" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,muna cikin mummunan tashin hankali" ya fada da muryar kuka wadda a wajen ya qirqireta "Me ya faru?" "Ibtila'i ne ya samemu,na fita lafiya na dawo na tarar da ita cikin wani yanayi,ina shigowa kawai ta cakumeni ta fara fadin mugu azzalumi,ka cuceni zaka kasheni,Allah ya isa,Allah ya sakamin,ina tsammanin mummunan gamo tayi,don cewa tayi waita ganni da wata muna aikata alfasha,bayan kuma ni dawowata kenan daga tafiya,kwanana uku bana garin,yanzun haka gata ta sume,da qyar na samo kanta,duk tayi fashe fashe a dakinta" salati ummi ta saki tana sallalami cikin matuqar tashin hankali "Yanzun tana ina?" "Gamu a gida,amma na yiwa wani malami waya yana kan hanyar zuwa" "Ganinan nima" ta fada a gaggauce tana kashe kiran. Iska ya furzar daga bakinsa,sannan cikin hanzari ya fara kiran wata number wayar daban. Bugu uku aka daga,sai ya miqe yana fita a dakin,yana amsa wayar a gaggauce. Sake lumshewa idanunta sukayi hade da wani zazzafan hawaye,zuwa lokacin sama sama takejin komai,hakanan dishi dishi take ganin abubuwa,amma duk da haka kwanyarta bata daina aiki ba,bata kuma daina haska mata girman cin amanar da adam yake Shirin aikata mata ba,wadda tafi abinda ya aikata mata a baya girma da muni. Kafin ya dawo bacci tuni yaci qarfinta. Sanda ta farka ta ganta ne kawai kaca kaca cikin shirgi da shara,tana yashe a qasa cikin dattin,gaba daya dakin ya kacame,hatta da mirror da wanda ke jikin sif din a farfashe yake,duk wani kayan ado da qawa dake dakin wanda hannu zai iya kaiwa gareshi a fashe yake. Cikin mamaki ta miqe ta zauna tana jin kallon ko ina,ita daya ce qwallin qwal a ciki,saita zabura ta miqe ta sauri ta nufi bakin qofa,tana fatan ta samu qofar a bude. Tana isa bakin qofar muryar ummi ta fara jiyowa,wannan ya sanya da azama ta dora hannunta kan handle din ta fara jijjigashi tana fadin "Ki taimakeni..... kasheni yakeson yi,ki budemin,ki tafi dani don Allah" ta furta iyakar budewar muryarta,wadda bata da wani amo sam sam kasancewarta mai sanyin murya tun asali. Adam dake zaune qasan kujera wurjajan ya daga jajajyen idanunsa da sukayi jajur ya kalli qofar,kamar yadda idanun ummi dake sharce hawaye itama suke duban qofar "To hajiya kinji irin takeyi,kuma duk sharrinsu ne" cewar wanda ke zaune daura da adam din,cikin babbar rugar malum malum harda rawani,da kuma tsayayyen gemun da wala'alla ciko ne akayi masa yayi irin wannan cikar,hannunsa kuma zabgegiyar tasbaha ce yake ta janta daya nabin daya "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,wannan wacce irin jarabawa ce ta saukarmiki sãahar da qananun da ko ashirin basu haura ba?" Ta fada cikin kuka "Hajiya kar ayi sabo,shi lamarin ubangiji haka yake,jarrabawa kuma babu ta inda bata saukarwa bawa" malamin qaryar ya fada yana shafa gemunsa cikin nuna zallar taqawar da babu ita ko kusa ko alama cikin zuciyarsa "Yanzu ba yadda za'a yi na ganta?" Da sauri ya girgiza kai "Ai hajiya muddin aka rabata da wannan dakin ba abinda bazai iya faruwa ba,zasu iya dauketa ma a nemeta a rasata,shi kansa likitan da kikaga ya fita yanzu saida Allah yasa bacci ya dauketa ya iyayi mata gwaje gwajen da yayi,shima kuma yaga alamun tabuwar kwanya kadan,duk da hakan na iya yiwuwa duk cikin sharrinsu ne". A yadda suka tsara komai abune mawuyaci ka fahimci cewa shiri ne irin na adam da muqarrabansa,cikin kwana daya tal ya maidata mahaukaciyar qarfi da yaji,kusan kullum a nan ummi ke yini,gudun tonuwar asirinsa yasa aka dinga yawaita yi mata allurar bacci da aka cakudata da allurar sanya maye,abinda ya qara nakasta garkuwar jikinta,ya zamana ko cikakken zama bata iyayi,data zauna din sai bacci,kota dinga bin kowa da kallo kamar sokuwa,sukayi amfani da wannan damar sukace maganin da malamin yakeyi mata ne ya fara aiki a jikinta. Fadin irin tashin hankalin da iyalan Dr mamman jarma suka shiga a qasar saudiyya sakamakon mummunan labarin tabuwar qwaqwalwar sãahar da suka samu bata baki ne,kada ma afifa taji labari,wadda a jikinta ta dinga jin cewa ba haka bane,hauka yana da sila da kuma sanadi idan ma har haukanne,koda ta sanadiyyar jinnu ne suna nuna wasu alamomi kafin sukai ga taba lafiya kwanyar mutum,tunda suke da sãahar basu taba ganin wani abu na daban tattare da ita ba da yake da alaqa da irin wannan lalurar. Mutane ne masu tsananun dattako da yarda da Allah wahidun ahadun,sun yi imani suna qofar waraka,qofar karbar dukkan addu'ar me neman,wajen biyan buqatar duk wani mabaraci,dukkaninsu sai suka duqufa da addu'a ta nema mata sassauci da waraka,tana da gata me yawa da soyayyar iyaye da yayye,hakanan qananun yaran da suka kasance 'ya'yan 'yan uwanta suna tsananin sonta,saboda ita din mutum ce me son yara qwarai,akwai soyayya da sabo sosai a tsakaninsu. Kwanakin da suke gabansu na ranar dawowa Nigeria sai suka zame musu kwanaki mafiya tsaho,duk da haka basu bari sunyi asarar kwanakin ba,sunci gaba da addu'a da ibada,tare da samin information na halin da ake ciki a wajen ummi. **************Ta fuskanci duk wani abu da zatayi babu abinda zai hana adam aiwatar da abinda ya shirya mata,hakanan a yadda ya tsara din ta tabbata cikakkiyar mahaukaci ga idon kowa,tana jin muryoyin 'yan uwa makusanta daga parlor din gidan masu zuwa dubiya gurin ummi,saidai ta zame ta kwanta lamo tana jinsu,don zuwa lokacin tayi kukan da batasan iya adadinsa ba,bai kuma qara mata komai ba hakanan bai rage ba,don ba abinda adam ya fasa,saidai yana gaya mata a kullum,zabin fitarta daga wannan yanayin ko tabbatuwarta a ciki yana hannunta,ta sallameshi shima a ranar zai sallameta kowa ya kama gabansa. Kwata kwata daina tanka masa tayi,saidai ya qaraci maganarsa ya tashi ya miqe ya fice,abinda yake sake dugunzuma ransa kenan tare da qara masa bacin rai a kanta "Banda ina tsoron na qarasa gawar daba tawa ba,tabbas da sai nayi miki dukan da zaki raina kanki,amma ko a hakan ma muje zuwa wai mahaukaci ya hau kura" ya miqe yayi fatali da gantalelallen abincin da ya kawo mata,ya samu kyakkyawan mazauni akan qafafunta,zafin abincin ya ratsata,amma bata iya janye qafafun nata ba saboda wani azabtaccen ciwon kai da take fama dashi,ko gani bata iyayi sosai. Da zugin ya isheta saita zame kawai ta kwanta a wajen tana maida numfashi,babu abinda zuciyarta ke ayyano mata sai irin rayuwar da sukayi ita da adam a baya,yadda ya kula da ita ya tattalata,amma zuwa wannan lokacin ya juye ya koma mata wani irin baqirin shaidanin kumurcin maciji me cike da guba da kuma dafi. Lokacin data fuskanci jinin cikin da cisge mata ta qarfi da yaji ya dauke,sai tayi wanka ta daura babban towel tayi sallah,baya rufe bandakin,don bazai iya jigilar gyara gurin ba idan ta bata. Darajar sallar data fara yi sai ta fara samun nutsuwa cikin ruhinta,daga mugun likitan har annamimin malamin,duk sanda sukazo saidai tabisu da ido,kowa ya gama mugun alkaba'insa ya fice,me allura yayi,me kawo tofin qarya ya kawo ya ajjiye saboda adam din yanason ya tara evidence na cewa yana kula da ita,kuma tabbas lalurarta akwai aljanu a ciki. Ko sau daya bata taba bata ba a lissafin kwanakin daya ragewa ahalinta su dawo,ranar da take sanya ran kwanaki biyu ko daya suka rage musu su dawo,bayan likitan ya gama dirka mata allurar ba tare da sunbi takan matsanancin ciwon kan dake gallabarta ba,wanda ya sake sanyawa ta zuqe ta rame ta koma 'yar firit,sai sassanyan kyantannan da har yanzu yana nan shinfide a fuskarta. Page 50 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 50 Idanunta a lullumshe,tana ganinsa dishi dishi,amma ranta cike fal da baqinciki da kuma zallar bacin rai na hana mata samun salla,don tana gama alwala kafin takai ga tayar da sallar suka shigo mata "Kaji tsoron Allah" ta samu ta fusgi kalmomin daga bakinta,cikin sautin galabaita,a fusace ya dawo gabanta ya tsaya,ya sa hannu ya matse fuskarta cikin hannunsa da kyau,wani zafi ya ratsa fatarta,ta runtse idanunta a galabaice "Ke zan cewa kiji tsoron Allah,muguwa wadda bataso a qaru da ita,kina ta sakani ina sake asarar ragowar kudin hannuna gurin siya miki alluran da zasu ladabtarmin da ke,na rantse miki da Allah bazan taba barinki ki kubuta ba har sai kin fiddomin da jakata" yana kaiwa wannan ya jefar da ita ya fice yana huci. Duk da hankalinta ya kusa gushewa amma bata gaza tantance dacin kalamansa a kanta ba,a sannan tarwai take iya tuno sanda afifa dama maama ke jaddada mata tayi iskhara kafin ta bawa adam damar turo magabatansa, murmushi kawai tauiy,tana ganin tunda har Allah yasa abba ya karbeshi ya amince ya turo,duk da su ya Saifullahi basu gama gamsuwa ba,to ba shakka shi din Allahn ya zaba mata,bata kokwanto,bata kuma buqatar qarawa da istikhara din,kada taje hankalinta ya kasu biyu. Kuka takeson yi amma ruwan allurar yabi jikinta,haka tayi shame shame a gurin,ita bame rai ba,hakanan ita ba gawa ba. Abu daya da bata sani ba shine,yadda take lissafin ranar dawowar su maama haka shima adam yakeyi,ya kuma gama shirya komai,da dukka wasu allurai masu qarfi da za'a sauya mata dasu,wanda zasu sake sakata cikin bacci da maye mai qarfi,su kuma zabura qwaqwalwarta,ta yadda komai qwaqwafi da hasashenka baka isa ka fahimci lafiya qalau take ba. A washegari aka shiryo raihanatu aka kawota gidan da sunan zata dinga kula da sãahar,saidai duka hakan wani shiri ne da akayi don amintar da zukatan iyalan dr mamman girema. Da qaqqarfar gargadi momee ta tsare raihanatu akan babu ruwanta da dukkan abinda zata ji ko zata gani a gidan adamu,iyakar abinda akace tayi shi zatayi,wanda ba'a sanyata ba kome zai faru kada ta tsoma hannu ko bakinta,sabawa wannan umarnin nata,dai dai yake data rasa rayuwarta gaba daya,maganar datayi mugun daga hankalin raihanatu kenan,fitsari ya balle mata,ta roqi momee kan tayi haquri,kada ma ta kaita,saboda ta fahimci akwai abubuwa masu muni dake faruwa da anty sãahar din mutuniyar kirki me qaunarta,duk da bata gama fahimtar komai dari bisa dari ba,to amma jikinta da zuciyarta sun bata,kumnuwanta kuma sun tsinci kadan daga cikin wasu qulle qullen da momee din keyi tare da adam din. "Bakin alqalami ya riga ya bushe,tunda har wannan gargadin nawa ya shiga kunnenki dole zargi xai darsu a ranki,tunda zargi ya darsu kuma dole kici gaba da rayuwa damu harmu cimma gaci" tana ji tana gani aka tattarata aka kaita gidan. Cikin kwana daya tak ta dinga jinta kamar cikin maqabarta take rayuwa,gunji da buge buge hadi da fashe fashen da takanji duk bayan wasu lokuta daga dakin anty sãahar din yana mugun dugunzuma mata hankali tare da daga mata hankali,kamar afifa,itama a jikinta ta dinga jin cewa tabbas sãahar ba zata haukace ba,Allah bazai taba barin mace me kyakkyawar zuciya irinta ta samu tawaya da naqasa irin wannan ba,idan tace ga sau nawa tayi kuka a kwana biyun nan saboda tsananin tausayin sãahar to tayi qarya,cikin dare bata iya bacci,har cikin ruhinta takejin tashin hankali da kuma damuwa da yanayin da sãahar din take ciki,don haka ta dinga shimfida abun sallah tana miqawa ubangiji kokenta akan ya kubutar da sãahar din daga dukkan kaidi da sharrinsu. (Ita kyakkyawar mu'amala da kuma kyakkyawar dabi'a yado takeyi,a yayin daka shiga tsanani,sai dukkan wanda yake tare da kai ko kuma ya sanka sai ya shiga damuwa me tsanani,wanda bai sanka bama sani na haqiqa labarinka yakeji,sai shina zuciyarsa ta shiga tayaka damuwa da kuma alhini,wannan duka sirrin kyakkyawar zuciya da kyakkyawar mu'amala ce,wannan soyayyar daga ubangiji take,a yayin da ya soka saboda nagartarka,sai ya sanya wannan soyayyar taka a zuciyar dukka bayinsa,suyita qaunarka ba tare da kun hada komai dasu ba,wasu ma baka taba yi musu wani abu na kyautatawa da zasu iya nunawa duniya ba,amma dai kawai suna jin labarinka,sai suji soyayyarka ta shiga ruhinsu,ya Allah,kayi mana baiwa da tsarkin zuciya da kuma kyakkyawar mu'amala 👏🏽 da daukacin bayinka) *_RANA BATA ƘARYA_* Inji bahaushe,tunda ya samu labarin a gobe ne ake sakaran isowar jirgin KABO AIR da mahajjatan da suka hada da iyalan Dr mamman girema adam ya kasa zaune ya kasa tsaye,a ranar sãahar taga izaya nau'i daban daban,wata allura data sake birkitata akayi mata,tun safe bata farka ba sai yamma liqis,babu azahar ba la'asar,abinda yafi komai qona mata rai. Tana yunqurin tashi yana sanya muqulli ya bude qofar dakin,idanuwansa da suka canza launi suka kuma zuzzurma saboda bala'in da yakeji rayuwarsa tana ciki ya zuba mata,ya tako ya tsaya a kanta,sai kuma ya kalli agogon hannunsa,ya girgiza kai da sauri "Nafison allurar da tafi wannan qarfi" ya fadi kansa tsaye,saboda ba tun yau ba,baya shakkar fadin dukka wani shiri nasa a kanta,ta dade da gama haddace koshi waye,ainihin tarihin rayuwarsa da komai nasa da yadda ya shirya faruwar komai kawo yau. Stool ya jawo zuwa gabanta ya zauna,sai ta miqe taja baya da sauri,duk sanda ya zauna gab da ita tana jin kamar ta cinnawa kanta wuta ne saboda tsabar tsanar data yi masa,duk ranar kuma da yayi kwanciyar aure da ita,ikon Allah ne kawai yake sanyata taci gaba da rayuwa. Takanji zuciyarta ta wani irin kumbura kamar zata buga,saidai bakinta baya rabo da kiran sunayen Allah,ta haka kadai take samun sassauci. Wani mugun murmushi ya saka ganin yadda taja baya "Kwantar da hankalinki,yau da gobe bana neman komai daga guriki,so nake sai sha'awata ta taru nayi miki wankin babban bargo,ta yadda tafiyama zata gagareki,da haka sai na sake lanqayawa aljanunki nace sun fara ma kwanciya dake,hanya mafi sauqi da zan rattabamiki sakinki uku qwarara bayan na karbe jakata daga gurinki" maganganun nasa sune abinda suka sake fusata qwarai da gaske,karon farko data saki murmushi ta zauna sosai tana kallonsa. "indai har yanzu wannan jakar tana cikin mafarkinka,ba shakka ba zaka gushe ba cikin buri da fata har qarshen rayuwarka,kayimin duk iya sharrin da zaka yimin,ka laqabamin dukka ciwon dakaga dama,kayimin dukka iya muguntar da kake jin ka iya,amma karka manta,Alla baya bacci,kuma baya barin zalunci,kuma alqawarin ne yayi rantsuwa sai ya taimaki wanda aka zalunta,bani da baqinciki koda ta sanadinka na mutu,amma ina me sake jaddada maka,daukan fansa daga ubangiji tana nan tafe zuwa kanka,a kusa ko a nesa" dariya sosai ya saki,ya dawo gabanta ya tsugunna "Waya gaya miki inason ki mutu?,kuma ma a hannuna?,har yanzu ina sonki,ina qaunarki,kodon wannan kyakkyawar surar taki da bata gushewa,bin qwaqwafinki da bincikenki ya sanya kika tono wuqar yanka kanki,idan da ace baki zurfafa bincike ba,cikin biyu za'a yi daya,ko muci gaba da rayuwarmu a gefe ina tawa irin rayuwar dana zabawa kaina na kuma saba da ita,ko ki tashi dare daya ki nemeni ki rasa,amma zaki ci karo da takardar sakinki,salin alin koma gaban iyayenki ba tare da kin cutu da komai ba illa dukiyar kawai da zan kwashe,dukiya kuwa ana iya maida madadinta" kamar yau ta fara ganinsa haka ta zuba masa ido,ta karanci cewa yayi wani mugun nisan nisan da ko kira baya ji,tana zaune a nan idanunta suka fara lumshewa,ya miqe ya tsallaketa ya fice abinsa. *_W A S H E G A R I_* Tun daga airport su da motocin da suka daukosu basu saukesu ako ina ba sai gidan sãahar din,tun kan hanya afifa ta fara kuka tana jin tsinkewar gaba da tashin hankalin yadda zata riski 'yar uwarta,hakanan maama daurewa kawai takeyi. Iya su yasu ne,yayyenta maza dukkansu sun wuce Egypt suna laluben asibitin da za'a kawota ayi mata magani,don sunce ba zasu iya dawowa su ganta a haka ba. Mutum biyar ne a falon nasa,malamin bogin da yake kira da sheik usama,sai almajiran daya hayo guda hudu,bude da qur'ani suka karantawa,shi kuma da baisan ko bihim ba yana zaune a qasa,ya tanqwashe qafa yana faman can tasbaharsa me dubu. Shine ya fara miqewa da sauri sanda su maama ke shigowa falon ya daga musu hannu alamun suyi shuru. Page 51 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 51 "Mahalan,mahalan(ku kwantar da hankali)" ya fadi da sigar lallashi "Aiki mukeyi,kuma kukanku zai iya bada matsala,ayi haquri da qaddarar Allah,mijinta yana bakin qoqarinsa qwarai da gaske,kuma ko yanzu ma an fara ganin nasara,son ba ko yaushe suka sakata surutan da bige bige ba". A nan suka zauna cikin matsanancin halin kuka da jimami,shi kansa gidan gaba daya ya sauya yayi wani iri,dama raihanatu tana bakin qoqarin tsaftaceshi da kula dashi,ita kanta tana zaune rakube daga gefe,tausayin iyalin duka ya kamata ganin tashin hankalin da suka shiga da cutar bogin da aka laqabawa matar da bataji ba bata gani ba. "Ko zan iya ganinta?" Maama ta fada cikin zallar alhini da tashin hankali. Kallon juna adam da malam usama sukayi,sai ya maida dubansa ga maaman "Bako yaushe ake shiga gurinta ba,saboda hakan yana sakata yunqurin guduwa,da kuma surutai marasa kan gado,amma yanzu barin na fara shiga nayi mata wasu addu'o'i,yadda ba zata cutar da ku ba koda kun shiga din" ya fadi hakanne saboda allurar da aka danqara mata sunason ta fara aiki,jikinta ya saki gaba daya,yadda ko magana ba zata iya dasu ba barw ta fadi wani abun da zata shanshano ainihin batun. Lokacin da ya shiga dakin ya isketa allurar ta fara mata aiki,ya hadiyi wani yawu muqut yana qare mata kallo,kullum yaga yarinyar sai ransa ya biya,tana da wani mugun kyau da kyakkyawar suffa,Allah Allah yake wataran ya samu dama kamar hakan nan sanda bata da sauran qarfi shima yadan dandanata,ya rage qishirwar dake ransa,baisan ma wanne irin rashin rabo bane ya sanya adam din yake mata wannan izayar,shikam inda shine ya mallaki zuqeqiyar mace irin wannan,baisan wanne asarar bace zata sakashi yayi sakacin da zai rasata ba,ai shi kam zai iya cewa ma Allah ya sallameshi a duniya dai. Kamar masu cutar rashin kuzari haka suka shigo dakin,su hudu ciki harda afifa da maama,gaba daya dakin a hautsine yake da fasassun abubuwa,wanda duka setup ne. Wani irin kuka afifa ta saki,ta kuma durfafi sãahar a gigice ganin yadda gaba daya ta koma zararriya sak,dakatar da ita malam usama ke shirin yi yana fadin "Subhanallahi,karki qarasa gareta,na samu nayi musu addu'o'in kashe jiki,karki zaburar dasu" saidai kafin ma ya qarasa bayaninsa tuni ta isa. Rungume sãahar din tayi cikin jikinta,dumin afifan yana ratsata ta sauke wata iriyar qaqqarfar ajiyar zuciya,ta lumshe idanunta da suka kasa sauka daga fuskar maama dinta,tanason koda motsa labbanta ne ta fadi kalmar da maama zata fahimci diyarta lafiya lau take amma ta kasa furta komai. Irin kukan da suka wuni sunayi zai baiwa dukkan me imani tausayi,don ko raihanatu haka ta dinga boyewa a kitchen tana tayasu kukan, tare da jin qaqqarfar tsanar momee da shi kansa adam din,duk da kasancewarsu jininta. Abinci kuwa ba wanda ya iya sakawa cikinsa dukkansu,har zuwa dare suna zaune a gidan,daren da ya riski sãahar batasan ma me akeyi ba,tana can wata duniya ta daban da adam da likitocinsa suka kaita. Da qyar Dr mamman ya lallabasu maama da afifa suka wuce gida,da nufin gobe sa dawo. Hankalin adam ya tashi sosai jin su yaa Saifullahi suna can neman asibiti me kyau da zasu dauketa su kaita,hakan ya tabbatar masa asirinsa yana gab da tonuwa,sannan kuma yana gab da tafka asarar da gwara mutuwar sãahar a wajensa akan yayi wannan asarar ta dukiyar daya narka zuwa dollar,ga passport dinsa na yaransa dana matarsa duka a hade. Kwana maama tayi tana kuka,tana ganin abun kamar almara, innocent sãahar dinta,wadda duka duka shekarunta tsakanin ashirin ne zuwa ashirin da daya,idan tayi wuta sa biyu amma wannan mummunar qaddarar ta afka mata. A daren gaba daya afifa bata samu bacci ba itama,duk inda ta juya fuskar sãahar take gani,kamar yadda adam baiyi bacci ba shima,yanata juya yadda zai matsa sãahar din ta sallameshi salin alin,tun bata ritsa dashi ba. Wannan tunanin ya sanya washegari ya yayyaba mata maganganun da suka qona mata rai yasa kuma akayi mata allurar maaye da kyau waiko zata magantu,wannan yasa ta zabure,ta dinga fashe fashe tare da surutai a dakin saboda qarfin allurar,hakan kuma sai yayi dai dai da zuwansu afifa. Abun ya yiwa adam dadi ganin tashin hankulan dake kan fuskarsu tare da sake yarda da cewa eh lallai sãahar din ta haukace,wani irin mawuyacin yini sukayi a gidan, qwayar shinkafa babu wanda ya kaiwa cikinsa sai zallar ruwa. Sãahar na kwance daga bakin qofar dakin inda allurar ta bugar da ita daga qarshe tana jin muryoyinsu jifa jifa,wannan yasa ta yita motsa bakinta tana magana dasu,amma babu me jinta kasancewar sautin baya fita,taji muyar maama dinta na addu'ar Allah ya yaye mata ya bata lafiya yafi sau shurin masaki, furucin dake qonawa gami da soya mata zuciya,ya tabbata dai da gaske adam yaci galaba a kanta,ya kumma manna mata haukan dai,sannan ya sauya mata suna zuwa MAHAUKACIYA, sunzo sun taddata tana attitude na mahaukata tuburan. *_W A S H E G A R I_* *_waiwaye_* "Ina sonki.....kuma banajin zan daina sonki,saidai kin shiga hurumin daba naki ba,kin shigar gonar daba taki ba,kin tsallake iyakarki,kuma a yanzu nafi buqatar wadan nan abubuwan fiye dake,ki daukominsu ki damqamin,ke kuma na barki kici gaba da rayuwarki cikin salama" kai take girgizawa tana hawaye,wani irin mamakinsa tana jin kamar zai kasheta, kowacce rana da zata bullo zuwa faduwarta cikin shakka da kokwanto take,anya wannan din ADAM NE?,anya adam dinta ne?,anya musanyensa akayi mata ba?,ko kuma wata rundunar mugayen shaidanun aljanu ta shige jikinsa ne ta samu mafaka?,don abinda yakeyi a yanzun da ainihin wannan suffar tasa ta yanzu.......bata taba ganinta a tattare da adam dinta ba,koda kuwa cikin mafarkan bacci bare a kai ga rayuwa ta zahiri,adam din da ko quda baya qaunar ya sauka a kanta?,adam din dake kuka da idanunsa idan bata da lafiya?,adam din da yake kasa bacci saboda ta shiga damuwa?,adam din da yake kasa sukuni idan tana da buqata har sai ya adar mata?,dole ta shiga shakka.....amma kuma kullum yana qara tabbatar mata da cewa shi dinne fa,bawai kama ko musaye bane,to me yake faruwa?. "Bazan taba baka ba.....burinka bazai taba cika ba,saidai na rasa rayuwata,kayi duk abinda kaga dama" ta fada tana jin bacin rai yana taso mata,tare da wani irin qwarin gwiwar tunkarar duk nau'in kalar azaba tuggu da makircin daya shirya mata. Wani murmushi ya kuma saki yana dubanta,da wani irin kallo na qasa qasa mai cike da tarin mugunta "Ke kike jawa kanki koma meye,tunda ke muguwa ce ba zaki iya sallamamin abinda kikafi qarfinsa ba tako ina,to nima bazan sassauta miki ba har sai sanda kika gasu,kikaji cewa zaki iya sallamawa" daga haka ya miqe,ya fara fidda kayan jikinsa yana zubarwa a wajen. Idanu ta bude da kyau cikin tsananin tashin hankali tana dubansa,kada dai ace haqqinsa na aure yake shirin karba kamar yadda ya saba?,zallar rashin imanin da yake gwada mata bai sanya ya daga mata qafa ba,yakance "Har yanzu fa a sunan matata kike,ban saki igiyar ba,wannan abun dake faruwa wani issue ne na daban daya shafi interest dina da kuma naki". A duk lokaci irin wannan idan ya rabeta tana jin inama zata bude idanu taganta kwance cikin ramin qabarinta?,banda addininmu ya haramta kisan kai,naka ko na Wani,tabbas da tuni ta tsufa da kai kanta kiyama. Da gaske so yake ya kusanceta alhalin yasan cewa cikin jinin al'ada take,rashin imanin nasa qara gaba yake,dole tace rundunar shaidanun aljanu ne suka shigeshi,don lamarinsa yafi qarfin shaidani guda daya. Kansa tsaye ya nufota gadan gadan,kamar ba adam din nan da abaya a lokutta irin wanann yake sanyata taji babu ya ita cikin 'ya'ya mata ba,ya sanyata taji duk duniya babu macen da tayi sa'ar abokin rayuwa irinta ba,a yanzu ya koma mata wani tsohon annamimin ifritu mashayin jinin bil'adama da ko motsinsa bataso ji bare ya rabeta,bashi da maraba da qaton shaidani a idanuwanta. Ringing din wayarsa ya dakatar dashi daga sake tunkarota,sai ya koma cikin aljihun wandonsa da ya yasar yana lalubar wayar. Cikin hanzari ya karata a kunnensa,sai kuma yace "Ok,yanzu yanzu?,tom" ya latse wayar da sauri ya maidata,sannan ya soma mayar da kayan jikin nasa tana daga zaune tana kallonsa. Ga mamakinta sai taga yana bi yana balle button na rigarsa yana watsarwa,ya kama gaban rigar da qarfin tsiya ya ciccisge,sannan ya tsugunna ya jawo plate din tangaran din dake ajjiye gefe wanda ya kawo mata abincin da bata budawa bare ta taba,ya dagashi har abincin ya tamfatsa shi da qasa ya tarwatse,ya dauki wani yanki daga ciki ya yanki jikinsa ya kuma shashshafe maiqon a jikinsa. Sake miqewa yayi ya fara fatali da kayan dake saman madubi da duk wani abu na glass dake dakin yana cewa da matuqar daukaka murya "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,ki tsaya......ki tsaya don Allah,ya salam,karki jiwa kanki ciwo, Hasbunallahu wa ni'imal wakeel,ya hayyu ya qayyumu ya baki lafiya" yana fada hawaye na sauka a idanunsa,yana kuma ci gaba da tarwatsa dakin tare da sake hargitsashi,bayan tsaiwa da tayi tayi masa gyara na nutsuwa,waiko hakan zai sanya wani daga cikin ahalin nata su ankara da cewa akwai hankali tattare da ita. Sanqamewa tayi a zaune,tunaninta ya dinke cifff kan meye manufar adam na aikata haka?,saidai koma meye tasan halinsa,ungulu ne baya jewar banza,ba shakka akwai abinda yake shirin sake qullawa. Kafin takai ga lalubo abinda ke shirin faruwa sai ta tsinci muryoyin mutanen da a kullum take addu'ar isowarsu gareta,qila akwai wani haske da zai risketa,ya kuma zama silar fitarta daga duhu zuwa haske. Da mugun qarfi ta yunqura zata dira daga gadon,yayi caraf ya tsallako ya damqeta ya cukuikuyeta da kyau yana sake yamutsa rigata da yamutsatsen gashinta. Ya mata mugun riqon da bazata iya qwacewa ba,saboda banbancin qarfi da kuma qarancin garkuwa jiki dake tare da ita,don haka ta bude baki da zummar kiran daya daga ciki "Koda kin kirasun ma sun shigo sunanki bazai canza ba a idanunsu,sunanki mahaukaciya har yau har gobe,sai ranar da kika fanshi kanki,ni kuma zan wankeki a idon duniya" daga haka yaci gaba da qaraji da ambaton sunan Allah yana mata kyakkyawan riqo,ita kuma taci gaba da yunqurin qwacewa hawaye na gudu bisa fuskarta, kokawa ta barke a tsakaninsu duk da cewa ba wata nasara a hakan sai azabar riqon da yayi mata da takesha,dai dai sanda aka turo qofar da sauri aka shigo,ya saki wani lafiyayyen murmushi daga can qasan zuciyarsa,burinsa ya cika,plan dinsa ya tafi a dai dai,dama abinda yakeso kenan,shigen abinda ya faru jiya,yau ma sun sake samunta a mahaukaciyarta. Page 52 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 52 Afifa ce wadda ta kasa jurewa ci gaba da jin muryar sãahar din cikin wannan birkitaccen yanayin,da sassarfa ta nufo sãahar dake riqe a hannun adam da yayi wata irin wajiga,yayi hajaran majaran "Karki ce zaki tabata, qoqari nake a yanzun ma kada ta yiwa kanta illa,don ko kanta bata ganewa bare wani" "Komai girman haukan da bestie takeyi jikina ya bani ba zata taba illatani ba,saketa" afifa ta fada da wani irin zafin zuciya. Tashi zuciyar shima tazo wuya,amma dole ya sakar mata sãahar din saboda su maama dake a tsaye daga bakin qofa,can qasan ransa kuwa yana sake cika maqil da afifa din,baya qaunar mu'amalarta sam sam da sãahar,saboda ita din sãahar ba mai damuwa ko maida hankali akan abubuwa bace,tana da mugun kawaici da kuma sanyi akan abubuwa,duk da zazzafa ce ta fannin miskulanci da kima qin daukan raini wulaqanci ko qanqanci daga gurin kowa. Talau haka tayi a jikin afifa,maama ta taimaka mata suka kwantar da ita saman gadon,tanata buda baki da zummar yi musu magana,saidai kalma ko daya ta kasa fita daga bakinta,don allurar da aka shimfida mata ta fara aiki a jikinta. Shurun dakin ya dauka saboda bacci daya kwashe sãahar,afifa ta dauke dubanta daga fuskar sãahar tana jan majina saboda kukan da tasha,ta maida dubanta ga adam dake tsaye jikin qofa,gaba daya fuskarsa babu komai kwance a samanta face zallar tashin hankali "Zan samu qur'ani?" Ta tambayi adam din,sai ya daga kai da sauri "Eh,akwai,amma karki ce zakiyi karatu ne,an samu ta samu bacci ba kuma wani matsalan ya biyo baya" kai ta girgiza tana kafeshi da ido "Ba inda karanta qur'ani yake zama matsala,saidai waraka,ka daukomin" ta fada tana miqewa zuwa toilet din sãahar din don ta daura alwala. Tayi alwalar tana fitowa ta taka wani abu,sai ta tsaya taja baya da sauri tana furta "Subhanallah" ganin kwalba ce,ta sunkuya ta dauketa ta cillata a dust bin din,ta shimfida abun salla kusa da maama wadda ke zaune tun dazun,riqe da hannun sãahar,ta zuba mata ido tana mata wani irin kallon qurilla,cike da zallar tausayinta,time to time tana tofa mata addu'o'in da taketa karantawa. Sanda ta idar da sallar saita dauki qur'anin da adam ya kawo ya ajjiye ya fita,ta zauna dai dai saman kan sãahar din ta bude ta fara karantawa. Sai data shafe awanni uku cur sannan ta miqe ta sauka daga gadon,ta ajjiye qur'anin,ta sake juyawa da nufin komawa bandakin don tayi fitsari. Kamar gilmawar walqiya hasken kwalbar data yar dazu ya gifta mata,saita tsaya ta koma da baya,ta tsaya gaban sharar tana duban kwalbar wadda takewa kallon sani. Duqawa tayi ta sanya hannu ta cirota kusa da syringe din dake nuna dashi aka zuqe ruwan aka zubawa duk wanda aka sakawan ma,ta soma bin rubutun jiki tana son tantance allurar data sani din ce?. Wani irin dimuwa firgici da kuma tashin hankali ne suka shigeta farat daya,ta waro idanunta kamar zasu fado qasa,saita juya da sauri fa koma saman gadon. Gaba daya jikinta rawa yakeyi,zuciyarta na ayyana mata abubuwa kala daban daban,babban burinta a yanzu sãahar din ta farka,akwai abubuwa da alama masu tarin yawa,akwai wasu abubuwa a lullube a kima binne babu ko shakkaMaimakon karatun da taso yi,saita kasa aiwatar da komai,ta koma ta zauna saman gadon tana riqe da hannun sãahar gam kamar wadda zata bacewa ganinta,kwanyarta nason hakaito mata abinda yake faruwa da sãahar amma gaba daya tunaninta yaqi aminta da hakan. Ta jima a cikin wannan yanayin kafin taji an budo qofa. Maama ce tare da Dr mamman,dukkansu suka tsuguna a gaban gadon sãahar din,kowanne fuskarsa a narke zuciyarsu cike da rauni. Addu'a yayi mata kamar ko yaushe,sannan yace su shirya su wuce gida,duk da ya gama karantarta sam batason tafiya gidan "A nan yau zan kwana" afifa ta fada kanta tsaye,saboda zuciya da gangar jikinta suna bata abubuwa da dama da takeson tabbatar dasu,akwai qaqqarfan zargin daya shiga zuciyarta "Anya?,zaki iya?" Dr mamman girema ya fada yana kallon afifan,kafin ta bada amsa adam da yake shigowa yayi caraf da zancan cikin tashin hankalin daya bugi qirjinsa na jin cewa zata kwana da sãahar "Gaskiya abba banajin zata iya,zan iya ci gaba da kwana da ita kafin randa zamu wuce asibitin,babu abinda ta rasa,zan kuma ci gaba da kulawa,ba zata rasa komai din ba in sha Allah har zuwa lokacin da Allah zai bata lafiya" "Kana qoqari kam,mun shaida mun kuma yaba sosai,a qalla yau kaima ka kwanta kayi bacci sosai yadda ya kamata, saboda haka yau ni zan kwana da bestie in sha Allah,don na tabbatar koda nice irin hakan ta sameni,ba zata gujeni ba koda na kwana daya ne" ta fada tana sakin qwalla,don tanason karya zuciyar dr mamman ya qyaleta ta kwanan. Ta samu nasara kuwa,don dukkansu qas sukayi da kansu,yayin da maama ke share hawaye "Gaskiya ne,kaima ya kamata ka huta koda iya yaune, ubangiji yayi maka albarka bisa qoqarinka" "Ameem ya Allah abba" ga fada kansa a qasa yana murza yatsunsa,zuciyarsa na wani irin bugawa da zallar tashin hankali tare da tunanin mafita,don ba shakka zuwa nan da awa daya zuwa biyu sãahar din zata iya farkawa,farkawarta kuma dai dai yake da tonuwar asirinsa da tashin ballin dukkan wani rufaffen asirinsa. Har motarsu dr mamman ta tashi yana tsaye kamar wanda aka kafa a wajen,daga qarshe dabara ta fado masa,ya fada motarsa kai tsaye yabi bayansu ya wuce gurin likitansa. Allurar da ake mata me sanya nannauyan bacci har fiye da wadda aka saba yi mata,da kuma wadda ke sanya birkicewar kwanya ya karbo,dukkansu yasa aka sauya musu gida,tunda yasan me afifan ta karanta,harkar kafiya ne,a yanzun tana cikin matasan likitoci masu qarancin shekaru da jahar kano ke dasu,yanason yayi wasa ds hankalinta,ta kuma yiwa 'yar uwar tata da take mutuwar so take aibatashi sabods ita allurar da zata sake mata illa tako ina. Tana zaune tana karanta qur'anin ya tura qofar,ta daga kai a hankali ta qare masa nutsatsen kallo amma a fakaice,sai a yanzun ta lura da wasu abubuwa a tattare dashi,cikin son nuna kulawa ya qaraso ya ajjiye ledar hannunsa,sannan ya matsa gaban gadon ya shafi wuyan sãahar din dake baccin mutuwa,ganin bata motsa ba ya tabbatar akwai ssuran lokuta kafin allurar ta saketa "Alhamdulillah,Allah ya qara lafiya" ya fadi da sigar dake nuna damuwa da kuma kulawa. Waiwayawa yayi ya kalli afifa "Ina ganin kije kici abinci sai ki buda daya dakin ki kwanta ko?" Qaramin murmushi ta sake "Banda abinka mr Adam,ai ba hutawa nazo yi ba,jinya nazo yi,yau kaine da baccin nan,kada ka damu" tsaki yaja cikin ransa yana tsinewa afifan,yassn tunda har ra dawo dole ne aikinsa a yanzu ya hadu da qalubale masu yawa,amma idan tasan wata ai batasan wata ba,zaiji da ita "To yayi,yanzu ga alluranta nan,za'a yi mata su kafin ta farka,hakan yana taimakawa wajen farkawarta ba tare da buge buge ko surutai ba" "Okay" ta furta tana ajjiye qur'anin,ta buda ledar tana fiddo ruwan alluran hade da syringe din. Duban farko ta yiwa alluran tasan cewa ba ainihin mazubinsu suke ba,abu na biyu kenan daya qara qarfafa zarginta,ta fitar dasu kaf ta zuqe ruwan allurar a syringe,ta matso ta dora tsinin allurar saman hannun sãahar da batasan abinda akeyi ba. Page 53 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 53 Sai kuma ta daga kai ta kalli adam din dake tsaye qyam a kansu yana duban alluran "Bani tissue mana" amsawa yayi da to cikin hanzarin da baiso ta aiwatar da wani abun da zai kawo kuskure wajen yin allurar,ya ciro tissu din ya bata,ta karba ta dora a bakin tsinin allurar,ta fara zirarawa ruwan zuwa cikin tissue din data linkata,sai data qarar da ita a ciki tas sannan ta zare allurar,tayi hanzari danne tissue din a qasan cinyarta gudun kada ya fahimci jiqewar da tayi. Sanda yaga ta kammala wani dadi ne ya kamashi,ko yanzun hankalinsa ya samu ya kwanta,yaukam zaiyi bacci abinsa sosai,yasan har gobe zuwa wajejen azahar tana cikin bacci da tambele idan ma ta farka din kafin sannan,wala'alla ma ya gayyato wata cikin 'yammatansa idan kowa yayi bacci ta tayashi debe kewa,da wannan tabbacin gaibun daya samu ya fita a dakin abinsa hankali kwance. Kwanciyar hankalin da afifan ta gani a fuskarsa sanda yake fita din ta sake dasa qaqqarfan zargi a ranta,sai ta bude alqur'anin cikin nutsuwa ta fara karantawa da madaidaicin sauti me cike da nutsuwa. Kusan awa guda cur ta shafe a hakan,a hankali taji wani sassanyan hannu ya dafa hannunta dake saman qur'anin,kafin ta daga kai taji ta kira sunanta da wata iriyar siriryar galabaitacciyar murya "Bestie,kema wai kin yarda ni din mahaukaciya ce?,na haukace?" Wasu irin birkitattun hawaye ne suka shiga silalowa afifa,banda ta sanya hannunta ta toshe bakinta da kuka mai qarfi zata barke dashi,hannunta na saman bakinta tana girgiza kai,sai kawai ta rungume sãahar din a jikinta tana sakin kukan data boye sautinsa "Bazan taba yarda ba bestie,koda ma da gaske ne ina qaunarki a hakan" kuka dukkansu suka saki rurus,suka dinga rerashi babu wani me rarrashin wani,har tsahon wani lokaci kafin afifa da idanunta sukayi jazur ta magantu "Bestie,wanne irin mummunan abune kika yiwa adam ya yanke hukuncin mai dake haka?" Ido ta lumshe ragowar hawayen dake maqale a idanunta masu zafi suka gangaro,tabba inda ace ruwan hawaye yana qarewa da tuni nata ya jima da qarewa "Wannan damuwar da kika tafi kika barni a cikinta,wadda nayi alqawarin gaya miki ita,ashe itace zata zaftaro bisa kaina,tayi shirin kaini lahira koda ban shirya ba" a nutse ta rattabawa afifan komai. Wani mugun birkicewa afifan tayi,ta miqe zata sauka a gadon da zafi zafinta, fuskarta gaba daya ta sauya kamanni. Da sauri sãahar ta cafko hannunta,don tasan halinta sarai komai ma zata iyayi "Ina zaki?" "Adam din zanje na samu ayita ta qare,tsinanne matsiyaci dan wuta" girgiza kai ta hauyi da sauri "Tunkarar adam a irin wannan yanayin abune me hatsarin gaske,idan baka iya kama barawo ba sai shi barawon ya kamaka,sai kinbi ta takatsantsan da hikima sosai kafin ya zamana mai laifi red handed,baki tsoron kema yace dalilin kwanan da kikayi kin shafi aljanuna ko ciwon haukata?" Sanyaya jikinta yayi,lallai a yadda idanun adam suka rufe babu abinda bazai iya aikatawa ba,yadda ya matsu da jakar koma meye akace zaiyi zaiyi din,saita koma ta zauna tana ci gaba da kukanta,zuciyarta kuma ta zurafafa da tunanin daukan fansa. Da qyar suka lallashi juna,ta kama sãahar da jikinta sam ba qwari ta rakata toilet,ta daura alwala tazo ta rama sallolin da ake binta,afifa na gefe tana kallonta tana kuka, sãahar din da bata wasa da sallah?,duk tsanani duk rintsi bata yarda lokacin sallah ya wuceta ba ba tare da ta yita akan lokacinta ba. Abincin da raihanatu ta bayar adam ya shigo dashi tun dazu ta buda,ta saka sãahar din a gaba akan sai taci,da qyar tayi cokali biyar,saboda cikinta ya sake wani mugun tsukewa,baya iya daukan abincin sam me yawa,dama kuma tun asali na gwanar abincin bace. Daga ita har sãahar ba wanda ya rintsa a daren,sãahar din nata bat labarin irin azabobin da adam ya gana mata,tayi kuka tayi kuka har ta bawa uku lada,a daren ta gama shirya yadda komai zai tafi,tsarin kuma ya yiwa sãahar din itama. Washegari da adam din daya kwana da wata macen suna holewa kan gadon aurensa ya shigo ko a fuska bata nuna masa komai ba,saima zallar tsoron kwana da sãahar din data nuna masa ta dinga ji. Murmushin jin dadi da samun cikakkiyar nasara ya saki yana sauke dubansa ga sãahar daje kwance shame shame kamar dai yadda take a jiya,a yanzun sauran tsoronsa ya kau,abinda ya rage masa ya sake matsa qaimi kawai ta bashi jakarsa kafin yayyenta su iso su wuce da ita wani banzan asibiti. Afifa ce dama tsoronsa,yasan halinta tsafff, za'a iya fuskantar matsala ta sanadinta,amma a yadda yaga tayi firgai firgai ta kuma ce a jiyan batayi bacci ba,alamu sun nuna ba zata iya sake kwana ba(baizan qarfin aminci da soyayyar dake tsakaninsu ta ginu sosai bisa tubalin Allah da ma'aiki ba,ba abota irin ta wannan zamanin ba,iya fatar baki). Ilai kuwa yadda ya zata hakance ta afku,afifa ta hada kayanta tayi musu sallama bayan ta gama tsara komai ta fice a motarta. Ba gida ta wuce ba,can cikin kasuwar qofar ruwa ta zarce,ta kuma sauka kai tsaye gurin mutumin da yafi kowa qwarewa wajen yanka muqullin da zai dace da kowacce qofa, cikin lokaci qanqani aka gama yanka mata saboda kudin data zuba ta biya,ta karba ta dawo gida,ta hada wasu kaya ta baiwa maama dake shirin tafiya gidan,tace ta ajiiye mata dakin sãahar din gobe zata koma ta sake kwana da ita "Kada ta barnatar miki fa" hawaye ne suka ciko idanun afifan,mutum da hankalinsa amma ya sanya kowa yana mata kallon tabbabiya "Ba zata taba ba in sha Allah" shuru maaman tayi tana juya kayan "Na rasa abinda yasa har yanzu naqi ji a jikina sãahar ta samu tabin qwaqwalwa,jiya muna hanya da abbanku dana fada yace shaidan keson yimin wasa da imani na,na yarda da qaddara ne kyau ko akasinta" "In sha Allah nan kusa bestie zata dawo cikinmu muci gaba da rayuwa kamar kowa" abinda afifa ta fada kawai kenan tana sharce hawayen fuskarta. Fitar maama daga gidan ya baiwa afifa damar shiga dakinta ta dauke jakar ta canza mata muhalli,saboda gudun abinda zaije yazo,ta gama sarawa girman sharrin adam,tasan bazai taba rasa kawowa a ransa jakar na gidan ba,zai kuma ya tsara komai da zai sanya a aminta dashi a damqa masa ita. Kuka sosai ta zauna tana yi sanda ta gama qarewa kayan dake cikin jakar kallo,burinta kawai taga ta watsawa passport din wuta da sauran takardun,to amma suna buqatar evidence,don haka tayi haquri ta tattarasu ta kaisu cikin motarta. Kamar ko yaushe bayan kowa ya tafi yaja qofar ya kulleta,don ba kwana dakin yakeyi ba sai idan yana da buqata. Cikin sanda ta bude kayan da maama ta ajjiye cikin drower dinta,wanda tunda ta shigo dasu take ankare dasu tare da fatan kada hankalin adam yakai kai. Ta warware kayan a nutse ta ciro muqullin ta maidasu gurinsu,ta duba daya bangaren kayan nata ta ciro hijabi ta sakawa jikinta, sannan ta fara takawa cikin sanda da takatsantsan,qirjinta yana wani irin bugawa,bakinta dauke da tarin addu'ar samun nasarar ficewa daga gidan ba tare da kowa ya ganta ba,tana takawa iska na yawo da ita saboda jimawa da tayi rabon da tayi doguwar tafiya,ga ciwo da uban allurai rashin cin abinci da uban tashin hankalin da yasa ta zabge ta rame. Cikin nasara ta bude qofar dakin da muqullin,ta budeta a hankali ta fara takowa ta falon,motsi taji me qarfi daga bayanta,abinda ya kada hantar cikinta kenan ta waiwaya da sauri har tana shirin kaiwa qasa saboda tsananin razana. P Page 54 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 54 Raihanatu ta gani a tsaye,itama jikinta rawa yakeyi,plate din data debo suna shirin watsewa a hannunta. Bud baki sãahar tayi zatayi magana raihanatu tayi saurin dora yatsanta saman labbanta alamun sãahar din tayi shuru,sai ta maida plates din saman dining,ta sauko da mugun hanzari cikin wani taku na sand'a,ta qaraso inda sãahar ke tsaye ta finciki hannunta da mugun sauri ta bude mata qofar parlor din suka fice. Tsakanin baranda da farfajiyar gidan suka ja cak suka tsaya,dukkansu kowa yana maida numfashi,qirjinsu yana wani irin dagawa "Mai gadi.....yana nan anty,bari na dauk....ke masa hankali" bata tsaya jin ta bakin sãahar din ba ta lallaba tabi ta cikin flowers din ta zagaya bayan dakin me gadin. Dutse ta samu me dan girma ta jefa ta saman roofing din ya bada sauti qwaalll,sautin da ya dan ja hankalinsa,sai yayi tsaki yaci gaba da abinda yakeyi. Sake daukan wasu dutsunan har biyu tayi ta sake jefawa,ya sauka kuwa a tare,sai ya fusata ya miqe don ya zagaya ya duba daga ina jifan yake,kafin ya qaraso tuni ta fita ta koma wajen sãahar,ta sake jan hannunta gudu gudu sauri sauri,ta bude mata qofar gate din tana magana cikin ruwan hawaye "Jeki anty,Allah zai dafa miki,ubangiji yayi miki sakayya,duk da ban gama sanin kan komai ba amma zuciyata da gangar jikina sun gama gayamin me yake faruwa,ko yanzun yana dakinki da wata,ko iya wannan sakayyar Allah ne kadai zaiyita" tana gama fada ta maida qofar cikin matuqar takatsantsan ta rufeta ta koma cikin da sauri ba tare data bari me gadin ya ganta ba. Bibbiyu ta dinga gani cikin qwayar idanunta,jiri sosai ya dinga dibanta ta fara hada hanya. Da hanzari afifa dake zaune tana jiranta tsahon sa'a guda ta buda murfin motar ta fito da mugun sauri,ta tarbeta a hanya ta riqeta qam ta sanyata cikin motar,dai dai lokacin da numfashinta ya fara sauyawa,alamu suka fara nuna tana neman suma ne,wanann ya saka afifa tayar da motar da mugun gudu suka bar layin. A lokacin babu wanda ta gayawa abinda ke faruwa,saboda bataso a sani din,don taci alwashin saita wujijjiga rayuwar adam din. A yanzun da sãahar ta sume mata dole ta nemi taimakon wani. Kai tsaye anty farheen ta kira,ta gaya mata asibitin da take tace tazo yanzu don Allah "Wa kikai wannan asibitin me nisa?,duk hospitals din da muke zuwa na kusa damu" "Ba lokaci anty don Allah ki qaraso yanzu,its urgent" "Ba laifi,gani nan" ta fadi maganar tana ajjiye wayar. Muhyiddeen baya nan already,don haka ta barwa masi aikinta duka yaran,ta tayar da driver suka fito daga gidan cikin motarta. Ba qaramin razana tayi ba lokacin da afifa ta gama zayyane mata komai,kuka sosai ta saki ita kanta anty farheen tana tsinewa adam din "Dole mu dauki mummunan matakin shari'a a kansa,tabbas baici bulus ba" kai afifa ta girgiza "A'ah anty,mubi komai a sannu kamar yadda sãahar ta shawarta,ni kaina yanzun tsoro yake bani,kaidinsa ya wuce tunaninmu,duk yadda nakai ga tsanarsa da qin jininsa......ban taba kawowa zai iya aikata haka ba,so sai mun iya takunmu,tsaf zai iya wanke kansa a wajen iyayenmu maza da 'yan uwanmu,bari kiji plans dina" a nutse ta warwarewa farheen shirinta,shirin ya yiwa farheen din sosai,kuma itace hanya guda daya da zata iya sanyawa adam ya tona asirin kansa da kansa. Anty farheen bata bar asibitin ba sai kusan qarfe daya saura na dare,tace gobe zata dawo asibitin secretly ta kawo musu breakfast,don so samu a gobe ta maida sãahar gidanta aci gaba da yi mata treatment a can,don batason rashin ganin gilmawar afifa ya sanya adam ko wani cikin 'yan gida ya fahimci akwai wani abu,basason hakan ya kasance,har sai zuwa sanda suka tsara faruwar hakan. ^^^^^^Sam adam bai waiwayi dakin sãahar ba tun bayan tafiyar afifa,duk da yasan afifan a yau ta tafi gida,sai ya tattare shi da karuwarsa suka qule dakinsa sukaci karensu babu babbaka. Kwata kwata bai doshi dakin ba sai bayan sallar asuba,ya miqe yana jiri saboda buguwar da yayi a daren jiya,da kuma masha'ar daya aikata son ransa. Zama yayi a bakin gadon yana jiran fitowarta,amma sai yaji shuru,don haka ya miqe ya nufi bandakin yana zage zage "Na kusa kawo qarshen matsalata,tsaf zan iya hallakaki muddin kikace zakici gaba da boyemin jakata,ke kiyi asarry rayuwarki ni nayi asarar dukiyata" wata muguwar razana yayi lokacin da yaga bandakin wayam,ya fidda idanunsa waje kamar yana shirin zurarosu qas,ya waiwaya da sauri yana tuna cewa lokacin da yazo shiga dakin baifa budeshi da maqulli ba,yana turashi yaga ya bude,a zabure ya fito yana kwarara ihu kamar hauka sabon kamu,yayo falo yana qwalawa rahinatu kira. Tunda ta idar da sallar asuba take zaune tana zaman tsammanin jiran jin makamancin wannan kiran,sai da tayi addu'ar neman samun tallafin nutsuwa daga ubangiji ta shafa sannan ta fito,a sannan har ya gagara zaman jiranta ya bankado qofar dakin,kadan ya rage ta daki fuskarta "Ina sãahar take?" Ya tambayeta cikin tsawa "Tana dakinta yaya" ta amsa masa a nutse,kamar da gaske batasan komai ba,ido ya zaro waje "Tana dakinta zanzo ina tambayarki inda take don ubanki?" Cikin nuna zallar mamaki tace "Bata dakinta kuma yaaya?,to ina ta tafi?, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" duk sai ta nuna rudewarta a fili "Ni tunda ka shigo kacemin na wuce dakina,kada ka sake ganin gilmawata ai ban sake fitowa ba yaaya sai yanzu daka kirani" yadda yaga ta rude shine ya sake gigitashi ya kuma rudashi,ya saki qofar da sauri yana barin wajen hadi da kama gashin kanshi da hannunsa bibbiyu kamar wanda yasha cocaine ya bugu da kyau,haka ya dinga zirga zirga kafin ya afka dakinsa. Tana nan tsaye taji hayaniyarsu shi da kilakin tasa,kafin zuwa wani lokaci taji yana jibgarta,ba jimawa sai gata ya jawota kiiiii zuwa falon gidan da wasu gantalallun kayan bacci da basu da maraba da tsirara "Tsinanniya mitsiyaciya,ke kika jawomin,saida na gaya miki kada ki bani abun bugarwa,a situation din da nake ciki bani da buqatar sa amma saida kika bani,yanzu kina shirin jazamin masifar da tafi kowacce girma,fita ki barmin gida" haka ya korata ko kayan jikinta bai bari ta canza ba. Dawowa yayi yaci gaba da yin safa da marwar cikin tashin hankali "Ya akayi ta fita daga dakin dana kulleta?,ina ta tafi?" Tambayoyin daya dinga yiwa kansa daya gama cakewa kenan,sai ya juya a gurguje ya durfafi me gadi yana tuhumarsa,saidai ya tabbatar masa yau din banda afifa data fita a gaban idanunsu dukka ba wanda ya sake fita daga gidan. Qaramin hauka ya dinga yi tuburan, raihanatu na maqale tana hawaye,gami da janjantawa kanta game da muhallin da rayuwa ta jefota,dangin uwa marasa saiti,marasa imani jahilai masu shegen son kansu da kwadayin abun duniya fiye da komai. Sanda ya kirata yace itama ta fito tabar gidan yana auna mata zagi,hakan dadi yayi mata,don duka tsoro ya kamta,ganin gidan ba kowa sai ita dashi yanata kuma wani abu kamar me tabin hankali,don haka a gurguje ta zira slippers dinta bata ma tsaya daukan komai nata ba ta qara gaba. *_BAYAN AWA UKU_* Mutum takwas ne cikin falon,ciki harda afifa maama da dr mamman sai yaa muhyi da yaa Saifullahi,wanda ba wanda yasan da zuwansu a yau din,sai kuma gashi sunzo sun tarar da tashin hankalin rasa sãahar. A falon saika rasa tantance waye yafi wani shiga tashin hankali?,maama Kuka kawai takeyi wiwiwi wanda yake taba ran afifa,yakeson kuma ya karyar mata da gwiwarta. Duk bayan mintuna saita saci kallon adam da yake shirin zaucewa,ya kasa zama ya kasa tsaiwa,sai kai kawo kawai da yakeyi yana kiran sunan Allah,ta sake sarewa,ta kuma sake jin tsoron kaidin mutum,lallai dan adam me buhun sharri ne,ba wanda bai tausayawa adam din ba a falon yanayin da suka ga ya shiga,ba tare da sanij cewa shine ummul aba'isin faruwar komai ba Zaman da sukeyi a yanzu na zaman jiran tsammani ne,bayan sun bada report na batanta a kafafen yada labarai da kuma police station guri guri. "kayi haquri adam,in sha Allah za'a ganta cikin aminci" abba ya fada cikin son qarfafawa adam din gwiwa,duk sa cewa shi dinma bawai yana da qwarin gwiwar bane "Abba bansan ya akayi ta fita ba,ina ta tafi?, innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya fada da madaukakiyar murya,kai afifa ta kawar ta tabe baki,tabbas bawai yana cikin tashin hankali bane saboda batan sãahar,yana cikin tashin hankali ne kawai saboda jakarsa. Wuni sukayi ranar a haka,har zuwa dare,ba wani labari ko alamun samun sãahar. Ta fannin afifa duk da tanason komawa gidan yaa muhyi su kwana da sãahar din wadda tuni anty farheen ta samo likita ya fara bata kulawa ta musamman,to amma zamanta tare da maama dake cikin tashin hankali yana da matuqar amfani,tunda tasan ko ba komai zata debe mata kewa ta kuma kwantar mata da hankali,don haka ta bita gida,amma tana tuntubar anty farheen akan duk yanayin da ake ciki,ta shaida mata tana samun sauqi da kuma kyakkyawar kulawa. Lokaci lokaci take satar jiki taje taga sãahar din. Sosai sãahar din ke murmurewa tana sake samun lafiya,saboda kulawa ta musamman da anty farheen din take bata,duk da cewa sãahar din bata da aiki sai koke koke,saboda matuqar dimuwa da kaduwa ta shigeshi akan abinda adam yayi mata,gaba daya so take ta zama depressed,amma dagewar anty farheen da jajircewarta yanata aiki a kanta,baji ba gani haka take bata kulawa da shawarwari "Um um ummin abba,baki godewa Allah ba kenan?,baki godewa ni'imarsa ba?,ya kubuto dake daga sharrin da bakisan iya zurfinsa ba?,da yawan koke koke zaki sakawa ubangijinki?" "Dole nayi kuka anty,ashe dama haka maza suke?,dama masoyi yana iya komawa maqiyi mafi ban tsoro me muni?,ashe su din basusan halacci ba?,basusan soyayya ta ainihi ba?,basusan tausayi imani da jin qai ba?,ashe adam zai iya yimin haka anty?,me yayi saura kuma a duniya?,tunda har adam zaiyi haka,wanne masoyi ne bazai iya cin amanar masoyi ba?" A lokacin dukka bayanin da zata yi mata bazaiyi amfani ko tasiri ba,don haka sai kawai taci gaba da lallashinta cikin hikima da kwantar da kai. KOMAI NISAN JIFA Bayan zamun tabbacin warwarewar sãahar,suka tabbatar ta dawo cikin hayyaci da nutsuwarta,da taimakin likitansu dake duba mafi akasadin matsalar data shafi familyn gaba daya. Ba abinda afifa ta boyewa Dr usman,ta kuma nemi taimakonsa ya zama jagora wajen zama MABUDIN tonuwar asirin adam,ba tare da jinkiri ba ya amince,don shi kansa al'amarin yayi masifar tsimashi tare da tayar masa da hankali matuqa da gaske. Tun cikin satin ta tayar da maganar zuwa duba filaye da kadarorin sãahar,tace "Ya zaid,ya kamata a duba,kasan mutane babu amana, qilan wasu suji labarin batanta suje suyi rub da ciki a kai" zaid din ya gamsu da zancanta,yace zai samu lokaci yaje ya dudduba din. Lokuta lokuta sukanje gidan,basu barshi hakanan ba,kamar ko wanne lokaci,yau ma sun je gidan kusan su dukansu,banda zaid da yace zai fara wucewa duba filayen sãahar din,abinda yayi matuqar yiwa afifa dadi,ta dinga kallon adam da yaketa mazari irin na rashin gaskiya a tsakaninsu,tana jiran jin dawowar zaid. Maama na tsaka da jajensa kan ya dade ya iso gidan,cikin wani irin yanayi daya tabbatarwa afifa boom din data dana ya soma tashi "Lafiya?" Maama ta tambayeshi "Akwai matsala maama,lokacin dana isa na fara da duba filayenta daka bakin titi,amma ga mamakina kusan fiye da rabinsu an tada gini a cikinsu harma anyi nisa,ko dana zauna na fara bibiyar lamarin,na nemi haduwa da ainihin masu filin,na samu ganin mutum uku a ciki,don suna gurin suna duba aikin da akeyi musu,kuma dukkansu sun shaida min siyan fili sukayi,kowanne kuma ya nunamin takardar shaidar mallakar filin original copy" wani irin sauti cikin adam din ya bayar,wanne irin sabuwar masifa ce kuma take shirin afko masa bayan yana tsakiyar wannan dumu dumu bai gama fita daga cikinta ba?,dakiya da qarfin hali ya aro,cikin nuna bacin rai gami da mamaki yace "Kai,wanne irin rainin wayau ne wannan?,me yasa mutane masu da kirki basu da imani?,daga batan baiwar Allahn sai kawai su hau gine mata filaye?" "Basu x laifi,kuma suna da gaskiya,don kowanne ya shaidamin a hannun mijinta ya samu damar mallakar filin,ya tabbatar musu kuma babu wata matsala" ai baisan sanda ya miqe ba,ya soma fada yana yarfa hannu,sam ya manta a gaban su waye yake "A gidan ubanwa suka sanni?,ni zasu yiwa sharri saboda sunga Allah ya rufamin asiri?,muna zaman lafiya da soyayya da matata?,ko su waye wlh bazan qyalesu ba,tabbas saina kaisu qara kotu" relaxing ya zaid yayi yana qare masa kallo "Ka kwantar ds hankalinka,ko nima bazan qyalesu ba sai nayi shari'a dasu,so shi yasa a gobe na yanke hadaku ku duka acire me gaskiya da mara gaskiya,tun kafin ta ritsa da wanda baida laifin komai" mummunar faduwa gabansa yayi,amma ya maze '"hakan yayi,ko baka hadamu ba ni zan nemesu,na kuma nemi fansar batamin suna da sukeso suyi" sai yaci gaba da fada,ya kasa shuru hakanan ya kasa nutsuwa ya zauna guri guda. Daren ranar bacci barawo duk qwarewarsa bai iya satarsa ba,ya dauki wayarsa ya kira momee ya zayyane mata komai "Kada ka wani damu,kuje din,iyaka ka murje idonka kace baka sansu ba,zanma shigo gidan goben saboda ka samu supporting " akan hakan suka samu matsaya,saidai abinda basu sani ba,tuni afifa ta gama nata shirin na goben,don ko da suka tashi zuwa,tare da Dr suka taho,bisa shawarar adam din ya bada report na duka lalurar sãahar din ya duba da kyau. Tace hakan yana da kyau,idan da yiwuwar suyi attaching nasa cikin cigiyar neman sãahar da akeyi,qila wannan ya sauqaqe samunta da wuri. Page 55 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 55 A nutse ya zauna a falon gidan yana duba report din qarya da Dr din bogin da adam yayi hiring ya hada,ga duk qwararren likita yana kallon abun zai fahimci an tsarashi ne kawai,saboda babu gaba babu baya,bayanan babu wani cikakken abun kamawa. Nannauyar ajiyar zuiciya ya sauke,wannan mutumin bayan qwarewa da yayi wajen hada plan,harda sa'a ma daya taka cikin al'amarinsa,ko kuma qaddarar da bahaushe yakewa take da bata wuce rana da lokacinta,saboda ya duba ya dubo,family irin na dr mamman girema,ba abu bane me sauqi kayi musu irin wannan abu lokaci guda hankalinsu bai kai kai ba,duk da akwai tasirin boko sosai a tattare dasu,amma suna da ilimin addini a tattare dasu. Daga qarshe ya rufe file din yana sauke ajiyar zuciya,lallai banda ma wannan......sun bashi amana qwarai,ta yadda tunaninsu bai taba kawo musu wai adam din zai aikata wani abu makamancin wannan ba. A nutse likitan ya maida dubansa ga momee dinsa data iso tanata kumfar baki akan case din filayen,tana ta fada akan duk wanda ya murqushe dukiyar,ya kuma bi d'anta da sharri bazasu qyale ba. Duba daya yayi mata ya karanci 'yar bariki ce tsantsa,amma dattako da karamci irin na iyalan dr mamman girema yasa basu taba nuna mata komai ba face zallar karamci da mutuntawa. Afifa dake dakin sãahar tana tattaro dukka kwalaben alluran da aka dinga juyewa gangar jikin 'yar uwartata,tana jiyo dukka kumfar bakin momee,tun ranar tasan cewa komai da hadin bakinta ake aikatashi,tsanar da take wa matar ta sake ninkuwa cikin ranta. Qoqarin dauke hankalinta tayi akan maganganun amma kuma ta kasa,bala'i biyu ne ya hade mata,na farko qarfin alluran da aka dinga dibgawa sãahar din,wanda tasan banda ikon Allah,babu abinda zai hana kwanyarta juyewa,na biyu kuma yadda momee din ke magana kamar mutuniyar arziqi,wannan yasa ta miqe a fusace,ta daga inda ta yiwa jakar ajiya ta musamman ta cirota ta kuma fito daga dakin da wani irin hanzari,tana huci kamar ta hadiyi kunama. Yadda ta buda qofar da qarfi har tana dukan bango ya dawo da hankalin dukka mutumin dake falon kanta,yaa zaid yana shirin tambayarta lafiya?,saita miqa kwalaben ga likitan "Dr,dubamin wadan nan kwalaben,allurar meye?" Hannu biyu yasa ya karba ya fara dubasu daya bayan daya. Wani gumi ne ya yanko masa shima,ya daga kansa ya zubawa adam idanu. Tun baice komai ba ilahirin jikin adam din ya dauki rawa,ko kadan baisan da zaman kwalaben ba a dakin,yasan duk sanda akayi allurar indai ya tuna zai kwashesu ya fita dasu,to waye ya tarasu?,ba shakka sãahar dince,hakan yana nufin duk lokacin da akayi mata allura tana fakar idonsa ta dauki kwalbar kenan ta adana?,lallai ta shiryama zuwan wannan ranar "Wanne dan wutar ne cikin likitoci yake iya zuqar wannan ruwan allurar ya zubesu ga jikin dan adam?" Abinda likitan ya fara tambayarsa kenan cikin matsanancin bacin rai. Duk yadda yaso ya shirya qaryar da zata sanyashi ya bulle amma bakinsa yaqi bashi hadin kai,saboda rawa kawai labbansa sukeyi,da qyar ya fusgo kalmar "Bansan a inda aka samosu ba,don wannan kwalaben ni ban taba ganinsu bama"ya tabbatar qarya yake,tunda ya riga yasan da komai,sai kawai ya maida dubansa ga ya zaid ya fara karanto masa aikin da allurar takeyi a jikin dan adam,da kuma girman illarta. Kuka kawai maama ta fashe dashi tana kiran sunan Allah,yayin da adam ya jiqe jagab kamar an masa wanka da ruwa,jikinsa yana bashi yau ba ranar sa'ar sa bace,yau ranar tonin sililinsa ce,momee ce mai qarfin halin miqewa,cikin borin kunya ta fara maganganu "Dama dai kawai kun shirya ci mana mutunci da wulaqantamu,saboda talakawa ne mu bamu da komai,banda haka ta yaya yaron da bashi a zaune bashi a tsaye game da al'amarin diyarku amma ku rasa sharrin da zaku jefeshi dashi sai wannan,idan banda shi da yasan girman halacci ma waye zai zauna da mahaukaciya....." "Ke tsohuwa,ki iya kalamanki" afifa ta dakawa momee tsawa da muryar da ita kanta batasan tana da irinta ba "Tunda har kuna da bakin kare kanku,ai waqa a bakin me ita tafi dadi" saita fidda waya tana kiran anty farheen "Muna hanya afifa,muna gab da shigowa layin" "Saikun qaraso" sai ga juya gasu dr mamman "Abba,don Allah ku jira minti uku,ga raba gardamar nan isowa" jin kalmar afifa ta qarshe ta kada hanjin cikin momee,zatonta ya bata jami'an tsaro kawai suka kira musu kai tsaye,sai ta kama hannun adam tana cewa "Tashi mu tafi,Allah zai saka mana da wannan qazamin qazafin da sukayi maka saboda kana auren diyarsu" "Ina zaku?,ku koma ku zauna,ai bakwa tafi muna zarginku ba,gwara a warware gaskiya ko hajiya?" Cewa dr mamman girema. Jikinta ne ya dauki rawa ta fara kame kame,saidai kafin ta dire kame kamen nata sallamar sãahar ta dauki hankalin kowa. Sanye cikin wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin doguwar riga,da gyale mahadinsa,fuskarta har yau bata cika ba a yadda take a baya,saidai sassanyan kyan nan da baya gushewa kwance saman fuskar tata. Akwai alamu na samun nutsuwa a tattare da ita,sabanin satittikan baya da dukka wata natsuwa tayi qaura daga rayuwarta,ake shirin haukatata,a maidata mahaukaciya zalla,idan ta yiwu ma yazo da qarar kwana,bataga abinda zai hanata ta baqunci lahira ba. Cikin azama tare da son nunawa duniya shi din wankakke ne,kuma masoyi ga matarsa ya miqe cikin zallar mamaki ya nufeta yana qwala kiran sunanta. Rungumeta yayi nufin yi,saidai kafin yakai ga aikata hakan ya samu tsarabar wani lafiyayyen mari saman fuskarta,sannan ta tattara dukka qarfin data shigo dashi ta ingizashi baya ya fada saman momee dake zaune cikin kaduwa da tsurewa. Zumbur ya miqe yana shafa wajen,sannan ya maida dubansa a kanta,sanda take tsaye ta kafeshi da fararen manyan idanunta dake dauke yau din da wani irin matsanancin fushi da bai taba ganin irinsa tattare da ita ba "Baki warke bane sãahar?,subhanallahi" "Kaine zaka shiga taka haukar yanzun nan,mayaudari maciyin amana,ina neman tsarin Allah daga kai" sai ta fashe da kuka ta soma sulalewa a gurin zata zauna,anty farheen ta riqeta da kyau tana bata baki. Tuni maama ta qaraso bayan ta tabbatar ba mafarki takeyi ba,ta rungume 'yarta tsam tana jero addu'o'in godiya ga Allah "Ya kamata kowa ya samu waje ya zauna" yaa Saifullahi ya magantu cikin nutsuwarsa,domin ya karanci akwai babban al'amari dake shirin faruwa,komai ya fara bayyanar masa saman fuskar adam da babarsa,sannan ya akayi sãahar take a gidan muhyiddeen duk da tsahon lokacin da aka dauka ana nemanta ba tare da kowa ya sani ba?,ga adam da momee suna matsawa daga bakin qofa?,tamkar yaa zaid ya lura,sai ya matsa yayiwa kansa mazauni daga can hanyar qofar,suka zamana a tsakiya. A nutse afifa ta qaraso tsakiyarsu ta dire jakar. Lokacin da idanun adam suka sauka a kan jakar sai ga fitsari ya balle masa yana daga zaunen,zazzafar gudawa ta soma qoqarin kufce masa amma ya matseta da kyau,gurbatacciyar ziciyarsa tana gaya masa akwai sauran dama adam,kada ka karaya,muddin baka amsa ba ba wanda ya isa ya tilastaka,koda kuwa a kotu ne. A gaban kowa sãahar ta matso,ta daga jakar ta zazzage komai ya tarwatse a qasa,wani zazzafan kuka ya taso mata,amma ta danneshi. Daya bayan daya ta soma basu labarin yadda suka fara hadaka a rayuwarsu,yarjajeniyar rashin daukan ciki,canjin halayensa,kamashi da tayi a waya da zuba mata tablet da yayi na zubda ciki,bayyanar ha'incin da yake mata ba tare amma data kama sunan raihanatu ba,azabar daya dinga gana mata har zuwa sanda Allah yayi fitarta daga gidan da taimakon afifa da kuma raihanatu. Kamar wani mahaukacin zaki ya miqe ya soma zage zage,yaa zaid baisan sanda yasa qafa ya kwasheshi ba cikin matsanancin fushi,sai gashi kif a qasa "Idan ka sake mana magana sai na cire maka harshe" kota ina jikin momee rawa yake,duk sauran qwarin gwiwar da take dasu sun kwaranye sunbi ruwa,don itama wasu abubuwan batasan dasu ba. Jakar ta fara musu bayani,tana zazzage abubuwan ciki tana nunawa kowa,sai maama ta kasa daurewa,ta rufe fuskarta da hannunta kuka mara sauti yana qwace mata. Duka duka nawa sãahar din take da har zata fuskanci irin wannan cin zarafin cin fuska da zallar cin amana daga gurin da namiji?,ko ita data kawota duniya bata taba fuskantar wani abu da yayi kamanceceniya da wannan ba "Duk abinda ta fada gaskiya ne,ni shaida ce" muryar raihanatu ta ratsa falon,sai suka waiwaya suna kallonta, idanunta cike fal da qwallar tausayin sãahar din,don itama wasu abubuwan sai yanzu takeji. Mamaki ya cika momee qwarai,wato raihanatu zata zame mata 'yar kuka?,ta raini makashiyarta? "Ki daina mamaki momee,ko kina tunanin bansan ba don Allah kike riqe dani ba?,bayan bautar da nake muku kina lissafin sake maidani machine din tatsar kudinki?, bayan kin cinye dukka abinda mahaifiyata ta mallaka,tun tana raye bata da bakin musa miki?" Maganar ta sake zuwarma momee a bazata,lokaci guda ta nemi sukurkuta mata runani,ya akayi yarinyar tasan wannan "ni zaki butulcewa raihanatu?" "Dalla malama ki rufewa mutane baki" yaa Saifullahi ya fada cikin muguwar tsawa,ransa baqiqqirin,tamkar zai kifawa momee din mari,hannu Dr mamman ya daga masa,saboda shi wani abuma ya tsaye masa a wuya ya kasa magana,idanunsa qirrr saman fuskar adam,yana tuna girma da nauyin karamcin da ya yiwa rayuwarsa,tarin alkhairai wanda ko sãahar da take matarsa ya hana ya gaya mata,yakance masa "Nayi maka ne fisabilillahi saboda Allah,ko ummin abba banaso ta sani,kasan su mata,wani qaramin tunani garesu,qanqani abu zai hadaka dasu sai su goranta maka". Sam basu farga ba,ashe tuni yaa zain yayi kiran mopol,kafin kace wani abu sai isowarsu akaji da sanyo kansu cikin gidan "Waye yayi hakan a cikinku?" Dr mamman ya tambaya "Kayi haquri abba,nine" ya zaid ya fada yana miqewa,yanason a hukunta masa adam da mahaifiyarsa hukunci Mafi tsanani da radadi,irin hukuncin da har su koma ga Allah ba zasu mance dashi ba. "Amma ina zaune ba zaka fara neman shawarata ba zain?" "Kayimin afuwa abba" yana gama fada ga fita,cikin second biyar suka cika falon. "Wait please" ya Saifullahi ya fada,ya miqa hannu ya ciro paper,ya zaro pen daga aljihunsa ya dorawa adam da ake qoqarin cukuikuyewa "Maza rubuta mata takardarta" kai ya girgiza cikin taurin zuciya da taurin kai "Matata ce,kuma ina sonta har yanzu,don haka bazan saketa ba,saidai......." Bai qarasa fada ba ya Saifullahin ya daukeshi da wani kyakkyawan mari "Mu zaka gayawa maganar banza da wofi?,wato saboda baka daku ba har kana da qwarin gwiwar yi mana musu ko?" Duk da marin amma sai ya sake girgiza kai "Saidai ta mutu da igiyar aure na" "Ba zata mutu ba kuwa,saboda mudin ba jahilai bane,kawai kotu akwai shari'a kuma" ya muhyiddeen da mamakin adam ke sake kasheshi ya fada. Saidai yana rufe bakinsa mopol din ya saukewa adam din wani irin zazzafar mahangurba da lokaci guda ta sauke masa jini ta hanci da labbansa,ta kuma tara masa wani lafiyayyen jini a gefen idanunsa. Ihu momee ta saki tana neman taimakon wai za'a kasheta ita da danta "Saketa,ka saketa nace karsu kasheka baka da gata" koda momee din bata fada ba zai rubuta,shi kadai yasan kalar azabar da yaji,idanunsa a rurrufe ya rubuta mata saki daya. A fusace ya Saifullahin ya duba "Don ubanka qarashe mata sauran biyun" dr mamman ne da nasa mamakin ya qarasa daskarar dashi ya daga masa hannu "Rabu dashi" ya basu umarni a taqaice,daa yaso ya hana a tafi dasu,amma yadda suka nuna rashin nadama kwata kwata bisa fuskarsu yasa ya kasa hana mopol din tafiya dasu. "So nake a azabtarmin dasu yadda ya kamata,a sassaba masa kamanni shida uwarsa,banason kowa yasan inda suke,kada kuma a daga musu qafa ko na kwana daya,zamuyi waya" yacewa da shugabansun "Karka damu,sakamakon mummuna ai mummuna ne" shima ya fada cike da jin takaicin adam da uwarsa. Ko minti biyar basu qara a gidan ba suka tattara nasu ya nasu suka fice a gidan,sãahar ce tabi raihanatu da kallo wadda ta hada nata kayan ta fara yin titi "Abba bata da kowa a qasar nan,kuma ko yanzun bata da wajen zama,dama suke riqe da ita,na tabbatar kuma ba zasu ci gaba da riqonta ba" wannan yasa suka dauki raihanatun,abban kuma ya tabbatarwa sa sãahar zai kula da nauyinta da rayuwarta,zuwa gaba kadan kuma zasuje ghana a binciko danginta na qwarai,don susan irin riqon da momee tayi mata. Ajiyar zuciya sãahar ta sauke "Allah yasa su iya wani abu,saboda momee ta cikasu da kyaututtuka,a yanzu kuwa lalacewa ta tattaru a cikin dangi,duk lalacewarka izgilancinka da rashin ganin girman mutane,taka mutane da mugunyar halinka kaida iyalinka,muddin kana ungo ungo,sai idanun 'yan uwa su rufe daga aibunka,a rasa wani tsayayyen da idan kayi ba daidai ba za'a tsaya a tsawatar maka a kuma hukuntaka dai dai da laifinka" kai abban ya jinjina,maganar sãahar tana kan hanya "Wannan shine yake kawo lalacewar zumunci da tabarbarewarsa,dole sai an hadu za'a gyara,dole sai an hadu an hukunta me qarfi ko mara qarfi,ya zamana kowa baifi qarfin doka ba,Allah ya kyauta,yasa mufi qarfin zukatanmu" _NOTE:wadannan matsalolin da suke babbar masifa ce suna nan suna ruruwa cikin al'umma,a yanzu dan qanwarki ko dan yayarki yana iya cin zarafinki,uwarsa ta goya masa baya,saboda suna yiwa dangin nan dan ihsanin da bai taka kara ya karya ba,su kansu masu fada aji a dangin sai kaga sun zama hoto,basu da wani amfani saboda ba kowa suke iya juyawa ba,sun wulaqantar da kansu saboda suna tsoron wasu sashe,idan sunyi ba dai dai ba basu isa su hukuntasu ba,ke kuma uwa wallahi wallahi kanki kikewa baqar dabara,kin nunawa 'ya'yanki kowa baida mutunci,babu me gaya musu suji,saboda kema a haka kika taso,kina ganin kinfi qarfin a baki shawara ko a tsawatarmiki,kin ruguza iyalinki da hannunki,bayan babu ranki haka zasuci wahala,saboda masuyi don ganin idanunkin guduwa zasuyi su barsu,kina qabari ke kuma kina amsar query akan tarbiyyar da kika yiwa yaranki,kina qabari ana nan duniya ana alawadai da halin yaranki,abinda kina raye babu me iya fada,kin mutu kin barwa dangi masifa,qila akwai mata a cikinsu,sai kiga yarinya ta kasa zaman gidan miji,ta kasa biyayyar aure saboda a tarbiyyar da uwarta tayi mata batasan biyayya ba saidai ita a bita,sai tsananin rabo yake zaunar dasu,to duka mu sani,dake uwa da kika zama shashasha sauna,wadda ke iya bari diyan cikinta su wulaqanta 'yan uwanta saboda yunwar ilimin addini da qarancinsa,dasu dangi da suke ganin barna su kasa tsaiwa a gyara saboda kowa yana tsoron fadin gaskiya,ta silar haka zumunci ya gurgunce,wallahi wallahi kowa sai ya tsaya yayi bayani gaban Allah,da wanda aka cuta da wansa yayi cutar,Allah ka bamu dacewa,ka bamu ikon tsaiwa akan gaskiya akan mutum ko wayeshi,komai girma da matsayinsa,ka rabamu da kwadayin abun hannun kowa,ka wadatamu da wadatar zuci daga gurinka👏🏽_ Page 56 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 56 Cikin lokacin kowa qoqari yake ya faranta ran sãahar,tamkar rige rige akeyi,kowa yana bakin qoqarin ganin ya sanyata walwala,dukkansu sun fahimci depression ya fara kamata,ta soma wasu attitude da suke bayyana hakan. Anty farheen ita ta tashi tsayin daka a kanta,daga qarshe ta karbeta daga hannun maama,duk da maaman taso a barta da diyarta,to amma farheen din nada wani irin kirki da tausayi,dole ta haqura ta bar mata ita. Zamanta hannun farheen yasa ta qaru da abubuwa masu tarin yawa,sannan ta taimaka mata wajen mantawa da wasu abubuwan,tare da fara dawowa cikin saitinta. A lokacin ya muhyiddeen ya samu wani aiki a Scotland,sai duka suka tattara har sãahar din suka wuce can. Koda sukaje din asibiti me kyau farheen tasa yaa muhyi ya duba musu suka fara zuwa ita da sãahar din,akwai sashen guiding and counselling masu kula da matsaloli irin wadan nan da hanyoyin kubutar da tunani daga wannan damuwar,abinka da qasashen da sukaci gaba,watanni kadan saiga sãahar din ta koma dariyarta da walwalarta,ta sake murjewa,gayu ya sake zama a jikinta fiye da kima saboda tasirin zamanta da anty farheen,idan ka ganta saita bala'in burgeki ke da kika diya mace ma,nan da nan anty farheen tayi amfani da wannan damar ta nema mata makaranta da kanta,ta dora karatun mastering degree dinta. Cikin shekarun komai yazo ya wuce,saidai babu ta yadda za'a ji ciwo sannan a warke ba tare da ya barwa mutum tabo ba,koda a gangar jiki ne bare kuma a guri me matuqar muhimmanci da sammatsi irin ZUCIYA,zalincin adama gareta yasa ta hadu sa ciwon kai mai matuqar tsanani sanadin alluran da aka dingayi mata ba bisa qa'ida ba,wanda inda ace anci gaba da yinsu,tsaf kwanyarta zata juye cewar likita,wannan tabon shine abinda ya haifarwa da sãahar tsanar maza,tsana me tsanani,babu halitta da takewa bahagon kallo irinsu,ta tsani taji kalmar soyayya,kalmar AURE kuwa tana sanyata jin wani tashin hankali,kwatankwacin mutumin da yaqi ya tunkaro shi,duk wani abu da zai sanyata hulda da maza ta datseshi,wannan ne yasa tunda suka dawo Nigeria tayi zamanta wajen anty farheen dake ji da ita,take kuma sake maidata macen da idan aka kalla sai an sake juyawa an kalla cikin hikima. Batason kowa yayi mata zancan aiki,shi yasa taqi fidda results nata data samu,results me kyau da yayi bala'in burge yayyenta,duk da dama tunda can sunsan ita din bata da wasa ta fannin karatu,hakanan tana da kwanyar da dukka cikin gidan ita da yaa Saifullahi keda irinta,duk da sauran suma ba daga baya ba,wannan yasa kowanne yake riqe da wani babban matsayi,ya kuma tara dukiyar da a qananun shekarunsu idan aka gaya maka yawanta zakayi mamaki,dukka cikinsu babu rago,babu kuma koma baya. A wancan lokacin sati guda dr mamman yace su zain su saki adam,su barshi da halinsa,yayi imanin bazai gama rayuwa a daron duniya ya wanye qalau ba tare da Allah ya hukuntashi ba,duk kuma yadda sukaso hukuntashi hukuncin Allah shine gaba da nasu. Hatta da afifa bata bayar da goyon baya ba,ita inda son samu ne,akai adam din muhallin da hatta hasken rana baya shiga gurin ayi masa daurin rai da rai. Sun bar dr mamman aka cewa an sakeshi,amma basu barsu ba saida sukayi watanni uku cur suna karban hukunci a hannun sajoji,kafin sannan kuwa gaba dayansu ba wanda baiji a jikinsa ba,duk wani abu da sukasan ya mallaka ta silarsu sun karbeshi,ciki harda gidan da momee ke zaune,da wanda suka rayu shi da sãahar,sai a sannan suka gane cewa gidan ashe shima ya saidashi,ta yadda idan yabar qasar saidai sãahar taji ana batun ta tashi ga masu gida. Tuni suka sayar da gida,su kuma ainihin wadanda suka siya a wajensa dama baikai ga basu takardun ba,ya karba kudinne kawai,nufinsa sai ranar da zasu bar qasar ya danqa musu ya qara gaba,sukace ba zasu yarda ba,yaa zain yace su nema kudinsu a hannun dan damfarar da suka bawa. Sunsan tako ina family din dr mamman girema ba abun wasa bane,sunfi kuma qarfin wannan gidan bare suce cuwa cuwa sukayi,don haka suka karkata akalar tuhumarsu ga adam wanda a sannan ko gidan da zai kwanta a ciki ya huce tarin gajiyar da sojojin suka hada musu ya kuma yi jinyar raunukan jikinsa bashi dashi. A sannan tuni abba ya samawa raihanatu karatu a maryam abacha American university dake garin maradi a jahar nijer,tana can ta dora karatunta daga inda ta tsaya,babban burinta kenan a rayuwa,wanda momee tasha gaya mata bazai taba cika ba,ba zata dinga adashin da batasan ranar kwasarsa ba. *Dama hausawa sukance ALHAKI KWAIKWIYO NE,ME SHI YAKE BI* _DUK INDA ZA'A JE AZO KA TABBATAR KAI AKA CUTA,KARKA ZAMA KAINE WANDA KAYI WANANN CUTAR,A RABUWAR AURE 'YAN UWANA MATA,KARKI YADDA IDAN TA KAMA A RABUN YA ZAMANA KECE ME MATSALA KO KECE AZZALUMAR, WALLAHI KIKA BARI HAKA TA FARU KUMA KIKA FITO SAIKIN RAINA KANKI,MUDDIN KE AKA ZALUNTA,KARKIYI KAICO,KADA KUMA KIYI BAQINCIKI,DOMIN ALLAH BAYA KI GYANGADI BARE BACCI_ *_wannan kenan_* *_Dawowa labari_* Juyawa ta sakeyi a karo na babu adadi bayan gama dukka wannan bitar da qwaqwalwarta tayi,gefan da afifa ke kwance ta kalla,kusan wasu matsalolin tare suka fuskancesu ita da afifan,amma sau tari sai taji inama itace afifan?,inama bata taba sanin wani adam ba bare ya shiga rayuwarta ya cutar da ita haka ba?. Tsaki taja qasa qasa bayan fargar da ita da zuicyarta tayi,saita miqe ta sauko daga gadon a hankali ta nufi toilet,cikin ranta tana sake jin yaqini da qwarin gwiwar cewa,ya zame mata tabbas tayi wani abu,har yanzu batajin cewa tayi warkewar da zata doshi wani aikin ko kuma aure,dole tayi hobbasar da zata sake nesantata daga dukkan wata mu'alama da zata sake hadata da azzalumar halittar maza,marasa tausayi da jin qai,marasa amana kuma,dole ta yiwa kanta wannan aikin. Daren gaba daya ta raya,da tarin addu'o'in ta da buqatunta jingim wajen Allah,ko kafin ta kammala ma wata irin nutsuwa ta maye gurbin bacin rai da fargabar dake motsa zuciyarta,albarkacin wannan kuma a nan saman abun sallar daddadan bacci ya saceta. Afifa ta rigata tashi sallar asuba,batayi mamakin ganinta a kwance a nan ba,saboda ba kowanne dare ne take iya kwanciya ta shareshi dukka tana bacci ba,saita qarasa cikin tausayawa da qauna ta tabata tana kiran sunanta. Idanunta ta bude tana kallon afifa "Ya shehiya sãahar,a tashi ayi sallar asuba,Allah ya amsa addu'ar nan,ina fatan kin sakani a ciki,Allah ya kawo masoyi na gari" qaramin murmushi tayi duk da cewa daga bacci ta tashi,hakan kuma ya sake qarawa fuskarta kyau,sai da tayi brush ta daura alwala ta fito sannan ta amsa mata "Allah ya kakkawo,saidai ita afifa akwai wanda take jira" bata tsaya jin amsarta ta tayar da sallah ta barta da baki a bude tana cewa dariya nason kamata "Kajimin yarinya zatamin sharri?". Dukka wani azkar data saba yi sai data yishi,haka kawai taji idanunta babu wani sauran bacci,duk da cewa ba wani baccin kirki ta samu ba adaren jiyan,don haka ta shafa addu'o'inta ta nade abun sallar,ta dauki wayarta ta koma saman gadon su,tana kallon afifa da idanunta ke rufe,da alama bacci ne sosai a kanta, saita ja duvet itama tana shirin rufa,dai dai lokacin da tex din ahmad ke shigowa wayarta. Ko bata buda ba tasan saqon barka da safiya ne,taja qaramin tsaki,tana tunanin sai yaushe zai gaji da naci yace ya haqura da ita?,ba amsa,don haka ta share saqon bayan ta buda wayar. Watsapp tahau zata buda wani qaramin document na addu'o'i da anty farheen ta turo mata,yana da dan nauyi,don haka da tayi clicking akai,sai ta fita da zummar rage jira kafin ya kammala buduwa. Haka kawai ta samu kanta da buda jerin list na mutanen da sukayi status a safiyar ranar,duk da cewa kuwa ba dabi'arta bane hakan. Sunan mr sadeeqa yana sama sama,auntie din su nurain 'ya'yan yaa Saifullahi. Sam ta mance da matar a rayuwarta,duk da cewa tana da kirki qwarai,tun kafin tayi aure lokacin da takanje gidan yaa Saifullahi din,wani lokaci ita ke kaisu school da safe,a nan suka dan saba da ita saboda matuqar kirkinta,sai kuma dabi'arsu tason yara tazo daya,wannan ya sanya suka dan saba suke gaisawa,har sukayi exchanging numbers. Batasan ya akayi ba hannunta ya taba status din mrs sadeeqa,take ya bude,hotone na wata baby girl,duk da cewa hoton ya danyi blurry kadan,amma hakan bazai hanaka iya gane kyan yarinyar ba,tayi rubutu a qasan hoton kamar haka _she has being suffering and battling epilepsy,she is looking for a good nanny,praying for an easy recovery my class cute angel_😥😥. Epilepsy qwaqwalwarta tayi mata tariyar maganarsu ta jiya da sukeyi da afifa kenan kafin ta fita,take tausayin yarinyar taji ya taba zuciyarta duk da bata iya ganin fuskarta sosai,fingers dinta guda biyu ta saka tayi zooming hoton,still dai it was blurry,hakanan kawai tayi replying status din da cewa _"is that serious?,she's looking for a Nanny"_ sai data tura saqon kuma sai tayi shuru,ita kadai tana tunanin meye amfanin tambayar data tura. Da sauri ta koma ta jerin charts dinta da zummar gogewa,amma sai ta tarar mrs sadeeqa din tuni ta gani,har ma tana typing wani abu,hakan yasa ta haqura ta koma duba document dinta da take budewa,amma kuma hankalinta nakan inbox din mrs sadeeqa. Har zata buda taga shigowar saqo daga mrs sadeeqa din. Sake fita tayi ta duba "Yeah,she's my student,ina tausayinta sosai,akwai wata ne daga bangarenki?" Tausayin data darsu a zuciyarta taji ya sake motsawa,a taqaice ta tafa mata "No,but zan bincika,i will back to you idan na samu Allah ya bata lafiya" "Ameen,thanks for your concern". Kashe data din tayi,ya dudduba addu'o'in sosai,zuwa lokacin garin ya fara haske,sai ta kashe wayar gaba daya ta sake gyara kwanciyarta ta kwanta tana rufe idanunta da fatan samuwar baccin. Bacci tayi sosai,har na kusan awanni hudu,wanda qarshen baccin yazo mata da mafarkin da ya sanyata farkawa. Miqewa tayi ta zauna sosai tana duban gefan afifa,bata a gurin,tabi dakin da kallo,da alama ma harta gyara dakin,gadon da take kwance a kai ne kawai bata gyara ba. Hannunta ta sanya ta tattare gashinta daya zame daga band din data matseshi dashi saboda santsinsa,ta daureshi gudi daya tana sauke qaramar ajiyar zuciya,tunaninta na komawa baya kan mafarkin da shine silar farkawarta a yanzu,zuciyarta cike fal da mamaki,to meye hadinta da yarinyar da bata taba ganinta ba sai dazu a status din mrs sadeeqa da har zata yi mafarkinta?,ko a dazun ma bata gama tantance fuskarta ba,kamar yadda a mafarkin ma bata gama ganin fuskarta sosai ba. "La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" ta fada a hankali,sannan ta zamo ta sauka daga gadon,har yanzu zuciyarta bata daina mamakin yanayin data ga yarinyar a mafarki ba. Kuka takeyi sosai tana riqo hannunta,yayin da ita kuma take qoqarin zame hannun nata ta tafi ta barta,daga bayan yarinyar kuma wata matace take biye da ita da sharbebiyar wuqa tana son caka mata. Da wannan tunanin ta isa toilet din,ta ciri brush ta matsa toothpaste ta fara wanke bakinta,har yanzu tana nacin son gano abinda mafarkin ke nufi amma ko daya tunaninta bai iya hasaso komai ba,to shin me ma zata hasaso din?,bayan batasan wace yarinyar ba,daga qarshe sai ta tattara tunanin ta watsar,ta barwa ranta cewa tsabar son yara da take dashi a jininta ne,da kuma yadda zuciyarta ke da rauni akan dukka abinda ya shafi yaro. Wanka tayi gaba daya sannan ta dawo dakin tana shiryawa,afifa ta shigo da dan tray data shiryo breakfast dinta a kai,hannunta daya riqe da waya tana amsawa. Idanunta akan fuskar sãahar din harta qaraso,sai ta miqa mata wayar muryarta can qasa tace "Please" hadi da karyar da kai gefe daya alamun roqo. Kafeta tayi da idanu tana son nuna mata bata kyauta mata ba da zata sanyata yin abinda batayi niyya ba,sai kuma daga bisani ta miqa hannu ta karba wayar,don afifa ce tafi qarfin komai a wajenta,ta kara wayar a kunnenta tana qoqarin tsane jikinta da qaramin towel. Page 57 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 57 Kamar yadda tayi tsammani mahmud ne,ajiyar zuciya mai nauyi ya fara saukewa "Kiyi haquri,duk yadda naso nayi miki yadda kikaso,zuciyata ta gaza bani hadin kai,na mugun jarrabtata da sonki har bansan iyaka ba" bakinta ta tabe,tana jin kamar ta saki wayar ta tarwatse,da wadan nan kalaman nasa gwara ya sakar mata ihu a kunnenta yafi mata sauqi,amma hakanan ta daure ta amsa a taqaice "Is okay,bana dan jin dadi ne,that's why na kashe wayar" "Ya salam" ya fada cikin nuna kulawa "Me ya sameki?" "Noo,lite headache ne,amma i feel better" "To alhamdulillah,kibar wayar a kashe ki samu ki huta sosai,idan inason jinki zan kira ta line din afifa,bata wayar zamuyi magana" batace komai ba ta zare wayar ta miqa mata tana harararta,tana danne dariya ta karba,batasan me ya gaya mata ba,taga ta miqe ta fita,ta bita da kallo tana tabe baki taci gaba da shiryawa. Tana cikin saka kaya afifan ta dawo,ta koma ta zauna tana ci gaba da cin abincinta,saita fasa daurin dankwalin da tayi niyya,dama can dankwali asara ne cikin dinkunanta,ta qaraso gaban afifan bayan ta jawo stool ta zauna ta sanya hannu suka fara ci tare. Har suka danyi nisa babu me cewa da dan uwansa wani abu,afifa ta karanci yau mutanen ne a kusa,ita kuma bakinta magana ce fal,don haka ta koma ta zauna sosai tana kallon sãahar "Na baki shawara?" Dubanta sau daya tayi sannan tace "Bani mana,is ether na dauka ko na bar miki kayarki" "Alright,ammm......magana ta gaskiya na jima banga soyayya me zafi irin wadda mahmud yakeyi miki ba....." "Tam, contract din kuma da kika karba kenan da safen nan,ko azahar batayi ba?" Dole ba tare data shirya ba dariya ta qwace mata sosai "Allah ya isa bestie,wait......wai me kika mayar dani?" "Me dalili,naga alama sana'ar da kikeso ki koma kenan" wannan karon ma saida wata dariyar mai sauti ta kufce mata har tana shirin qwarewa,a nutse sãahar din ta tsiyaya ruwa ta miqa mata "Maza karba kisha kada ki wuce gana ya rasa campaign officer dinsa" tana dariyar tana sha,har taji dai dai ta ajjiye,tayi gyaran murya kadan tana dubanta da idanunta da suka tara hawaye "Seriously nake miki magana,amma naga kinason ki maida abun wani joke,don Allah bestie ki manta da komai,ya kamata kiyi moving forward mana,kina tunanin zamanki a haka adam bazaiyi tunanin shi kike jira ba?,har yanzu soyayyarsa ta hanaki kallon kowa bare ki aureshi?" "Soyayya?" Ta furta kalmar kamar ranar ta fara jinta,kai afifa ta jinjina "Yes" wani qaramin murmushi me ciwo sãahar din ta saki,sai kawai ta miqe "Banda bayan soyayya dake tsakanin namiji da mace,kawai nau'ikan soyayya kala kala, kamar wadda ke tsakanin 'yan uwa da iyaye,da nace Allah ya tsinewa soyayya albarka" ido afifa ta zaro,ta kuma hangame baki yana kallon sãahar,wadda tayi furucinta hankalinta kwance,saima ta gyada kai ta juya tana nufar qofa "Naga alama tunda kika samu annual leave din nan rashin aikin yi ya sameki,shi yasa kika amsa contract daga wajen gana,to wallahi ke dashi ba wanda zaya matsamin" tana kaiwa qarshe ne dai dai sanda take fita a dakin gaba daya. Gurin ummee tayi tafiyarta,wunin ranar gaba daya taqi tsaiwa sauraron bayanan mahmud. Saidai wani abun mamaki,duk bayan wasu mintuna sai yarinyar da ko sunanta bata sani ba ta fado a ranta,hakanan maganar da sukayi da mrs sadeeqa,wunin ranar har yamma,batayin minti arba'in cikakke bata fado mata a rai ba. Ta idar da sallar la'asar tana yiwa ummee din gyaran wardrobe dinta kiran yaa Saifullahi ya shigo wayarta,cikin girmamawa ta daga kiran ta kara a kunnenta,ta gaidashi a aladabce,saboda shine babba duka gidan,kuma hatta da yaa muhyi yana bashi girma,duk da cewa shike binsa,akwai girmama na gaba sosai a tsakaninsu "Kina gidan inna ummee dinne?,akwai baqo da zayazo ya sameki,abba yace a shaida miki" gabanta ne ya fadi,rudewa kuma ta sameta lokaci guda,har ta kama sunansa ba tare data shirya ba "Mahmud?" "Eh fa,da wani abu?" Ya tambaya kai tsaye da seniority din nan nasa "A'ah,daman.....dama munje therapy saloon ne" "Alright,zai kiraki yanzun saiki gaya masa" daga haka ya yanke wayarsa abinsa. Wayar ta jefar gefe kamar zata saki kuka,da qyar ta tsara qaryar gashi kuma da alama haqanta bai cimma ruwa ba. Bata gama wannan tunanin ba kiran mahmud din ya shigo,kamar ta dora hannu aka tayi kuka haka ta daga kiran. Akwai wani irin farinciki sosai cikin muryarsa "Can I get the address?,saina sameku a can?" "no,mu hadu a gida kawai after one hour" kamar zai zuba ruwa a qasa yasha haka yaji,cikin madaukakin farinciki yace "Thank you,thank you so much" bata tsaya jin qarashen godiyar tasa ba ta yanke kiran tana gunaguni,ta ajjiye wayar gefe tana dafe kanta. Ko kwalli bata sanyawa idanunta ba haka ta fito,afifa tayi tayi amma tayi biris da ita,daga baya ma cewa tayi "Idan kika matsamin Allah sai na fasa fita" "Allah ya baki haquri masifaffiya" sai taja bakinta tayi shuru,tasan kadan daga aikinta. Tun kafin ta isa afifa tasa an cika shi da kayan motsa baki kala kala,tahowarta ya sanyashi miqewa,bai zauna ba har sai data zauna sannan ya zauna yana mata barka da fitowa,ta danne zuciyarta ta gaidashi,abinda ya masa dadi sosai. Duk yadda yasan zai sha kanta sai da yayi,tana zaune tana saurarensa har ya gama,sannan ta motsa labbanta "Inda zakayi haquri da hakan yafi,saboda tuni na rufe babin soyayya daga rayuwata" kai ya girgiza "Banajin zan iya,banajin zan iya daina sonki,kiyimin alfarma ki amincemin ki aureni,zan iya zama dake a hakan koda ke baki sona" tsam ta miqe,saboda ta fuskanci mahmud din yayi nisa,kuma bayajin kira sam. Ta bude bakinta da niyyar magana ya zaid ya iso wajen. Yanayin yadda taga suna gaisawa da shi cike da sanayya mutunci da girmama juna ya daga hankalinta,sanda suka gama gaisawan da tambaye tambayen juna sai zaid din ya kalleta "Ki riqeshi da kyau,mutumin kirki ne sosai" maganar tayi mugun tabata,har kuma mahmud yayi mata sallama ya wuce bata sake fahimtar abinda yake fada ba. Haka taci gaba da kasancewa har zuwa dare,tabbas!,ba shakka komai zai iya faruwa,muddin mahmud yaci gaba da samun irin wannan soyayyar daga wajen 'yan gidansu,idan tace komai,tana nufin komai din,ciki harda tausata ta karba aurensa ba tare data shirya ba!. Wannan sautin da ya tsarga daga cikin kwanyarta shi ya sakata miqewa zumbur ta zauna saman gadonsu,afifa dake gaban system tana wani aiki ta waiwayo tana dubanta,saita maida kai tana ci gaba da aikinta ganin ta dauko wayarta itama ta bude. Tun bayan tafiyar mahmud ta fahimci tana cikin damuwa,ta riga da tasan damuwarta na meye,so shi yasa ma bata tambayeta akan komai ba. Kai tsaye ta kirayi layin mrs sadeeqa,bugu daya tal ta daga,da alama tana kusa da wayar,cikin mamakin ganin kiranta da kuma zumudi hadi da girmama suka fara gaisawa,tana tambayarta tsaffin dalibanta su fadeel "Basu dawo qasar ba har yanzu....." Ta furta cikin son yankewar tambayoyin ta kuma isar da nata saqon "Ma sha Allah" mrs sadeeqa ta fada "Inason tambaya ne naji,your student,ta samu nanny din nan kuwa?" Kai ta girgiza "Kai,gaskiya i don't think so" "So if you don't mind nace akwai me buqatar aikin" murmushi ta saki "Ma sha Allah,so far dai banajin akwai wadda tayi musu,duk da hajiyan tata tace akwai wadanda aka yiwa screening,amma basu cancanta ba" duk da batun screening wa nanny's din ya bawa sãahar mamaki,amma ba wannan bane yanzun a gabanta "Alright,hakan yayi" "Naji dadi,nasan ko wace za'a samu daha bangarenki she wil be the best among others in sha Allah,wace a ina take?,sai na yiwa hajjajun magana" "Nice" ta fada da qwarin gwiwa. Ba mrs sadeeqa ba,hatta afifa dake aiki batasan sanda ta tashi ta zauna sosai tana duban sãahar da wani irin madaukakin mamaki ba,tare da tantamar abinda kunnuwanta suke son jiye mata "Na'am madam,me kika ce?" Mrs sadeeqa ta tambayeta cike da kokwanton abinda taji daga bakinta "Yes,nice,ni zanyi aikin" dan murmushi mrs sadeeqa ta saki "Madam,ko baki kula sosai da wanne irin aiki bane ake magana,ba aikin company ko na banki ko lecturing bane......raino ne,na yarinya me lalura,duk da ba qarama bace sosai,amma dai raino ne" ido sãahar ta lumshe sannan ta budesu lokaci guda "Ya salam ya Allah" ta furta a qasan zuciyarta,batason ta fara da samun matsala tun yanzu,saboda ba zata iya jurewa ba,zuciyarta ta karkata matuqa,ta kuma kwadaitu da buqatar aikin "I Know,na fahimta,just......ina sha'awar yin aikin ne" shuru mrs sadeeqa tayi cikin kokwanto matuqa, kafin daga baya tace "Zaki iya kuwa madam,wouldn't it be a disgrace?" "Surely mrs sadeeqa,ko ba komai aikin lada ne" ta fadi hakan har zuciyarta "Gaskiya ne,i will talk to hajiyan,zan miki magana,kin gama samu ma in sha Allah,you are not the kind of people to be ignored" "Thank you ma'am" sãahar ta fada tana gintse kiran "Thanks for what sãahar?,wanne mummunan tsari ne wannan?,a nanny?" Afifa ta furta kamar zatayi kuka,kalmar na sukar ranta. A nutse abinta hankali kwance take kallon afifa din harta gama,saita sauka daga inda take zaune,ta dawo kusa da afifan ta zauna sosai tana fuskantar ta "Wannan shine burina a yanzu, abinda kuma nakeso,bazan iya boye miki komai ba bestie,shi yasa nayi wayar ma a gabanki,jikina yana bani mahmud nason yin galaba akan su abba dasu ya Saifullahi,idan banyi wasa ba kuma komai yana iya faruwa,so I want to be far away from him for a while that's why na nemi wannan aikin,banason mahmud afifa,bazan iya aurenshi ba,zanyi nesa dashi,duk sanda na samu tabbaci da yaqinin iya zama da wani namijin.....koda shi mahmud dinne zan dawo a kurkusa,i won't be longer,support me please bestie" "What a bad idea sãahar?,you mean....zaki koma 'yar aiki fa kenan?,wait.... idan na yarda ma su abba kina tunanin zasu yarda da ke?" Murmushi ta saki kadan "A yanzun nafi sha'awar zama 'yar aikin bestie,ko banza babu ruwana da kowa da matsalarsa,zan zauna guri daya nayi rayuwata da yarinya qarama,zan cika burina na raino wanda adam ya dakushe min.......zan samu ladan yarinyar dake dauke da cutar epilepsy,ban sani ba,kota silar jinyar Allah ya yayemin tawa damuwar bestie,don Allah ki maaramin baya,kada ki watsamin qasa a ido" shuru afifa tayi tana jin yadda sãahar ta riqe hannunta da kyau,da alama tana buqatar yin hakan,kanta ya kulle sosai,ta yaya zata mara mata baya ta mayar da kanta nanny?,bayan da gantanta?,duk randa maganar ta bayyana me zatace da su abba da maama?. Sosai sãahar din ya tsareta da ido cikin laushi da salon rarrashi,sai ta rasa amsar da zata bata,daga bisani Allah ya kimsa mata,ta waiwayo ya dubeta tana sauke ajiyar zuciya "Ni dake duka muje muyi istikhara,idan mun samu nutsuwa akan abun,zan maara miki baya" "Kin tabbata da gaske kike?" Murmushi ta saki "Da gaske nake,amma ki tanadi abinda zaki gayawa su abba,don ni bazan iya musu qarya ba" miqewa tayi daga tsugunon da tayi ta zauna sosai "Kinfi kowa sanin ba dabi'ata bace,so nima ba qaryar zanyi masa ba". Akan haka suka samu matsaya ita da afifa din,sannan kuma dukansu suka shiga istikhara din kamar yadda afifa ta shawarcesu. Cikin kwana ukun kuma baki dayansu ita da afifan,kowanne ya samu nutsuwa cikin ransa,rudanin dake ran afifa ya kau,haka dan kokwanton da ita sãahar din kanta takeyi game da aikin sai taji babu shi,taji har cikin ranta zata iya,fatanta daya kada abba yace ba zatayi ba. *_TOFA😂,me yake shirin faruwa kuma?,GUDUN K'ADDARA sãahar ke shirin yi ko kuwa?,ku biyoni dai muje zuwa_* Page 58 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 58 Kwana biyu kacal Mrs sadeeqa tayi kiranta,ta gaya mata cewa hajiyan tayi accepting nata,saboda haka ta shirya kwana uku masu zuwa zasu zo da mota a dauketa ta kama aikinta. Taji dadin hakan,amma kuma fargaba ta lullubeta na yadda zata tunkari abban,wuni tayi cikin rashin sukunin,afifa na kallonta taqi bata shawarar komai "Na gama aikina ai,tunda har nace bazan gayawa abba manufar komai aka aikinki ba" "Haba bestie" "Da gaske nake" ta sake jaddada mata,sai daga bisani ta samu qwarin gwiwa,bayan wata idea ta fado mata,ta dauki wayarta da sauri ta fara kiran anty farheen. "anty,zan sameki yau a gida?" "Eh ba inda zani yau,akwai wani abu ne?" "Saina iso kawai" tace da ita,saita ajjiye wayar ta fada toilet kawai ta fara wanka,so take ta gama da kowacce matsala a yau,tayi shirin tafiyarta hankali kwance. Cikin lokaci qalilan ta shirya cikin wata doguwar rigar abaya qirar qasan oman mai sulbi da kuma tsarin zubin duwatsu masu daukan hankali,fuskarta ta sake wani fresh da wani irin haske me kyau,kalar abayan na charcoal color ya karbi farar fatarta sosai,sassanyan qamshinta na bin kowanne sashe na dakin har zuwa falon da batakai ga fitowa ba. 'Dan abinda take da buqata ta dauka a wata qawatacciyar qaramar jaka me jikin mage,dai dai lokacin da afifa ke kitchen tana duba girkin abbansu da basu aikin gidan suka dora ta dawo dakin,ta murza qofar ta shigo,idanunta akan sãahar "Madam nanny" ta fada tana murmushi hadi da tabe baki, zagayyun fararen idanunta ta juya tana goya jakar a bayanta "Yes,daga yau sunana kenan" qaramar dariya afifa tayi tana zama saman stool "Kinsan Allah zaiyi wuya ma su karbeki as nanny,shin wai ke baki kallon kanki ne?,wace zata daukeki 'yar aiki muddin tana da aure?,wace wawiyar ce?....." "Don Allah afifa tsaya,kiyimin fatan alkhairi mana,wannan duka fatan tsiyan na meye ne ha'an" "Baqinciki nakeyi, bestie na zata zama 'yar aiki" "Okay,that's fine,kici gaba da fada" saita fara zura dogayen qafafunta cikin wani lallausan plate din takalmi "Ina zakine ma babu ko gayyata?" Ta jefeta da tambayar bayan ta dakata daga danna wayarta "Gidan yaa muhyi" "Jirani don Allah na shirya" ta fada tana miqewa da gudu bayan ta cillar da wayar tata ta shige toilet ba tare data tsaya jiran jin abinda sãahar din zata ce ba. Iska me zafi ta fitar,afifa dole saita bata mata lokaci,tanason ta gama komai da wuri ta iske abbanta a gida,ta kalli agogon dake daure a hannunta dan india dan kamfanin Daniel Wellington,saita maida dubanta ga qofar bandakin "Ki sameni a wajen ummee,don't stay longer please" saita tsugunna ta dauki laptop dinta me tambarin apple ta fice daga dakin. •••••••••"daga ina kuke halan da yamman nan?" Farheen ta fadi tana zama saman kujera,bayan ta fito musu da plate din snacks,me aikinta dauke da daya try din data shirya musu smoothie,don ita din gwanar girki ce kala kala,fridge dinta kawai idan ka bude zaka samu fresh snacks sosai,a nan din sãahar ta koyi girki masu yawan gaske "Nanny sãahar ce ta tasomu,ni fa amma gayyar sodi nazo,don bata gayyaceni ba nace ta tsayani mu taho tare" afifa tayi maganar tana duban sãahar daketa ji da rigimar khalipha shi da aleena data qara wayo sosai "Nanny kuma?" Farheen ta fada tana dan dariya,a zatonta fadan da suka dan saba tabawa ne da shaqiyanci ma juna ya motsa tsakaninta da sãahar din "Eh mana anty,koda yake dai ance waqa a bakin me ita yafi dadi" ta qarshe zancan tana jawo cup din da smoothie din yake,ta gyaran zaman straw din jiki ta fara zuqa a hankali tana lumshe ido,zaqi da dadinsa yana ratsata "Uhmmmm,ta yaya don Allah ya muhyi zai iya qara aure ana masa wannan delicious din" qaramar dariya farheen tayi,tasan afifa qwarai badai iya tsokana ba,amma hakan na mata dadi,don babu komai tsakaninta da dangin mijinta face tsantsar girmama juna da zaman lafiya hadi da qaunar juna "Basu da tabbas fa,iya girki ko qwarewa a wani abun baya hanasu qara aure idan sunso,koda kuwa ke din hurul'eeni ce,saidai kawai dai ki iya din don ki amsa sunanki na mace,sannan saboda lafiyarki yaranki dashi kansa me gidan,yaranki mata kuma ki zame musu makaranta,sannan koda wata zatazo din ya zamana ba'a fiki da komai ba,kin wuce kiyi kwaikwayo saidai keda ita ku goga,kowa ya baje hajarsa" kai sosai afifa take gyadawa cikin gamsuwa,zaiyi wahala ka zauna da farheen baka qaru da ita ba ta kowanne fanni na rayuwa. "Ke kuma yaushe kika zama nanny?" Ta maida tambayarta ga sãahar,daga kanta tayi,sai kuma ta zaunar da aleena sosai tsakanin qafafunta "Shi mutum idan gulma tayi masa yawa sai addu'a,da kin barta ta qarshe miki labarin..... bestie naga alama bazaki rufan asiri ba" dariya sosai afifa keyi harda kwanciya cikin kujera,abun yana bata mamaki yadda sãahar lokaci daya ta daukaki batun aikin da zahiri tafi qarfinsa,ita kanta a gidansu 'yan aiki nawa ne?,so amma a yanzun ita bata jin komai akan aikin,tunda suka tsaya sukayi addu'a a tare. "To nayi miki qarya ne,ba nanny din bace?" "Ban sani ba.....am anty don Allah alfarma nazo nema" ta qarashe maganar tana maida hankalinta ga farheen "Ina jinki,Allah yasa bata fi qarfina ba". Komai ta zayyanewa farheen shi,saboda babu 'yar boye boye a tsakaninsu,sannan ta qarashe da cewa "Matsalata daya abba zaice zaiyi bincike akan inda zani aikin,abu daya nakeson kiyimin,zance masa kin sansu,sannan wata uku kacal zanyi na dawo" shuru farheen tayi tana jinjina kai,tana qaunar sãahar har cikin ranta tamkar qanwarta uwa daya uba daya,zata iyayi mata kowacce alfarma,to amma kuma akwai matuqar girmamawa da ganin mutuncin juna tsakaninta da surukanta,batason tayi musu qarya "Zan iyayi miki kowacce alfarma,amma bazan iya shaidar abinda bani da tabbaci ba,inason ki bani address dinsu na gani,zan aika ayimin binciken ingancin halayyar mutanen gidan" "Alright" ba wani jinkiri ta kira Mrs sadeeqa kai tsaye,ta kuma tura mata komai da komai. Address din ta tura mata,ita kuma ta miqawa farheen wayar. A fili ta karanta address din "Wannan layin ai kamar layin gidan qawata sauma,bari nayi confirming" khalifa ta tura ya dauko mata wayarta,saita tashi tabar gurin. Duk da hankalin sãahar nakan yaran,amma kuma fiye da rabin tunaninta yana kan farheen data fita a falon. Ta kusa mintuna ashirin sannan ta fito,ta koma ta zauna a inda ta tashi "Yanzu kuma ina da qwarin gwiwar bada shaida,layin gidan qawata ne,tasan gidan,sanann me gidan ma tacemin sananne ne sosai,mutumin kirki ne qwarai da ya samu yabo da shaidar al'umma,ko jiya shine wanda ya qaddamar da committee na tsaro na unguwar,kusan ko yaushe suna tare da me gidanta tsakanin sallar magrib da isha'i,duk da ba mazauni bane,yakanyi watanni ma baya gari,yarinyar ce tace bata santa sosai ba,tunda ba inda take fita,amma tace eh tabbas yana da diya guda daya. Ajiyar zuciya sãahar ta sake,sai ta sake jin nutsuwa tana ratsata,yanzun kam ta samu qwarin gwiwar tunkarar abba,muddin farheen tace ta san gidan,tana da yaqinin babu lallai abba ya zurafafa ko yace zai hanata,yana ganin kimarta sosai cikin surukansa. Ana idar da magriba sãahar din ta miqe "Zan wuce gida bestie ya za'a yi?" "Kije kawai,drivern anty farheen sai ya saukeni" "Ba wata damuwa?" "Babu miss nanny" harara ta watsa mata,ta dauki qaramar hand bag dinta ta tsugunna tayi kissing aleena a cheeks dinta. A kan hanya ita kadai tana driving tana tsara zantukan da zata tunkari abba dasu,wani lokacin takanji abban me sauqi ne akan maama,amma tasan muddin abban ya amince,maama din ma komai zaya zo da sauqin in sha Allah. Mintuna talatin kacal suka kaita gida,saboda tana tuqin tana duba lokaci,tanason ta saita lokacinta dai dai da sanda zata riski abban yana hutawa. Baaba habu ne mutum na farko daya fara yi mata barka da zuwa bayan ya dage mata gate din gidan ta wuce zuwa ciki,ya iso gaban motar sanda take fitowa "Barka da zuwa farar d'iya" qaramin murmushi dake qawata fuskarta qwarai ta saki tana fitowa a motar "Baba habu,baaba rabi ta koya maka ko?" Murmushin dake dauke da dattijanka yayi "Sunan ya dace da me shine ai,kedai Allah yayi miki albarka keda sauran 'yan uwanki" "Ameen ya Allah baba habu,Allah ya qara girma" kamar sauran lokuta,bata fiya wucewa ba tare data yi masa alkhairi ba,tun tasowarta yake cikin gidansu yake kuma musu aiki bisa gaskiya da amana,ko sau daya bata taba jin wani yayi kuka a kansa ba,hakanan baaba rabi,ba kasafai gidansu suke sauya me aiki ba,saboda suma masu aikin idan suka fara,basa barin gidan haka siddan saidai mutuwa ko kuma aure. Hannu biyu yasa ya karba yana godiya,ba kasafai ta fiyason yawan godiyarsa ba,ko ya dinga sanya hannu bibbiyu idan zai karba abu daga wajenta ba,to amma koda zatayi maganar ma bazai canza ba,ya riga ya saba "Ameen ameen,baba habu ayi min addu'a" ta fadi tana rufe jakarta "Kullum cikin yi muku nake,amma a yanzun ma bazan fasa ba,Allah ya tabbatar miki da dukkan alkhairi a rayuwarki" "Ameen ya hayyu ya qayyumu,na gode sosai" cikin wannan girmamawar da mutuntawar ta nufi entrance na gidan,bakinta dauke da "La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" don taga motar abban nata,hakan kuma ya tabbatar mata yana gidan,koda ya fita to masallaci ne kawai. Falon nasu ba kowa,ta danja qaramin tsaki,ta tsani wannan loneliness din na gidan sam,shi yasa bata cike sati guda a gidan,kwanaki taji maama tana batun zuwa nijer cikin 'yan uwa ta dauko yara biyu mata,batasan inda zancan ya kwana ba har yanzu. Dakinta ta duba don sanar mata da isowarta amma bata risketa a can ba,saita zarce kitchen tana tafe tana yaba tsafta da kulawar da gidan nasu yake samu,wannan ya sanya ta taso da dabi'a ta masifar tsafta qwarai. Sallamarta ya sanyata waiwayowa sanda take juye tea a flask "Daga ina da daren nan?" "Gidan ya muhyi" ta fadi tana zagayowa ta rungumeta ta baya "Yau kuma?,sakeni to kada na qone" "Da kin barta ai hajiya,auta ce fa" cewar lariya me aikinsu "Wannan gansamar?" Ta fadi dai dai sanda sãahar din ta zagayo ta karbe qaramar rariya da cup din da take tace shayin taci gaba da aikin "Amma na hanaki tafiyar dare irin haka ko?,abbanku ma kuma bayaso" "Za'a kiyaye in sha Allah maama" "To Allah yayi albarka" "Ameen maama na". Tsaf ta gama hada mata komai sannan suka fito tare bayan taji abban yana masallaci,ita tayi dakinta ita kuma ta wuce sassan abban. Kayan jikinta ta fidda,ta shiga wanka,ta wanke jikinta da kyau da ruwa me dumi sosai,sai data fara yin sallar isha'i sannan ta shirya cikin riga d wando masu laushi,rigar ta kawo mata har cinya me gajeran hannu,sai wandon shima daya saukar mata har qasa,ta kama gashinta ta hade da pink ribbom sannan ta shafe jikinta da lallausan turarenta. Wani kyau tayi sosai,kayan sun karbeta kamar bana barci ba,idan ka ganta a lokacin zata dauka duka duka shekarunta sha takwas ne zuwa sha tara. Remote din ac ta dauka ta rage qarfinta,ta ajjiye saman bedside table sannan ta dauki hijab dinta me hannu ta saka,ta zira slippers dinta ta fito daga dakin. Tana takawa qirjinta yana dukan uku uku,addu'o'i fal bakinta,daga jiya zuwa yau ta wani mugun damuwa da aikin,damuwar da ita kanta takanji mamaki,batasan dalili ba,tafi danganta hakan da abubuwa biyu,neman mafaka da kuma tausayin yarinyar da ya sauka tun daga saman zuciyarta har ciki tun jiya. Da sallama ta shiga parlor din abba,ya amsa mata yana dauke dubansa daga kan zain dake zaune a gabansa ya mayar kanta,ta qaraso cikin nutsuwa tana zama a gefansu. Abban ta fara gaidawa sannan ya zain,sai ta karbi maama dake qoqarin serving nasu abinci ta fara zuba musu,data kammala sai ta koma gefe ta lafe kawai,hankalinta yana rabuwa gida biyu, rabi a hirarsu,rabi kuma tana tauna yadda maganar zata fita a bakinta "Yadai ummin abba?,akwai labari?" Dr mamman ya fada sanda ya gama tauna lomar abincin dake bakinsa,murmushi ta saki,tayi qas da kanta tana murza yatsunta "Babu abba" "Ban yarda ba,bari mu gama cin abincin tukunna" ba abun mamaki bane sam don ya fahimci damuwarta lokaci daya,shi din wani irin mutum ne daya samar da shaquwa da sabo sosai tsakaninsa da iyalinsa,akwai fahimtar juna da kuma sakin fuskar da bai haifar da raini ko rashin girmamawa ba a tsakaninsu ba. Ba jimawa zain yayi musu sallama ya wuce,falon ya zama daga ita sai abban,don maama ma ta wuce bedroom dinsa tana sanya turaren wuta,wanda hakan din dabi'arta ce,duk da ko yaushe gidan ma gaba daya cikin turare yake,amma muddin abban yana gab da kwanciya sai ta kunna burner ta saka wani turaren,wanda yawanci yana riqe dakin har zuwa safiya,a gurinta sãahar ta koyi wannan,yana qarawa bacci dadi da armashi sosai. "Ummi na,ma yake faruwa?,kada kiji nauyina,ki gayamin" sake takurewa tayi kadan tana jin fargaba,ta saci kallon abban,abinda ya alamta masa da gaske akwai magana me muhimmanci da takeson gaya masa "Ehmmm,ina jinki ummi na" "Abba....." Sai ta kasa ci gaba "Ina jinki,fell free mana ummi" "Abba don Allah wata alfarma nazo nema,wadda nake da tabbacin indai ka amince tafi dukkan wani aiki da zanyi kyau da samun lada me tarin yawa,abba.....inason ka saurareni,sannan kayimin alfarma" "Ina jinki" ya fada yana tattara hankalinsa a kanta. Page 59 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 59 "na samu aiki abba.....amma ba irin aikin da kuke tunani zanyi ba,aiki ne na kula da mara lafiya" "Kula da mara lafiya kuma?" Ya tambayeta cikin mamaki,kai ta jinjina "Banda abinki ummi,ai ba sai kinyi da kanki ba,idan kikayi bayani,sai na biya a daukowa mara lafiyan me kula dashi har zuwa sanda Allah zai bashi lafiya" kai ta girgiza alamun a'ah "Ba jinya bace ta kullum kullum da ake kwance ba,abba yarinya ce marainiya,wadda take fama da epilepsy,tana buqatar kulawa ta wasu watanni daga gurin tsayayyar nanny da zata iya kulawa da ita da kyau" "Ikon Allah" kawai dr mamman ya fada,ya gyara zamansa yana kallon sãahar din,abinda ya bata damar dorawa "Zanyi aikin nan abba idan lamuncemin,bawai don neman kudi ba,sabida babu abinda na rasa daga wajenku,zanyi ne kadai saboda kwadayin lada wajen Allah,wanda na tabbatar hatta ku zakuyi tarayya a cikinsa,don Allah abba ka lamuncemin,haka kawai na tsinci kaina cikin kwadayin wannan ladan" kai ya gyada,maganarta gaskiya ne,saidai abun ya masa banbarakwai,diyarsa da aikin nanny a wani gidan?. "Duk maganarki haka take,to amma banda abun ummin abba,ko biya kikayi akayi kina da wannan ladar ai" zamanta ta gyara "Abba suna da wadatar da zasu iya biyan kowanne mutum,amma kudi basa iya taba siyan nagarta da cancanta" kai ya jinjina cikin dogon nazari "Abba bazan jima ba,tana samun lafiya shikenan" ta yanke masa tunaninsa ta hanyar fadin haka. Dole murmushi ya kubce masa saboda yadda tayi maganar cikin kwantar da murya tana langabe kai,da alama da gaske har cikin zuciyarta takeson tayi aikin. "Shikenan,kiban address,zan sa fahad ya yimin bincike akan nagartar mutanen gidan,don bazan bawa wani cikin yayyenki bama" "Kana iya tambayar anty farheen,ita ta fara bincikawa ma, neighbors na qawarta ne,kuma Alhmdlh basu da matsala,shi yasa aikin ya sake kwanta min a raina" fadin farheen din ya sake sanyawa hankalinsa ya dan kwanta "Zan nemeki" ta miqe tayi masa sai da safe ta wuce sashensu. Washegari da safe taga sauyin fuska daga wajen maama,sai tasha jinin jikinta,abban yana fita kuwa ta kirata,sababi ta fara tare da gaya mata itakam bataga dalilin wannan aikin ba,sosai ta kwantar da kai tana kwatanta mata amma maama tayi biris. Wuni guda ana abu daya har dare,shima abban ya gaza shawo kanta,sai da tayi kiran afifa. Itama afifan qin zuwa tayi da farko,ko da tazo dinma sai ta hadasu duka ta fatattakesu,daga bisani afifan tabi bayan maama,batasan ya suka qarke ba,tadai shigo tana harararta "Burinki ya cika new nanny" murmushi me kyau ya subucewa fuskarta,yadda tayi maganar ya tabbatar mata da ta shawo mata kan maama,saita rungumeta tana cewa "Allah ya barmin bestie na" murmushi itama ta saka "Ba wani dadin baki fa,bawai ance kije ki manta da mahmud ba" baya taja tana hade rai,afifa ta bita da kallo tana jan qwafa,itadai batasan sai yaushe sãahar zata dauka daga kan wannan aqidar ba,tana addu'ar Allah ya kawo mutumin da zai sauya wannan tsattsauran ra'ayin nata. *****Cikin takun nan nasa me cike da tsantsar qasaita da kuma wani irin aji suke nufar sassan hajiya qarama. Sanye yake da yadin baby cashmere me tsada dan qasar indai,wanda aka tsarawa wani irin dinki shi ba dinkin suit ba hakanan ba style na Pakistan ba,sosai dinkin ya qara masa kyau da kwarjini,ya kuma fidda qirar jikinsa qwarai dake dauke da siffar qarfi,duk inda ya gifta sai ya bada ajiyar sassanyan qamshin turarensa me masifar tsada daya sanya qamshin baya bajewa da wuri. Hnunsa riqe da siririn hannun fadeelan suke takawa zuwa sassan momy qarama,daga kan fuskarta har idanunta shabe shabe suke da hawaye,wanda rabi na shagwaba ne,rabi kuma tana ji har cikin zuciyarta yadda zatayi kewar mahaifin nata. Qasa qasa yake magana da ita tamkar wata babba "Calm down my angel,ipad dinki na wajen momy qarama,nayi alqawarin kiranki kullum through video calls,i will do my very best na dawo da wuri,new nanny dinki na nan zuwa" kafada ta maqale tana zirara da hawaye "Nikam banason wata nanny kuma,kai zanbi" murmushi ya saki saman miskilar fuskarnan tasa,sai ya sanya hannuwansa ya dagata ya azata zuwa kafadarsa yana ci gaba da takawa hadi da lallashinta cikin hikima. Duk duniya ita daya yake iya tsaiwa ya lallasa haka,banda a kanta,baisan koda hanyar yadda ake rarrashi ba. Suna shiga falon momy qarama na fitowa daga kitchen,hannunta riqe da mug dake cike da tea "Badai har ka fito ba?" Agogonsa ya duba yana amsata "Am ready to go,banason na wuce haka kada nayi missing flight" "Gaskiya ne" ta fada tana neman wajen zama,sai shima ya zauna saman daya daga cikin qawatattun kujerun dake falon "Na sanya jibril yayi magana da mutanen can,za'a kawo food stuff,idan akwai abinda babu ki gaya musu kawai,zan saka elyas yayi transfer ta account dinki,naki ne keda fadeela,shikenan koda wani abu?" Qasaitaccen murmushi ta saki,a duniya idan akwai wadda ta shigo rayuwa a sa'a to tana cikin sahun farko na jerin wadan nan matan,tana jin dadi,kanta kuma yana sake fasuwa a duk sanda toufeeq ke treating nata haka "Eh to,batun nanny din fadeela ne,yau in sha Allah zatazo,wannan karon ina saka ran an samu wadda zata iya kula mana da fadeelan in sha Allah,duk da naso ka ganta kafin ka wuce" miqewa tsaye yayi "Ba damuwa,indai tayi miki fine,just ta kula da aikinta shine abun buqata,and then ta fadi nawa takeson salary dinta,every month ko qasa da haka,duk ba damuwa indai zata kula da qa'idoji da sharuda" "Karka damu in sha Allah" tare suka sake fita da fadeelan,still tana maqale dashi. Kuka ta saka masa sosai security dinsa ya buda masa motar ya shiga,sai da yasa akayi kiean baaba ramatu,da wayau da dabara ta rabata da gurin tana kuka. Har suka fita a gidan yana jin sautin kukanta cikin kwanyarsa,ya lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi saboda wani bacin rai daya sokeshi,sannan ya budesu sosai yana jin wani ciwo cikin ransa,sam wannan ba itace kalar rayuwar daya tsarama kansa da kuma 'ya'yan da zaya haifa ba,wannan din wata bahaguwar rayuwa ce da qaddara ta tsago da ita cikin nasa shirin da tsarin ta kuma wargaza komai "AMEESHA" sunan da bazai taba gogewa cikin tarihin rayuwarsa ba,koda ace ya fita daga zuciyarsa da dukkan wani abu daya danganceshi. Cikin hanzari ya watsar da tunanin,ta hanyar ciro wayarsa ya laluba wata number da yayi alqawarin kira ya kira din,ya fara amsa wayar cikin wani irin sanyi bayan ya maida bayansa yayi relaxing a jikin kujerar. Koda ya gama wayar shuru yayi yana juya wayar a hannunsa,kamar wanda take sabuwa ga idanunsa ranar ya fara saninta,yau din gaba daya duk wanda ya kalleshi yasan yanayin komai ne cikin sanyi,yanayin da sam bashi a halittarshi. Tsaiwar motocin ya janye hankalinsa,ya daga kan nasa yana duban driver dinsa "What's happening?" "I don't know sir,but.... lemme check" ya fada,sai driver din ya bude ya fita ya barshi shi da guard dinsa guda daya dake zaune a gaban motar. Ko minti uku baiyi ba ya dawo da gaggawa "An samu matsala sir,harith ne ya bige wani tsoho......" "Ya salam" ya furta da sauri,ba tare da ya bari ya kammala bayaninsa ya bude qofar motar da kanshi ya sanya qafafunsa ya fito wajen,cikin sakanni guard dinnasa dukka suka fito suka take bayansa. Har a sannan tsohon yana zaune a qasa yanata bala'i,harith din da wadanda suke mota daya suna tsaye a kansa. Tsawa daya ya daka musu cikin bacin rai dukkansu sukaja baya suna sunkuyar da kai,ya ratsa ya tsakaninsu ya isa gaban tsohon,ya duqa zai dagoshi suka matso da nufin karbarsa,ya daga musu hannu alamun dakatarwa,ya tsugunna gaban tsohon bayan ya tadashi sosai. "Kayi haquri baaba,am very sorry,bada niyya bane na tabbatar,amma kayi mana afuwa gaba daya" dukka wani fushi da fada daga dattijon sai ya sauka,saidai idanunsa suna zube cikin na toufeeq din yana kallonsa,ya saki ajiyar zuciya "Shikenan,ba komai" "Ina fata baiji maka ciwo ba ko?" Ya sake fada yana kamashi ya miqar dashi ya tayar dashi tsaye yana kade masa jiki,cikin matuqar martaba da mutuntawa,duk da alamu da suka nuna babu wani sukunin rayuwa me yawa tattare da tsohon "Ba komai yaro,banji ciwo na,buguwa ce kadan a hannu na" "Dole a dubaka kada ya zame maka matsala baaba" cancel din mota daya yayi cikin jerin gwanon motocin,yace su miqashi asibiti a dubashi,sannan su kaishi ga iyalinsa, yayi kiran elyas da hannu,y qaraso cikin girmamawa,ya gaya masa abinda yake da buqatar a bawa tsohon "Okay sir" ya fada a ladabce. "Yaro!" Yaji muryar tsohon ta kirashi dai dai sanda yake shirin saka qafafunsa a motar,ya tsaya cak ya waiwaya yana dubansa "Ban taba tsammanin mutum me arziqi har haka zai iya tsaiwa ya saurari talakan da bai mallaki komai kamata ba,na gode qwarai da karamcinka,a duk lokacin da kaji tasowar fushi daga zuciyarka,ka yawaita ambaton A'UZUBILLAHI MINASH SHAIDANIR RAJIM, HASBUNALLAHU LA ILAHA ILLA HUWA ALAIHI TAWAKKALTU WA HUWA RABBUL ARSHIL AZEEM" Shuru toufeeq yayi yana kallonsa har ya shige motar harith ya rufe,ya zagaya ya tayar da motar "Sir..... it's getting late,we should leave" jikinsa a wani irin mace ya shiga motar yana maimaita kalmomin da dattijon ya gaya masa,daidai sanda jibril ya rufe qofar kira ya shigo wayarsa "Maji" sunan daya bayyana kenan wanda furtasa ya hade masa da faduwar gaban da baisan dalilin saukarta ba. Tattaro dukka nutsuwarsa yayi sanda motar ke dagawa ta dauki hanya sosai,cikin muryar da ita daya duk duniya yakewa magana da ita,duk da baisan hakan yana faruwa ba yayi mata sallama,sannan ya gaidata,ta amsa masa da wani irin kulawa "Ina fadeela tah?" Ta tambayeshi a sanyaye. Wani nauyi yaji ya saukar masa,ya shirya yana hanyar barin qasar,tun da bai shaida mata ba sai a yanzu?,a yanzun ma da itace tayi kiranshi?,yaya zataji idan ya gaya mata hakan? "Ko baka gida nayi kira da layin da zan sameta?" Ta jefa masa tambayar. Sosai nauyi ya sake kamashi,ya sani tana da wancan layin na baaba ramatu,to amma takan tsallake kowa tayi kiransa koda lokuttan da take da yaqinin baya tare da fadeelan,tun da jimawa ya fahimci tana hakanne don taji tasa muryar da lafiyarsa,tunda har yanzu hannayenta sun gaza iya koyar daukar wayar suyi kira a nata lambobin da layin domin suji lafiyarta,koda wasa.....koda sau daya......koda da gwaji. Wani al'amarine da yake damun qwaryar zuciyarsa qwarai cike da wata irin damuwa,amma ya gaza ta kowacce fuska.....ya gaza kawo gyara koda qanqani ne.......sau tari yanajin naqasu,gazawa da kuma kasawa,hadi da wata cikakkiyar tayawa me wawakeken girma daga rayuwarsa,amma baisan ta yadda zai gyara ba.....ta ina?,kuma a yaushe?,rashin matallafine ko kuwa?,duka shima bai sani ba. "Allah ya kiyaye,ya tsare, ubangiji ya bayar da dukka sa'a da kariyarsa,fatan alkhairi" ta fada a taqaice ta kuma gimtse wayar. Wani abune ya sauko ya daki zuciyarsa,take tayi wani irin rauni,yanajin wata irin kunyarta na mamayarsa, kunyar da dukka d'a na qwarai yakeji a lokacin da yayi wani abu na sabawa ga iyayensa,duk da a karan kansa yasha gayawa kansa shi din ba na gari bane......yanajin wani irin karyewa a tata muryar,kamar wadda kuka ke shirin subucewa,amma duk yadda yaso ya juya zuciyarsa ta bita don taji meye damuwarta ya kasa,sai ya soke hannayensa guri guda yana matsesu da wani irin qarfi,kamar yana shirin ballasu. ⚜️⚜️⚜️ Kebantacce falo ne wanda ke dauke da wasu qasaitattun kujeru da suka zama cikamakin cikar adon falon,bashi da wani girma,amma yana da tsari me matuqar kyau tare da jan hankalin me kallo. Saman daya daga cikin kujerun falon sãahar ce zaune,cikin kamilalliyar shigarta ta jilbab,wanda yake hade da doguwar rigarsa me dogon hannu,gefe da gefe na dan qaramin hijabin madin rigar a tsage yake,an masa wani irin ado daga bakin tsagar,farar kyakkyawar fuskarta ta fita sosai ta tsakiyar fuskar hijabin da wani irin kwantaccen kyau me daukan hankali. Tun farko shigowarta gidan take nazarinsa daya bayan daya,ta kowacce fuska gidan ya amsa sunansa,ya kuma sake bayyana mata tarin dukiya tare da arziqin da masu gidan suka mallaka. Ta taso cikin gata soyayya kulawa tsakiyar nasu arziqin da dukiyar,tun daga kan mahaifinta zuwa yayyenta,hakanan dangi na mahaifi da mahaifiya,amma a yau daya,cikin mintunan da basu gaza goma ba kanta yana shirin kwancewa ta zama 'yar qauye cikin gidan. Ba iya wannan ba,ta lura akwai tarin doka da bin tsari daga dukkan ma'aikatan gidan,kula gami da takatsantsan da tsoron kaucewa qa'ida,tun daga mai gadi,zuwa wadda ta rakota qofar sassan hajiyar gidan,kawo wadda ta kawota wannan falon da take zaune a yanzun tana jiran isowar matar,don ta ganta ta kuma karbeta gami da sake mata bayanin aikinta cikin gidan. Wayarta na hannunta a lokacin tana shaidawa afifa ta iso,afifan da tace sam ita ba zata iya rakota ta ganta a bigiren 'yar aiki ba,saidai duk da haka batayi fushi ba,tana maqale a online tana bibiyar dukka motsin bestie din tata. Qarar takalmin da ya fara ratso falon yaja hankalinta,saita kashe data dinta,ta kuma ajjiye wayar tsakanin qafafunta,ta daga kai tana aje dubanta daga guraben da sautin tafiyar yake fitowa. Guri guda idanunsu suka hadu nata dana hajiya qaramar. Daidaita kallonta ya sakeyi kan fuskar sãahar duk da bata kai ga qarasowa gurin ba,wani abu yana sauka a zuciyarta,tanason ta karanceta irin karatun kallon farko,tanata qoqarin daidaita zuciyarta da taji kamar ta tsaya guri daya,ta gaza wanzar mata da kowanne feeling akan sãahar din,ba kamar yadda takanji ba akan sauran dukka nannys din fadeela na baya da sukabar gidan. Page 60 *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Page 60 Cikin takunta na qasaita da nuna isa ta qaraso,ta dauke filon dake saman kujerar dake fuskantar sãahar din ta zauna,tana maida filon saman cinyarta,bayan ta dora qafarta daya saman daya "Sãahar ko?" Hajiya qaraman ta jefeta da tambayar sunanta kai tsaye,kai ta gyada mata cikin tabbatarwa gami da furta "Eh nice,barka da yamma" "Barka kadai" ta amsa mata tana qare mata kallo a fakaice,zuciyarta cike fal da mamaki irin sassanyan kyan da yarinyar ke dashi,babu alama ko digo dake nuna wahala ko buqata daga jikinta,asalima ko ita din sãahar din fatarta tafi tata nuna jin dadi da hutu,to amma ta wani bangaren tasan zata samu nutsuwa,zata samu sauqi itama,ilimi zallah ya nuna kansa tattare da sãahar din. Gyara zamanta tayi tana sauke qafafun nata,har yanzu idanunta akan fuskar sãahar din,kyanta yana sake bata mamaki "Nasan mrs sadeeqa ta gaya miki komai,so amma koda zata gaya mikin ba komai zata iyayi miki bayani ba kamar yadda ni zanyi miki.....da farko kina iya kirana da hajiya ko hajiya qarama ko mommy qarama,kusan nice shugabar gidan nan,kowa da kika gani ya kwana ya tashi cikin gidan nan qarqashin ikona yake,hatta dashi me gidan kansa da abinda ya mallaka ya kuma haifa......aikinki guda daya ne tal cikin gidan nan,kula da jikata tamkar ke kika haifeta,munason ta samu kulawa fiye da yadda zaki bawa kanki kulawa,saboda yanayin ciwonta,bamason kiyi nesa da ita,saidai idan tayi bacci ne, kuma koda kin koma naki dakin zakici gaba da dubata ne gudun faruwar wani abun,wankanta da tsaftarta yana wuyanki,abinda zataci kuma wannan ba dolenki bane" sai Tayi shuru tana maida numfashi. A nutse sãahar ta daga kai tana dubanta tare da nazarin kalamanta,wanda suke cakude da sautin izza a cikinsu "Fadeela.....ita daya muke da ita,itace sanyin idaniyarmu,farincikinta shine namu, sabawa daya daga cikin ayyukankin nan suna iya zama silar rasa aikinki" ci gaba kawai sãahar tayi da nazarin mommy qarama tana kuma kallonta "Kin fahimta?" A nutse kuma a hankali ta gyada mata kai "Da kyau,gidan nan yana da tsari,bawai zama bane kamar na sauran gidaje da kika sani,abu na gaba kowa aikinsa ya sanya a gaba,ba ruwan wani da shiga sabgar wani,ban yarda da zama tsakanin ma'aikata ana hira ba,kowa yayi abinda ya kawoshi ya wuce mazauninsa" shuru ta sakeyi tana kallon yadda sãahar ta kame,ta kuma bata hankali tare da manyan fararen idanunta tana kallonta "Magana ta qarshe" ta furta tana zama serious sosai "Nasan kinsan kalar ciwon da yake damun shelelenmu,right?" Kai ta jinjina tana ci gaba da sauraronta "Yauwa,akwai magunguna da takesha,so gaskiya banason yawan qwayoyin da yake yawan bata,saboda haka duk lokacin da ya dace tasha magani zan shaida miki,kota waya,ko na tako har zuwa sashen da kaina,ban yarda ba ko sau daya ki dauki magani ki bata ba tare da sanina ba" wanann maganar ita ta zowa sãahar din a hagunce,sai ta gyara zamanta itama,ta kuma dora qafarta daya saman daya ba tare da tasan tayi hakan bama "Amma why not ki yiwa likitan magana,idan zai yiwu da kansa zai fada,zai kuma rage mata,idan wasu kuma za'a yi exchanging dasu duka zai fadi" "Look!" Hajiya qarama ta fada tana fidda idanunta waje "Ina cewa ko minti biyar banyi ba da gaya miki rule's na gidan nan,who are you da zaki shiga lamarin da bai shafeki ba daga zuwanki?,na gaya miki hakanne don na taimakeki,bijirewa hakan zai iya shiga list na dalilan rasa aikinki" mamaki ne ya kama sãahar,tadan yamutsa fuska kadan tana juya maganar a ranta,kaf cikin maganar bataga inda tayi wani lafazi da bai dace ba "Ke ba kowa bace face nanny da zatayi aiki a biyata" zuciyarta da kwanyarta suka tuna mata matsayinta cikin gidan,sai ta zame qafafunta data dora saman na juna a hankali lokacin da taga hajiya qaraman na kallon yadda ta hade qafafun "Am sorry,zan kiyaye in sha Allah" "Kin samawa kanki lafiya" ta furta tana sake tsuke fuskarta,saida can qasan ranta tana cike da mamakin yarinyar,kwata kwata batayi kama da masu aiki ba,koda kuwa makaho ne ya shafa zaiji hakan,duk da sun nema well educated amma kuma wannan kamar ajinta ya d'ara wajen. Waya ta dauka tayi kira na qasa da second goma sha biyar,cikin minti daya tak matar ta iso,daya daga cikin masu aikin gidan,wanda basai ka tambayi hakan ba,saboda uniform da take sanye dashi,ta rusuna cikin girmamawa "Sabuwar nanny din uktie,a kaita sassansu,ki damqata a hannun baaba ramatu" "An gama ranki ya dade" ta fada cikin rusunawa,luggage din sãahar din ta dauka tayi gaba,don dukka nanny din data kasance ta fadeela ce a gidan,tana samun wani respect da kyautatawa darajar fadeelan,wannan haka tsarin gidan yake. Har takai qofa momy qarama na rakata da kallo,batasan me yasa yarinyar ke jan hankalinta har haka ba,yadda take takunta a nutse daya na bin daya kadai yana nuna mata kamar akwai wata extra qasaita a jinin yarinyar "Sãahar" ta kirayi sunanta da dan kaushi kadan,dakatawa tayi sannan ta waiwayo tana dubanta "Mrs sadeeqa nada matuqar kirki,tana kuma da darajar da zata baki dukkan wata kima da martabawa a gidan nan,ba tare da ko na miki screening ba na dauki aikin kula da 'YAR SO na baki,ki kula da kyau,kada kuma ki gota iyaka" har yanzu kalaman matar basu daina bata mamaki ba,sai ta saki wan siririn murmushi ta jinjina kai kawai,sannan ta juya a nutsenta tana barin falon,tabi bayan ma'aikaciyar. Kamar ko yaushe katafaren ni'imtaccen falon nasu a tsaftace yake sannan killace,iskar na'urar sanyaya daki tana busawa ta kowacce kusurwa na falon tana cakuda da qamshin fresheners. Sau biyu me aikin tana sallama kafin qofar glass ta falo na biyu ta bude,baaba ramatu ta fito cikin kamalarta da carbi a hannu,da alama tana azkar din yammaci ne "Qaraso mana,ke da baquwa ce?" Tayi tambayar idanunta akan sãahar dake tsaye a baya "Nanny din fadeela ce hajiya tace a rakota" juyawa baaba ramatu tayi tana duban sãahar,sai kuma ta sakar mata murmushi "Maraba,sannu da zuwa,Allah yasa tana jin hausarmu" tayi maganar cikin tantamar sãahar din tasan zo na kasheka da hausa. Murmushi ne ya subucewa sãahar din,karon farko tun shigowarta cikin gidan,yadda dattijuwar tayi magana cike da barkwanci yana burgeta "Ina yini?" Ta fada a nutse don kore shakku daga zuciyar baaba ramatu,a mamakance riqe da baki t juyo ga sãahar "Ma sha Allah,lafiya alhamdulillah,sannu da zuwa" "Yauwa sannu" ta maidawa baaba ramatu "Shigar mata da kayan nata ciki,dazu dazu aka kammala kintsa dakin muje ko 'yata?" tayi maganar da sakakkiyar murya tana yi mata jagora ga tsararren hallway din da zai sadaka da dakunan baccinsu. Daya daga cikin qofofin dake kulle baaba ramatu ta tura ta shiga tana cewa sãahar "Bismillah" sai tabi bayanta,bakinta dauke da addu'ar shiga sabon guri ko zama a baqon guri. Daki ne me yalwa wanda yake dauke da qawatattun kayan gado 'yan asalin qasar turkey,komai na dakin kwantacciyar kalar yellow green ne me kyau da daukan hankali,kalolin dake qarawa idanu qarfin gani,dakin nada wani irin tsari me burgewa,bai cika girma ba,hakanan bai cika qanqanta ba. "To ga dakinki nan,idan kina da buqatar wani abun kina iya magana a kawo miki,aikinki kawai ki kula da fadeela" baaba ramatu ta fada cikin murmushi. Murmushin itama tayi "Bana buqatar komai,amma ina ita babyn?,inaga ita ya kamata na fara gani ko?" Qaramin murmushi ya sake sauka a fuskar baaba ramatu,haka kawai kallon farko taji sãahar tayi mata,fadeelan bata tana nanny irinta ba,yawancinsu tun daga hanyar shigowarsu gidan zuwa hanyar isowarsu dakin suke rudewa da kalle kalle da kuma santin tarin dukiyar dake jibge a gidan,hakanan duka cikinsu babu wadda ta taba tambayar a kaita gurin wadda tazo gidan aiki dominta,har sai baaba ramatun ta buqaci hakan "Tana dakinta,tun dazun taqi fitowa rigima takeji,tunda babanta yayi tafiya dazun ya barta take fushi da kowa harda ni dana daukota daga waje,ko abinci taqi ta karba" baaba ramatu ta fadi tana dan dariya. Kai sãahar ta girgiza tana dan murmushi "Ayyah,tana kewarsa ne tun yanzu,muje na gani ko zata yarda ta fito" gaba baaba ramatu tayi tana dan yi mata hirar fadeelan,yadda halayyarta da dabi'unta suke. Qofar dakin dake facing ta sãahar din baba ramatun ta tura ta bude, tsararren dakinta cikin kalolin white cream ya bayyana,wani irin daki da yafi kama da dakin hamshaqiyar mace me aure,dakin dake aka sanya masa dukkan wani abu na buqata jin dadi da kayan qawa,wanda hakan bai sanya ya cika tarkace da yawa ba,sai wani irin kyau da tsari na musamman daya bayar,ga tasirin tsafta sosai a tare dashi,ko ina qal qal yana fidda qamshi me dadin gaske. "Fadeela" baaba ramatu ta ambaci sunanta sanda suke shiga dakin. Tana nade cikin duvet,ko motsi batayi ba "Ki tashi ga sabuwar me kula dake tazo ganinki" kafadarta ta maqale,ta kuma bubbuga qafafunta "Bana sonta" idanu baaba ramatu ta zaro waje tana kallon sãahar cikin rashin jin dadin kalaman fadeela,sãahar din da siririyar muryar fadeelan ta sanyata dariya tare da qarin dariyar zallar quruciyar data fuskanta tattare da ita "Kul na qarajin kince bakiso wani,bakya sonta?" "Eh ta koma,saboda nima daddy ya tafi...." Ta fadi tana yaye duvet din da sauri,sai kuma ta tsaya cak tana rarraba kallonta akan fuskar sãahar dake jifanta da murmushi. A hankali ta zame duvet din duka daga fuskar tata tana ci gaba da kallon sãahar. Waiwaya sãahar din tayi ta kallo baaba ramatu "Baaba a kawo abincin nata" "To shikenan" ta fadi tana juyawa ta fice daga dakin,cikin ranta tana jin cewa sãahar din zata bada fiye da abinda ake zata. Bata taka ba taci gaba da kallon fadeela tana murmushi,har sai da yarinyar ta miqe ta zauna sosai da kanta,sannan ta sauke hannuwanta ta taka zuwa bakin gadon ta zauna daga gefanta "Kiyi haquri" sãahar ta fada tana kallonta,tana iya ganin sanda ta waiwayo da sauri tana kallonta,saita sake mata murmushi "Ummmm" "Ba abinda kika yimin fa amma kike cewa nayi haquri" "A'ah,kince bakya sona,na dauka nayi miki wani abun" kai ta girgiza da sauri,saita shagwabe mata "Abby ne ya tafi ya barni,bayan yace bazai sake tafiya ba dani ba" siraran hannuwan yarinyar ta kamo tana kallonsu,babu wata qiba sam,kamar bata cin wani abu da zai gina mata jiki,duk da daular da take ciki,saidai kyau da gogewar fata kawai "Abbynki ba zaiyi qarya ba,lallai uzurin da sai yayi tafiyar ne kuma ba tare da ke ba ya kamashi,but na tabbatar bazai dade sosai ba" murmushi ya qwacewa fadeela "Shima haka yacemin" "So....you must trust him" kai fadeela ta jinjina tana murmushi "Wait.....yanzun kinci abinci?" Kai ta girgiza fuskarta na sake narkewa,ido sãahar ta zaro "Eehhhh,bakyason abby ya dawo yaga kin zama qatuwa?,baby fadeela ta zama 'yar lukuta?" Dariya fadeelan ta saki,yadda sãahar din ke bubba hannayenta tana mata sign na qiba "Inaso auntie,inaso" "Good,chubby fadeela" "Yes anty,not slimy,a chubby,a daina tsokanata a school" "Aha,oya gate up" tayi furucin tana miqa mata hannunta,sai tayi hanzarin dora nata hannun,cikin kulawa sãahar ta riqeta sosai ta sauko da ita tana karantar yadda walwala da farinciki ya maye gurbin bacin rai data dawo ta sameta a ciki,wani irin nau'in tausayinta ya sake saukar mata,saita ajjiyeta saman lallausan carfet din dake gaban gadonta,itama ta zauna akai,ta fara diban abincin tana bata a baki. "Kin iya feeding mutum like my abby" murmushi sãahar tayi "Really?" Kai ta gyada mata "Okay,nayi alqawarin zaifi na Abby din naki gaba kadan. Wani dariya me cike da nishadi fadeelan ta saki, sãahar ta tsaya kawai tana kallonta,an gaya mata tana da wuyar sabo sosai,nannys dinta suna jimawa kafin ta fara sakin jikin dasu,duk da ba wani dogon zango sukeyi ba a gidan,amma sai gashi ita lokaci guda ta sake sosai da ita. uhmmm,ga sabuwar nanny a sheqar da batasan ta waye ba, za'a dore kuwa?,to lokaci shi zai nuna mana,asha hutun weekend lafiya,fatan alkhairi a gareku gaba daya,masu comments ina gani na gode sosai,gurin amsa comment dinne baya dannuwa,but am really appreciating *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Page 61 Tsaf ta gyara gurin bayan ta gama bata abincin,duk da akwai wadda ke da alhakin hakan amma bata jira ba,ta shiga toilet dinta ta wanke hannunta,ta zari towel din dake ajiye musamman saboda goge hannu tana gogewa baaba ramatu ta shigo. Tayi mamakin yawan abincin da taga taci "Ke ai baki iya bayarwa ba,new nanny ta fiki iyawa" baki ta kama tana dariya "'yeee,zakici qaniyarki,yau nice ban iya bada abinci ba?,tun kina koyar yadda akecin abincin to ni nake baki don gidanku" dariya ta saki tana buga tsalle a gadon,abinda yasa sãahar murmushi kenan tana dan binta da kallo,abinda ta karanta,yarinyar nada sauqin kai,sanann irin mutanen nan ne masu son abinda zai nishadantar dasu,a yadda ta karanta gasa da minti arba'in a tarayyarsu,tana bugatar kulawa da zata dace da hankalinta. A dakin ta barsu,ta dauki excuse don ta kintsa kanta da dakinta. Tana shiga ta zare mayafin jikinta ta ajjiye saman gado tana furzar da iska daga bakinta,yarinyar ta shiga ranta lokaci guda fiye da yadda tayi zaton zata kasance,wani abu takeji game da ita a ranta,tana jin kamar daga jininta ta fito. Sai data gama shirya kayanta a wardrobe tsaf ta fidda komai ta ajjiyeshi a muhallinsa,bath stuff dinta ta kaisu bandaki,sannan ta zare kayan jikinta ta shiga bandaki tayi wanka. Koda ta fito cikin wata doguwar riga ta lallausar auduga ta shirya,ta gabatar da sallah,zuwa lokacin dakin ya fara kama qamshin turarukanta masu sanyin qamshi. Hijabinta ta zare ta tsaya bakin mudubi tana taje gashinta,ta gama tana hadeshi akayi knocking,ta qarasa a nutse ya yafa qaramin hijab ta bude gofar. Me dafa abincin sashence,itama sanye da uniform dinta,saidai su nasu akwai banbancin color dana sashen hajiya qarama dana sauran ma'aikatan dake gidan,nasu din fari ne qal da ratsin bagi "Its time for dinner maa" ta fada cikin rusunawa "Alright,thank you" ta fada cikin sauqin kanta da ba kasafai yake bayyana tattare da ita ba. Ciki ta koma ta fidda slippers din da aka bata cikin wata jaka,wanda qa'ida ne na dukka ma'aikacin da zai fara aiki cikin gidan,ta sanya a qafafunta,saita kashe wayarta ta jona a charge da nufin sanda zata dawo ya cika,sai tayi kiran dukkan wanda ya kamata,don batason suyi kiranta bayan bata nan,ta maida qaramin hijabin daya sauka har kusan qugunta sannan ta fito a dakin. Kai tsaye dakin fadeela ta koma,ta sameta sunata rigima da baaba ramatu akan kayan da zata sanya, kowa da yake gidan ya saba da wannan agenda din nasu,sosai take maidata kamar kakarta. Cikin hikima da dabara ta fidda mata wasu kayan,da lallashi ta sakata ta sanyasu,bayan tayi mata alqawarin bata zabin kayan baccin duk da takeson sakawa,sannan suka fito cin abincin ita da fadeela da baaba ramatu. A gasa sãahar ta sauko musu dasu,sabanin yadda suka saka ci a saman table. Sãahar ta buda abincin tana gare masa kallo. Abinci ne yankunan Europe da Asia,saita ajiye murfin warmer din tana duban fuskokinsu. Ba wani karsashi a fuskar baaba ramatu,amma fadeelan har zumudin a zuba mata takeyi. Damar zubawa ta bawa baaba ramatu,ita kuma ta zubawa fadeela,sannan ta zauna ta bata da kanta kamar wancan lokacin,sai data tabbatar ta qoshi sannan ta zauna sosai,kadan ta tsakura ta ture,don ba jituwa tsakaninta da abinci, especially ma abincin dare, tafi qaunar coffee fiye da komai a rayuwarta. Suna daki tana shirya fadeelan wadda taketa gogarin bata labarin abby dinta, magana daya biyu saita sakoshi, murmushi kawai sãahar ke binta dashi,tunda batasan komai a kai ba,kawai dai tana ji a zuciyarta cewa yarinyar ta rabauta da uba daya san darajar diyarshi,yake bata dukkan kulawa,ya kuma damu da damuwarta. Ruwa me dumi sosai tayi mata wankan dashi,ta shiryata cikin wasu kayan bacci masu taushi dai dai da shekarunta,ta sake mata gashinta yadda zatafi in dadin kwanciya. Har wani lumshe idanu fadeela keyi,tana jin dadi sosai a jikinta "Aunty nanny kin iya wanka wallahi" dole dariyar da saahar batayi niyya ba ta qwace mata,ta rige siraran hannuwan fadeelan "'Wankan ma akwai wanda yafi wani dadi?" Kai ta gyada "Sosai,na abby da naki yafi dadi, amma shi abby sai ya daina yimin, waina girma,sai randa na fadi bani da lafiya shine yakemin" ta garasa maganar cikin karyewar murya dake nuna itama tasan halin ciwon da take ciki "Aunty nanny,abby yace wai zan warke watarana hakane?" Qwalla ce ta cika idanuwan sãahar,saita jawo ta ta zaunar da ita saman cinyoyinta "In sha Allah, kina addu'a?" § . 865 4C16 "' Ai ban iya ba" fuskarta ta dago ta shafa, komai nata siriri,saita saki murmushi "Zan koya miki,zamu dinga sallah abby's chubby" magaleta tayi tana dariya saboda sunan ya mata dadi. Dai dai lokacin aka turo gofar dakin fadeelan. Dukkansu suka daga kai suna duban me shigowar,mommy qarama ce,cikin wasu kayan bacci da suka zubu,tayi rolling da wani qaramin mayafi kalar kayan,ikinta sai fidda qasaitaccen qamshi yakeyi. Miqewa fadeela tayi ta isa gurinta,saita miga hannu ta ruqota suka qaraso cikin dakin "Mummy amma abby bazai kori wannan nanny din ba ko?,ita ina sonta sosai" ta fadi tana dora kanta akan cinyar hajiya garama. Hannu ta dora saman kanta tana shafawa,idanunta akan fuskar säahar Нд "'Indai ta kiyaye doka da qa'idoji,sannan ta riqe alkinta ta kula dake yadda akace mata" "Mommy tana kula dani sosai" tayi maganar da accent na quruciya a muryarta "Okay,jiki wajen baaba ramatu kice ta baki kayan dana bata ajiya", fellawa tayi da gudu ta fice, saita tattaro hankalinta kan säahar. Idanu tadan kafeta dashi,wasu lokutan takanji shakka da kokwanto akan yarinyar,tana da wani irin kwarjini da bata ganinsa saman fuskar kaf ma'ikatan gidan sai ita,sannan daga shigowarta zuwa yanzu ta fahimci kwata kwata bata rawar jikin da dukka maaikacin daya shigo gidan yakeyi,kamar zai kwanta a hanyarta tabi ta kansa,dazu data kira mrs sadeega ta gaya mata haka yanayin ta mrs sadeeqa ta gaya mata haka yanayinta yake,bata da son yawa surutu da kuma hayaniya,MISKILA CE. Ад miskilar data fadi shi yafi qara kwanta mata,saboda tasan muddin tana da wanna dabi'ar ba zata saba da kowa ba,ba kuma zata zauna tayi hira da kowa ba akan abinda ya shafi gidan ba,aikinta kawai zata yita yi babu waiwaye ba duban kowa. Wata jaka ta ajjiye mata tana Kallonta "Ya lafiyar fadeelan?” "Alhamdulillah" ta amsa mata a taqaice tana kwashe cosmetics din yarinyar data bazasu a gasa "Madallah,wadannan... ...sune magungunan ta,zaki dinga bata da safe da rana bayan ta dawo daga school sai da dare idan zata kwanta,kamar yanzun kenan,ba'a son fashi ko daga qafa,ki kula da kyau,ba kowa ake nunawa maganinsu ba,idan ya qare ni kadai zaki gayawa,zan sake kawo wasu,a ciki akwai tablet dinta,u are educated a yadda aka bani information dinki,so koda baki taba amfani da ita ba zaki iya hada mata ita,na sanya an dora komai daya dace a kanta,so amfani kawai zata fara yi da ita" kai ta gyada kawai "Ki kular mata da tab,na tabbata bakisan darajarta ba,abace me tsada daga kamfani me daraja ta daya a duniya" sam sãahar din batasan murmushi ya subuce mata ba sai da taga hajiya qaraman na kallonta sosal,saita buge da gyada kai "In sha Allah " ta fada hankali kwance,cikin ranta tana mamaki,haka 'yan aiki sukeji?,haka ake dizgasu? ta godewa Allah data rayu a gidansu taga yadda ake karrama masu aiki,ta godewa Allah da bata taba sha'awar dauko me aiki a ravuwarta ta baya ba,ashe suma suna jin babu dadi idan aka fadi wani kalma na qasqanci a kansu,suma mutanene kamar kowa,a yanzun abinda yasa itan bataji wannan ciwon ba,saboda tasan daga inda ta fito, tablet zata iya cewa dai dai take da 'yartsanar wasanta,batasan nawa ta lalata ba tun kafin tayi hankali,ta yayunta da maaminta kafin ta mallaki nata kala kala. "Muddin wani abu ya sameta zan cirene cikin albashinki" wata dariyar taso taso mata amma saita danne ta sake gyada kai. Dauke idanunta hajiya qarama tayi daga kanta,tana mamakin yadda maganar bata dameta ba,ta fada ne don ta mata ciwo,amma bata alamun wannan a tare da ita ba. "Nawa kika yanke salary dinki,monthly ko weekly?" Hajiyan ta fada bayan ta miqe tsaye "Wannan ba matsala bane,aikin yafi salary din muhimmanci" da sauri ta waiwayo tana dubanta,maganar taba fusgar hankalinta,sai ta dawo da baya tana tsareta da ido "Ban gane ba,meye alaqarki da yarinya da aikin yafi miki kudin muhimmanci?,ana aiki don kudi ne haka ne?" Kai ta gyada tana lumshe ido. Ta girgiza kanta a nutse "Ba haka nake nufi ba,shi kula da yaro lada gareshi me tarin yawa,koda ba'a biyaka a nan duniya ba,ladanka na qiyama yana jiranka,abinda ubangiji zai maka sakayya dashi,yafi kudin da za'a baka" qogarin dai daita yanayinta hajiya qaraman tayi tana jinjina kai,sai ta juya ta fice kawai ba tare da tace mata komai ba. Da kallo ta bita har ta fice,saita dauke dubanta daga kan hanyar tana qoqarin fidda abinda zuicyarta keson suranta mata,ta jawo ledar ta buda kayan da suke ciki. Tashi tayi ta yiwa tab din gurin ajiya me kyau,sannan ta dawo ta zazzage magungunan. Zama tayi sosai tana binsu da kallo,mamaki yana dan kamata,wasu irin tablet da babu rubutu a jikin robobinsu bare kaga bayanin da kowanne magani ke zuwa dashi. Ta jujjuya mazuban dukka plain fararen mazubi ne, abun sai ya daure mata kai,ta dinga juyasu daga gaba zuwa baya har batasan adadi ba,kanta ya daure sosai,gefe guda na zuciyarta kuma ya cika wa wasi wasi da fargaba. Motsin shigowar fadeela ya sanyata ajiye bottle din,ta daga kai tana dubanta,hannunta riqe da wata babbar sweet,cikin sakalci da salo na shagwaba ta zauna gefanta "Uncle dina ne ya kawomin,yace gobe shima zaibi abby na,munyi waya da abby ta wayarshi, yace a barmin tab dina a bude zai dinga kirana kullum ta google meet muyi video call" cikin dauriya ta saki murmushi "In sha Allahu" ta fada tana tattare kayan magungunan,ta maidasu cikin ledar,ta sake kadema fadeela gadonta ta saisaita sanyin ac din dakin da kuma hasken,ta rakata toilet tayi brush suka dawo tare. Sai data tabbatar tay bacci sannan ta zauna gefanta tana kallon doguwar fuskarta,abubuwa da yawa data taras a gidan suna dawo mata kanta,tun daga shigowarta gidan kawo yanzu,haka kawai jikinta yake bata akwai wani qalubale,akwai wani abu tattare da rayuwar yarinyar,ina mahaifiyarta?,don daga baaba ramatu har hajiya qarama tasan sunyi girman da ba zasu haifi kamar fadeela ba,to amma tana da mahaifi,shi din me yasa bazai zauna kusa da yarinyarshi ba? ko don babban lalurar daka iya zamewa naqasu ga rayuwar mutum?. Da wannan tunanin ta tashi daga gurin ta fita a dakin bayan ta tofeta da addu'a ta shafeta da ita,ta rufe dakin ta shige nata ba tare da tabi takan magungunan da hajiya qarama ta bata ba,haka kawai ranta da jikinta taji basu aminta data dauka ta bawa yarinyar ba. Zuwa lokacin wutar dake bada haske a hallway din ta sauya launi,alamun dake nuna lokacin baccin yayi kenan. Sai da tayi sallar shafa'i da wutiri sannan ta zare wayarta a charge,ta zauna sosal saman gadon ta shafe jikinta da addu'o'i sannan ta kunna wayarta tana duba time. Taso shigowa da wuri ta kira kowa amma lokaci ya qwace mata sanadiyyar shigowar hajiya qarama,yanzun kam dare yayi ba zata iya kiran kowa ba a cikinsu. Wayar na gama daidaituwa saqon mahmud ya shigo har guda uku a jere,yau kam dai ta duba,saqon fatan alkhairi ne tare da nuna zallar kewarta da zaiyi,afifa ta gaya masa ta samu aiki amma ba'a kano ba. Ko data gama karantawar batayi reply ba ta soma kiran afifa,bugu biyu ta daga "Nanny bestie,me ya faru da wayarki tun dazun switched off?,ko gidan basa bari a daga waya ne?" Ta garashe maganar cikin shaqiyanci da zolaya "Ban sani ba,mu hadu a WhatsApp" daga haka ta gintse kiran,ta sani ai tunda ta zabi wannan aikin ta shiga uku gurin afifa,qilan sai tayi kamar zata zautata da tsokanarta. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Page 62 Bata sake tsokanar tata ba bayan sun hau online,suka gaisa saidai ta tambayeta ya vanayin alkin "There's is something terrible a cikinsa" ta amsa mata har zucivarta tana in akwai wani abu "'Kaman yaya?" Afifa ta tambayeta cikin fargabar kada ta sake fadawa wata cutarwar kwatankwacin na baya. A nutse ta gaya mata komai,ba jimawa voicenote me yawa. Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta gama saurara,dukka maganganun afifa akan hanya suke,kuma taji dadin yadda ta qwarara mata gwiwa "But afifa how she can survive without medication?" "Yes,her illness needs treatment,idan ba haka ba abun zaiyita worsening ne,so that zanyi prescribing miki wasu magunguna,su zata dinga sha zasu taimaka mata in sha Allah,but kafin sannan ki samo history na ciwon nata,yanayin yadda yake mata idan ya tashi da kuma asalinsa,ki ajiye wadancan,tunda babu sahihanci a cikinsu". Sosai suka tattauna da afifan,sai taji dadin shawarwarin data bata game da yadda zata kula da fadeela din,shawarwarin da afifan ta bata saita tsinci kusakurai da yawa game da yadda ake kula da yarinyar. Basu rabu ba sai can dare,don daya ma ta kusa,ta sauka ta daura alwala ta gabatar da sallar dare kamar yadda ta saba,ta miga bugatunta wa ubangiji idanunta cike fal da hawaye. Wannan din wani sirrin rayuwarta ne da babu wanda ya sani sai afifa. Data kammala fita tayi ta dubo fadeela,ta sake gyara mata kwanciya da rufa gaba daya sannan ta jawo gofar dakin ta fice,a ranta tana jin rashin kamatar barinta ta dinga kwana ita daya alhalin tana da irin wannan lalurar,anytime zata iya far mata. *WASHEGAR I* Komai na gidan ta fuskanci cikin tsarin yahudanci zata iya cewa yake tafiya,safiya a garesu tamkar dare ne,don ba da wuri suke tashi ba sam,fadeela ce kawai za'a yiwa abincin tafiya makaranta,a kuma shiryata ta wuce. Kowa rayuwarsa yakeyi,saidai idan an hadu a gaisa,kowa yayi aikinsa kuma ya kama gabansa,sai idan wani aikin ya sake hadaku. Tun bayan data shirya fadeela driver ya dauketa saita shiga dakin yrinyar,da kanta ta yiwa dakin gyara,ta fidda duk wani sharp objects da zai iya cutar da ita idan ciwonta ya tashi,ta gyara komai ta sanyashi a muhallin da koda faduwa tazo mata ba zata cutu ba Teddy's manya tayi list cikin abubuwan da fadeelan ke bugata,tanason aje mata agurare mabanbanta ya zama ko ina dakin bai cika da wani abu me tsini ko tauri ba,tashin ciwon unexpected abu ne,tanason tayi abinda zai zame mata first aid koda ba wani a kusa da ita. Tana tsaka da aikin me gyaran dakin ta shigo,sai kawai ta sallameta,da kanta ta shiga walking closet dinta,cike yake da kaya masu kyau da tsada na alfarma,saidai alamu sun nuna akwai kayan da ba'a sanya mata su,ko ba'a damu da saka mata su din bane oho ta gyarata fes ta sake jera komai. Bata fita a dakin ba sai garfe daya,sai sukayi clashing da baaba ramatu. Baya ta jaye mata cikin girmamawa,fuskarta da fara'a tace "Naji shurun yayi yawa nace bari na dubaki" murmushi tayi "Ina ciki ina aikin gyaran dakin fadeela" "'''ah,ina mabaruka?" "Ni na sallameta,akwai gyaran da na yiwa dakin ne" "To madalla,sannu da qoqari" baaba ramatu ta fada,har cikin ranta tana jin cewa yanzun fadeela ta samu nanny din da zaiyi wuya korarta,tun daga jiya zuwa yau taga tarin banbamce banbamcen da sauran masu kula da itan da tayi a baya. Cikin sati guda kacal ta gama fahimtar dukkan wasu tsare tsare na gidan,sannan itama ta gama tsarawa kanta yadda zata rayu da kowa. Cikin sati guda din nan kacal suny! wani mugun sabo da fadeelan,yarinyar tana da wani irin shiga rai da kuma masifaffen wayo dake da alaqa da kaifi basirarta a makaranta. Sannu sannu dukkan wasu ayyuka da sauran ma'aikatan gidan kewa yarinyar,kama daga abincinta,gyara dakinta,hada kayan wankinta a bayar zuwa laundry room duka ta qiya kowa yayi mata,dukka sun koma wuyan sãahar. Wani irin girma take bata,tana jinta a ranta ta zarta mata kowa a gidan,kafin tayi wata guda sai ya zamana sun koma tamkar ya da uwa,hatta da dakinta idan zata koma sai bayan yarinyar tayi bacci,data farka ta sauko a gadonta komai asuba zataji ana mata knocking,indai taji wannan bugun tasan fadeela ce,tare xasu qarasa kwanan,ayi shirin makaranta. Ayyukan makaranta kuwa shima ya koma aikin sāaharlesson dinta da ake mata still dai shima taqi malamin,a nan ne fadeela ta lura kamar akwai rauni wajen karatun addininta,da kanta ta zauna ta tsara yadda zata fara koya mata,duk da ason ranta yarinyar ta shiga islamiyya,to amma batasan yadda zata tunkari masu gidan da maganar ba. A nata bangaren ayyukan fadeela gaba daya nishadi suka sanyata,sun debe mata kewar yara sosai,sun kuma nesantata da dukkan wani namiji kamar yadda take da muradi,tana jinta kamar a killace,babu idanun kowa a kanta,ta samu cikakkiyar nutsuwa da gamsuwa cikin gidan,hajiya qarama da takejin kamar zata zame mata matsala ko akwai wani illa tare da ita,saita fuskanci ba wani damuwa tayi da sassan ba,saita share kwanaki ma bata shigo ba,sai idan fadeela taje mata. To amma,shin da gaske fadeelan jikarta ce?,idan jikarta ce ta yaya mu'amala irin wannan zata wanzu tsakanin jika da kaaka?,tanason sanin labarinsu,tana son sanin ainihin wacece hajiya garama a wajen fadeela,to amma ita din bata cikin sahun mutanen da suke shiga lamuran da sukayi yaqinin basu shafi rayuwarsu ba. *****K'arfe biyar da wasu yan mintuna na yammacin ranar ne,dai dai sanda madaidaiciyar motar me kyau ke shigowa cikin gidan,wanda da shigowarta da isowar masu aikin gidan duka duka bazaiyi minti biyu ba,cikin gaggawa kowanne ya iso,saboda sanin mamallakiyar motar,kowa yana gudun tsira da mutuncinsa. Bude murfin motar tayi,sannan ta qwalawa daya daga cikinsu kira,matsowa tayi da gaggawa,bakinta dake tauna chewing gum ta motsa "Daukarmin hand bag dita" "Tom" ta fada tana buda daya side din da jakar take ta dauka ta riqe "Kai jama'a,mutum ba uban kowa ba sai shegen ji da kai da izzar banza" tayi gorafi gasa qasa,saidai ya fidda sautin gunaguni "Me kike cewa?" Labiba ta tambaya taba juyowa,murmushi tadan saki a rikice "Bab.....babu komai,cewa nayi maraba da dawowa" bata sake cewa komai ba ta fita a motartabar musu aikin kashewa da rufeta hadi da rigo mata key din. Cikin jin kai take takawa,sanye da wani skinny jeans da yabi jikinta sosai ya lafe, kamar a jikin nata aka dinkashi,manyan mazaunanta da suke da wani irin dan banzan tsini sun fita sosai,saidai kuma shafaffen qirjinta dake boye a t shirt din jikinta ya kawo cikas waien cikar adon da akesonyi da bayyana abinda akeson a bayyana din. Kitson attache ne a kanta daya zuba har gadon baya,ya bullo da qasan gantalelallen mayafin data yane kanta dashi wanda iyakarsa wuyanta. Har ta doshi sassan hajiya qarama suka shaida mata ta fita, amma ba nisa tayi ba,saita sauya akalarta ta wuce sassan fadeela,tanason ta saba da yarinyar,to amma matsalar ita batasan yadda zata shawo kanta su shaqu ba. Dai dai lokacin da sãahar ke zaune a madaidaicin falonsu na biyu,suna zaune qasan carfet ita da fadeelan, ita tana cin abinci sãahar din na monitoring dinta,a daya bangaren tana duba homeworks din da aka basu ranar a makaranta. Sanye take da brown din chiffon gown budaddiya sosai,sai kanta data yafawa vail na plain chiffon din shima brown da bai garasa na jikin rigar haske ba, kyakkyawar fuskarta tayi fresh,tes take fatarta na nan da glowing dinta,babu digon ko tabo ballantana qurji,pink lips dinta sai shegin lips balm sukeyi,zara zara yatsunta take sanyawa tana buda book din page by page tana ganin performance din fadeelan a homeworks dinta na baya. Sau biyu tana buda baki da niyyar yin magana tana dora mata yatsa akan lips tace "Shshshsh" tasan tanason yin Santi ne akan abincin da takeci, wanda säahar dince yau ta dafa. A karo na uku data hanata saita langabar da kai "Please aunty ki barni nace wani abu mana" yadda tayi maganar yayi masifar baiwa sãahar dariya,saita rufe littafin tana murmushi idanunta akan fadeela "Say it fadee" "Wallahi anty ban tabacin abinci me dadin wannan ba,kamar daga aljanna aka kawosa" ba shiri dariya sosai ta kubcewa saahar,saita miga hannu ta dauki pillow ta saka mata daga gefanta "'Bari na tareki kada santi yasa ki fadi" dariya itama ta saki sukaci gaba da yi tare "Please aunty nanny,zaki ci gaba da dafamin abinci?,harda wanda zanje school dashi don Allah,nasan abincina sai yafi na kowa dadi" idanu ta lumshe tana gyada kai,a yadda takejin fadeela kamar jininta babu hidimar da bazata ivayi mata ba "Alright,amma idan satin nan ya wuce baki gama haddace suratul a'alah ba,to zan daina,kin yarda?" "'Na yarda aunty,nayi algawarin jibi zan gama" ido ta ya fidda tana dubanta da mamaki "Really?" Kai ta jijiga mata alamun da gaske take. "Hi fadeela" muryar labiba dake tsaye a kansu ta ratsa kunnuwansu,dukkaninsu babu wanda yasan da shigowarta bare wanzuwarta a gurin. Daga kansu sukayi kusan lokaci guda suka dubeta,dai dai lokacin idanunsu suka gauraya da juna ita da sãahar. Dan ja baya kadan tayi cikin yanayin dake nuna qaramar razana "Ya salam" ta furta can gasan ranta,tana hadiye wani abu me tauri a maqoshinta,a ina aka samo wannan cikin gidan?" Ta yiwa kanta tambayar da batasan amsarta ba,zataso ta jefa tambayar ga baquwar fuskar,amma idanunta zuwa fuskarta suna fidda wani irin kwarini. Sãahar ce ta fara janye idanun nata daga kanta,ranta yana dan baci da yadda ta riskesu gatsau kai tsaye tayi musu kuma tsaye a ka,saita maida idanunta ga duba littafin hannun nata ba tare data sake dagowa ta dubeta ba,saidai a jikinta tana jin kamar tasan fuskar,kamar ta taba ganinta a wani waje. Tana jinta ta isa gaban fadeela ta zauna tana ta janta da surutu,lokaci lokaci idanunta suna satar kallon sãahar,wadda bata sake duban sashenta ba,koda ace suna da dabi ar yahudawa,a qalla tunda musulmi ne su tay! musu sallama sanda ta riskesu "Na gama anty" fadeela ta fada bayan ta ajiye gorar ruwan hannunta "Good bari na dauko miki hijab,qur ani zamu fara yi" saita kife littafin ta mige zuwa dakin fadeelan. Kallo labiba ta bita dashi hankalinta yana tashi, ko ita da take mace ta tabbatar ta kuma yaqini hakanan ta sallama wannan din ta cika mace wani abu me cakude da kishi da tashin hankalin wanzuwarta a gidan yazo yayi mata tsaye,sai ta maida dubanta ga fadeela dake qoqarin dauke plate din da taga gama cin abincin tana tattare inda ta bata da tissue,abinda bata taba gani yarinyar tayi ba "Wacece wannan uktie?" Duban labiban kawai tayi,da yake itama miskilar kanta ce,kafin tace komai baaba ramatu ta shigo falon,hannunta dauke da humidifier da tasan sãahar na yawan ajjiyeta a gurin saboda tsananin son qamshinta,waccan ta lalace ta sauyo musu wata,tana respecting duk wasu buqatu na sãahar din,don zata iya cewa tsahon zamanta a gidan,bata taba jin dadin zama da wani mutum a gidan ba kamarta "'Barka da dawowa" baaba ramatu ta fadi tana duban labiba "Yaushe akayi baquwa a gidan nan?" Ta jefa mata tambayar ba tare data amsa marabar ta ba "Ba baquwa bace,kawai ita ke kula da fadeela yanzun" a take fuskar labiban ta washe,ta saki garamar dariya. "A'ah ramatu,kice nanny ce kawai,basai kin wahalar da harshenki ba" tayi furucin dukka a kunnen säahar data qaraso gurin hannunta dauke da gogaggen hijabin fadeela,cikin wadanda ta dinko mata da kudinta,saboda tazo ta risketa bata da jiba ko daya,sai wani fingilalle V shape na uniform dinta. Hada idanu sukayi da labiban,sai sauran maganar ta magale mata a magoshi,ta mige daga zaman da tayi tana fadin "Zan jira mommy a sassanta, fadeela enjoy your new nanny" saita dan daafa kan fadeelan ta soma takawa tana barin falon. Ran baaba ramatu ba dadi ta ajjiye humidifier din,tasan halin kowa a gidan,don kusan kowa a gabanta yayi girmansa, ta samu guri ta zauna lokacin da sãahar ke sanyawa fadeela hijab din nata,daga can qasan zuciyarta tana fassara kallon da kalaman labiba. Ta fahimci ma'anarsu fes,to amma abinda ya bata mamaki daga haduwar farko ko maganar farko babu a tsakaninsu me ya haifar da wannan matsanancin kishin cikin qwayar idanunta? "Wannan itace labiba, kuma za'a iya cewa ita din ganwa ce ga mahaifin fadeela,wato 'yar matar babansa ce,tana da wasu halaye marasa kyau wani lokacin,sai kinyi haquri da ita" a nutse ta daga kai ta kalli baaba ramatu,saita saki kyakkyawar murmushin nan nata da ba kasafai take yinsa ba,ta taka tana debo litattafansu "Karki damu baaba ramatu,haquri da ita bai zama dole ba,tunda bani da case da ita" jinjina kai baaba ramatu tayi,tasan sarai tana da kawaici da kuma sanyin hali,hakanan bata da kwaramniya ko hayaniya,amma labiban fa?,tayi imanin koda bata shiga gonarta ba ita zata shiga tata,saidai fatan Allah ya kiyaye. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_** Page 63 Sasai wuyanta ke cike da wani qatoton abu,sashen hajiya qaraman taso wucewa amma saita kasa,ta samu kujera ta zauna a nan farfajiyar gidan tana jan numfashi tana fesarwa,ba abinda ke gilma mata cikin idanunta sai kyakkyawar surarta,kamewarta da uban kwarjin da zai hana ta takata yadda taso. Ta yaya zaman wannan cikin gidan zai yiwu?,kuma a matsayin me kula da halittar da toufeeq yafiso duk duniya fiye da komai da kowa?,ta yaya zata bari su dinga gwama numfashi tare dashi?,anya idanun hajiya garama ba rufewa yayi ba kuwa harta amshi wannan surar a mazaunin nanny?. Qafa daya kan daya tana kadata makeken gate din gidan dake da rassa biyu daya daga cikin reshen(enter) wato shigowa ya bude,ta zubawa gun idanu tana fatan hajiya qarama dince ta dawo. Ita dince kuwa,bata iya haqurin jumurin tsaiwar motar bama ta miqe ta bi bayan motar har zuwa parking lot na gidan,dai dai sanda motar ke tsaiwa,tasa hannu ya bude seat din baya wanda tasan a nan hajiya qarama din ke zama driver yana tuqata,ta shiga ta zauna idanunta akan hajiyan dake amsa waya da dukka hankalinta "Nooo. karki damu MY BABY,duka duka watannin guda nawa ne? ki kwantar da hankalinki ki kammala karatunki,na miki algawarin duk lokacin da nazo bikin yayeku dake din zan taho,na miki wannan algawarin" girjin labiba ne ya buga,a duk sanda taji tana waya da BABY din,sai ta samu fargaba irin wannan,sunan da ita kanta me sunan ba qaramin barazana bane ga kunnuwanta da rayuwarta "Alright.....kada ki damu da wannan,ki maida hankali kiyi karatu sosai ki fita da result din da yafi qarfin raini... okay,bye,i love you" saita katse wayar murmushi me kama da dariya kwance akan fuskarta,soyayyarta tana sake ratsata,burinta a kanta yana sake hauhawa,lokaci kawai take jira,kuma mutuwa ce kadai zata shiga tsakaninta da cikar wannan burin nata "'Ya akayi labiba?" Ta waiwaya gareta bayan ta saka wayar a jakarta, numfashi ta ja ta hadiye yawu "Mommy, nazo na samu andauki wata me kama da aljanu wai a mazaunin nanny" "Shine me?" Tavi tambayar hankalinta kwance HA "Mummy bakiga irin kyau da halittarta bane?,bakya tsoron ta rudi yaa toufeeq da kyan nata?" Qaramar dariya hajiya qarama ta saki "Toufeeq.. . toufeeq dai? ke bakisan halinsa bane halan har yanzu?,kin taba ganin idanunsa bisa fuskar wata mace da zummar so ko sha'awa?,bare har yaji tayi masa? inama yake toufeeg din?" Shuru labiba tayi tana juya maganar mommy din. Tabbas ko ita din iya tsahon rayuwarta zata iya irga sau nawa ya daga kai ya kalleta,kallon da mafi yawan lokuta yana mata shine don hukuntata idan tavi wani abu daya saba da nasa ra'ayin,sai taji wannan case din kamar ya mutu ne "Mommy haseena zata dawo ne?" Sai data buda murfin motar ta saka qafarta waje sannan ta amsa mata Ад "Ba yanzu ba" ta fara qoqarin fita sai kuma ta dakata,shuru tayi kamar me nazarin wani abu,sanann ta fara magana da labiban a hankali "Toufeeq allura ce cikin ruwa,me rabo ka dauka,so ki dinga sassautawa kanki wasu abubuwan kinji daughter" daga hakan ta saka gafafunta waje ta fita a motar tabar labiba a ciki. Shuru tayi gumi na dan tsatstsafowa daga goshinta,mommy din tayi magana cikin kwantar da murya da kuma nuna kulawa,to amma kalaman dake qunshe cikin maganarta....sunyi mata wani iri,me rabo ka dauka?,allurar cikin ruwa?,duka me hakan yake nufi?. Shuru ta sakeyi tanason lallai saita fahimtar da kanta,amma ta gaza gano komai,tunda tace dawowar HASEENA ba yanzu ba,ta toshe duk wani kafa ta tunaninta,dole ta jawo qafafunta ta fita a motar don ta bawa driver din damar rufe motar,saidai a ranta tana jin ya kamata ta kira hajiyarta ta gaya mata ko ita din zata gano abinda ta gaza ganowa. Da daren ranar suna saman gadon fadeelan,bayan ta tabbatar ta bata magungunan da afifa ta rubuta ita kuma ta fita da kanta ta siyo. Ta shiryata cikin kayan bacci,kan fadeela na kwance saman cinyarta,gashinta me tsaho da santsi irin na saahar din ya baje saman gafafun sãahar din,ta nace wai sai sãahar din tayi mata kitso. Itama ba iya kitson tayi ba sai kalba,don haka kalbar taketa qoqarin kitsawa amma tana warewa, kunnuwanta suna kan fadeelan daketa complain din rashin kiranta da Abby din nata baiyi ba. Kusan duk wayar da zaiyi matan tana gurin baaba ramatu,a can suke wayarsu su gama "Abby yayi busy ne tabbas,amma ayi masa uzuri kinji,ki daina complain da yawa fadee,he cares about you fadee,you have to appreciate his efforts kinji" ta fadi ne don kawai kwantar mata da hankali tare da nuna mata muhimmanci haquri da kau da kai. Kai ta gyada a sanyaye,bata sake cewa komai ba. Kamar jira kuwa akeyi tayi shurun sai tab din ta fara gara, zamewa tayi da gudu ta dira a gadon ta nufeta,ta iya karatu sosai,don haka ta karanta sunan me kiran "Aunty,budemin google meet dina,abby ne a nutse ta sauka a gadon,ta dauko mata headphone da fold up stand,ta fara bata headphone din ta saka a kunnenta,sannan ta ware fold up din ta dora mata tab din a ciki don taji dadin amsa wayar,ta koma daga bayan camera din ta saita mata Google meet din. Cikin qawatacce kuma tsararren balcony din nasa yake a zaune,wanda aka rabashi sassa biyu lounge and eating area qawace yake da wasu irin stone tiles da kuma couch masu tsananin laushi hade da table din dake da kujerunsa guda hudu,sai swing bench daga can gefe guda daya dake mahadin furniture din. Da wasu irin fitilu aka yiwa gurin ado,hakanan aka wadatashi da potted plants a kowanne sago da kuma qasan gurin,tsirran dake iva garawa gurin kyau iska me dadi da kuma qamshin furannin dake magale dasu. Pajamas ne a jikinsa,farare tas tas dasu,rigar me gajeran hannu ce qwarai,v shape neck dake iya baka damar hango lallausar gargasar dake kwance lambam a girjinsa,hakanan gajartar hannun rigar yasa kake iya ganin dantsensa dake da wasu irin muscles,daga can gasa zuwa tsintsiyar hannun kuma gargasa ce itama me santsi baga sidik. Wandon jikinsa iyakarsa gwiwa,yayi crossing gafafunsa yana jiran kiran da ya yiwa halittar mafi soyuwa a gareshi ya shiga,hannun damansa coffee dinsa yake sipping kadan kadan. Duka duka bai cika awa guda da dawowa daga office ba,ya sake maida kansa busy qwarai da gaske da tunanin hakan shi zai zame masa abokin debe dukka wata damuwa da kewa. Miskilin murmushi ne ya subuce a labbansa sanda innocent face din fadeela dake zaune tsakiyar gado da hargitsatsen gashinta ta bayyana "Assalamualaikum abby" sallamar tata ta ratsashi qwarai,ta kuma dace sosai da muryarta 'Waalaikumus salam,daddy's angel ta girma da gaske,an iya sallama da kyau‚barakallahu fiik" "Abby,aunty nanny ce ta koyamin" sai ya jinjina kai yana murmushi "Tace min tafi lada akan ace hello" "'Da gaske ne" ya amsa mata yana gyara zamansa,ya buda baki zaice wani abu,saidai kafin yace komai din ta rigashi,ta barke da bashi labarin aunty nanny,abubuwan da take koyamata,abubuwan data hanata yi da wadanda ta gyara mata,karatunta da sauransu. Shuruuu kawai yayi yana bin bakinta da kallo tare da sauraren bayananta,yana tsintar abubuwa masu yawa game da labarin nanny din da take bashi,a hankali ya samu kansa da furta "Alhamdulillah" a gasan zuciyarsa,tana sake gaya masa abubuwan da suke gudanarwa nutsuwa na sake saukar masa game da hannun da diyar tasa ta fada a wannan karon,abinda yake ta taraddadi kenan,sai ya gara sakewa sosai ya bata dukka hankalinsa yana sauraronta,cikin ransa yana jin mai yiwuwa Allah ne ya dubeshi ya share masa damuwarsa ya hada sanyin idaniyar tasa da nanny ta gari "Kanason ka ganta? daddy na nuna maka ita?" Tayi gasa gasa da muryarta harda dan sunkuyowa screen din wayar alamun quima,tana maganar kuma tana satar kallon säahar dake tsaye bakin mudubi tana taje kanta tare da gogarin hadeshi cikin ribbon,fadeelan ce ta watsa mata kan a dasu garin cewa lallai saita koyi kitso itama a kanta. Yadda tavi maganar da sunkuya da yin qasa qasa da murya ya bashi dariya,ya daga hannu yana shirin dakatar da ita,amma inaaa... bata tsaya jin ta bakinsa ta juyar da screen din zuwa sashen da sãahar din ke tsaye tana daure gashinta da ya zuba har bayanta. "aunty na juyo miki da camera kizo ku gaisa da abby na..." Wani muguwar faduwa gaban sãahar din yayi,tamkar wadda aka dasa taci gaba da baiwa camera din baya ba tare data juyo ba,ba abinda take tunawa sai kayan jikinta,inda Allah ya taimaketa doguwar rigace sakakkiya a jikinta,amma duk da hakan tasan tudun mazaunanta da kuma gashinta dake sake a baya yana lilo bazai kasa ganuwa ba,lallai ta yarda quruciya na damun fadeela sosai, banda haka ba wanda zaiyi irin abinda tayi. Da sauri ya janye idanunsa daga kallon abinda baiyi niyyar gani ba,ya dunqule hannunsa sosai yana fadin "Angel,move the camera,basai mun gaisa ba" kasancewar akwai headphone a jiki ya sanya ita daya take jin abinda yake fada,saita kyabe fuska tana fadin "Anty na dauke camera din,yace basai kun gaisa bama" ido ya zubawa fadeelan sosai yana kallonta,can qasan magoshinsa yana qogarin harhada abinda zai fada mata,saboda ta sanyashi kallon abinda bai shiryawa ganin ba,dole ya mata bayani cikin hikima yadda zata fahimta,don ya fahimci ita kanta matar batasan zata juyar mata da camera ba. Zama yayi sosai yana fuskantarta,ya maida fuskarsa serious da zummar mata bayani da kyau,kada wataran ta sakashi ganin abinda baiyi niyya ba "Fadeela" "Abby" "Kina iina?" "En daddy" "Daga yau idan na kiraki,idan bance ki bawa wani waya ba kada ki sake yin hakan kinji?" Kai ta gyada a sanyaye "Kome zaka yima mutum saida izninsa,kinga yanzun ba hijab ko dankwali a jikinta,kuma ba kyau aga mutum a haka,kin saka mata camera,kinga ba zataji dadi ba ko?" Kai ta sake gyadawa da alamu jikinta ya mutu "Good girl,idan mun gama waya ki bata haquri" "In sha Allah" sai murmushi ya sake subuce masa,in sha Allah din kamar a bakinta aka radata,bai taba jin ta fadi ba,kamar wata babba,amma yanzun data fada sai yaji wani sanyi a ransa "Khairan in sha Allah" ya fada a ransa yana jin hope sosai akan sabuwar nanny din fadeelan. Tunda ta fahimci ta janye camera din sai ta koma gefe ta zauna tana maida numfashi, wani abune da bata taba zata ba shi yasa ta razana,wayarta ta jawo ta buda don rage zaman da bugawar da zuciyarta keyi akan abun,tana danne danne tana kiran sunan Allah,har batasan fadeela ta kammala wayar ba,saijin mutum tayi tsugunne gabanta "Aunty,am sorry,abby yace na baki haquri,na juya miki camera without your permission" ido ta zuba mata,sai ta murmusa ta sanya hannunta ta dagota ta dorata kan cinyarta "Abby yace babu kyau kada na sake" kai ta jinjina "Abby dinki is a good person,gaskiya ya fada,na haqura nasan kema ba kina sane bane ko?" Kai ra gyada mata tana murmushin jin dadin yabon da ta yiwa mahaifinta,riqe hannunta tayi suka miqe "Oya,muje a kwanta,gobe da school,next week kuma zaku fara revision,sai C.A then exams ko? "Yes" ta fada tana murmushi "Abby yamin alqawura da yawa,yace ya gaji da ganin third position,da second yakeson ganina,if possible ma first,idan na kawo first din kuwa,sai ya gyada kai,nasan abby naidan ya gyada kai baice komai ba.....hmmmmm,zai baka mamaki ne,anty ki tayani addu'a na samu first position" ta garasa maganar tana marairaicewa dai dai sanda sãahar ke lullubeta da duvet. Murmushi ta saki,ta kama hannunta ta rige cikin nata "Kiyi karatu sosai kiyi addu'a da yawa,you will pass in sha Allah, kuma duka zan tayaki fadee" qanqameta tayi tana dariya cikin jin dadi "Na gode aunty nanny" Shuru yayi idanunsa akan system dinsa bayan sallama da fadeelan,hannunsa rige da dan qaramin spoon yana ta juya tea din da already ya riga ya gama juyuwa,ya rasa me yake tunani,hirarsu da fadeela....abubuwan da yaji. .ko abinda ta nuna masa bai shirya gani ba?, Sai kawai ya zame hannunsa daga tea din,ya mige yana zuba hannuwansa dukka biyu a aliihun wandonsa yana furta "La haula wala quwwata illa billah" tattaki yayi kadan ya matsa gaban balcony dinsa,ya zube idanunsa a gurin yana kallon jerarrun tsirran dake gurin suna rayuwarsu hankali kwance,duhun dare da hasken fitilu suna sake qawata ganin mutum. Qarar wayarsa ta sanyashi waiwayowa,ya zubawa wayar ido yana karanta sunan NADEEYA cikin ransa,sai data kusa katsewa sannan ya daga ya sanyata a kunnensa yayi shuru ba tare da yace komai ba. *HUGUMA* 64 * TABARMAR KASHI_* Page 64 "barka da warhaka yaa toufeeg" daga can daya sashen aka fada cikin d'ari d'ari,kamar me tsoron yin magana "Barka" ya fada a dake kuma a taqaice "Ya aiki yaa?" "'Alhamdulillah" ya sake amsa mata a taqaice,duk sai taji ba dadi,saboda ba haka suka saba yin waya ba,ba kuma da irin wannan yanayin yake magana da ita ba,duk da ta saba da miskilancin sa,amma yanayinsa na yanzu ba dashi suka saba magana ba "Yaaya upper week zan dawo gida,finally na gama exam dina,zaman canada ya qare" "Good.....ina miki murna" ya sake amsa mata a taqaice. Marairaicewa tayi zuciyarta na karyewa,tamkar tana a gabansa "Am sorry yaaya" "Sorry for what?" Yayi tambayar hankali kwance kamar dai da gaske baisan abinda yake faruwa din ba "Yaaya,nasan kasan nayi maka laifi,amma wallahi it was not my fault,tanata sakamin pressure akan tanason ganin FADEELA.. "Ki gaya mata,ta sanya a ranta bata haifi wata 'ya ba a duniya kwata kwata,fadeela a yanzun ba jininta bace" yayi maganar cikin zafi tamkar itace a gabansa. Laqwas NADEEYA tayi cikin toro da firgicin jin sautin muryarsa mara hayaniya lokaci guda ta cika da kauri. Iska yadan furzar yadda nadeeya din tayi shuru ya tabbatar masa ta tsorata da yadda yay maganar ne,sai ya lumshe idonsa yana gogarin yiwa kansa saiti,bayan ratsawar shuru na wasu sakanni sal yace "Ticket din wacce rana kikayi booking?" "Sunday" ta fada a sanyaye "Alright,zan dawo miki da abinda kika kashe,don nayi fushi bashi zai baki lasisin yiwa kanki wata hidima ba,don't tray to buy anything da kudinki,as long as iam alive" "In sha Allah" ta amsa masa a sanyaye, zuciyarta cike fal da qauna da kuma soyayyarsa,irin zallar soyayyar yan uwantaka,wadda babu algus a ciki. Labarai kadan ta bashi suka katse kiran,don ta fuskanci yanayinsa kamar he's not in mood. Ya jima da wayarsa a hannu yana jujjuyata ba tare da iya yin komai ba,haka kawai wasu abubuwa na rayuwa suke dauko kansu suna kawo kansu da kansu gabansa,rayuwarsu yadda ta gudana shi da 'yaruwarsa,shekara kusan ashirin da biyar baya. Ajiyar zuciya hade zazzafar iska ya fesar,ya sake juya wayar a hannunsa sannan ya lalubi number hajiya qarama. Tashi tayi ta zauna sasai tana cire hankalinta daga lissafin ribar kayan data kawo daga china da suka samu qarewa,ta bada dukka hankalinta akan wayar ganin me sunan,tayi gyaran murya sannan ta saka wayar a kunnenta. "Barka da dare" "Barka kadai,yanzu yanzu na shigo daga gurin mutuniyar,suna can ita da nannynta suna shirin bacci" "Ummm,yayi,batun nanny dinne dama na kira,nawa ta buqaci albashinta?" Wuyan rigar lace din jikinta ta gyara "Har yanzu taqi fadin nawa,ni bansan kalar nanny din da muka samo ba wannan karon,nayi mata zancan kudin amma sai tacemin ba komai,aikin yafi kudin muhimmanci" gyara zamansa yayi,shima maganar ta dan bashi mamaki "'Noo,ta fadi ko nawan ne,sai a yiwa elyas magana,a dinga cire mata on time " yayi maganar ne har qasan zuciyarsa, yana lua hangen canji qarara daga fadeela,a yadda zuciya da ransa sukayi masa dadi,yana ganin ko nawa ne ta bugaci a biyata baiyi tsada ba "Okay,i will talk to her' "Yayi' ya amsa a kasalance,tanaso su tattauna wasu abubuwa amma ya bata uzurinta,sai tayi masa addu'a sosai sannan ya katse wayar,ya jefara gefe yana jin dukka gabban jikinsa suna sake zama weak,don haka sai ya kwashe wayoyinsa yabar dukka sauran tarkacen a gurin, saboda akwai wadanda xasu gyara gurin,komai kuma su sanyashi a muhallinsa. Wanka yasoyi daya dawo amma saboda ya kira fadeelan baiyi ba,don haka yana shiga ya zare kayan jikinsa,ya lullube murdadden jikinsa da babban lallausan towel. Minti talatin kacal ya fito yana qamshin shower gel,da hair shampoo dinsa me tsada da yake amfani dashi waien wanke sassalkan gashinsa da ko yaushe yake cikin daukar idanu da hankulan tarin matan da shi kansa baisan adadinsu ba,saboda mafi yawansu bashi da masaniya akan fadawar da sukayi cikin matsananciyar soyayyarsa. Mintuna sha biyar ya gama shirinsa,a hakan yayi sauri akan yadda ya saba,don shirinsa yana daukar lokaci,sosai yake bawa jikinsa da fatarsa kulawa da mayuka da turaruka masu shegen tsada,ko nawa yana iya kashewa ya siya turare zuwa mayuka,ko a yanzun kudin wasu turarukan nasa sun isa jari a waien mutane da dama. A gurguje ya feshe gashinsa da turaren ka,hakanan beard dinsa da nasa turaren na musamman tamkar wani mace haka yake a wannan bangaren. Guri na musamman da yake gabatar da ibadunsa ya shimfida lallausar dadduma,cikin daidaituwa da miga dukka tunanin damuwar duniya izuwa bayanka ya fuskanci alqibla,cikin cikakkiyar tsaiwa da daidaito ya kabbara sallarsa. Dukka raka'o'in daya saba yi babu wadda ya rage a ciki,ya dade saman abun sallah yana addu'o'in sa,bayan ya kammala yana nade abun sallar akayi masa knocking,sai ya waiwaya yana duban wata maqalalliyar na'ura dake nuna masa fuskar wanda ke knocking din. Jibril ne,matsawa yayi gaban bedside drawer ya ciro wasu files,sannan ya zura wasu lallausasan takalma da aka yi da wani gashi me laushi ya buda gofar da zata sadashi da setting room na gidan. Cikin girmamawa ya rusuna yana gaidashi "Sir... bakaci dinner dinka ba,ina fatan lafiya" kai ya girgiza yana miga masa files din "Am too tired,ina bugatar hutu,gobe inaso mu fita da wuri,zan kwanta yanzun,ko meye please kada wanda ya tasheni,zan nemeka idan ina da buqatar hakan" hannu biyu yasa ya karba cikin girmamawa "Yes Sir,have a goodnight" "Allah ya tashemu lafiya" sai ya juya a nutse yana komawa dakin. Saman lallausan carfet din dakin ya yada pillow,ba kasafai yake iya kwana samam shimfida me laushi ko katifa ba,yayi rigingine idanuwansa na kallon roofing din dakin cikin dim light din daya saki,ya kammala addi' o'insa ya shafe jikinsa,ya koma riginginen ya kwanta yana sauraren zuwan bacci. A hankali jinsa da ganinsa ya fara nisa da wannan duniyar da muke ciki,ya haurawa zuwa duniyar bacci,irin baccin da kake tsakanin wannan duniyartamu da duniyar baccin,zuciya da ruhinsa suka fara haska masa wani abu da ya faru zahiran dazu dazu cikin rayuwarsa ta ainihi. Tana tsaye ta basu baya kamar yadda ya gani a mafarkinsa, dogon gashinta me tsananin duhu da sheqi daya raba tsakiyar bayanta,hips dinta da mazaunanta da suka fita ainun ta shape din doguwar rigar. A mugun firgice ya bude idanunsa,sannan yayi wani irin tsalle ya miqe ya zauna sosai saman carfet din,hannunsa ya sanya ya tallafi goshinsa da ya dan fara hada zufa,a hankali labbansa suka motsa da fadin "Hasbunallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" ya maimaita ta kusa sau goma,sannan a hankali zufar ta fara ragywa tana bushewa da kanta,sai ya daga kansa yana bude idanunsa a hankali "Meye hadin sa da nanny fadeela da har zata biyoshi cikin mafarkinsa?,me yasa duk yadda yakai ga kame kansa da idanunsa daga kan kowacce diya mace,amma hakan bai rabashi da tarin mafarkan kasancewa da wata diya mace dako fuskarta bai taba samun nasarar gani ba? mafarkinsa na yanxun ya kusa yin dai dai da yarinyar dake yawan zuwa debe masa kewa,duk da baisan saurin murya ko ta fuskarta ba,ya tsani wannan mafarkin da ko yaushe idan ya yishi take sake haukatashi ya maidashi mabuqacinsa,lalurar da ya dauka yayi adabo da ita,ya tasa ta gofar da zai yaqi hakan,yawan nauye nauyen da yake dorawa kansa da ayyuka babu ji babu gani,ya dauka sun isa su cire wannan buqatuwar daga jikinsa. Yasan yayi nasara da idanunsa da kuma zuciyarsa,ta yadda duk tarin matan dake kai kawo a gabansa dama bayan idanunsa,bai taba daga kai ya kalli wata yaji shaawar kasantuwa da ita ko kuma ta burgeshi ba.amma ta bayan fage, wata mace guda daya tal da baisan wace ba na neman matsanta masa,cikin watannin da duka duka basu gaza biyar na. Siririn tsaki yaja shi daya cikin dakin,ya miqe cikin matuqar mutuwar jiki ya nufi toilet. Alwala ya daura,ya dawo ya tsaya gaban wardrobe ya cire qaramin towel ya goge lemar jikinsa,ya saki towel din ya koma makwancinsa na dazu. Duk da bayason kwanciyar rub da ciki ko kadan,amma yau din ta zame masa dole haka ya kwanta a rub da cikin yana qangame dukka pillows din dake kewaye dashi. ****Tsam fadeela dake sanye da uniform dinsu,cikin tsafta kulawa da kuma tsaarin sãahar ta rige hannun sãahar din tana langabar da kai "Ni ba itace zata kaini ba Allah kece zaki kaini" ta gadi a mugun shagwabe tana daf da sakin kuka. Waiwayowa hajiya qarama tay,tadan hade fuska "Me yasa bakiji uktie,ta yaya nanny zata kaiki school,shin tama iya mota da kike zancan ta kaiki makaranta? idan kuma kinaso ki makara ne shikenan" labiba dake tsaye riqe da key din tata motar da zata miga fadeelan makaranta,saboda driver dinta da hajiya garama ta aika ta jefawa fadeelan harara,sannan tace "Ta ina zata iya mota? bayan ba itace dasu ba a gida?‚an saba hawa motor din kasuwa?" A nutse säahar ta dag kai,kallo daya tayi mata ta bawa banza ajiyarta,don tun zuwan labiba gidan ta gama karantarta,ta kuma yi aji guda ta sanyata a ciki. "Allah mommy ta iya,Allan kuwa" "Ke ko ta iya bazan bayar da motata ba,saidai ku ira a wanke wata cikin motocin gidan nan sannan a kaiki" ta fada cikin fushi ta juva da zummar komawa cikin gidan "Zo nan labiba" hajiya garaman ta kirayeta,ta dawo a fusace ta tsaya tana huci "Bata key din ta tuqaku,saiku tafi tare ki dinga monitoring dinta kada ayi miki barna" fuska ta hade cikin fada take magana "Allah kune kuke sangarta yarinyar nan,sai abinda takeso sannan za'a yi mata?" "Waishin ba daga jikin kakanta da mahaifinta kudin motar suka samu ba?" Haiiya garama ta jefawa labiba tambayar. Sak labiba tayi tana duban tsakiyar idanun hajiyan,itama kafeta tayi da kallo. Sometimes kamar yarinyar tana manta waye ita,har suso wuce gona da iri a wasu lokuttan,shi yasa takanyi hakan,saboda makaho yasan cewa fa ana ganinsa. Jiki a sanyaye ba tare kuma data sake cewa komai ba ta migawa saahar key din. Kamar ba zata karba sannan tasa Hanna ta karba,tana ji a ranta wasu lokutan wasu mutanen suna da bugatar a koya musu hankali,a kuma basu darasin rayuwa. Jikinta ta kalla babu buqatar sai ta koma ta canza kaya,doguwar riga ce da hijab dinta madaidaici duka golden yellow,sai wani adon wani abu me kama da lace da akayi daga qasan hijab da rigar sai slippers dake qafafunta. Juya muqullin tayi tana duban motar,qirar motar ba baquwarta bace duk da tana da tsada,ta saki boyayyen murmushi,tana rige da hannun fadeela daketa tsallen murna sukayi gaba,labiba dake cika tana batsewa ta biyo bayansu. Kafin labiban ta iso tuni ta bude front seat ta sanya fadeela,ta zagaya sashen driver ta bude ta shige,dole da tazo back seat ta bude ta shigan tana qwafar raina mata wayon da sãahar din tayi "Ko ba komai yau mun samu new driver" ta fadi don ta baiwa sãahar din haushi Sarai ta jita,amma saitagi nuna hakan,murmushin da ya subuce mata ma kauda kanta tavi gefe don kada ta gani "Zakiga new driver gain idonki" ta furta gasan zuciyarta. Hira sukeyi da fadeela irin wadda suka saba,daga yadda suke hiran kadai zai gaya maka zallar shaquwar dake tsakaninsu da kuma gaunar juna,labiba na zaune a baya kamar zata fashe,ita taso samun wannan damar, amma kuma bata sameta ba koda quater dinta,yanzun ga wata banzan nanny daga sama tazo ta mamaye rayuwar yarinyar. Sai data tabbatar fadeela ta shiga class,ta kuma sanya hannu akan kawota sannan ta fito. Zata tada motar mrs sadeega ta sanvo kan tata,dole ta tsaya suka gaisa "Kina aiki me kyau miss säahar, kowa ya kalli fadeela yasan tana samun canji garara,hatta da performance dinta a class ya qaru,tiny baby ta fara komawa chubby ma sha Allah" "Alhamdulillah" sãahar ta fada,ita kanta tana jin dadi ko yaushe yadda yarinyar ke wayar gari da goshin lafiyarta da kuxarinta suna garuwa,basu jima ba sukayi sallama,mrs sadeega ta wuce su kuma suka fice. Ta cikin mirror ta dubi labiba dake zaune a bayan ta toshe kunnuwanta da earpiece tana bin waqoqin turawa tana gyada kai,murmushin mugunta ta saki, saita take motar ta qara mata gudu. Da sauri labiban ta daga kai,ta zare earpiece din daga kunnenta "Ke meye haka? ki rage gudu da Allah" tana kaiwa nan ta maida earpiece din. Da kadan kadan ta sake garawa motar gudu fiye da dazun,tuni labiba ta cire earpiece din harma da wayar duka ta ajjiye,cikin fada da tashin hankali take magana "'Wai bakya gani ne,wanne irin gudu ne wannan?,kashemu zakiyi ne,dake fa nake magana!" Kunnen uwar shegu tayi da ita,salma sake qara gudun da tayi,ta shiga kurdawa tsakanin motoci tana overtaking,ta tuna da tsohuwar dabi'arta na mugun gudu a hanya,don a baya saida yaa Saifullahi yasa aka hanata mota na wasu watanni sannan ta bari. Tun labiba na hayaniya har ta fuskanci hayaniyar ba zata kaita ba,ta koma lallashi da kwantar da murya,amma sãahar kam ko a jikinta,ta dinga shimfida gudu da ita,sai ga labiban tana sakin hawaye,kowanne sashe a jikinta rawa yakeyi,don babu abinda ta tsana a mota irin gudu. Daga bakin gate din gidan ta tsaida motarta bude ta fice abinta tare da bar mata key din a jikin motar,tayi knocking gofar gate din,daya daga cikin security din ya taso ya duba wacece sannan ya bude mata. Baya yaja cikin rusunawa,saboda sosai Allah ya sanya ma ma'aikatan gidan gaba daya gain wani irin girmanta. Yadda suke mu'alama da masu aikin gidansu haka ta dauki kowa cikin gidan,tana girmamasu qwarai, irin girman da duka cikin gidan ba wanda ke basu irinsa,bugu da qari me hannun kyauta ce ita,a hakanma afifa tace mata saita rage,don kada su lura da ita din wace,su sanya ayar tambaya a kanta. "Madam ya na ganki a qasa?" Ya fada da 'yaf gaurayayyiyar hausarsa da bata fita tarr "Daga waje na sauka" "Welcome" ya sake fadi yana dage gate din don yasan yana jinkirin budewa labiban yau shine mutum na farko da zata fara saukewa kwandon rashin mutuncinta na safe. 65 *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_*8 DON MARTABAR MANZAN ALLAH ME FITARWA KIYI HAKURI KIYI HAKURI. Hankalinta kwance tama manta da wani abu da ta yiwa labiban,ta gama shirinta tsaf ta canza kava,tana duba saqon afifa a waya da take gaya mata mahmud nason a bashi dama yazo ganinta,sai taji sallamar hajiya qarama cikin matsakaicin parlor din da daga shi sai hallway na dakunansu,don ba kasafai take fita babban falonsu ba indai ba kitchen zata ta shiryama fadeela abinci ba. A nutse ta daga kai tana amsa sallamar,kamar kullum hajiya qaraman cikin shigar alfarma dake nuna zallar alfaharinta take,labiba ce da tayi firgai firgai ke take mata baya,ta zamu daya daga cikin kujerun ta zauna idanunta akan sãahar tana karantar yadda yarinyar sam wani abu baya mata kwarjini ko va tsoratata "Barka da safiya" ta gaidata cikin salon data saba gaisuwa,sai data gyara zamanta sannan tace "'Barkanki,ya kwanan uktie?" "Alhamdulillah ta amsa mata tana qogarin katse kiran dake shigo mata waya. "Ya akayi kikayi gudun wuce sa'a haka da labiba.har kina shirin hallakata?" A nutse ta sake kallon labiba sannan ta maida kan hajiya garama "Ni din?" "Kefa" ta amsa kai tsaye tana kallonta,tare da mamakin yadda take bada amsa lokuta da dama kanta tsaye,kamar ba wadda ke aiki a qarqashinsu ba,ita din kuma sai ta gaza daukan kowanne hukunci koda da zazzafar magana ne,abinda bai taba faruwa ba tsakaninta da duk wani me hidima dake qarqashin ikonta. Ajiye wayarta sãahar din tayi sannan tace "To bansan sanda akavi haka ba,don normal driving nayi yadda na saba,saidai ko a idonta ne ya zamana gudun daya wuce qaida,asalima a waie na sauka nabar mata motarta ta qarasa shigowa da ita,kina iya tambayarsu idrith dake bakin gate" yadda tayi maganar a miqe kai tsaye yasa hajiya qarama duban labiba "Wallahi qarya takeyi,jini na saura kadan ya hau" labiban ta furta kamar zata saki kuka "Bansan waye me gaskiya a tsakaninku ba,sai kiyi haquri, tunda bakison hudu next time karku sake hada mota" baqinciki kamar zai kashe labiban haka ta juya ta fita, sãahar kuwa ko daga kai ta kalleta bata sake yi ba. "Ina fatan magungunan nan sun qare kamar yadda na irgasu?" Hajiya garama ta fada bavan ficewar labiba,wayar ta kuma ajiyewa,ta dora idanunta duka cikin na hajiyan. Wani abu me qarfi hajiyan taji tattare dasu,sai ta zame ganinta tana cewa "Kin zubamin ido baki amsamin tambayata ba" "Sun qare‚na yau kawai ya rage" "Kin tabbatar?" Saita jinina kanta kawai ba tare data ce komai ba. Tsam hajiyan ta miqe tana mata wani kallo "Yayi kyau,cikin satin nan ganwar mahaifin fadeela zata dawo rayuwa damu cikin gidan nan,banason komai ya canza daga cikin sharudan dana gindaya miki,and then....magungunanta duka zasu dawo hannuna,duk lokacin da zata sha ki kaimin ita tasha sannan ta taho,wasu lokutan tafiye tafiye na kasuwanci na suna kamani,idan hakan ta taso zan damqa su a hannunki ta yanayin daya dace" daga haka ta juva tana fita daga falon. Kasa dauke kallonta sãahar tayi daga kanta,haka kawai a yau din wani qaqqarfan zargi ya taba zuciyarta,sai taji gaba daya zuciyarta tayi mugun matsewa da takurar son jin wanne matsayi hajiya qaraman ke dashi a gurin fadeelan. Kusan zaman banza tayi a gurin,ta kasa tabuka komai,zuciyarta da kwanyarta nata jujjuya mata al'amura masu dama game da rayuwa,hango kanta ta dinga yi shekarun baya,lokacin da adam ya maidata mahaukaciya tuburan,ya dinga shayar da ita gubar allurai da magungunan da suka kusa sanyata amsa sunan mahaukaciyar me license ma,tsoro ya shigeta bayan wata zuciyar ta ayyana mata. .. hajiya garama na daya daga cikin masu wanna hali da dabiar. Wani gumi ne ya karyo mata,ta yaya zata bari hakan ya faru da zuciya da ruhin da suke da rauni,salihar zuciya da kyakkyawan ruhin da basusan sabo ko cuta ba,sam sam....ba zata taba bada wannan damar ba,zata yi dukkan me yiwuwa ta katange fadeela daga dukkan wata cuta muddin ranta matugar ta samu kuma tabbaci da yaqinin abinda take zato din,sai inda qarfinta ya qare. Sau uku baaba ramatu na wuceta,tun batayi magana ba harta tambaya "Antyn fadeela lafiya kike yau kuwa?" Dan garamin murmushi ta saki tana gyara kwanciyarta cikin sofa "Lafiya lau nake baaba, kasala kawai nakeji" "Jiki da jini dama,to Allah ya garemu da lafiya" "Ameen ya hayyu ya gayyumu" ta amsa mata tana maida idanunta ta lumshesu Dawowar fadeela daga makaranta ne ya tasheta a wajen,yau gaba daya zancanta na dawowar sister nadeeya ne(haka take kiranta kamar yadda taji abby dinta wani lokaci yana kiranta da shi),ta hana sãahar yau sakat,alamu sun nuna akwai qaqqarfar shaquwa a tsakaninsu,bata samu hutu ba sai da suka kammala komai,ta hau google meet ta kira mata abby dinta,ta ja mata qofar dakin ta barta a ciki. Tun wancan ranar bata sake bari nasu take barin parlor din ko gurin,har sai ta kammala sannan ta biyota tana bata labarin hirar da sukayi da abby dinta. Tana kitchen tana hada mata abinci ta shigo da gudu da tab din a hannun ta "'aunty,don Allah sister nadeeya zaki kiramin" ta fada a marairaice,murmushi ta saka ta ajjiye wuqar hannunta,ta goge ruwan hannun nata jikin towel,ta koma ta watsapp din da aka budeshi saboda ita kadai ta kira matan,cikin sa' a tana online sai ta miga mata ta koma aikin nata,ita kuma ta juya da gudu ta fice. Tun daga kitchen din take jiyo hirarsu da dariyarsu,allai nadeeyan uwa ce da fadeela keyi da ita sosai. Har ta gama abincin ta baro zuwaira hirar bata qare ba,sai ta wuce dakinta ta daura alwalar sallar la'asar. Tana idarwa fadeelan na shigowa rungume da tab din,murya qasa qasa tace "Sister nadeeya tace na kawomiki ku gaisa,nace abby ya hana sai an fara tambayar mutum tukunna,don Allah aunty nanny zaki gaisa da ita?" Murmushi ya subuce mata, fadeelan badai jin magana ba,saita miqa hannu ta kamota jikinta,ta karba tab din ta ajjiye a gabansu,fuskar nadeeya ta fito sosai a screen din. Murmushi ya wadaci fuskar nadeeya, okaci daya da idanunsu suka gauraya waje daya kowa yaji wani abu game da dan uwansa "Barkaaa" nadeeva ta fada tana waving hannayenta wa sãahar "Barka kadai" sãahar ta maida mata itama cikin murmushi "Yamma ne nan ko? to kin yini lafiya auntynmu?" Murmushi ya sake subucewa sãahar tare da jin nauyin kiranta anty da nadeeya tayi tunda ko a ido kana ganinta zaka san sun kusa sa'anni da ita idan ma zata girme mata to da kadan ne "Lafiya alhmdlh sister nadeeya,ya karatu?" Cikin jin dadin sunan data ambaceta dashi da qaramar dariyar farinciki tace "Karatu ya qare, in sha Allah nan da kwanaki uku ina tare da ku,nazo naga the world talented nanny dinmu" murmushin sãahar ta sakeyi "Ma sha Allah,to Allah ya amince sisternmu" matsowa fadeela tayi tana sake zayyano mata dame dame zata taho mata da shi. Saahar din zata matsa don ta basu guri nadeeya tace "Don Allah karki tafi,yanzu kin fini iya ji da rigimammiyar 'yar nan,ki zauna kya tayani lissafa wadan nan kavan wasan da taketa fadi,ta dauka ni abbynta ce da zan mata tawagar kaya?" Ta fada tana dariya. Murmushi saahar ta saki,sai ta koma ta zauna,wayarta na hannunta ta hau watsapp tana duba kwantan sagonni;,lokaci lokaci takan daga kai ta kallesu cikin ban sha'awa da burgewa idan sukayi wani abun,duk sanda zata daga kan sai sun hada idanu da nadeeya,saidai su sakarwa juna murmushi. ******Washegari aka bude daya dakin da tun zuwan säahar din yana rufe,saboda me dakin wato nadeeya din bata nan. Dukka furniture din din ciki aka fidda,aka shirya sababbi,sannan aka maida mata kayanta ciki aka sake gyara dakin da kyau. Fadeela da suke tare da sãahar din ta kasa sukuni saboda murna,dole karatun ranar da ba'a yi ba kenan,sai ta barta. *******Karfe hudu da rabi na ranar lahadin motar da take mallakin nadeeya ta shigo da ita katafaren farfajiyar gidan mahaifin nata. Seatbelt dinta ta cire tana duban ilahirin harabar gidan,ita sam banda Dr jarma din yace lallai ta sauka a nan din,da sai ta gama kwanakinta a gida sannan zata zo gaidasu,sam zama a gidan koda na minti daya ne bai taba mata dadi ko kuma ya burgeta ba,bawai don bata samun kulawa ko wani abu na jin dadin rayuwa ba. Oofar motar ta bude da kanta ba tare data jira tarin ma'aikatan dake yungurin mata hakan ba,fuskarta a sake,kasancewarta mutum itama me fara'a da haba haba da al'umma cikin kuma kulawa take amsa barka da dawowar da kowa keyi mata,bayan tafiyarta karatun data shekara hudu tana yinsa,wanda a shekara hudun sau biyu kacal tazo gida bisa tsarin yaa toufeeq da yace baison yawo,idan karatun zatayi tayi basai tazo musu gida ba A haka ta gama gaisawa kaf dasu,sannan ta tuqe ga hajiya mansura dake tsaye tana faman doka mata murmushi "Lale maraba da dawowar diyata cikin aminci" ta furta tana yunqurin kamo nadeeya zuwa jikinta. Kadan tadan zame tana murmushin itama "'Na sameku lafiya?" "Wannan gaisuwar sai a ciki za'a yita,abbanku yana toilet yana qarasawa shiryawa,muje cikin tukunna" waiwayawa tayi tana bawa masu aikin umarnin shigowa da jakankunanta "A'ah,ai basai sun shigo dasu ba,zan wuce gidan yaa toufeeq ne" fuska tadan bata "Me zakiyi a can nadeeya?‚ga gidanku?" "Fadeela nacan na jirana,zanfi jin dadin can din" ta bata amsar tana takawa zuwa cikin gidan rungume da wata jaka data sako kaya masu muhimmanci a mazaunin tsaraba wa mahaifinta. Baki galala da kallo hajiya mansura ta bita dashi, cikin ranta tana jin wani irin kishi yana kamata,a fakaice kamar anaso ne ayi wining a kanta,bayan tarin nasarorin da akaci a kanta,har yanzu wannan matar... ..wannan mutum dayar ta gagara cimmata yadda ya kamata,tsakaninsu kar rasan kar ne, amma har yanzu qudurinta bai isa ga inda taso ya qarasa ba,MUTUM DAYA TAK! Ita ta samu dukka wasu damarmaki da taso ace ita ta samesu,duk da tayi musu nisan zangon da suke da imanin kasantuwarta a cikinsu abune mai wahalar yiwuwa,wannan ya rage garfi da kaifin wasu damarmakin nata ainun WACECE?! AMSARKU TANA GABA_. Juya cokali kawai takeyi cikin abincin da hajiya mansura ta gabatar mata,tana kuma amsa tambayoyin dr jarma. Gaba daya hankalinta bai waien, Allah Allah kawai takevi a tashi daga zaman cin abincin da akace an shirya da sunanta don tayata murnar dawowa,cikin ranta tana fata da addu'ar kada Allah yasa dr din yace ta zauna tare da su. Yana tsame hannunsa itama ta tsame nata tana gogewa da tissue,haiiya mansura ta kalli plate din nata "Ya haka kuma?,banga kinci komai ba" "alhamdulillah ‚naci abinci a jirgi" "Abincin jirgi wani abinci ne? ki zauna ki garasa ci, yanzu zan yiwa su taiba magana su sake gyara miki dakinki" tana gama maganar nadeeya na miqewa,ta goya jakarta tana duban dr jarma "Abba zan wuce gidan yaa toufeeq,fadeela tun ina hanya tasa ake kirana" "Alright,ki mintsinemin kumatunta ja'ira,tunda tayi sabuwar nanny ta rabu da zuwarmin, kullum kuma nayi kiranta cikin bani labarinta take,ki gaya mata nayi mata garin salary akan abinda ake biyanta,ina mata godiya da kyau da kyau,don da alama tasan aikinta sosai" murmushi nadeeya tayi,tana jin dadin yadda Dr bai hanata tafiya ba,sanann kuma ita kanta tana jin sãahar har ranta,duk da basu dade da sanin juna ba,amma tana jin tamkar ta dade da saninta. Sai da taga sun dau hanyar barin gidan ta sauke ajiyar zuciya,koda ta yiwa dr alqawarin zasu zo suyi kwanaki da fadeelan,batajin zata iya wuce kwana daya ko biyu. Guri hajiya mansura ta samu ta zauna bayan fitar nadeeya "'Dr inason magana da kai" kansa ya cire daga wayarsa da yake dannawa,daya hannun nasa kuma yana sakace da toothpick "Nikam nace ba,bai kamata ace kana raye ba amma dukka yaran da Allah ya baka basa rayuwa tare da kai,ka tattarasu ka barsu a wani guri na daban,ni kaina da nake matsayin uwa a waiensu sam babu wata shaquwa a tsakaninmu" a nutse ya ajjiye tsinken sakacen yana dubanta "Tohhhh... ...yau kuma wajen qarama dinne ya koma wani guri na daban?,kin manta suna rayuwa ne garqashin gidan da toufeeg ya gina da kansa? nadeeya da ita tafi sabawa,a hannunta ta garasa girmanta, taoufeeq dinma kusan hakane,sannan shi namiji ne wanda banda gaddara da a yanzun yana qarqashin kulawar matarsa ne,so a ciki bansan meye matsalarki ba" ya qarashe maganar yana kafeta da idanu. Ajiyar zuciya ta sauke,dama tayi zaton hakan daga gurinsa,yadda qarama ta tattare yaran gaba daya ta maidasu qarqashin mulkinta ita kadai yana mugun ci mata tuwo a qwarya,wanann dalilin ya sanya ta tattara labiba ta miga mata ko hakan zai sanya a samu wani sauyi,amma dai jiya i yau babu wani abu da ya canza "Shikenan" abinda ta fada kenam cikin suyar zuciya ta miqe tana tattare gurin,zuciyarta kamar zata fito ta qirjinta. Binta shi kuma yaci gaba dayi da kallo,yana mamakin yadda har zata iya gaya masa wannan maganar akan qarama,ko ta mance cewa ta silarta ta sanshi?,ta silarta ta zama abinda take a yanzu take kuma amsa sunan da take amsawa na matarsa. Dukka wannan shi ba damuwarsa bane,abu daya ya sani,duk abinda zai takura yaran ya sakasu cikin qunci zuciyarsa ko qangani bata so,muddin dai wannan abun bai kaucewa hanyar addini da al'ada ba,can qasan rai da zuciyarsa yasha kasa runtsawa cikin dare,he have feeling of guilt akan TOUFEEQ da NADEEYA,saidai har yanzu kwanyarsa ta kasa gaya masa meye ainihin tagamaimen laifin?,idan ya matsa da bincikar kansa kuma sai matsanancin ciwon kai ya saukar masa. _uhmmmmm hmmmmm_ Turus ta tsaya cikin mamakin ganin cewa ba wani mummunan abu bane ya sameta sanadiyyar ihunta data jiyo tun daga toilet din dakinta. Suna rungume da juna ne ita da nadeeya kamar wadanda suka bace tsahon shekaru sal yau suke ganin junansu. Nadeeyan ta daga fadeela tayi juyi tayi juyi da ita har babu adadi sai kawai sãahar din ta saki murmushi ta juya ta koma ta garasa abinda takeyi,saboda taga basa ganin kowa sai kansu,masu aikin gidan nata wucewa da kayan nadeeya din zuwa cikin dakinta "Ya zaki tafi?,ki tsaya mana mu gaisa" muryar nadeeya ta ratsa kunnensa sãahar dake yunqurin komawa ciki. Waiwayowa tayi tana murmushi "Ai naga baku gama ba" ta fadi tana duban nadeeva da take sake ganin wasu kamanni saman fuskarta,tana ji a jikinta kamar ta santa a wani guri daban kafin wannan lokacin. Karamar dariya nadeeya ta saki tana takowa zuwa inda säahar ke tsaye "Indai nida ukhtie ne wallahi bakiga komai ba" saita buda hannuwanta tayi hugging säahar kadan tana murmushi yadda larabawa ke marabtar 'yan uwansu "'Fatan na sameku lafiya" ta fada tana janye jikinta,fuskarta cike da fara'a "Alhamdulillah" "Tambaya ta farko,don Allah me uktie takeci ta fara kumatu?" Dariyar da sãahar bata shirya ba ta subuce mata,yadda nadeeya tayi tambayar tana riqe habarta da yatsarta,da alama da gaske abun yana bata mamaki,ko ba'a gayawa sãahar ba alamu sun nuna mata nadeeya mutum ce me barkwanci da faran faran da yawan surutu "Ki nutsu ki huta,zaki ganewa idanunki" baaba ramatu ta bayar da amsar tana dariya "En lallai to nima ko dole aci dani, bari na garasa" nadeeya ta fada tana daukar garamar suitcase din data rigo suka wuce ciki tare,saahar ta koma kitchen,fadeela tabi bayan nadeeya. 66 *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* DON MARTABAR MANZAN ALLAH ME FITARWA KIYI HAKURI KIBAR MANA KAYANMU To kusan yinin ranar fadeela na tare da nadeeya,har sai da sãahar tayi mata dan biki "An samu sister nadeeya an manta da ni ko?" Dariya tayi,ta taho da gudu ta rungume sãahar din ta baya tana fadin "A'an Aunty,sorry". Duk da säahar din na dan basu guri tana Kame kanta a dakinta,amma duk da haka nadeeyan bata qyaleta ba,komai saita sanyota a ciki,kota biyota dakin ta fiddota,da dare ma sai gata da dalleliyar kaftan abaya ta mata me kyau da sulbi 'yar saudiyya "Ga tsarabarki aunty nanny" sosai kyautar ta burgeta,ta kuma yaba tare da yi mata godiya. Cikin sati guda kacal da dawowar nadeeya sukayi wani irin sabawa da sãahar,sabon da ita kanta sãahar batasan lokacin da ya faru ba,kafin cikar sati biyu sai suka zama tamkar wasu 'yan uwa. Abubuwa da yawa na kula da fadeela tare suke yinsa,idan tayi wani abun,wani abun nadeeya ce zata karba. Wani irin qaunar sãahar nadeeya takeji har cikin ranta,bata sani ba,ko don bata taso da 'yar uwa sa'arta kamar sãahar din bane? to amma kuma akwai LABIBA da HASEENA,SU din kusan zata iva cewa sun dan rayu tare,to saidai ko kadan bataii abinda takeji game da sãahar ba,ko don ita din tana da wasu dabi'u da kuma halaye tare da wasu qualities da bata taba ganinsu daga gurin su biyun da suke kamar sune dolenta ba?. Zuwan nadeeva sai ya sanya itama ta dan sake,takan fita zuwa gida tayi wasu awanni ta dawo,a nan ne afifa ke tsokanarta,wai nadeeya nason qwace mata faada,tayi maganar tana dariya. Afifa tasan labarin nadeeya kaf daha bakin säaharduk da basu taba ganin juna ba. Murmushi kawai säahar ta saki "Bestie,da alama har yau bakisan matsayinki a guri na ba" hararar wasa ta jefa mata "Na sani mana,tunda gashi har yau kingi amsar mahmud yadda ya dace" zancan da ya sanyata miqewa kenan,ta lalubi mayafinta tana maida rolling din kanta "An ambato maqiyin naki ko?" "No,kawai inason na biya a wankemin kaina sannan na wuce gida,yau na yiwa fadeela algawari zan dafa mata burabusko ita da nadeeya....tashi don Allah ki kaini,saiki saukeni a gida" gyara kwanciyarta afifa tay! "Bazan iya ba,ki dauki motar ki kawai ki dinga amfani da ita" "Kin manta ni din nanny ce?" Ta fada tana murmushi,don zuwa yanzun ita dadin sunan ma takeji,hakanan rayuwar da takeyi din tana bata wani irin nutsuwa,ta kauce daga idanun maza kwata kwata,gidan ya zame mata kamar wata mafaka "Kina sauri ne kawai ki gudu kada ku hadu da abba" murmushi tayi tana maida agogon hannunta "Duka koma meye zakice bazan musa ba,tashi don Allah kafin ya dawo mu hadu" hakanan afifa ta mige,ta dauko abaya ta dora saman kayan jikinta tanata mita,ta dauki key din motar tabi bayan sãahar din. A kitchen ta tadda maama,tayi mata sallama,sai ta waiwayo tana dubanta "Zo nan sãahar" ta kirata tana tsame hannunta daga ruwan da take wanke alayyahu,ta yiwa baaba rabi sign saita fita a kitchen din,ta barsu su uku "Zauna" tace da ita bayan ta jawo kujeru guda biyu dake kitchen din ta zauna a daya. Cikin mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa tayin zama bisa garwashin wuta ta zauna "Wannan rayuwar ba ita nake da muradin ganin kinayi ba,nafi bugatar ganinki a dakin mijinki kamar kowacce mace,kije ki sauya tunani ki kuma canza shawara" iya abinda tace kenan da ita. Duk da kalmomin da tayi amfani dasu ba masu yawa bane amma nauyinsu ya cika mizani taf,jiki a salube ta mige ta sake iaddada mata sallamar sannan ta fito. Tuni har afifa ta tayar da motar ta kuma barta a kunne saita shige seat din gaba ta maida murfin ta rufe,afifan tadan juya kadan ta kalleta,saita dauke kai ba tare da tace mata komai ba ta motsa motar zuwa gaba,ta saki hon kadan,baaba habu ya taso ya bude musu yana musu fatan sauka lafiya. Suna gogarin fita a layin motar Dr mamman girema na shigowa,ya kuma gansu,don haka yasa driver dinsa yin slow da motar har suka hade a tsakiya,ya sauke Glass din motar yana duban afifa da idanunsa dake saye da gilashin garawa ido qarfin gani "Sannu da dawowa abba" "Yauwa sannu,ku dawo ciki,inason ganinku" hantar cikin sãahar ce ta kada,don bata manta da awa gudan da suka share dashi a waya ba wancan satin,yau din sai da tayi kamar ba zatazo gida ba,so amma zuciyartat a damu dason ganin maamanta,wannan dalilin ya sanyata fitowa. A gofar gate afifa ta faka motarta kalli sãahar da gaba daya takejin wani rugugin tashin hankali yana sauko mata "'Muie ko?" "'Na shiga uku afifa,wallahi zancan mahmud ne" wani duba afifan tayi mata "'To ai yayi kyau" da kallo tabi afifan,ganin yadda tayi hankalinta kwance bata ma wan damu ba,ga furta sunan Allah da qarfi tana runtse idonta da sauraron bugun da zuciyarta takeyi,ta bude murfin motar tabi bayan afifan. Tuni har ya isa falonsa yana cire hularsa ya ajiye yana zare agogon hannunsa. Kamar kaiin da aka watsawa ruwa suka samu guri qasan carfet suka zauna,yanayin fuskarsa shine ya fadar musu da gaba tun baikai ga cewa komai ba,a yadda yake da sauqin kai da kuma haba haba da iyalansa,dole yanayinsa a yau ya sanyasu a fargaba. Sosai ya zauna saman sofa yana maida bayansa ya jinginar da kujera yana dubansu daya bayan daya "Aishatu" yayi kiran afifa da ainihin sunanta,kai tadan daga kadan sannan ta amsa "Na'am abba" "Me kike jira har yanzu baki gabatar min da mijin aure ba?" Shuru ta danyi tana dawurwura,saita rasa me zatace da abban. A halin yanzu tana da samari da a qalla sun kusa mutum hudu,kuma dukkansu da aure suke sonta,saidai babu wanda ta maida hankalinta a kansa "Na sani nasan komai,saboda haka kije na baki wata uku ki karancesu ki fitar da wanda kikeso a cikinsu" "' In sha Allah abba" dauke dubansa yayi ya mayar kan sãahar,a jikinta taji irin duban da yayi mata,wasu daga cikin maganganunsa kuma suka dawo mata "Na miki alfarma na kuma daga miki qafa saboda banason na matsanta miki,na kashe miki gishirwar yin aikin duk da sam aikin bai dave dake ba,amma na barki kinje kinvi saboda babu haramci sai tarin lada a cikinsa.. ... okaci yayi da zaki tsaya ki fuskanci wanda yake sonki da gaskiya. "Ummee,a ina maganarmu ta kwana? ya muke ciki?" Yayi mata tambayar da a waienta tamkar gatse ce. "Abba‚bamu gama fahimtar juna ba" gafarsa daya ya dora kan daya "Ta yaya zaki fahimci juna bayan akwai nisan tazara a tsakaninku?,to ni na gama nawa,na gama fuskantarsa,hatta bincike nayi a kansa,babu wata matsala tattare da shi,abinda kawai ya rage shine ke ki fuskanceshi,don haka daga yau yana da lasisin zuwa gurinki zance a duk lokacin da ya buqaci baka,sannan damar fuskantarsa da kike da ita wata daya ne kacal,daga lokacin duk abinda naga ya dace zan iya yankewa" sanda ya sauka a zancan yayi daidai da jin tsargawar gumi me dumi daga kowanne sashe na jikinta,sai take jinta kamar ba'a zaune take dai dai ba,batu fa abba yakeyi na aure a karo na biyu cikin rayuwarta,bayan ko shekara hudu cikakku batayi ba daga fita daga siradin data afka ba,tayi zaton saita debe shekara koma ma babu wanda yayi mata sha awar yin aure bare akai ga batun yi mata tayinsa "Ku tashi kuje,Allah yayi muku albarka,banason kuma kowacce takai magariba a waje ba tare data nufi inda ta dosa ba" "To abba" afifa ta samu damar fadi,yayin da sãahar keta qoqarin ganin ta mige ta fita a falon ba tare da an samu matsala ta fadi qasa ba. "Kaini nasarawa kawai,na fasa wankin kan" abinda sãahar ta fadi kenan tana kwantar da kanta jikin kujerar tana jin toro da fargabar hukuncin da abban zai iya yankewa a wata gudan daya deba mata "Aure fa kenan,aure da mahmud,ta karba sadakinsa.ta amsa sunan matarsa,har ta hada shimfida dash. "A'uzu bi kalimatillahit tammati min sharri ma khalag" taji bakinta yana furtawa bayan runtse idanunta da tayi. Kadan afifa ta waiwayo ya dubeta,sai ta mayar kan titi,a irin wannan yanayin ba kasafai ta fiya son yiwa sãahar din magana ba,don haka batace komai ba har sai da suka iso katafaren gate din gidan,tana shirin fita afifa tace da ita "Take care of yourself.... kada kie ki zurafafa tunani,kinsan dai kina da ciwon kai" kai kawai ta gyadawa afifan,ba tare dat waiwayo ba ta wuce kai tsaye zuwa qaramar qofar dake manne da gate din daha gefe ta fara knocking da wani irin sanyi da mutuwar jiki kamar wadda aka yiwa mugun duka. Allah ya taimaketa sanda ta shigo gidan nadeeva tana tare da fadeela,ta jiyo kakacinsu a dakin nadeeyan,kamar ma game suke bugawa ita da ita,sai ta sulale ta wuce dakinta ba tare data bari sun ankara da dawowarta ba,don a yanzun kadaici kawai take bugata,batason hayaniya ko doguwar hira. Kwance kawai tayi tana saqa da warwara,ba tabbatuwar aure a kanta ba,'ah....ambatar kalmar kadai tana sanyata fargaba da razani,wai ta yaya zata iya hada muhalli da wani d'a namiji kuma wai a kirata matarsa? iya wannan tunanin kadai juya mata kwanya yakeyi tare da gara sanyata a wata dimuwa da kuma damuwa. Gab da magariba ta shiga wanka,ta fito ta shirya cikin wata lallausar riga me hade da wandonta,ta sanya hijab tayi sallar magariba,taci gaba da zama saman abun sallar,tana jin motsi da gilmawar nadeeya da fadeela,wani lokaci harda baaba ramatu. Tasan ba lallai su san ta dawo ba,saboda duk wani qwan lantarki me haske ta kasheshi,sai dim light kawai. Har nadeeya ta gota dakin ¡ilkinta ya bata kamar akwai mutum,saboda kana iya jin gamshin turaren sãahar me sanyi da baya buya yana ratsa qofar zuwa hallway din. Komawa tayi da baya ta murda qofar,sai ta bude,ta sanya kai cikin mamaki bakinta dauke da sallama,sãahar dake shirin tayar da sallar isha'i ta dakata tana amsawa "Antvn fadee,har yaushe kika dawo haka?,muna can muna jajenki,i called you several times amma ban sameki ba? mutuniyar tana can tana dakon dawowarkita kasa zaune ta kasa tsaye tun dazun‚bakinta da labari" dan lumshe ido tayi cikin murmushi "Nafi awa da dawowa,na shigo ne banjin dadi shi yasa na kebe" "Ya salam! me ya sameki?" Nadeeya tayi maganar sautin muryarta na nuna tsantsar kulawa damuwa da qauna "It's not something serious,i felt relieved" "Really?" Kai ta gyada tana murmushi,saboda ta hangi wani irin damuwa da kulawa da ita shigen na afifa "Bazan gayawa faadee dinki ba,if not ta zama itace patient din,please zakiyi joining dinmu muyi dinner?" Kai tadan yada gefe "Banajin yunwa,amma zanyi qoqari ko ban fito dinner ba,zamu hadu kafin animan" "Is okay,Allah yasa kaffara ne'ta fadi cikin mutuwar jiki ta juya ta fice tana jawa sãahar qofar. Ajiyar Zuciya ta sauke me qarfi,tana mamakin yadda suka damu da ita da al'amuranta a lokaci guda haka. Sai wajen Tara na dare,dai dai lokacin kwanciya baccin fadeela sannan ta shirya ta fita don tayi mata shirin bacci,aikin kulawar ya rage mata sosai tunda ko yaushe nadeeya na kula mata da ita koda bata a kusa. Qaramin hijab ta zura ta fito a dakin. Kasancewar qofar dakin bata kammala rufewa ba tun bata gama shiga ba ta fahimci video call sukeyi,duka ita da fadeelan na samon gado sunyi rub da ciki,sun sanya system din nadeeya din a gaba suna faman surutu. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* 67 "'yauwa maji....gata nan" nadeeya ta fada tana murmushi idanunta akan fuskar sãahar. Tsarguwa kawai tayi,tasan hirarta akeyi kenan batasan itakam wanne irin gauna nadeeya da fadeela ke mata ba da basa gajiya da ambatonta ba a duk wurin da suka zauna ba "Marhaban da ita‚ta qaraso mu gaisa" wata nutsatsiyar murya dake dauke da accent na arabic ya fidda amon maganar. Bata da wani zabi,tunda taji abinda ta fada,uwa uba sunan maji ba bago bane a kunnuwanta,suna ne da a galla tana jinsa daga bakin nadeeya da fadeela yafi sau uku a rana. A nutse ta taka zuwa gefan gadon,nadeeya ta zauna sosai tana juyar mata da fuskar system din zuwa tata fuskar "Ma sha Allah, intee jameela" murmushi sãahar ta danyi,tana dan sadda da kanta daga kallon tata kyakkyawar fuskar,fuskar da shekaru suka fara bayyana samanta,amma kuma bisa dukkan alamu kyakkyawar kulawa da ingatacciyar rayuwar da take ciki bai bar tsufa ya bayyana ba. Wani irin kyau me daukan hankali wanda dukka kamanninta sune tsaf bisa fuskar nadeeya a yanzu "Ki dayra,wesh wella famille?" Ta tambayeta da tantagaryar labarancin larabawan Algeria "Maii namu larabcin fa ba irin naku bane" nadeeya tayi magana da shagwabar da sãahar bata taba gani tayi ba "Ya salam, ina mantawa ne,kina lafiya? ya kuma iyalinki?" Murmushi ta sake "Alhamdulillah, da fatan kina lafiya" "Alhamdulillah, Allah yayi albarka,naji dadin ganinki,na san sunanki da kyau,amma bansan fuskarki ba" maii ta fadi mayalwacin murmushin dake dauke da nutsuwarta ta halitta na fita a fuskarta. Har qasan zuciyarta tana jin dadin yadda idanunta ke iya hango sauyi daga jikartata,fadeela rayuwarta ce,tana mata wani irin so da zata iya cewa soyayyar da takewa toufeeq da nadeeya ce tayi tsuntsuwa ta koma kanta,fadeela ita daya ce makamin data tabbatar a yanzun dukkan maqiyinta dake Nigeria zai iya amfani dashi ya cutatar da ita,cutarwar kuma ta risketa kai tsaye har gasarta Algeria. Cikin dabara ta sulale ta wuce wardrobe din fadeela tana fidda mata kayan bacci,saidai hakan bai hanata jin wasu hirarrakin nasu sama sama,duk da bata dora hankalinta a kai ba. Tana fita daga closet din taji an daneta an riqeta qam qam,kafin tace komai muryar fadeela ta ratsata "Albishir dinki aunty nanny" dariya taso kubce mata,saboda yadda tayi hausar ma kanaji kasan ba iya karin maganar tayi ba,saita zura hannu ta kamota ta dawo da ita gabanta "Wannan hausa taki....to ba laifi goro" "Ni bana cin goro,amma dai.. .. ki tayani murna,am very happy today, next week abby zai dawo" sai ta qyalgyale da dariya tana nuna zallar murnarta. Da kyau sãahar ta kama hannuwan fadeela cikin nata tana tayata murmushin,duk da hakanan taji zuciyarta ta harba ba tare da wani dalili ba "Am so happy nima fadee,congratulations" rungume sãahar din tayi,itama sai ta buda hannayenta ta sanyata sosai a jikinta tana tayata murnar. *******Cikin kwanakin gaba daya shire shiryen dawowarsa akeyi cikin gidan,nadeeya gaba daya ta kasa zama,ita da fadeelan batasan waye yafi wani murna da zumudi ba,itadai 'yar kallo ce,amma kusan kullum sai an fita shopping na dawowar abbyn fadeela. Tun tana janye jiki har nadeeya ta sakata tsundum a harkar,tunda ta fahimci sãahar din ta iya mota ta hanata sukuni,duk inda zasu saita marairaice mata akan tayi drive nasu Zuwa gurin,hakanan ba yadda ta iya take karba su tafi. Sai a sannan ra fahimci siyayyar da suke fita sukeyi,a nata gurin tsabar son yawo ne irin na nadeeya,qananun kayayyakin amfani dake sashensa ake canzawa,abinda taji hajiya qarama na cewa nadeeyan tayi magana da company suzo su sauya masa komai kamar yadda aka saba,amma son yawo dai yasa tace da kanta zata siyo komai. Duk da ko sau daya bata taba takawa sassan sa ba,amma bataga wani abu daya baci ko ya lalace da za'a sauyashi ba. Kamar nadeeya tasan me take tunani, ranar suna tafe cikin ShopRite tana zaban wasu turarukan daki na ruwa masi shegen tsada,ta dan ja tsaki kadan ta waiwayo tana duban sãahar dake amsa wayar afifa "Aunty N,don Allah tayani zaben turarukan nan mana,yaa toufeeq akwai shi da taste a zabi inason kome na siyo ya zama unique" zare wayar taki daga kunnenta tana duban nadeeya,duk lokacin data ambaci sunan TOUFEEQ sai taji gabanta ya fadi,ranta kuma ya baci "Basu isa bane haka sis nadeeya?" Ido tadan fidda "Da saura,indai yaa ya dawo daga tafiya muddin ya wuce one month yakai two to sai an canza masa irin wadan nan kayayvakin" batace komai ba sukayi sallama da afifa,ta tako gurin zuciyarta na tuna mata maganganun da sukayi da afifa yanzu akan mahmud. Ta fuskanci ta garfi da yaji mahmud din yakeson kafa kanshi a gidansu tare da maida kansa dan gida,to amma zata gani indai ana siyan so a dole. Sosai ta nutsu ta zaba wasu kalolin, wadanda ita kanta nadeeya sai data yaba "Wow,gaskiya u are the best selector" murmushi ya qwacewa saahar din,saita koma gefe tana jiran su kammala. Tana ganin yadda suka koma zaben kayan da zasu saka ranar da abby din zai dawo, nadeeyan tayi tayi tazo ta zaba itama,saita girgiza musu kai alamun a'ah,fadeela ta marairaice kamar zata saki kuka,ta rige hannunta kam "'Please anty N"ta fada itama kamar yadda taji nadeeya ta koma ce mata "Okay,kije ki zabarmin fadee na,koma meye i will accept it" da haka ta samu ta barta,bayan sun kammala kuwa sai gasu da leda wai duka kayanta ne na tarar abby "Wai wai,sis nadee, thank you, amma kayan is too much gaskiya" murmushi ta sake "'Wallahi Allah ko?" Ta fada tana duban sãahar "Ina jinki ne kamar wadda muka fito ciki daya da ita,banajin banbanci tsakaninki da yaa toufeeq " ambatar sunan ya sake sanyata lumshe idanu sannan kuma ta budesu, Allah ya sani bata qaunar jin sunan sam,saidai don babu yadda zatayi,shi daya ne tal ambaton sunansa yake sanyata jin faduwar gaba. A falonsu na biyu ta barsu baaba ramatu tana tayasu duba siyayyar ta shige dakinta ta watsa ruwa,sannan ta wuce kitchen don ta samar musu da abinda zasuci,saboda fafur sukaqi girkin zuwaira,sal ya zamana ita ke musu girki su hudun,nadeeya fadeela ita sai baaba ramatu. Ta sauya musu abinci sosai,daga girke girken fararen fara zuwa abinciccikan hausawa da abincin yaran maamanta wato buzaye,sai na yaren abbanta wato shuwa,duk da har yanzun bata tantance yarensu ba su din, amma kana kallonsu kasan babu ta inda suka hada Jini da HAUSA banda yaren dake bakinsu,a ido kuma sai ka rantse zo na kasheka da hausan basu sani ba. Ita dinma mutane da yawa kallon da suke mata kenan. Tun a ranar suka gama tsara bin guard airport su taho da abbyn fadeelan, harda sunanta suka jefa a ciki, murmushi tayi can qasan zuciyarta tace "Saboda gayyar sodi" amma a zahiri batace dasu dai komai ba,ita haka kawai take jin dama me gidan da suketa zumudin dawowar tasa zaiyi zamansa a can,cikin gidan yaci gaba da kasancewa iya yasu yasu mata. ********Ana gobe zai dawo nadeeya ta hanata sakat,duk da yana da cook dinsa permanent da yake masa girke girke tare da tanadar dukkan abinda yakeso,qwararren cook daya qware waien sarrafa nau'ikan abinci,cook din da ake biya da kudade masu nauyi,samfurin albashin wani ma'aikacin na wata guda…...amma duk da haka nadeeya sai data shirya nata dafe dafen "Yaa moha ya jima baici abinci na ba,zan bashi mamaki wannan karon,zaiji canjin taste" yadda nadeeya keta sanyata a abubuwa tana zugewa yasa a wannan gabar don kada taji babu dadi ta karba ragamar yin fried rice. Saidai kuma a daddafe ta gama hada kayan bugata ta ajiye,saboda wani ciwon kai da ya saukar mata lokaci guda,sauqin abun taji suna maganar evening flight ne,sai tasa a ranta zuwa goben xata warware in sha Allah. Ba wanda ta gayawa a cikinsu don kada su sanya damuwarsu a kanta,ta kawowa walwala da farincikin da suke ciki naqasu,sai ta wuce daki kawai ta kwanta abinta. Washegari ta kammala komai akan lokaci,duk da har lokacin tana dannewa ne kawai amma bata dawo dai dai ba,tana gamawa ko wanka bata iyayi ba ta koma gado ta nade tana sauke numfashin,sauqin abu daya tana fashin sallah,a haka bacci yayi nasarar daukarta. Da zumudinta fadeela data gama shirinta tsaf ta shigo dakin,tana tsammanin ganin sãahar ta shirya,sai ta sameta akwance tana bacci, zuciyarta a karye fuska a jagale ta koma falon "Ta gama shiryawa?" Nadeeya ta tambayi fadeelan tana qoqarin cire wayarta daga chargy "Sister nadeeya,bacci ma fa anty N din takeyi" "Bana tunanin lafiya qalau take gaskiya, kamar na fahimci bata da lafiya" baaba ramatu ta fada fuskarta na nuna alhini. Take damuwa ta bayyana saman fuskarsu gaba daya "Rabu da ita fadeela muje,may be ma jiyan bata samu isashen bacci ba.na fuskanci kamar tana da zurfin ciki" "Alamu sun nuna kam" baaba ramatu ta maidawa nadeeya amsa sai suka fice baaba ramatun na rakasu da addu'a. Har sai da suka garasa ficewa ta dauke idanunta tana girgiza kai sai wasu qwalla masu dumi suka biyo kuncinta,ta saka gefan yalwataccen mayafin jikinta ta goge sannan taci gaba da abinda takeyi cikin falon. / *******Cikin tarin nutsuwa kamewa da kuma kwarjinin nan nashi yake saukowa daga cikin jirgin tare da jerin matafiya da suke jerin first class. Ba abinda zaka fara hangowa sai kyakkyawar farar fatarsa din nan me surkin ja ja,wadda bata cika wani fari me yawa sosai ba saboda surkin jaa din da take dashi. Sanye yake da button up shirt me dogon hannu cream color dake da maballai gun metal color hakanan slim fit trouser din jikinsa me sulbi ya kasance kalar button din rigar tasa,wasu lafiyayyun loafers ne a gafarsa kalar trouser din jikinsa,nannunsa daure da tsadajjen agogon rolex daya fito sosai sakamakon tattare dogon hannun rigar tasa da yayi kadan ya rage yakai gwiwar hannunsa. Kwantacciyar sumarsa da tasha gyara take a kwance luf cikin wani tsari da gyara me daukan hankali sai glowing takeyi,hakanan eye glasses din da yayi amfani dashi ya sake fidda kyawawan qwayoyin idanunsa dake da wani yawa. Ko sau daya bata daga qafa ba wajen sauke tata gafara a duk inda ya ajjiye tasa ba,tana yi tana shagar qamshin lallausan turarensa daya zama abu na farko da ya fara jan hankalinta game dashi,duk bayan wucewar kowacce daqiqa sai taji kamar zuciyarta zata narka a kansa, tsahon awannin da suka dauka kadai a jirgin a tare tana jin kamar zata zauce a kansa,duk da cewa ko kalmar ZO bata hadasu ba,hasalima bata zaton ya ganta. Tana yawan ganinsa a shafukan MEENAL YA'AQOUB AJI,amma batasan cewa hotuna rage masa kyau da kwarjini sukeyi ba sai yanzu data ganshi physically "Hi mr man" ta fadi tana dan qara sauri don ta cimmasa,ganin baiko san tana biye dashi ba. Wani faduwa gabanta yayi lokacin da ya waiwayo ya zube mata idanun nan nasa dake da wani irin kwariini da maganadisu "How can I help you?" Kalmar sai tayi mata nauyi,taji kuma ta muzanta,abinda yasa tadan diririce kadan kenan,tayi gyaran murya sanda yake juyawa zaici gaba da tafiya ganin bata da abin cewa "Mmmm..... ammm,kamar nasan fuskar nan taka,idan ba damuwa....may i get your phone number?" Wani irin haushi da takaici ne ya kamashi,ya tsaya cak har ta cimmasa,ya waiwayo yana dubanta "What amount do you need?" Hannayenta ta harde a girjinta,tana dan ware idanunta kadan akan fuskar sa,cikin zuciyarta tana jin wannan din dama ce me kyau a gareta,don haka ta saki murmushi kadan "Five hundred thousand to one million" waiwayawa yayi yana duban jibril,hannunsa daya a aljihun trouser dinsa "A bata" va dawo da dubansa gareta "Wannan va zama shine lokaci na farko kuma na garshe da zaki yarda magana ta sake hadamu" daqa haka ta kewayeta yayi gaba cikin qasaitaccen takun nan nasa,ransa yana sake baci,zuciyarsa na motsuwa,yana in tsanar mata da halinsu gaba daya,ya gama yarda kudi yana gaba da komai a wajensu!,kuma tabbas zasu iya aikata komai akan kudi. Yaja tsaki har baisan adadi ba,zuciyarsa na sake quntata a duk inda ya gifta ya tsinci idanuwansu suna binsa da kallo duk da bawai kallon nasu yakeyi ba,amma yana ji a jikinsa, kyakkyawar fuskar yarinyar na dawo masa "Ya tsani mace me kyau,hadari ce,ya yadda da wannan" ya sake jaddada maganar can qasan zuciyarsa. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* 68 Tun daga nesa da ya hangi angel dinsa bacin ran ya fara narkewa,saidai wannan miskilar fuskar tasa na nan a hade,murmushi bai kubce mata ba sai da yayi hugging fadeelan,wani sanyi da nutsuwar ruhi na saukar masa,hancinsa ya zuqi daddadan turaren sãahar da take amfani dashi,qamshin ya cika masa zuciyarsa da kwanyarsa gaba daya. Zamewa tayi sannan ta duga har qasa tana gaidashi tare da yi masa maraba da zuwa,sosai murmushi ya wadaci fuskarsa,yasa hannu ya kamota yana amsawa da lallausar muryarsa dake nuna zallar gaunar diyar tasa "Waye ya koya miki angel?" Murmushi ta saki "Anty N" "she taught her a lot" nadeeya dake tsaye tana dubansu ta qara masa haske ita kanta tana jin alfahari da sãahar din. Miqewa yayi tsaye yana kallon nadeeyan,fuskarsa a dan hade,saita langabe kai tana dubansa,abinda yasa ya zare hannunsa daga aljihun wandonsa ya miqa mata,dariya ta kubce mata itama ta bashi sukayi musabaha, she's very proud with him,ta yarda yayanta miskili ne na qarshe,yana da wuyar sha'ani wasu lokutan,musamman idan kayi masa bahaguwar fahimta,amma kuma mutum ne me tsananin kula da damuwa da duk wanda yake alhakin hakan yana rataye a kansa,a yanzun tasan fushi yakeson ya gara nuna mata,amma ta karya lagonsa. Haka suka jera su uku,sun sanyashi a tsakiya,yana riqe da hannun kowa a cikinsu sun baibayeshi da surutu. Duk da rashin son magana da hayaniya irin nashi amma yana qoqarin bawa kowa hankalinsa,har suka isa inda motocinsa suke jiransa,daga daga cikinsu BMW sabuwar qirar shekarar Jason ya bude musu suka shiga ya maida murfin ya rufe. Har yanxu hannunsa na cikin na fadeela yana mamakin yadda tayi kumari,ta ciko sosai ta murie, ta gara haske gashinta ya qara kyau da tsaho,komai nata ya canza sosai "Abby baka tambayi anty N ba....bata jin dadi,tana bacci ma muka fito, sister nadeeya tace a ayaleta wai" saita karyar da kanta gefe bayan ta gama bashi labarin. Kanta da tun jiya sãahar ta gyareshi tsaf ya shafa "That's right ‚ku barta ta huta,she will be okay in sha Allah" sai ta magaleshi da kyau tana murmushin jin dadi. "ya kamata ayi doubling salary dinta ko?" Yayi maganar yana duban fuskokinsu. Murmushi nadeeya tayi tana gyada kai "Yaa salary din da har yau ba'a taba karbarsa ba?" "Like how?, Ya mata kadan ne?" Kai nadeeya ta girgiza "Bana tunanin haka,tunda mommy qarama ma kafin tayi tafiya last week naji tana tambayarta tana bugatar qari ne da taqi karbar salary dinta? amsar dai kawai No ce,tace bata bugata ne a yanzun,tafi sha'awar kula da fadeela kyauta,wannan ya qaramin qaunarta da ganin girmanta sosai yaaya" ta qarashe maganar tana kallon fuskarsa. Shuru yayi yana juya maganar nadeeya a ransa,zuciyarsa sai yaji sam bata aminta da tsarin ba "She must collet her salary,coz banga muhallin kulawa da ita a kyauta ba,we can afford all her needs da abinda muka mallaka,basai anyi mana aiki kyauta ba" dan murmushi kadan nadeeya tayi,ta karanci har yanzu akwai wannan zafin cikin ransa bai gushe ba "Kyautatawa ce fa yaya" waiwayo yayi ya kalleta,kamar zaice wani abu sai kuma ya fasa ya maida hankalinsa ga hanya,cikin ransa da zuciyarsa ya soke tsammani ko ganin kyautatawa daga dukkan wata macace muddin ba wadan nan jinin nasa ba. Kamar ko wanne lokaci idan ya dawo tafiya irin haka,yakan dauki wasu mintuna a farfajiyar gidan,saboda dukka ma'aikatan gidan masu masa barka da dawowa,ya bincika wasu abubuwan ya tabbatar komai haqqinsa ne ya sansu sannan ya wuce ciki nadeeya jibril da fadeela na biye dashi. Jibril ya ajjiye duk wani abu daya danganceshi ya sallami jibril din don shima yaje gida ya huta,su elyas zasu kasance dashi nadeeva ma sai ta wuce sashensu don ta kammala masa komai don yace abinci zai fara ci,yau kam tace nasu zaici,tacewa jacon yau duk abincin daya shiryawa ogan nasa saidai yayi haquri,yana dariya kasancewarsa me saugin kai, kuma yasan barkwancin nadeeya yace babu komai "Amma madam,ya za'a yi da abincin?" "Kaie dashi kuci kai dasu Jason kafin su wuce" cikin farinciki ya dinga juye musu abincin yana fita dasu,duk da cewa dukkan wani dake aiki a qarqashin gidan yafi qarfin ci sha da kuma suttura masu kyau,toufeeq yana daga parlor dinsa yana jinsu,baice komai ba,amma kuma zaiga wacce rigima ce ta sanya nadeeva bayar da kyautar abincinsa bayan yunwar da yakeji,kuma tasan baya son missing abincin Jacob din,ya yarda dashi da girkinsa,expert ne sosai ta wannan fannin,shi yasa salary dinsa yake na daban. Sai daya sallami fadeela da wasu daga cikin tsarabarta dole saboda yadda ta matsa masa ta bashi guri ya samu ya shige bedroom dinsa din ya watsa ruwa kafin ya zauna cin abincin. Kowa taqi kulawa a gidan da tarin kayan wasanta da bata gajiya da tara shirginsu,ta wuce kai tsaye dakin säahar. A nutse ta maida murfin gofar ta rufe,ta qarasa gefan gadon ta ajiye kayan tana kiran sunanta,ganin bata motsa ba sai ta haye saman gadon tana janye duvet din data qudundune a ciki "Anty N,abby is back,kinga abinda ya siyamin,yace sai ya huta zai daukomin sauran" wata miqa tayi tana jin dukka jikinta yana mata ciwo,dole ta yaye bargon ta miqe ta zauna tana karbar kayan wasan. Kusan dukka basuyi mata ba,saboda yanayin lafiyar fadeela da take kiyayewa,ta zabe wadanda basuyi ba a ciki tace mata "Wannan ki ragesu ki ajjiyesu ba yanzu zakiyi amfani dasu ba,saikin qara samun lafiya da kyau soon in sha Allah" kayan tabi da kallo,da alama tanason kayan,to amma tana bin maganar sãahar qwarai,duk yadda tace mata tayi abu ko ta bari tofa zata bi ne. Dole ta miqe suka wuce dakin fadeelan,ta tayata jera na jerawa,sannan ta dawo dakinta ta sauya pad dinta,ta daura alwala yadda zataji dadin jikinta ta fito parlor dinsu. Da baaba ramatu da nadeeya duka suna kitchen suna kacaniyar hada komai yadda zai dace da tsarinsa,a can ta taddasu "Yauwa anty N,yanzu nake shirin shiga naga ilkin naki" "Karki damu,alhmdlh,naji sauqi" ta fada tana karbar shirya abincin,nadeeya ta koma baya tana kallonta,har ta kammala shirya komai tsaf,cikin burgewa nadeeyan ta kasa shuru "Wow.ma sha Allah,anty N,anya ba catering kikayi ba?" Murmushi ya qwace saman fuskarta data dan canza kadan saboda baccin da tayi "Aikin maama na ne da anty farheen" "Nice name" nadeeya ta sake fada tana murmushi, zuciyarta kuma na mata kokwanto akan sãahar. Kota wanne bangare a waye take matuqa,kuma ta iya komai fiye da yadda ita din zatayi,ta zarta a abubuwa da yawa,bataga wata alama ta bugatar yin aikin nanny ba sam tattare da ita, komai nata na nuna wayewarta da zurfin iliminta,to amma she's very kind,suna in dadin zama da ita dukkansu,sai sukejin kamar wani gibi ne dake cikin rayuwarsu aka cike musu shi da ita,she's nice person,batason tayi mata wata tambaya da zata bata mata rai,ko tayi silar da zata tafi ta barsu. Ba yadda nadeeya bata juya ba akan tazo suje su gaisa da abby din koda ba zata zauna cikinsu suci abinci ba ta girgiza kai "Saurin me kikeyi sister nadeeya? munafa gida daya,kuma yau yau ya dawo shima,yana bugatar ya samu isashen lokaci daku,zamu gaisa ne" da haka ta doje tayi zamanta kitchen tare da baaba ramatu dake shirye shiryen yi musu tuwo yau,hakan ya yiwa sãahar dadi,don ita kanta tayi missing dinsa kwana biyu "Yadda kike maqalewa wannan bagin abun,ban zaci kina iya cin tuwo ba ai" baaba ramatu ta tsokaneta sanda take kunna gas tana dora ruwan tuwon a tukunya. Janye coffee din tayi daga bakinta tana murmushi "Inaci sosai baaba,tuwo abincine me sirri al a cikinsa" "Tabbas,amma mutan gidan nan basu sani ba,zuwanki yasa fadeela ta fara ci,amma ada idan nayi saidai naci abina ni kadai,ya kamata ki rage shan wannan bagin abun ko zakiyi kumari" murmushi ta sakeyi "Na iya kalolin tea baaba,amma nafi jin dadin wannan din,kamar wata jarrabawa" baki ta tabe tana murmushi "Jarrabawar ne ma,dake da baban fadeela bansan wanda yafi wani ba" a wannan gabar batace komai ba,sai taci gaba da sipping coffee din har ta kammala ta kamawa baaba ramatu wani aikin,daga bisani da zuwaira ta shigo saita sakar musu,ta dauki wayarta kuma. Karo na uku nadeeya ta iso masa da coffee din cikin wasu qawatattun kofuna da butarsu a tsakiya masu ruwan gold,bakinta dauke da addu'ar Allah yasa wannan ya zama na garshe. Sai daya balla mata harara sannan ya sauki qaramin cup din butar yakai bakinsa,kurba yayi ya hadiye,sannan ya dago dubansa yana kallonta bayan ya dora cup din saman tray din "the taste is still not good,lemme ask you" ya fada yana ritsata da idanunsa da gwara yasa bulala ya zaneta akan irin wannan kallon nasa "Don kinje karatu sai kika daina girki gaki yar gata?,wanne mutum zaki jewa a haka kuma kice sunanki mace?" Owalla ce ta cika mata ido,shifa yaa toufeeq damuwarta dashi kenan,akan tsafta da girki yanzun nan za'a ji kanku dashi,sannan baima tsaya yaga abinda ta dafa masa ba iarabar shan coffe dinsa ya motsa masa yace shi zai fara sha,ita sam ba ruwanta da wani coffee,bai dameta ba,shi yasa ma bata damu da iya hadashi yadda ya kamata ba "Am sorry yaa,nifa coffee kasan am not a big fan of it" sake wurga mata harara yayi "C'mon,come and serve me" yayi furucin yana duban siriryar wayarsa da yakeson maido network din gasar nan. Sai data gama serving nasa din sannan ta mige da sauri, "Ina zuwa yaaya" yasan bita da kallo,baice komai ba yaci gaba da danna wayar tasa yana jiran Jacob yazo ya hada masa coffe din har ta fice. Da kadan kadan qamshin shinkafar yake shigar masa hanciwani irin aroma da yasan bana Nigeria bane,tun baiyi niyyar kallon abincin ba har ya maida dubansa kai kallon farko girkin yaja hankalinsa,sai ya maida dubansa ga wayar yadan qara hanzarin don ya kammala abinda yakeyi din ya taba abincin yaji ko ya dace da taste dinsa. Da sallama cikin hanzari ta isa kitchen din "Madam coffee, zan samu coffee?" Ta tambaya sãahar dake goga kubewa a grinder "Yau kuma sister, lafiya?" "Me zanyi da wannan bagin abun naku" ta fadi tana dariya cikin salon tsokana "Yaa moha ne zai sha" "Eheenn,kinji ko?,yanzu na gama zancan,itama yanzu ta gama sha,Allah dai ya taqaita muku" cewar baaba ramatu,nadeeya ta tayata da "Ameen dai baaba" murmushi kawai tayi ba tare da tace musu komai ba,ta matsa gaban mini coffee maker din ta juye masa sauran ta hada a wani madaidaicin vacuum tumbler me rige zafi ta miga mata "Yauwa,thank you anty N,nasan zaiyi dadi duk da bansan dadinsa ba,amma qamshin was so perfect" ciki jin dadi ta juya ta fice. Yana gama aikin da zaiyi din Jacob na isowa da coffee din,ya rusuna cikin girmamawa ya ajjiye masa "Thank you" yace da Jacob,wanda sosai yakejin nauyinsa idan ya gode masa bayan ya masa hidima,shi a ganinsa shi ya cancanci yayita gode masa har qarshen rayuwarsa,sai Jacob din ya juya yana barin wajen bayan ya gyarawa fadeela kujerarta wadda ta bada hankalinta dari bisa dari akan game din da takeyi a sabuwar game din daya hado mata a kayanta "Ajjiye kici abinci angel" ya fadi yana qoqarin bude coffee din "Da anty N yanzu nakeci abby,kuma ma na goshi,ta bani abinci sosai kafin mu tafi airport" idonsa ya lumshe yana qara jin dadin yadda alamu ke nuna irin tsantsar kulawar da take samu. Ya sake yunqurawa zai bude nadeeya ta iso,kai tsaye ta dora tumbler din saman table din tana murmushi "Here's your coffe yaaya" duban kyakkyawan tumbler din yayi sannan ya maida kallonsa ga fuskarta "Daga ina?" "Kasha kaji yaya,i assure zakaji dadinsa sosai" "Thanks ajjiye a nan" sai ya maida hankali yana bude wanda Jacob ya kawo masa,ganin hakan ya sanya cikin sauri ta bude masa natan,wanda ta rigashi budewar,take tururinsa da qamshinsa suka cika wajen,qamshin da yaja hankalinsa,ya kuma binne na Jacob har baka iya jin scent din nasan. Tura masa gabansa tayi tana marairaicewa,hakanan yasa hannu ya dauka, yakai bakinsa yayi sipping. Sam baisan yana lumshe idanu ba,baisan ma sosai yake sha ba har sai daya daga tumbler din yaji ba komai,sai yaji yayi saurin qarewa,nadeeya na gefe cikin jin dadin yadda ya shanye din tas ba tare da yayi qorafi ba,sai kawai ta tura masa plate din abincin,wannan karon baiyi musu ba ya dauki spoon din ya fara ci. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* 69 Tunda ya fara ci din baice komai ba,cikinsa kawai yake kaiwa,wani dadi da gardin abincin yana ratsa kunnensa da kyau,zai iya cewa ya manta rabon da ya dorawa harshensa abinci me dandano irin wannan,cike da qamshin ganyayyaki da spices masu gara lafiya da qamsasa abinci. "it's delicious ko abby?" Fadeela dake leqen idonsa ta fada,kai ya gyada kawai "Anty N ce ta dafa fa,ta iya abinci sosai" dakatawa yayi da cin abincin,ya maida dubansa ga nadeeya "how a nanny turn to a cook?" Cikin gogarin daidata kanta ta masa gamsashen bayani ganin yadda ya hade rai nadeeya tace "Tafi kowa iya girki a gidan nan,ka tambaya fadeela,coffe din nan ma ita ta hadashi" ransa yadan baci kadan,saboda ba'a kowanne hannu yakeson yaci abinci ba "Amma.....you know my rules?" "Am sorry yaaya,ta fimu tsafta da komai da kimai Allah i swear" shuru ya danyi,sai ya ture abincin ya balle gorar ruwa ya zuba a cup ya fara sha. Ranar har dare suna tare har sai da sãahar ta kira nadeeya a waya fadeela tazo tayi mata shirin bacci "Kizo ku gaisa saiki dauketa please anty N" "Sorry nadeeya,ina uzurine ta nan haka,ki daure ki kawomin ita" "Okay" ta amsa mata tana kashe wayar. Basu jima ba suka snigo fadeela rungume dia ledojin tarin tarkacenta na cive ciye da wasa,daya hannun nata wata ledar ce, wadda ta tuburewa abby din nata sai daya bawa anty N din tata kyautar doguwar riga,sai wani designer din turare wanda zahirin gaskiya nashine na qashin kansa da yake amfani dashi wasu lokutan ya siyosu don ya ajjiye fadeela ta sanya rigima,to be honest baison sharing personal abubuwansa da mutane,amma fadeela ta daukarma anty N dinta. Sai data gama shiryata tsaf ta gudu gurin abby din nata tace yau a can zata kwana,ta dawo ta gama shirin nata baccin sannan ta zazzage ledar. Komai na ciki ya dauki hankalinta sosai da sosai,daga turaren har doguwar rigar, kana kallonsu kasan na musamman ne,tayi murmushi tana sake in gaunar fadeelan da yadda itama take sonta,ta yiwa kayan guri ta kwanta. ********Kamar kowacce safiya bayan alfir ya gama ketowa,yayi dukka azkar dinsa da addu'o'in sa,gym yake shiga wanda a nan hantsi yake riskarsa. Guri ne dake cike da dukka qarafuna da nau'in kayayyakin motsa jiki,wajen yana da girma sosai, kuma an masa tsari me kyau,kamar ba cikin gida aka yishi ba,kai kace daya daga cikin ire iren guraren motsa jiki na alfarma da aka gina ne domin neman kudi. Farare qal din sport wear ne a jlkinsa na kamfanin LULULEMON ATHLETICA,da suka fidda qirar jikinsa qwarai,shafaffen cikinsa dake da wani irin tattarar muscles,singalilin qafafunsa dake dauke da gargasa,a tsaye suke kyam suma da alama naman gurin ya saba da zallar gudu da motsa jiki,dantsensa da hannun rigar ya kamashi tsam shima,ya hada zufa sosai amma hakan bai sanya ya rage gudun treadmill machine din ba. Sai daya gama iya lokutan daya saba yi din sannan ya tsaida treadmill din, vana furzar da iska daga bakinsa yana dan fidda numfashi me kauri ya sauko,ya dauki water bottle dinsa ya bude ya kafa kai yana shan ruwa. Sai daya kusan shanyeshi ya ajiye bottle din,ya zari qaramin towel din dake ajjiye musamman a guri daban yana goge zufar. Ba abinda bakinsa da zuciyarsa ke marari irin dandanon coffee din jiya,duk yadda yaso ya kauda kai yanzun haqurinsa ya tuqe,a yadda ya gama motsa jikin nan shi kadai jikinsa yake bugata,sai ya tsugunna ya sassauta daurin takalmin qafarsa,ya ajjiye towel din ya fita daga gym room din. Yana tafe a veranda din da zata kaishi sassansa ma'aikatan da suke da aikin safe suna kawo gaisuwar su,da hannu yafi amsa musu sannan ya wuce cikin tsayayyen takunsa dake nuna zallar lafiya da mazantaka. A falo ya zare takalmansa,ya zura wasu dake ajjiye a gurin ya qarasa shiga cikin falon,hancinsa na jiye masa qamshin girkin Jacob,mudassir da ya kammala gyaran sashen yana feshe ko ina da wani freshener na musamman dake kashe qwayoyin cuta,kafin ya kunna kowacce humidifier dake aiki a lungu da saqo na sassan,ya rusuna yana gaidashi. Dan dakatawa kadan yayi da tafiyar yana amsa gaisuwar tasa,tare da qoqarin karantarsa "Ya akayi?" Ya jefa masa tambayar,kansa a qasa yana shafa kan nasa "Sir, matata ce ke labor tun jiya,amma bata haihu ba,so na barosu ne a asibitin inason tafiya da wuri" agogo ya kalla sannan ya maida dubansa kansa "Me yasa kazo aiki?,me yasa baka nema excuse ka tsaya ka kula da amanar da aka baka ba?" Ya fada cikin kaurara murya da alamun fada "Banason ne..” "Bakason me?,c'mon,saboda baa jikinka abun yake ba?, maza ka yiwa elyas magana,idan kuma saiiad ya shigo kace nace ya maka sallamar da zata isheka" godiya sosai ya zube yana masa,bai tsaya saurarensa ba ya wuce. Har yayi gaba ya dakata yace "idan ta wuce awa daya ka canza mata wani asibitin" "Yes sir,in sha Allah" daga haka ya wuce hanyar da zata sadashi da hallway. Duk da yanayin da rayuwarsa ta tsinci kanta a ciki amma Allah ya zuba masa masifar tausayin mace me ciki,koda kuwa cikin qarami ne,saboda har yanzu idanuwansa suna iya tuna masa wahalar da maji tayi,tun daga farkon cikin nadeeya har zuwa qarshensa,har yau bai manta ba. Wannan tunanin ya darsa masa ganin dacewar kiran majin ya gaya mata ya dawo,da wannan qudurin ya shiga dakinsa,saidai kafin yakai ga alkatawa sal ya manta menene ma yace zaiyi din,yakai gauro yakai mari amma ya kasa tunawa,sai kawai ya zare kayan jikinsa ya fada wanka. Da sallama a bakin nadeeyan ta tura gofar dakin fadeela ta shiga,murmushi ya wadaci fuskarta tana kallonsu "To bama dole kiyi kumatu ba? don Allah ki gani,da safen nan an tasheki ke daya kina cin kayan dadi ke kadai abinki" dariya kawai suka saka mata "'Ke da baki tashi da wuri waye zai rage miki?" Saahar ta fada tana goge hannun fadeela da tissue. Hamma nadeeya tayi "Yanzunma wallahi yaa moha ne ya tasheni don Allah coffe zaki taimaka ki bani na kai masa da sauri,kada yace ya fasa sha nayi jinkiri " kai sãahar ta daga tadan kalli nadeeya tana mamaki a ranta,don anyi jinkiri kawai sai mutum yace ya fasa shan abu? "Indai sauri kikeyi to yanxun kam sai milk tea wanda na dafawa faddee,babu coffee" RA "Ya salam....a zubamin nayi shahada,idan kuma nasha maruka to kin jawomin tare zamuyi jinya" ta fada tana zare ido. Miqewa sãahar tayi cikin fuskar mamaki "Maruka kuma? haba dai" "Allah ba komai bane wajen yaa moha,yaushe ya daina ne? tafiyata karatu fa" maganar sai tadan daure mata kai,to amma batason tsawaitawa tunda ba huruminta bane,don haka fadeelan na biye da ita tana bata labarin tsaurin yaa moha din har suka isa kitchen, itadai tana saurarenta harta gama zuba milk tea din a wani siririn qawataccen silver flask, qamshin flavour din da yakeyi da su cardamom gaba daya ya cika kitchen din "Yawuna ya tsinke Allah,wannan wanne irin tea ne? don Allah anty N ki ragemin" dariya nadeeyan ta bata,yadda tayi maganar da gaske cikin marairaicewa "Ya rage miki,bana zaton zai iya shanyewa" dukka ta zaro fararen idanunta waje "Wa? niii?yaa moha din zance ya ragemin abu?,idan kin ganni a lahira kaini akai" da mamaki ta juyo tana dubanta "Wanne irin mutum ne shikam haka?" Abinda takeson cewa kenan,amma saita maida maganarta ta hadiye. Idan ta saba yin hakan da nata yayyun,nan din ai ba gidansu bane,kowa da irin tsarinsa da nasa ra'ayin,so ba huruminta bane. Yana amsa waya ya fito daga dakinsa,yayi fes cikin wasu fararen kayan still, da alama zabinsa kenan farin abu ko kuma abu me haske,musamman idan ka duba vanavin furniture din dake qawataccen falonsa. Da ido ya tsire tea din har ya kammala wayar,ya kashe ta ya ajjiye wayar a gefe yana hada hannayensa guri daya,kafin ya maida dubansa ga nadeeya "Me ya hau kanki ne?,wannan yanzu coffee ne?ko dama inashan tea da madara?" Tasan dama tsaf hakan zai iya faruwa,don haka ta sake maida fuskarta kalar tausayi "Ba wancan yaaya...amma please kasha wannan,idan baiyi ba Allah na rantse, kayimin hukunci" "Ya isa,Gate out" ya fada calmly,da sassarfa ta juya ta fice tana dafe qirjinta saboda arzigin data auna yau bata shiga ukunsa ba. Kaman bazai sha ba kamar dai jiya,sai qamshin ya buwayi hancinsa,a daqile ya dauki cup din idanunsa akan TV ya kurba. Kasa wassafa komai yayi a ransa, saboda qamshi da gardin madarar daya kai masa ko ina,karon farko bayan shekaru masu dama ya samu tea din da yafi masa coffe dadi. _tom,nikam nace tun yanzu MR JARMA?,WAI YA HADUWAR ZATA KAYA NE? KOWA NA YABON DAN UWANSA BA TARE DA YASAN WAYE SHI BA.MUJE ZUWA_ *DON ALFARMAR ANNABI MUHAMMADU ME FITARWA KIYI HAKURI KIBAR MANA KAYANMU* *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Page 70 . Baisan ya akayi ba,shidai ya tsinci hannunsa riqe da empty cup,ya maida a hankali ya ajjiye yana tunanin rabonsa da shan madara a tea,sai gashi yanzu ya shanye ta tsaf,har yana jin buqatar qarin wani tea din,to amma bayason ya aika din,zaidai binciki yadda ake sarrafashi. *********A tsaye suke suna fuskantar juna,duk da cewa ita din bashi take kalla ba hakanan akwai 'yar tazara a tsakaninsu. Irin kallon da yake mata kadai zai gaya maka zallar yadda zuciyarsa ta narke da soyayyarta "Zan tafi.don Allah ina roon kici gaba da bani dama" "Allah ya kiyaye ka gaida gida" ta fada tana Juyawa,zuciyarta a quntace saboda abubuwa biyu,na farko tasa yasa an tilastata ta bashi damar zuwa zance gidan mutane,taso ta furje amma Dr girema ya kirata da kansa,yayi masa irin fadan da bai taba mata irinsa ba,sannan kuma ya tabbatar mata wa'adin sati biyu kacal ke gareta,ruwanta ta bashi dama ta bude masa zuciyarta ta fadada tunaninta su fahimci juna,ruwanta ne kuma taqi. Maganganun dr sun daga mata hankali sosai,don bai taba mata magana da salon fada da bacin rai irin haka ba. •Ci gaba da kallonta mahmud yayi har zuwa sanda ta bacewa ganinsa,ya sauke hannunsa yana furzar da iska daga bakinsa,sannan ya juya yana nufar inda gurd dinsa da ya masa rakiya yake. Hakan yayi dai dai da shigowarsa ta qaramar qofar gidan,yana sanye da wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin african kaftan na maza,fuskarsa ta cika da wani irin kwarjini,elyas da jibril na biye dashi. Dawowarsu kenan daga masallacin layinsu wansa aka gudanar sa taro da akanv duk sanda aka samu dama,kusan duk wan ke muqami ko babba a unguwar yana halartar taron. Lokaci guda idanunsu suka sarge ana juna,murmushi mahmud ya saki cikin hanzar ya maida akalarsa zuwa gabansa "Sir" ya furta yana saluting nashi cikin murmushi,fuskar toufeeg ta motsa kadan alamun murmushin shina yayi, ya migawa mahmud din hannu "Barka da yamma sir" "Barka,kana lafiya?" "Lafiya alhamdulillah,kwana da yawa sir,tun a Singapore,ban zaci zamu sake haduwa nan kusa ba" "Gashi Allah ya nufi hakan" ya fadi yana maida hannunsa ga aljihunsa fuskarsa a dan sake ba kamar yadda take ba "'Gaskiya ne,ina fatan zamu sake haduwa anan kurkusa" "In sha Allah" ya fada yana gyada kanshi "Nazo ne wajen qanwata da kuka riqemin a gidanku" "A nan din?" Ya fadi cikin mamaki "Yes sir" ya fada yana waiwaya hadi da duban inda sãahar ta tsaya a dazun. A ran toufeeq din ya danji mamaki,me kuma zaya kawo qanwar mahmud gana gidan?,ko cikin qawayen nadeeya ne?,shine tunanin da yafi kwanta masa "She's my soulmate,inata qoqarin ganin mun dai daita ne,she's my wife to be in sha Allah" sake daurewa kansa yayi,har ya kalla ainihin sashen cikin gidan ba tare da ya shirya ba,sai ya gyada kai yana sake bashi hannu "Allah ya taimaka" ya fadi ya zame hannunsa bayan sunyi musabaha yayi ciki. Dab da zai shiga sashensa nadeeya ta fito tana laluben sãahar sabida shurun da taji tun bayan fitarta,tayi masa sannu da zuwa ya amsa yana tambayar fadeela,sai tace masa tayi bacci yanzun nan bayan ta gana jiran dawowarsa,yana wucewa ciki yana gaya mata ta kawo masa cottee nan da kamar awa daya, murmushi ta saki gain yadda ta zama addicted da coffee din nanny,shi da baya cin komai a hannun kowa. Har ya zarta ya dawo da baya yana tambayarta waye yayi bago a gidan? "Nanny N ce,ko ba mahmud ba?" Kai ya jinjina,sai kuma yayi gaba ba tare da ya sake cewa komai ba,amma can qasan ransa cike yake da mamaki,mahmud ke son nanny din gidansa?,abun sai yaji baiyi making sense ba,so amma shi din ba mai damuwa da shiga rayuwar wasu bane,don haka tun bai isa sashensa ba ya tattara lamarin ya watsar. Sai daya gama komai ya sauya kayan jikinsa zuwa wata shirt,v neck ne daya fidda sirrin ginannen girjinsa me yawan gargasa,sai dogon wandon joggers pants,qafarsa saye da socks da baya rabo da ita yawancin lokuta. Farfajiya ce ta musamman da akayi mata gofa daga cikin falonsa, wanda aka qawatata da wasu irin sofas masu retractable canopy a samansu,wanda zasu baka daman zama comfortable kamar kana kan gado,samansu ya zauna yayi relaxing sosai sannan ya kunna system dinsa bayan ya duba lokaci ya tabbatar lokacin da suka sanva don yin meeting dinsu through video call da directors na companies dinsa dake gasashe daban daban lokacin ya cika,ya bude system din ya saita komai sannan yayi group call in general. Ba jimawa kusan kowa ya daga din,mutanene da sukasan muhimmancin lokaci da kuma na aikinsu,don haka komai suna yinsa ne akan lokacin da aka tsara zaa yi din. Cikin salo da qwarewa da sanin makamar aiki suke tattaunawa,da zallar qwarewa a harshensa na furta kalmomin yaren turanci,a haka suka cinye awa guda cif,wanda basu qara ba kuma basu rage ba aka tsaida taron,suka sanya wani lokacin da zasu sake haduwa su tattauna. Sake zama yayi saman sosai saman sofa din,yana gyara rumfar dake saman sofa din. A yanzun yana jin aminci da nutsuwa sosai akan kasuwancinsa,dukka directors dinsa amintattu ne,ya tabbatar koda babu shi zasu iya gudanar da kamfanin fiye ma da yadda zaiyi. Wayarsa ya ciro ya lalubi number nadeeya,bugu daya ta daga "Yaa gani nan,kana ta baya ne?" "Yeah be hurry" "Okay tom" ta amsa masa,tana maida dubanta kan säahar dake hada coffe din zata dora masa "Don Allah yafi na ko yaushe,zan tambayi wani abune, inaso a bani da wuri,kinsan yaa moha shi da girki two and one ne" murmushi tayi tana girgiza kai,tuni ta fahimci hakan al,yanason laflyayyen abincihakanan baya shiri da yunwa. Tun kafin ya kashe kiran da ya yiwa nadeeyan yaga kira nata shigowa wayar tasa baisan number din ba bashi da niyyar picking,saidai yana gogarin katse kiran nadeeva din kiran ya shigo ya daga lokaci guda ba tare da ya shirya ba,dai dai lokacin kuma true caller dinsa ya nuna masa sunan me kiran AMEESHA!. lya sunan kawai ya haifar da wani irin bala'i cikin zuciyarsa,lokacin da sautin muryarta kuma ya baqunci kunnensa sai ya ja fikinsa ya sauko daga saman sofa din yayi tsaye,kowacce jijiya ta jikinsa tana miqewa "Ina fatan kana lafiya,babu wata doguwar gaisuwa,don na tabbatar ba amsamin zakayi ba.....inason naga 'yata,inason a bani lokaci nazo na dauketa tayimin hutu,tunda nasan zuwa sati me zuwa zasu fara exam,upper kuma sun gama.. "'Stop!" Ya tsaidata a tsawace, yanajin wani abu na masa tururi tun daga zuciyarsa zuwa saman fuskarsa "Lokaci na farko kuma na qarshe da zanyi warning dinki,ki cire a ranki cewa kin taba haihuwa da toufeeq jarma,ki cire a ranki cewa kina da 'ya a duniya tare dani,wannan shine gargadina gareki" yayi maganar yana nuna gabansa cikin wani irin fushi da deepness a cikin muryarsa "Ta yaya? ka taba ganin an raba uwa da 'yarta?,laifin dana aikata tsakanina da ubangiji na ne,so bai shafi alaqata da dangantakata da 'yata ba,inata kawaici,inata dannewa,ina tsoro da fargabar kiranka,for what! fadeela yata ce, kuma har abada ba'a taba canzawa tuwo suna" "Idan kin isa ki kusanceta da taqi daya tak!,kiga yadda sunanki zai sauya" ya fada cikin tsawa da matsanancin fada "Bazan kusanceta a zahiri ba,amma zan kusanceta ta hanyar da duniya zata sake shaidawa diyata ce halak malak' "Go ahead. karki fasa,zan nuna miki other side dina da baki taba gani ba,stupid idiot" ya fadi yana wurgar da wayaryasa hannunsa ya shafi sumar kansa da qarfi hadi da yarfar da hannunsa. "Ka dinga yawan ambaton Allah duk sanda zuciyarka ta zafafa" daya daga cikin maganganun maji suka fado masa a ransa,sai ya koma da baya da baya ya zauna gefan sofa din,qafafunsa a qasa,ya lumshe idanunsa yana kiran "Hasbunallahu wani'imal wakil,wala'udwana illa alazzalimin,ya hayyu ya qayyumu birahmatika astagis, aslih li sha'any kullah,fala takilni ila nafsy darfata ainin" a hankali sai numfashinsa dava fara canzawa sakamakon tuna wace ameesha da tabon da ta barwa rayuwarsa ya fara daidaita. Duban sãahar data shirya tea din nadeeya tayi "Don Allah anty N,taimakeni,magana mukeyi me muhimmanci da maji banason ta katse,ki migawa yaa moha din,yana ta baya idan kuma ta falonsa zaki shiga ki tambaya guards zasu saita miki" duban nadeeyan tayi,sai taji ta kasa musanta mata. Ba sau daya ba ba sau biyu ba,a kwanaki goman da yayi da dawowa tana nemanta alfarma taje su gaisa,har ta gaji ta daina,batason taji wani abu a ranta kota dauka wani abune na daban,don haka ta gyada kanta tana gyara yafen dan mayafin pakistani dress din dake kanta,wanda ya lullube asirin sumarta me tsaho cika santsi da kuma laushi,ta juya a hankali tana fita a kitchen din "Maji tace tanaso yau ku gaisa, wana biyu bataga fuskar diyarta ba,kamar ma tace akwai maganar da zakuyi,zan rige wayar harki dawo" "Alright" ta fada tana murmushi,haka nan itama Allah ya sanya mata gaunar matar kamar yadda take gaunarta,tana burgeta,tana da wata irin kamala da dattako sosal. Haka nan takejin gafafunta babu nauyi sanda ta nufi gofar bayan da zata sadata da farfajiyar da yake din, taci gaba da takawa a nutsen,sassanyar iskar dake gurin tana kada turaren iikinta zuwa kowanne sashe na wajen. Kafin ta garaso ta hangi mutum zaune saman bagar sofa din da aka yiwa farar shimfida,saidai bata iya ganinsa fuskarsa saboda yayi qasa da kansa. Tana sake kusanto gurin tana kasa sarrafa idanunta daga dauke dubanta daqa kansa,cikin jikinta takejin kamar tana dosar wani mutum ne data taba saninsa ko ganinsa,a haka har ya rage saura taqi kadan ta cimmasa,ta bude bakinta da taji ya soma rawa da nufin yin sallama,dai dai lokacin da ya daga fararen manyan idanunsa da suka rune zuwa kalar jaaa. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Page 71 Guri guda idanunsu suka hade,wani abu me matugar garfi ya fusgeta,ya kuma ratsata tun daga tsakiyar kanta har zuwa tafin qafafunta,a hankali tray din dake hannunta ya sulale yayi d'ai d'ai a gasa,bata bawa kanta wani option ba da ya wuce juyawa cikin hanzari da sassarfa tana barin gurin. Ko motsawa baiyi ba daga inda yake zaunen,tamkar an dasa shi a wajen ya bita da kallo harta qule ta bacewa ganinsa. Kaf tunaninsa ya katse ya kuma tsinke,babu abinda ke kai kawo a fuska da kuma zuciyarsa sai fuskarta,his ex president......me takeyi a gidan? wayo ya kawota cikin gidan?. A hankali ya sauke dubansa kan farantin da yayi d'ai d'ai a gurin,komai ya kama gabansa,tunanin da ya darsu a ransa ya sanyashi zaro wayarsa ya sake kiran number nadeeya,bugu daya ta dauka "Waye kika aiko ya kawomin coffee?" "Am sorry yaaya,muna magana ne da maii nannyn fadeela ne" "Nanny?" Ya tambayeta da wani irin murya "Eh yaa,am sorry ya mohai didn't intend to offend you" bai tsaya ce mata komai ba ya kashe wayar kawai "What if itama ta shigo rayuwar su ne ta cutar masa da fadeela?" Shine kawai abinda ya samu zuciyarsa na jaddada masa,dukkan alamu sun nuna she's not in need bare yace hakan va sanyata aikatau,bata fito daga gidan da suke da qaramin qarfi ba bare yace a buqace take,ko kuma ta cancanci tayi aiki a wani guri, qaramin aiki ma irin wannan, she's well educated,tana da qualifications din da zata iya samun aiki ako ina Nigeria da waienta,amma sai ta zauna yin aikin nanny?no...ko daya zuciyarsa bata kwanta masa da hakan ba,kai tsaye ya tashi a wajen,ya bulla ta falonsa ya shiga ya dauki wayarsa ya fara neman layin mommy qarama. Da gyar ta isa dakinta saboda wani irin bugawa da zuciyarta keyi,kamar zata balle qirjinta ta fito ko kuma ta amayota ta baki. Gefan gado ta samu ta zauna tana maida numfashi,idanunta dukka a rufe,tana ganin shacin inuwarsa ta cikin duhun rufaffun idanunta "Yaa moha,shine toufeeq? daddyn fadeela? ‚yayan nadeeya?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar,wanda motsin fadeela da sunan kiranta da takeyi tun kafin ta shigo dakin ya sanyata bude idanuwan nata,sai ta mige da hanzari ta fada toilet ta maida gofar ta rufe. Tsaye tayi a jikin gofar tana jin sautin siriryar muryar yarinyar tana kiranta,sai zuciyarta ta gaza jurewa da shurun da tayi mata "Anty N idan kin fito maji na jiranki" saita sake mata gyaran muryar alamar ta amsa 'i love you anty" ta fada tana dariya ta fice. Hawaye masu zafi ne taji sun taru mata a ido,yarinyar ta saba gaya mata wanann kalmar duk sanda ta danyi wasu awanni bata ganta ba,a yanzun data gaya matan sai takeiin kamar furucin da zai shiga tsakaninta da ita kenan na qarshe ita fadeelan ......koda wasa batajin zata iya lamuntar zama gida daya da MT jarma,mutumin da ya wulaqantata,ya tozartata,yaci mutuncinta,mutumin da baisan darajar dan adam ba,sai taji tana jajantawa fadeela,yarinyar batayi sa'ar uba ba sam,ta fito daga tsatson da bai dace da halayyar yarinyar ba. Wani kuzari ne yazo mata da ya sanyata bude gofar dakin ta fito,ta nufi qofar dakin ta murza mata key sannan ta dawo da sauri ta jawo luggage dinta ta fara zuba kayanta a ciki. Cikin mintuna galilan ta gama hada dukka kayanta waje guda,dama ba wasu kaya masu yawa take bari cikin gidan ba,tunda kowanne sati tana zuwa gida ta maida wasu ta dauko wasu,ta zari Vail dinta dake saman couch ta nannade kanta zuwa wuyanta,ta jawo luggage din ta bude qofar dakin fa fito. Tana sako gofarta a hallway din suka bangaji juna ita da nadeeya wadda ga biyota da iPad din ta bata maji din kamar yadda maji ta bugata. Da sauri nadeeya taja baya tana kallonta mamaki kadan na nunawa saman fuskarta "Ina zuwa haka da akwati da yammar nan?" Sosai tayi gogarin dadaita muryarta "Gida zan koma nadeeya" razani ne ya nuna sosai a fuskarta,sai lokacin ta samu damar qarewa birkitaccen yanayin sãahar din kallo "'Gida kamar vaaya anty N,me ya faru?" Hannun nadeeya ta laluba ta sanya mata key din dakin a hannunta "Kuyi haquri,bazan iya ci gaba da zama tare daku ba" "Me kike cewa säahar? don Allah me mukayi miki? …baaba ramatu!" Nadeeya ta gwalawa baaba kira a rude ganin sãahar ta ja luggage dinta tana barin hallway din zuwa falonsu,wanda daga shi sai babban falonsu sai fita daga sashen gaba daya. Kiran baaba ramatu din da tayi yaja hankalin fadeela ta fito daga dakin nadeeya din "Baaba,wai anty nanny ce kawai ta hada kayanta wai gida zata koma" "Subhanallahi,me ya faru?,me akayi mata?" "Wallahi ban sani ba baaba" nadeeya ta bata amsa ita da fadeelan suna rige rigen cimmata. A falon garshe suka tareta har baaba ramatun "Haba Khadija,me ya faru haka rana tsaka zaki ce gida zaki koma" "'Ba komai baaba,na ajiye aikin ne" teddy din hannunta fadeela ta yar,ta kama hannun sãahar ta rige tsam "Don Allah anty karki taft,idan kuma zaki tafin bari na dauko kayana mu tafi tare" zuciyarta ta sosu da yadda taga yarinyar ta rude lokaci daya,sai ta tsugunna a gabanta tana riqe da hannayenta "Tafiya ta zama dole faddee na,kiyi haquri kinji,babu komai, sister nadeeya tana tare da ke,zata kula da ke,hakama baaba ramatu" saita zame hannun zata miqe,amma fadeelan taqi sakinta,ta fara hawaye tana cewa "Allah ni bazan zauna bake zanbi" "Am sorry my faddee" ta fada tana shafa sumarta da ta gama gyara mata ita dazu da azahar,tayi mata ado da wasu pink din ribbons. Zame hannunta tayi ta soma nufar waje,tana qwararawa kanta gwiwa daga raunin da zuciyarta ke shirin yi,batason ta karaya har taji ba zata iya tafiya ta barsu ba,tanason ta tsira da mutuncinta,wanda ta tabbatar idan tana gidan a qarqashinsa babu inda mutuncinta zaije,tunda har ya nemi take mata kima da martabar ta a muhallin da ba nashi ba....yaya kenan zai faru a yanzun da zata zamanto qarqashin ci da sha da inuwar gidansa?. Iska me zafi ya furzar daga bakinsa sanda ya gama jin komai daga bakin hajiya garama,zuciyarsa bata nutsu ba,yafi gasgata akwai manufa cikin shigowarta rayuwarsu,don haka zuciyarsa tafi aminta da sallamarta daga gidan,koda ko wanne irin kulawa take bawa fadeelan. A hankali kunnuwansa suka fara jiyo masa sautin kukan fadeelan,ya mige a nutse yana riqe da wayarsa a aljihunsa,ya kuma tunkari barandarsa ta inda yake iya ganin komai dake faruwa a farfajiyar gidan. Itace a gaba janye da luggage dinta,fadeela na biye da ita,nadeeya da baaba ramatu kuma suna biye da su cikin hanzari da alama suna nufin dakatar da ita ne,sauran maaikatan gidan kuma sunyi carko carko cikin damuwa,kowa ya kasa aikata komai,saboda basusan maqasudin abinda ke faruwa ba. Ransa ya sosu da ganin yadda fadeelan ke binta gudu gudu sauri sauri,amma ko sau daya bata tsaya ba bare ta waiwayo ta dubi kukan da takeyi ba "Fadeela!" Ya kirata a tsawace,abinda bai taba yi ba tsahon rayuwarsu shi da ita. Dukkansu suka tsaya cak,har saahar din da kiran nasa yayi wata irin tsawa a tsakiyar kanta,ta kuma runtse ido tana fatan Allah ya sanya ba dukan fadeelan zaiyi ba. A zafafe yake takowa har ya iso gurin "Tashi ki wuce ciki!" Ya fadi da muguwar tsawar da ta sanya nadeeya ja baya da sauri ta koma bayan baaba ramatu ta boye,saboda a yau din gaba daya a birkice take ganin yaa moha din. "Abby tafiya zatayi ta barmu,me mukayi mata,don Allah ka bata haquri" "Ba abinda kukayi mata,ko bata tafi ba daman zan sallameta,saboda bata dace ta rayu daku ba" maganganun nasa sai suka zame mata tamkar zubar dafi tsakiyar naman zuciyarta,tana da muradin ko sau daya ta waiwaya ta sake kallon fadeelan dake kuka iya qarfinta saboda ita kadai,amma kalmarsa ta sanya ta lanqwasa zuciyarta taci gaba da takawa ba tare data waiwayo ba. Tsawar data sake ji ya yiwa fadeela karo na biyu ya sanya qwallar dake magale a idanunta qarasa gangarowa,zuciyarta na kwarara da wata matsananciyar tsanarsa,sai ta qara sauri tana ficewa a gidan,lokacin da ya sanya hannu daya ya dauketa cak ya nufi cikin gidan,ta qwalla garar kiran sunanta full, abinda bata taba yi ba "Anty saahaaarrrr" kamar zata shide,sai ya dageta ya rungumeta tsam a jikinsa zuciyarsa na wani irin bugawa a mugun jargiy,yana jin kamar ana yankar naman zuciyarsa. Duk yadda taso riqe qwallarta cikin mota amma abun ya faskara,sai tasa tafukan hannayenta kawai ta lullube fuskarta tana sauke hawaye masu dumi qwarai,ba abinda ke dawo mata cikin kwanyarta sai sautin kukan fadeela da yadda ta qwalla kiran sunanta har zuwa sanda sautin ya dusashe daga kunnuwanta. Sanda suka isa qofar gidansu ta cire kudin ta miqawa me napep,yana fadin "Hajiya ga canjinki fa" ko waiwayowa bata iyayi ba ta daga masa hannu,ya fuskanci me take nufi sai hau zabga godiya yaja macnine dinsa yayi gaba Baaba habu ne ya karba mata kayan,yadda yake mata sannu da zuwa yaji batace komai ba sai ilkinsa ya bashi akwai matsala,don haka bai sake cewa komai ba ya migawa jamilu luggage din yace ya garasa mata ciki da ita. Can gasan magoshinta tayi sallama,falon nasu ba kowa kaman yaushe,yana nan a tsaftace da qamshinsa,da kuma ac dake bada iska me sanyin dadi,sai gamshin sanwar dare dake sirarowa kai tsaye daga kitchen dinsu. Baaba rabi ce ta fito daga kitchen din sai taci burki tana cewa "Ah ah,maraba da farar diya,kece yanzun nan akan hanya?" Kai ta gyada muryarta can qasa "'Nice baaba rabi,barkanmu da yamma" "Yauwa barka kadai" daga haka tayi hanyar bedroom dinta tana tambayar maama "Basu jima da fita ba ita da afifa" "To yayi" abinda ta fadi kenan ta wuce shige dakin nata. Saman gadonta ta zube kamar wata kayan wanki tana qoqarin samarwa kanta saugin abinda takeji a zuciyarta,tayi lamo idanunta a rufe tana jin yadda zuciyarta ke gonewa. Inda ace ta san wannan gidan nasa ne,inda tasan ace wannan ahalin nasa ne inda ace tasan wannan diyar tasa ce.....to babu shakka,duk yadda zuciyarta zata kai ga tausayinta ba zata taba rabarsu ba. Duk iya yadda yake tunanin zai iya lallashinta ko kuma ya bata baki amma abun ya faskara,har ya gaji da lallashin,ya koma bakin window din dakinsa yayi tsaye yana duban farfajiyar gidan, zuciyarsa na masa mugun zafi. Me yasa suna zamansu lafiya suna lallaba rayuwarsu zata shigo ta hargitsasu?,bayajin fadeela ta taba kuka irin wannan,koda kuwa ranar data rabu da mahaifiyar da tayi silar kawota duniya ne. Wai me yasa ne su mata basu da tausayi?,basu da imani?,a duk sanda zuciyoyinsu masu cike da ra'ayoyin qeta da son kai ta mosa musu,tabbas sai sun shiga rayuwar dukkan wanda suka hara sun aiwatar da koma meye sukayi niyya. Bayajin zai saurari kuka ko rigingimun fadeela,zata gaji ta haqura ta bari, dole ta koyi rayuwa babu mutanen da zasu zame mata baraza ko matsala,kamar yadda suka tashi shi da NADEEYA,suka rayu kuma a hakan,babu kuma wani abu da ya canza kalar qaddararsu,gasunan cikin qoshin lafiya da wadatar Allah. Bismillahir rahmanir rahim *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 01 A ranar cikin su hudun säahar nadeeya taoufeeq da mai gayya me aiki fadeela babu wanda yayi wani cikakken baccin dadi, nadeeva ranta a jagule zuciyarta fal tambayoyi tare da neman dalilin tafiyar sãahar din lokaci guda,sai kuma yadda yaga zallae bacin rai daga fuskar ya moha,idan har kunnuwanta sunji mata dai dai da bakinsa yake gayawa fadeela "Let her go,zaki ci gaba da rayuwa ko babu ita.." Sake juyawa nadeeya tavi tavi rub da ciki tana sake nazarin matsalar,a yadda idanunta suka karanci yaa moha din,kamar wata alaqar sanayya a tsakaninsu,to amma a ina ya santa ko kuma a ina sukasan juna? ,shine dai bata sani ba. Iska ta furzar daga bakinta,fatanta dai Allah yasa ba wani abu me muni bane va hadasu kwatankwacin na Ameesha. Sai ta girgiza kai da sauri tana gayawa kanta A'AH. ********Duk da kumburin idanuwan da basu samu bacci ba,da kuma ciwon kai da yakeson taso mata kadan kadan,amma hakan bai hanata shiga kitchen taya maama hadawa dr breakfast dinshi ba. Tana aikin amma yau so silent take,ba kamar baya da takanyi hira da masu aikin nasu ba. Afifa tun sassafe ta fice asibiti,saboda samun marasa lafiya da akayi daren jiya wadanda sukayi hadarin mota. A daki ta iske maaman,ta gaya mata ta gama "Ki shiryawa abbanku a dining na sashensa,fita zaiyi yau din yana da baqi,yanzu zan iso sashen" amsawa tayi da to ta juya tana fita, maaman ta bita da kallo. Tun jiyan datayi mata sannu da zuwa bayan dawowarsu da afifa ta karanci akwai wani abu dake damunta,to amma tasan halin kayarta da shegen zurfin ciki. Sannan tana zaune ma afifa zata gano musu komai. Sau da dama tana iya gayawa afifa damuwar da ita bata iya gaya mata ita,wannan din kuma wani haduwar iini ne da zumunci me qarfi a tsakaninsu fiye dasu iyayensu. Ta gama shiryawa tsaf ta juya zata fita muryar dr girema ta sauka kunnenta,cikin kamilalliyar muryarsa yake sallama a falon. Sai da gabanta ya fadi,amma ta tattara dukka nutsuwarta waje guda ta amsa masa sannan ta rusuna tana gaidashi "Zauna muyi magana" ya fada maya shima yana laluben wajen zama,sai ta zame ta zauna daura dashi kanta a qasa. "Jiya akacemin kinzo,ina fata ki dawo kenan,saboda ba zaki sake komawa ko ina ba,ladan da aka samu Allah ya amfanashi" a ladabce tace "'Eh,na dawo kenan abba,ina godiya kuma da dukka damar da aka bani" "Bata haka nake buqatar godiyarki ba ummi na" sai ya gyara zamansa sosai yana dora hannunsa saman hannun kujerar "Zuciyata ta gama nutsuwa da aminta da yaron nan,don haka ina me shaida miki,muddin kin bani dama kamar yadda musulunci ya tsara mu nemi izinin bazawara,to zan bashi damar turo magabatansa,yazo ayi a gama komai a wuce gurin,kema ki tattara hankalinki waje guda" "Na baka izini abba" ta fada kanta tsaye, zuciyarta na qeqashewa,tana jin yanzun bata da sauran mafaka kuma,guje gujenta ya qare,babu wani abu da ya rage mata, MAHMUD GANA yayi winning. shuru dr girema yayi yana son karantar fuskarta,yadda tayi saurin amsawa yadan daure masa kai,saboda ya riga ya ajema ransa ko yaya zai ta dan ja,amma karon farko babu jaa babu komai ta sallama?. Kai ya gyada "Shikenan kije,Allah yayi miki albarka,ko meye ake ciki zan sanya mahaifiyarki ta sanar miki" "Ameen abba" ta amsa tana migewa, kowanne sashe na jikinta na qarasa sakewa yana mutuwa dukkan wani qwarin gwiwarta yana zagwanyewa,qarshen tika tiki tik,mai afkuwa zata afku a kanta. Da gyar ta tattara nutsuwarta tayi wanka,batason duka wannan bacin rai qunci da damuwar da take yawaita samun kanta a ciki,ga tunanin fadeela cunkushe cikin zuicyarta,duk wani motsi da zatayi sai taji kamar sautin muryar fadeela ne keci gaba da kiranta. Wannan ya sanya ta shirya ta nema izini wajen maama,ta wuce gidan yaa muhyi ta dauko khaleefa,daga nan suka zarce gidan ya Saifullahi ta dauko fadeel,ta sauka gidan yaa zaid ta dauko zaahid. Tana Sanya ran kasancewarta tare da yaran zaiyi matuqar debe mata kewa,duk da cewa yara maza ne ba mata ba,amma tana da yaginin zai dauke mata damuwa me yawa,ya kuma rage mata zaman kadaici. ********Dukka manyan idanunsa ya ware a kanta,yana ci gaba da sanya spoon din abincin a bakinta cikin tsare gida tare da sake tsuke dinkakkiyar fuskarsa. Hakan ya qara ta'azzara rashin fara'arsa tare da garawa fuskarsa kwarjini. Duk sanda zata karba abincin saita kalli idanunsa sannan,ya sake kawo spoon din bakinta,sai taqi bude bakin bare ta amsa.a maimakon haka ma ruwan hawaye ne ya biyo baya. Ajiye spoon din yayi yana tsareta da idanu "Meye kuma?" "Anty N" ta fada hawaye na sake sauka a idanunta. Sosai ranshi ya sosu,don ko sunanta bayason yaji daga bakin fadeelan "Idan kika sake yimin maganarta. .. saina zane bakinki tas" ya fada yana zare idanunta cikin baraza "Oya,gate up" muryar sajjad ta ratsa tsakaninsu ya fada yana migawa fadeela hannu. Da hanzari ta miga masa hannun nata hawayen da suka magale suna garasa zubowa,ya tayar da ita tsaye yace "Muje ki gayawa sister nadeeya ta canza miki kaya,ki barshi yaci kansa shi daya,ya Allah. ..ina rogonka ka danqara masa soyayyarta azababbiya naga ya zaiyi da wannan zafin kan da zafin zuciyar" ya fadi maganar yana wucewa gaba abinsa. Ji yayi kamar ya tashi ya shago sajjad ya nannausheshi,adduar da yayi masan yazun jinta yayi bata da maraba da mutumin daya rogar maka saukar ajalinka a kurkusa. Shima sajjad din yasan me ya aikata,don haka ya dauki fadeela cak suka fice da sassarfa daga sashen,yana jiyo muryarsa yana sake kira masa wani alkaba'in na zurmawa soyayya. Sumar kansa ya shafa yana furzar da iska,zuciyarsa tana gogarin bashi nutsuwa ta hanyar jaddada masa babu ta yadda zaiyi a yanzun yaso wata diya mace, babu wata d'iya mace da zata iya galabar tsallakawa takai ga zuciyarsa,an gama yiwa ruhi da zuciyarsa barna,bazai kuma sake bari hakan ta faru ba,kai kwata kwata ma yanajin cewa a yanzun babu wani abu waishi SOYAYYA dake existing,zaifi kyau a canza masa suna da sha'awa ko son zuciya. A lokacin ne ya samu damar shiga toilet yayi wanka,duk yadda yaso ga yaci jerin abincin alfarmar da Jacob ya saba dafawa ha ajiye masa amma yau ya kasa dora komai saman harshensa,kukan da fadeela keta faman yi a kwanakin ya tsaye masa a rai,yau ta bugaci wani abu da yakejin bazai taba iya bata shi ba,sai kuma rashin walwalar nadeeya,duk gidan sun maidashi wani so silent, damuwa ce fal cikin zuciyarsa,wadda har sai data taba kuzarinsa. Yana tsaka da duba wasu ayyuka a system dinsa,ya shanya abincin da tun daxu Jacob yayi serving nasa amma ya kasa ci,aka gaya masa baaba ramatu nason ganinsa. Kafafunsa ya sauke yana bada izinin shigowarta,ta shigo cikin kamala da nutsuwarta,yayi mata da nuni ga saman kujera,ta koma ta zauna "Barka da yamma" baaba ramatu din ta fada,cikin girmamawa yace "Barka kadai,ya aiki?" "Alhamdulillah " ta amsa shi tana murmushi "Idan babu damuwa shawara ce dama nazo da ita" ta furta a nutse tana dubansa. Kansa kawai ya gyada mata alamun ya bata dama,ta danyi gyaran murya kadan tana tauna abinda zata fada "Nikam nace me zai hana kayi haquri da korar nannies din fadeela,saboda dole sai ana haquri da halaye da dabi'un mutanen da kake rayuwa da su,ba ta yadda za'a yi kowa yayi maka abinda kakeso dari bisa dari,yarinyar cikin watannin da tayi qalilan tayi aikin da babu wanda ya taba yiwa fadeelan shi,tana da kula da takatsantsan da iya raino,idan ba damuwa kayi haquri ka dawo da ita taci gaba da kula da fadeela don Allah" kansa ya dago ya kalleta,sai kuma ya maida kan abinda yakeyi, kamar bazaiyi magana ba kafin daga bisani yace "Ba zata taba dawowa ba,ta tafi kenan,so ku koya mata haquri,tunda tun farko dama ba da ita ta saba rayuwa ba,dole zata ci gaba da rayuwa ko bayan babu ita" tunda baaba ramatu taji ya fadi hakan ta tabbatarwa kanta saahar ta tafi kenan. Kaifi daya ne shi,wanda tsanani baya sakashi sauya zancansa ko dawowa da baya. Migewa tayi sali alin ta fice a gurin,cikin ranta tana jin matugar kewa da takaicin subuce musu da yarinya kamar sãahar tayi,ta tabbatar ba za'a maida kamarta ba. Sai yamma sosai sajjad suka dawo da fadeela,ko bayan sun dawo din bata ma shigo sashen toufeeq din ba. Tana lafe jikin nadeeya,wanda kafin kace meye wannan wani mugun zazzabi yayi ram da yarinyarnar wani irin rawan sanyi takeyi. Sosao hankalin nadeeya ya tashi,ta dauki waya ta sanarwa toufeeq. Daga masallaci ya dawo, kwanakin tunda suka fara wannan rigimar saboda tafiyar sãahar din shima baya fita ko ina,a gida yake wuni,duk wani aiki ta system dinsa yake gudanarwa. Hankalinsa yafi na kowa tashi,saidai zuciyar 'yan maza wadda bata bari aga rauni a tattare da ita. Mota ya kaita,ya sanya baaba ramatu ta shirya tazo su kaita asibiti. Nadeeya na zaune tana sharar qwalla har suka fice,zuciyarta a mugun karye,ta tabbatar wannan zazzabin na fadeela yana da nasaba da yadda tayi mugun sanya sãahar a ranta,da qulafucinta da takeyi. Gaza jurewa tayi ta mige ta isa daki,ta cire wayarta dake saman dressing table ta budeta,ta zauna bakin gado tana lalubar number sãahar. Dai dai lokacin da suke zaune a falo ita da afifa suna hada fruit salad din abincin dare,cikin kwanakin gaba daya itama ta sake zama so silent,babu wani karsashi ko kadan a tattare da ita. Duk da yadda fadeela ke tsaye a ranta,amma taqi bawa zuciyarta damar da zata karaya. Har a ranta tana jin hukuncin data yanke shine dai dai,babu gudu babu ja da baya,ta yadda sabo turken wawa ne,amma idan tayi haquri wataran zuciyarta zata rusuna,taji tamkar ma bata taba rayuwa da fadeelan dama duk wani ahalin gidan ba. Gefe guda kuma dukka kunnuwanta na kan motsi da kai kawon gidan,duk da ta tattara lamarinta ta miqashi ga Allah,saboda ta tabbatar tunda har ta bawa Dr girema wuga da nama akan lamarin mahmud,to tasan fa babu fashi aure ne zai zama tabbatacce a tsakaninsu. Abu mafi razani dake jijiga zuciyarta,kaddarar auren adam me daci ce da hallaka dukkan buri da gusar da fata ko sha'awar ci gaba da rayuwa ta aure dama ta duniya gaba daya.. ...ita kuma qaddarar auren mahmud fa? yaya zata zo mata?. Tambayar kenan dake barazanar fasa mata zuciya a duk sanda tazo kanta. Ta sani cewa saidai suyi zaman haquri ita da mahmud kawai,amma babu ta yadda za'ayi ya samu yadda yakeso daga gurinta,ta gaya masa wannan ta sake nanata masa,ya shaida masa yes......a shirye yake yayi haquri da ita ya kuna zauna da ita koma a yaya ne. Wani sashe a zuciyarta kowacce rana nana ya mata cewa JINSIN MAOARYATA NE,JINSIN MAHA'NTA NE,duk abinda suka gaya maka bashi kake tararwa ba bayan aure,yaudara da cin amana da karya alqawari sun lullube zukata da harsunansu, bata tunanin akwai wata kalma ta soyayya da jan hankali, nuna zallar kulawa da rayuwa yare har bayan mutuwa wadda adam bai furta mata ba,amma yaya sakamakon hakan ya kasance?. To auren me zatayi? ‚AUREN BIYAYYA kenan ko me? tunda dai ita din batakai lokacin da za'a ce tayi auren kai buta da ruwan wanka bandaki ba. Tsakiyar wanann tunanin wayarta tayi burari,ta waiwaya a nutse tana duban me kiran,zuciyarta na gaya mata mahmud ne, wanda zuwa yanzu ta fara tsanarsa tare da tsanar komai daya shafeshi, yana yaiwata kiranta da sunan caring,caring din da ita kuma bata sonshi, don duk abinda yayi sai taga kamar yana bin footprint na adam ne. Mamaki yadan kamata gain sunan nadeeya. Bawai bata kiranta ba,a'ah,tun daga randa ta baro gidan,har tayi kwanaki bakwai babu ranar da bzata fito ta fadi bata kirata ba tana roqonta akan ya dawo. Randa tayi alqawarin ba zata sake kiranta ba tayi fushi ne saboda ta tabbatar mata ba zata dawo ba,suyi haquri ta kula da fadeela,tun daga ranar bata sake kiranta din ba,saidai kullum zata bar mata good morning massage through watsapp dinta. Wugar hannunta ta ajjiye ta miga hannu ta dauki wayar,ta daga kiran ta karashi a kunnenta. Gabanta yayi mummunar faduwa jin sautin kukan nadeeya,tayi saurin kama sunan Allah sannan ta samu qwari gwiwar tambaya "Sister nadeeya,me ya faru?" "Fadeela ce. " Sai kuma maganar tata ta tsaya,abinda ya haddasawa sãahar wani irin muguwar faduwar gaba,ta sake kiran sunayen Allah "Karki cemin wani mummunan abu ya faru da ita" *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_*6 Book 02 Page 02 "Ke da mahaifinta dama ba burinku kenan ba? vanzu haka tana asibiti, kuma ko meye ya faru da ita kune ke da alhakin hakan" daga haka ta katse wayar,tabar sãahar da waya a hannu. "Gaskiya ta fada,meye laifin yarinya da zaku shiga rayuwarta ku gigita mata ita?,rana daya saboda baki shiri da mahaifinta ya birkitaki ke kuma ki tattaro ki bar yarinya kwatsam?" "Bai isa ya birkitani ba,baida wannan qarfin ikon,abinda na sani kawai bazan taba iya rayuwa dashi a muhalli daya ba muna shagar iska daya” "'I dan kukayi kisan kai ai ku kuka sani" afifa ta fada cikin jin haushi tana migewa a wajen. Maganar Allah itama zuwa yanzun haushinsu takeji,kamar masu ganin hanjin juna? babu dama su hadi guri guda sai kowa ya hau tashi kamar kububuwa?. Tun daga lokacin da nadeeya ta kirata har zuwa wayewar gari ta gaza moruwa gaba daya, lokaci lokaci sai ta samu kanta da duba wayarta,tanason kiran nadeeyan amma kuma batason tayi abinda zai sanya zuciyarta karyewa. Ko a daren jiya baccinta rabi da rabi ne,iya baccin data samu yi din cike yake da mafarkan fadeela na koke koke,abinda ya hadu kenan yayi mata rubdugu ya kassara duk wani walwala da karsashinta. Don ko da safe kwance tayi a daki,ta kasa fita ko ina. Ba abinda takeson gani a wannan lokacin irin fuskar fadeela,ta rungume yarinyar a jikinta kamar yadda suka saba,to amma kuma ta yaya?,batason cin fuska da cin zarafi don haka ya zama dole komai wuya komai daci ta nisanci dukan abinda yake da jibi da MT JARMA. Zuwa la'asar juriyarta da dukka haqurinta ya qare,wunin daki tayi ita kadai afifa yau tana asibiti gaba daya,ta kalli agogo,biyar saura,lokaci irin wannan lokaci ne nayin karatunsu ita da fadeela,ko ya halin karatunta ya shiga ciki?,duk yadda taso ta jure sai da qwalla ta cika idanunta,saboda ta tuna algawarin da tayi mata na har ta gama exam tare zasuyi karatun,to saura guda biyu ta kammala ta baro gidan,batasan waye ya tallafeta sukayi karatun biyun da sukayi saura ba. Batasan ya akayi ba sai kawai ta samu kanta da laluben number nadeeya cikin jerin calls dinta na yau,ta danna number tayi dialing. Hannunsa zube a aljihun silky trouser dinsa daya dace da short sleeve shirt din dake jikinsa,yana takawa a nutse tamkar saboda shi daya akayi hanyar da zata sadaka da dakunan AMENITY na asibitin. Manyan dakuna dake dauke da dukkan wasu kayan buqata tamkar kana gidanka. Ko baka sanshi ba kalli fuskarsa kasan wani kwantaccen fushi ne zalla a samanta,saidai tarin nutsuwar da yake da ita data cakude da miskilancinsa ya sanya ba lallai ka lura da hakan ba kai tsaye. Babu abinda ke amsa kuwwa a kunnensa sai bayanan Dr anwar,wanda yake jaddada masa dole ya kiyaye yasan meye asalin abinda ya sanya fadeela a wanann mummunar damuwar,dole ne yayi qoqarin sama mata abinda zai sanya hankalinta kwanciya ya dawo da ita walwalarta,ko don lalurar da take da ita, wadda ta ragu sosai fiye da baya. Shi kansa dr anwar mantawa yakeyi wani lokaci da lalurar tata,saboda komawa baya da takeyi tana raguwa da kadan da kadan a yan watannin da sãahar din ta kasance da ita. Idan yayi zuzzurfan tunani hakan yana nufin babu makawa sai ta dawo cikin rayuwarsu?,kenan tayi galaba dukka shirinta yayi tasiri kenan?,sai ya furzar da iska me zafi daga bakinsa,ransa yana gonewa,yana jin wani irin zafin yarinyar a ransa. Daga ranar da ya shata layi tsakaninsa da kowacce diya mace,babu macen data sake shigowa rayuwarsa tayi masa wannan karan tsayen sai ita. Dai dai sanda ya isa gofar dakin,ya sanya hannu ya murda handle din ya bude,saidai kafin yakai ga shiga yaji sautin siririyar muryar fadeela da ko yaushe bata rabuwa da kuka tana kiran sunan "AUNTY N,don Allah ki dawo, Allah bazan zauna ba nima idan baki dawo ba,kinmin alqawari amma shine baki cika ba? kullum kuka nakeyi,amma abby yace bazanzo ba,a nan zan zauna,kema kiyi zamanki". Dukkansu ita da nadeeya basuga shigowarsa ba,bare baaba ramatu dake sallah saman abun sallah. Kai tsaye ya sanya hannu ya zare wayar dake magale a kunnen fadeela,ya juya a nutse yana fita a dakin,ransa na zafi. "Hello.. ...hello,nadeee" sautin lallausar muryarta ya sauka a kunnensa lokacin da yake magala wayar a kunnensa,ya lumshe ido yana jin tsanar "Nawa kike da bugatar a biyaki ki dawo cikin ravuwar da kika riga kika shigeta cikin shirin faruwar hakan?" Cak komai ya tsaye mata,cikin mamaki ta kalli number,ta sake tabbatarwa number nadeeya ce,don dama ita din bata taba ajiyar number dinsa a wayarta ba,saita sauke wayar daga kunnenta kawai ta katse kiran,saboda bata jin zata iya tsaiwa ta saurareshi. Komawa tayi ta lafe a gado,zuciyarta na wani bugawa a jejjere,kwata kwata ta manta da sautin murvarsa cikin kwanyarta,don bata sake iinta ba sai a yau din. Idanunta ta mayar ta kulle,sautika biyu na tsalle tsakanin qirjinta da kunnuwanta,sautin innocent fadeela,da kuma sautin deep and husky voice dinsa. Labbansa na qasa ya cije lokacin da ya fahimci ta kashe masa waya ne,abinda yafi tsana kenan a rayuwarsa,sai ya sake tunzura ya kuma dannawa number din nata kira. Karar wayarta a karo na biyu ya sanyata bude idanunta,ta kalli wayar,kamar ba zata daga ba sai kuma taga nadeeya dince,ta dannan Koren shudi ta sanya kiran a handsfree "Muddin kika sake kashemin waya sai na baki mamaki,don har cikin gidanku zan iskeki,nace nawa kikeso a biyaki ki dawo bakin aikinki?" Yayi maganar cike da wata izza da gasaita. Tunawa tayi da matsayinta a rayuwa,da kima da kuma darajarta ta diya mace,wannan ya bata qwarin gwiwa,ta mige ta zauna sosai saman gadonta "Bazan dawo ba!" Ta gaya masa kanta tsaye,ta kuma dakata tana jiran abinda zaya fadi. Har tsakiyar kansa yaji saukar muryar tata da kalaman da suke nuna rashin toro ko daga gafa "Dole ki dawo,ki qarasa abinda kika fara shiryawa,dole ki dawo inason naga iya gudun ruwanki na kuma qurewa wasanki gudu donki tabbatar da banbamcin dake tsakaninmu" ya fadu a zafafe. Katse wayar kawai tayi saboda yadda deep voice dinsa ke shiga kanta sosai,tana ratsa jijiyoyin jikinta tana jin kamar yana a cikin dakinne. Ba iya katse kiran ta tsaya ba,gaba daya wayarma ta kashe,ta koma ta kwanta rub da ciki idanunta a lumshe,muryarsa naci gaba da yawo a kanta. Abu guda daya data sake amincewa dashi,yana da izza izgili da girman kai,ta fahimci akwai damuwa sosai cikin muryarsa, damuwar kuma bata rasa nasaba da ciwon fadeela daya sanyasu dukka a damuwaryanaso ne ta dawo taci gaba da kula da fadeelan duk da ransa baiso hakan ba.amma shi baisan hanyar da zai lallaba mutumin da yake neman abu a gurinsa ba,a haka zata koma? kai koda da sigar lallashi yazo mata bata jin zata koma,bare a yadda yazo mata cikin izza da gadara,sai ta gyara kwanciyarta ranta na turereniyar abubuwa guda biyu,tausayin fadeela da kuma takaicin kalamansa. Hannayensa ya yarfar,nadamar karbar kiran dayi mata tayin dawowa na lullubeshi,tunda yake babu wani mahaluki daya taba masa abinda tayi masan, ji yayi kamar yayi jifa da wayar,ya juya wayar a hankali yana qare mata kallo "Ta yimin dai dai, kuma haka shike nuna baka shirya samarwa 'yarka lafiya ba" sautin murvar Dr jarma ya ratsa kunnuwansa. Da sauri ya waiwaya bayansa yana duban mahaifin nasa,sam baiyi zato ko tsammanin ganinsa a gurin ba,tunda ma tun wancan satin sukayi sallama dashi ya tafi china,kuma a galla zai kwashe wata guda bai dawo ba. Rusunawa yayi ya rage tsahonsa "Barka da warhaka" "Aikai za'a yiwa barka muhammadu" daga furta hakan da yayi sai ya juya kawai ba tare da yace dashi komai ba. Da hanzari ya rufa masa baya sukaci gaba da takawa yana qoqarin cimmasa,abinka da sabon jini nan da nan ya tarar dashi,suka jera kafada dashi ya sake russunawa yana gaidashi sanda suke shiga verandar da zata sadasu da dakunan "Barka kadai,ya goqari?" Ya amsa masa cikin salon gatse, kafin ya samu amsar mayar masa nadeeya ta fito daga dakinsu riqe da hannun fadeela wadda ke takawa da gafafunta,fuskarta a washe matuqa,tamkar ba ita ya fita ya bari da hawaye shabe shabe ba "Yauwa,ku qarasa mota ku jirani ina zuwa" Dr jarma ya fadi yana takawa zuwa office din likitan. Hankalinsa rabuwa yayi biyu,sallamarsu akayi ko kuma Dr dinne ya sallami fadeelan da kansa?,ganin zai batawa kansa lokaci sai kawai yabi bayan dr jarma da tuni ya isa office din Dr anwar. "In sha Allah nan da gobe ma zakuga ta mige sarai, damuwa ai matsala ce a zuciya,ita kuma zuciya idan ta samu cikakkiyar lafiya ta kubuta daga damuwa,to dukka gangar jiki ma zata samu cikakkiyar lafiya da kuzari" kai dr jarma da yaga shigowar toufeeq ya gyada "Gaskiya ne dr,zama da damuwa dama a zuciya saidai idan kai kaso,sai kayita zamanka a haka tunda haka ka zaba,kowa kuma yayi rayuwarsa cikin farinciki" sarai dr anwar ya fahimci magana ce me harshen damo, tunda bawai yau ko jiya yasan familyn JARMA ba,kusan abubuwa da dama tare dashi akayi. Hannu dr iarma ya bawa dr anwar yana masa godiya,sannan ya tako yana fita. Kallo daya touteeq yayi masa sai yayi masa nuni da zasuyi waya,yabi bayan abban nasa. Motocinsa hudu ne a parking lot na asibitin, motar da yafi zama a ciki yaga ya nufa ya bude,sai yabi bayansa. Har ya sanya kai ya tsaya ya waiwayo yana kallonsa "Af,bari na maka bayani don sauke haqqinka na uba ko? zan kaita inda aka saba kula da ita,idan ta samu lafiya kaje ka daukota,idan kuma kaie din,ba ita kadai nakeso ka dauko ba,har wadda ta kula da ita din zataci gaba da kulawa da ita nakeson su dawo cikin gidan suci gaba da rayuwarsu yadda suka saba" daga haka ya shige motar sajjad ya rufe,ya sanya drivers suka tashi motocin suka bar harabar asibitin. Sam kanshi ma a sanann a daure yake,bai kawo masa tunanin inda dr jarma din zai kaita ba "Sir....zamu tafi ne?" Muryar jibril ta shiga kunnensa,sai ya amsa alamu da hannu,ya matso da motar ya bude masa ya shige ya rufe suma nasa motocin sukabi kwalta. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02 Page 03 Fitowarta kenan daga kitchen bayan ta gama shan coffee ta maida mug din,qofar falon da taji an bude da sauri ya sanyata waiwayawa da sauri,cikin zallar mamaki ta tsaya cak,tana duban fadeela dake takowa da gudu tamkar almara ta cukukiyeta tana kiran sunanta da garfi. Zubewa tayi saman gwiwarta tana riqe yarinyar da kyau tare da tattaba likinta a rude "Fadee,waye ya kawoki? kinsan gidan nan? ya jikin naki? kin warke ne?" "Babu wani ya jikinta,kamar dai irin da gasken nan kin damu da ita" muryar afifa da sautin muryar fadeela ya fiddota daga daki ya wanzu a falon "Wallahi,gashi mu mun laluboki mun kawo kanji" nadeeva ta fadi tana takowa Sosai cikin falon,tare da kallon kusurwoyinsa,mamaki yana saukar mata tare da tarin tambayoyi fal cikin kanta. Migewa tayi dauke da fadeela tana murmushi "Babu yadda zanyi ne sister nadeeya,kada kiji haushina" ta furta tana mata tayin gurin zama "Fushi nake dake saboda haka bazan zauna ba,rakiya kawai na yowa abba" idanu sãahar ta fiddo waie cikin mamaki "Wai Dr?" Sai ta jiniina kai "Suna waje shida abban gidan nan" sosai mamaki ya kama sãahar,sai ta sauke fadeela ta kama hannunta sukayi kitchen don samarwa dr jarma din wani abun shan. Falon sai ya zamana babu sai su biyu ita da afifa,afifan ta qaraso tana murmushi "Yaudai naga sister nadeeya,ki zauna mana" tana murmushin itama ta zauna,sannan tace "Don Allah bestie kiyi haquri, kaina ya kulle,tambayoyi ne dani fal bakina,kuma nasan aunty N ba zata taba tsaiwa tayimin dogon sharhin da nakeso ba,and na tabbata kedin kina da amsar kowacce tambaya tawa" hannu afifa ta miga tana murmushi "Kaina ya kawomin wasu tambayoyin da kike dasu,nasan kuma dole ki bugaci amsarsu,zo muie ciki" tsam ta mige tabi bayanta,suka wuce kai tsave zuwa dakinsu säahar din. Ko afifa bata fada ba nadeeya tasan dakin na saahar ne,don kusan yadda ta tsara dakinta na gidansu haka wannan,har yafi wancan nesa ba kusa ba,komai a kammale cike da tsafta da qamshi da wani irin tattausan yanayi. Tana dauke da babban tray din fadeela na biye da ita tana zuba mata labari a nutse daya bayan daya,riqe take da gefan doguwar rigarta tana biye da ita kamar jela,kai kace guduwa zatayi ta barta. Tun kafin su qarasa sai kunya ta kamata ganin yadda Dr da abbanta suka bisu da idanu kamar dai irin kana zancan mutum sai kuma kukaga tahowarsa daga nesa. Ta qarasa gabansu cikin girmamawar nan da kuma mutuntawa takai qasa tana gaida dr jarma,tare ta bude murafun abubuwan shan da tazo dasu tana zuba masa fadeela na matso mata da cups din. Cikin matugar kulawa ya amsa "Amma daa saura kadan nima nayi fushi dake,kin biyewa wancan tsatstsauran kuna shirin yin sakarci?" Sai ya maida dubansa ga dr girema "Ban taba sanin ita ke kulamin da jikata ba sai da muka iso gidan nan na fahimci hakan,bana fatar wannan alaqar ta yanke ta tsaya iya haka" dr mahmud ya fada yana jin wani karsashi yana shigarsa. Tun farkon saninsa da sãahar ta kwanta masa,yanayin kamun kanta,sanin kima da martabar dan adam, da tsantsar tarbiyyar daya gani daga gareta,duk kuwa da zurfin karatun bokon da take dashi...hakan ba qaramin burgeshi yayi ba, dabi' unta sun banbanta dana sa'o'i da takwarorinta masu matakin karatu da gata irin nata. "Ga 'yarki nan na kawo miki,zata zauna tayi jinya a gurinki" kalaman da dr mahmud ya fada kenan lokacin da sukayo masa rakiya zasu koma shida nadeeya,maganar da tadan daurewa sãahar kai,anya da sanin wancan dan wulaqancin Dr jarma ya kawo mata fadeela?. "In sha Allah zaka jini,na gode qwarai da ziyara,duk da ba takanas akazomi ba,sahun diyarka ka biyo" muryar dr mamman girema kenan yake fadiwa dr jarma "Diyata ta cancanci a biyota,idan ban jika bama mamman ni zaka iini,ni zan fara nemanka ma" "Karka damu" ya fada yana murmushi,sannan ya maida masa murfin motar,suka tayar da motocin suna ficewa a gidan. Zuzzurfan tunani nadeeya ta shiga,daya bayan daya qwaqwalwarta ke mata bitar maganganun da sukayi da afifa,akwai abubuwa da suka bata mamaki tausayi da kuma daure kai,ashe already yaa toufeeq da anty N din sunsan juna?,but itafa laifin yayanta take gani to be frankly,a nan bataga laifin sãahar ba,cikar diya macen kenan ko ita ba zata dauki izzar d'a namiji ba. Amma abinda yafi gigitata rayuwar da säahar din ta fuskanta,wadda ta tilastata sauyawa daga ainihin dabi'unta. Abu mafi ban mamakin shine daya zamana wai ta taba aure,babu abinda zai nuna maka alamun hakan tattare da ita tafi miliyoyin 'yammata cikar haiba da komai na halitta. Sake juya kanta tayi wata shawara me girma na tsargawa cikin ranta,sai ta kira sunan Dr da "Abbana" "'Ya akayi?" Ya tambayi nadeeyan yana qoqarin ajiye wayarsa bayan ya gama duba wani abu. Idanunta suka dan kai kan wayar,sai taga kamar hoton MAJI dinta "Abba dama kana da hoton maji ne?" Bakinta ya subuce ta jefa masa tambayar,don basu taba magana makamanciyar irin wannan baidanunta a kansa tana kallonsa. Harara ya watsa mata "Yau nine na koma abokin wasanki?" Janye dubanta tayi zuciyarta da gwiwarta tana karyewa "Kayi haquri" ta fada a sanyaye,sai yaji tausayinta ya kamashi "Me ya faru kika kira sunana?" Gara zamanta tayi "Ka taba sanin wani abu akan anty säahar?" Shuru ya danyi sannan ya girgiza kai "A'ah,akwai wani abunne?,mahaifinta Dr mamman munyi karatu dashi tsahon shekara biyar,sanann musan juna sosai a wancan lokacin,yanayi da lokaci ya jefa kowa inda yaso sai kuma aka rabu,sai bayan dogon lokaci bayan mun hadu da muhyiddeen na fahimci dansa ne,shekaru masu yawa kuma sai yau Allah ya gaddara ganawarmu" kai ta jinjina,sannan ta warwarewa dr jarma din kome data ji daga afifa. Tsahon lokaci yana jinjina kai ba tare da yace komai ba "Amma abba ni ina da shawara" juyawa yayi ya dubeta "Wacce irin shawara ce?" ******Tun daren ranar da aka kawota take magale da sãahar,duk inda ta motsa sai ta bita gafarta qafartaji takeyi kamar zata gudu ta barta. Ko da sukazo kwanciya sai data rungumeta sosai,a haka bacci yayi awon gaba da ita. Afifa na gefe tana kallonsu,dariya tayi lokacin da take zare jikinta daga na nadeeyan a hankali "Ah kin hadu fa da chewing gum" murmushi sãahar tayi,tana shafa kan fadeela gami da maida mata gashinta da ya ya mutse baya "Ta saba aiko a gida sai tayi bacci kafin na koma dakina" kai afifa ta gyada tana kallon fuskar fadeelan cikin tausayawa,farat daya taji yarinyar ta shiga ranta. Kwana uku cakal amma sai ka dauka fadeelan ta shekara a gidan,ta sake sosai tana ta walwalarta da harkokinta,zuwanta sau ya sake raya gidan,baya rabo da motsinsu da kai kawonsu ita da saahar,maama dai 'yar kallo ce,amma ita kanta yarinyar ta shiga zuciyarta,idan ka gansu zaka dauka itama daya ce daga cikin jikokinta,hadda da dr girema fadeelan ta shiga zuciyarsa,yana kallonta kamar su Aleena,idan ka shigo gidan zakayi tunanin itama jikar gidan ce kamar su khalifa. Fadeelan bata taba jin rayuwa tayi mata dadi ba kamar wannan lokacin,saahar ce komai nata,yadda take kula da ita a gida haka a nan,harna sama da gidan,saboda a nan din a sake take fiye da can da take ganin bata da wani hurumi da can din. Batun ciwo kuwa tun randa aka kawota babushi ya tafi,gefa guda kuma kullum sai sunyi waya da nadeeya da kuma dr Jarma,wanda ya dauke nadeeyan ya maidata gidansa,yace itama ta zauna a can na wani lokaci. *****Duk yadda yakai ga son ya dauke kai ya bar musu fadeelan yaga iya gudun ruwansu amma ya gaza. A yau yana tsaka da aiki ya kashe system din ya mige gafafunsa saman table din hadi da relaxing bayansa jikin couch din da yake kai yana lumshe idanunsa,jiya ya kira nadeeya yayi mata titsiye,ta kuma tabbatar masa fadeelan tana can. Yaso qwarai ya tattara ya zuba musu idanu,to amma zuciyarsa ta kasa dauka,gidan gaba daya shuru,babu kowa,dr din ya dauke nadeeya kamar yadda ya dauke fadeela. Miqewa ya sakeyi yana kaiwa bakin corridor din dab da wasu flowers dake fidda sanyi me qamshi,ransa yana zafi sosai game da yarinyar. A baya yana lallaba rayuwarsa,yana yinta hankali kwance ba tare da wata baquwar fuska ta kutso musu ba. Amma daga bayyanarta cikin watanni kacal tana neman ta zame musu qarfen gafa "Idan kabar mata fadeela tayi winning a kanka" daga can tsakiyar zuciyarsa ake gaya masa,kamar an zaburar dashi ya dawo da baya ya dauki wayarsa yayi kiran number dr jarma. Bugu biyu ya daga ya koma ya zauna sosai yana gaidashi cikin girmamawa. Kadaran kadaham ya amsa masa,cikin kamewar nan tasa yace "Abba idan babu damuwa zan qarasa na dauki fadeela, kusan hutunsu nex week zai qare,ya kamata ta dawo ta shirya a nutsr kafin lokacin" gyara zamansa dr jarma yayi "Eh to ai babu laifi. ..ummm... babu laifi,amma idan kaje ka tano harda yarinyar khadijatu me kula da ita din kenan" hannunsa ya dunqule guri daya yana shigar da tafin hannunsa ciki "Okay abba" ya fadi yana jin kamar dr jarma din yayi masa wata mummunar bushara "Ka dauki saiiad kuma ku tafi tare" dr jarma ya gara fada,saboda yanason ya samu me masa monitoring abubuwa "In sha Allah" ya fada sanann ya gimtse wayar. Iska me zafi ya furzar daga bakinsa zuciyarsa na sake soyewa da bacin rai da kuma damuwa,dr yana girmamawa al'amuranta da yawa,ya bata wani matsayi me girma,ya bata kuma yarda dari bisa dari "Ya Allah, ya rabb,kada ka sanya yarinyar nan ta zame mana sharri cikii rayuwarmu,dukka abinda ya qulla ya Allah ga wargazashi" ya samu kansa da furtawa. Lokaci ya duba yaga akwai sauran lokaci da zai isheshi yaje ya dawo,sai ya fada toilet ba tare da ya kira sajjad ba,nufinsa idan ya gama shiryawa sai ya kirashi,idan yace baya cikin gidan shikenan sai yayi tafiyarsa,ya tabbatar aikin Sanya Ido zaije yayi,shi kuwa sam sam bazai iya wani tsaiwa lallabata ko neman alfarma daga gareta ba. Tsaf ya shirya cikin kamala da wani ajiyayyen kyau da kwarininsa cikin wani lallausan vadin boyel me garancin kauri,fari ne qal kamar yadda kake iya hango fara tas din singlet dinsa daga ciki,rufaffen takalmi ya saka charcoal color na kamfanin Stuart Weizmann me asalin kvau da tsada. Kansa sai dake dauke sassalkar sumar daya gada daga bangare biyu,dr girema asalin shuwa dan qasar borno,da kuma maji balarabiyar Algeria ta kwanta luf saman kansa tana sheqi da fidda tattausan qamshi. Lafiyayyar fatarsa yake daurawa agogo,dai dai lokacin sajjad ya tura gofar ya shigo sanye da wata abaya ta maza,da alama yana cikin gidan yana hutawa,idanunsa akan TOUFEEQ da yayi wani mugun kyau "Yanzu nake shirin kiranka ka fito zaka yimin rakiya" "Amma dai my man..... .Wannan kwalliyar zance zakaje?" Ya jefa masa tambayar cikin shakku. Kyawawan fararen idanunsa ya dago ya watsa masa,bayan ya dakata daga sanya agogon,wani abu yayi masa tsaye a wuya,kamar zaiyi magana sai ya maida bakinsa ya rufe yaci gaba da daura agogonsa,don yiwa sajjad magana ma bata bakine,kome zai fada bazai fasa jansa da magana ba,kuma gobe sai ya qara. Shi kuma a yadda yanzun yakejin zuciyarsa ko doguwar magana bayason yi. Gaban dressing table dinsa ya qarasa,ya dauki turarukansa ya fara feshe jikinsa daga wuyansa zuwa qirji,sannan ya sauya wani ya feshe sauran sassan jikinsa dashi,ya ciri key din mota guda daya daga inda yake ajiyesu yayi gaba yana fadin "Kada ka wuce minti uku,ina parking lot" ya garasa fita ba tare daya waiwayoshi ba. Qaramar dariya sajjad ya saki yana dan buga qafansa, already yasan da fitar,tuni Dr ya sanar masa,amma baisan da wurwuri haka zasuje ba "Ko second daya ka bani sai fa na rakaka" yayi zancan shi daya,sai ya juya ya fita daga dakin.bava iin zai canza komai a jikinsa,don dakin,baya jin zai canza komal a jikinsa,don haka takalmi kawai ya sanya ya biyo bayanshi. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 04 Sosai take zaune gaban dr girema gafafunta a tanqwashe kamar zata maidasu cikinta,ko cikakken motso batayi tun zamanta a wajen "Sati guda suka rage miki,har yanzu bazan hanaki damarki ba,ki bawa Mahmud dama,ko kuma ki gabatar da wanda kikeso ban hanaki ba,bance lallai sai mahmud ba,shikenan maganar,kina iya tafiya" kamar qafafunta ba zasu iya daukar gangar jikinta ba haka ta miqe tana hada hanya,tun jiya kanta yake mata ciwo kadan kadan tunda taji abban nata yana nemanta,ta sani dama tatsuniyar gizo ba zata wuce ta qoqi ba. Sannu sannu takai kanta daki,Allah yasa yau din afifa ta dauki fadeela sun fita yawonsu,itama meson fita guraren shan iska ne kaman afifa,sai biyu ta hadu sukayi tafiyarsu suka barta. Ba irin saqe saqen da zuciyarta batayi mata ba a sanda take kwance saman gadon,tana hasaso yadda yau za'a daura mata igiyar wani,wanda dukka wani nauyi nasa da haqgin aure zai rataya a wuyanta,duk wata kebantacciyar mu alama ta maaurata zata hadasu?, Saita runtse idanunta gabanta na tsananta faduwa. Bata shiryawa wannan al'amarin ba sam cikin rayuwarta,ta sake mallakawa wani namiji zuciyarta da gangar jikinta?,wani abu ne me wahala da ko cikin mafarki batason ganinsa bare a zahiri. Kuka takeson yi amma a yau din zuciyarta gaba daya ta ida qeqashewa,sai faman zafi da radadi da zuciyar keyi. Baaba rabi ce ta shigo dauke da wayarta data wuce ta bari a falo "Alhaji yana kiranki" tana daga kwancen ba tare data cire kanta daga cikin duvet ba ta miga hannu ta karba wayar ta kara a kunnenta "Kina ina?" Dr girema ya tambayeta "Ina dakina" "To yayi,ki duba nan veranda dake baya kina da bago" wayar ta saki ta sulale cikin duvet din. Wai me yasa mahmud bazai haqura ya sakar mata mara tayi fitsari ba? yafison suvi zama mara alfanu?,zaman da ba zai qaru da ita da komai ba?,tabbas yau zata sake jaddada masa da babbar murya,don bata shirya wani rayuwar aure da kowa ba,dole idan abba yaga ya janye kuma bata kawo kowa ba ya haqura ya ayaleta. Da wannan qudurin ta sauko daga saman gadon cikin bacin rai,Adire boubou ce a jikinta,saita yafa mayafinta zalla saman kanta ba tare data nema babban mayafi ba ta zura takalmanta ta fice. Tun bata qarasa ba jikinta taji yana bata ba mahmud bane,to amma idan ba mahmud bane waye zaizo har cikin gidansu nemanta?,tanason ganin fuskarsa amma babu dama saboda ya bada baya,sai lallausan gamshinsa daya karade ilahirin gurin har ya bazu zuwa wasu sass na gidan,da kuma cikakkiyar baqar sumarsa dake kashe ido, kasancewar bai sanya hula ba. Tsaye tayi daga bayansa nesa kadan dashi,yaji alamun takun tafiyarta,tsaiwarta ta sanyashi waiwayowa,lokaci guda idanunsu suka gauraya cikin na juna. Baya ta dania da sauri saboda juyowar da yayi sai taga kamar ya cika wajen,kamar kuma ya sake rage tazarar dake tsakaninsu ne. Ta lumshe idanunta tana jin faduwar da gabanta yayi wanda har yanzu bugun zuciyarta bai koma dai dai ba,yayin da tasa zuciyar yaji ta danyi shacking saboda yadda lallausar sumar kanta ta fito sosai saboda janyewar da siririn mayafin kanta yayi ya koma rabin kanta,sajen dake kwance gefen kunnuwanta shima ya fito sosai,sai bagin gashin ya zama ado ga kyakkyawar farar fuskarta. Kwashe idanunsa daga kanta ya maida gefe yana jan qaramin tsaki wani bacin rai vana sake taso masa. Tayi nufin juyawa ta barshi a nan,sai taga idan tayi hakan zaiyi tsammanin tsoronsa ko shakkarsa takeyi don haka ta gyara tsaiwarta tana harde hannuwanta a girjinta,abinda ya baiwa tudun girjinta damar fita sosai ba tare da tasan hakan zata faru ba "Lafiya kake nema na?" Tayi masa tambayar kanta tsaye da siriryar muryartan nan dake cike da tsiwa. Lokacin daya waiwayo ya kalleta sai da taji dukka wani qarfi da qafafunta ke dauke dashi yana raguwa,tsakiyar idanunta yake kalla sannan yace "Da zaki taimaki kanki da kin nemo mayafin arziqi kin suturta jikinki,duk da naga alama bakisan darajar jikin naki ba" ya qarashe maganar yana sake dauke dubansa daga kanta. Maganar tayi mugun sokarta,saita samu kanta da sauke dubanta ga jikinta,tunda dai tasan boubou ce a jikinta da take sakakkiyar da sai an saka mata irinta uku ma a ciki ko biyu bata matsesu ba. "Subhanallah " ta fada can gasa muryarta da dukka ilahirin jikinta suna rawa,cikin hanzari ta saki hannayenta,wannan ne ya bawa rigar damar komawa ta sake kamar yadda take. Qafafunta taji kamar suna neman kayar da ita,Allah yasa tana kusa da kujerun da aka aje a wajen domin hutawa,da hanzari ta nema daya ta zauna a kai,duk da yadda zuciyarta ta cika da burin takawa ta fice a gurin,to amma yadda qafafun sukayi sanyi tasan ba zasu bata hadin kai ba. Waiwayo ya sakeyi karo na uku,saiya tako sosai ya garaso gabanta,iska ta fara debo qamshinsa dake da wani irin scent na musamman tana watsawa tsakiyar hancinta har zuwa kwanyarta. Ya rage tazarar dake tsakaninsu sosai,ya duqa yana dubanta da kyau "Bari na baki amsarki da farko,ba lafiya bace tasa nake nemanki ba,saboda kalen dangi kin daukarwa mutane yarinya kin riqe kamar ke kika haifeta,ki fiddomin yarinyata,sanann. ..daga naira daya har zuwa cikar burinki na kudin da kikeson mallaka ki gayamin,zan biyaki ki koma kici gaba da aikatau dinki,badon son raina ba,sal don saboda cika umarnin Dr jarma" maida idanunta tayi ta runtse da kyau,ya zageta iya yadda ransa yakeso,bayan bata aikata masa komai ba,idan ta barshi bata mayar masa ba lallai yaci nasara a kanta,to amma yayi mata wani irin kwarjini a yau wanda bai taba yi mata irinsa ba,sai ta miqe cikin dabara tana dubansa kai tsaye "Sannu garuna,jinin mansa Musa, you are too proud mr jarma na sake maimaitawa,daga million daya har million dari idan zaka bani bazan koma aiki babazan koma ba nace bazan koma ba ana dole? yarinya kuma ka fini sanin yadda tazo gidan nan,so no need na tsaya maka bayani.. ...sannan wannan jikin da kake magana a kai, inason gaya maka idan ka saba bin matan turawa da sauran yarika na qasashe daban daban inda kake zuwa da sunan kasuwanci....to wannan ilkin da idanunka da baka yiwa shamaki suka sauka a kai,ka gaya musu yafi qarfinka har abada,har gaba da abada din,saidai kallon daga nesa" ta garasa fada tanason hana kanta sakin kukan da yake danqare a zuciyarta. Juyawa tayi zata tafi,saidai kafin tayi wani motsi yasha gabanta. Zuciyarta ta tsinke da ganin yadda yayi dab da ita,iskar bakinsa da hancinsa dake cakude da wani kalar qamshi tana sauka akan fuskarta kai tsaye saboda qarancin kusancin dake a tsakaninsu,fararen idanun nan nasa sun kada zuwa launin ruwan goro goro "Dan iska ne ni tatacce wanda yake bin mata daga qabilu da qasashe daban daban,amma kinsan wani abu?…....dukka virgin nake ballewa sabbi dal a leda,bana amfani da second hand ko zawarawa" a hautsine ta daga kanta tana dubansa,juriyarta tana katsewa, qyallin hawaye na ragaita cikin fararen idanunta. Bakinta ya bame bam,ta rasa wacce amsa zata bashi,cikin hakan muryar sajjad da fadeela ta soma dososu hakan kuma bai sanya shi ya matsa ba,sai itace ta zame ta zauna a gurin tana qoqarin boye ruwan hawaventa kada yaga zubarsa. Tana jin alamun sun iso gurin,bata Ko iya waiwaya wa ta hada ido dasu ba ta mige ta fice a gurin gudu gudu sauri sauri,sajjad ya bita da kallo,sanann ya dawo da dubansa kan toufeeq dake rungume da fadeela cikin kallon tuhuma "Me kayi mata haka?" "Let's go" kawai ya fada yana dauke da fadeela a kafadarsa wadda keta masa surutu. Sai da taga sun shiga mota suna shirin fita a gidan sai kuma ta marairaice "'Ina zamu abby?" "Gida,gidan ba dadi fadeela, hutun ya isa haka ko?" Kai ta gyada a hankali, itama tayi missing nasa,to amma tanason zama da sãahar fiye da komai "Amma ba tare da anty N zamu tafi ba? naga ko sallama bamuvi ba" "Zata taho daga baya" ya amsa mata a taqaice,don a yanayin da yake ciki baya bugatar dogon zance. Maganganun data gaya masa sunfi komai tsaya masa a rai,shi zata kalla ta yiwa qazafin neman mata?,shi Muhammad toufeeq?, wanda ko yatsar mace da gangan bai taba rigewa ba,bai taba sanin kowacce mace ba a duniya sai matarsa ta sunnah,ita dinma duk duka lokutane gayyadaddu da zai iya lissafasu. Idanunsa dake masa zugi ya mayar ya kulle yana sauraron radadin kalamanta a tsakiyar zuciyar tasa. Karon farko a rayuwarta da kalmar BAZAWARA ta taba gona mata rai,tayi kuka tayi kuka sosai,kukan kuma ya hade mata da wa'adinta da takeci a gidan. Shigowar afifa biyu tana neman inda fadeela ta shiga,amma saahar din tayi banza kamae bata ji ba,tana qudundune a bargo,ta tabbatar idan tayi magana afifa zata fahimci kuka takeyi,wannan ciwon kuma na yau batason rabashi da kowa,a barta ita kadai tayi jinyar kanta da kanta,itadai ta sani a yadda yazo din nan,bazai bar gidan ba sai ya dauki diyarsa. A shigowa ta uku kuwa taii afifa na fadi yanzu maama ta gaya mata abban fadeelan ya Aiko a bawa maama haquri ya wuce da afifa zata qarasa hutunta a gida,idan dr ya dawo a gaya masa. Tsaki taja qasan ranta "Badai shi ba,saidai sajjad,shi zai bada sagon" ta gayawa kanta. Maganganunsa sun mata munin da takejin ba zata iya yafe masa ba,duk da ta gaya masa masu zafin gaske,amma shi va jawo koma meye ta fada,don menene zai aibata mata jikinta? maganar ta zafafeta da yawa,don ko sanda ta miqe don yin sallar magariba sai data tsaya gaban mirror ta sake qarewa kanta kallo,ta kuma sake maimaita yanayin tsaiwar da tayin a dazun da har tasa ya fadi hakan "Allah ya sakamin" ta fada qasa qasa tana wucewa bandaki. Kwanakin haka ta dinga kwana tana tashi da zafi da ciwon kalamansa,wadanda ta rubutasu tas suka zauna cikin kwanyarta. Maama da dr girema sun dauka kawai kewar fadeela ce,afifa ta gama karantar akwai wani abu,saidai har lokacin sãahar din bata fito ta gaya mata me ya hadasu ba,saboda tana in haushin yawan yin wayar data tsiro dashi a kwanakin da wani da batasan waye ba. Bata nutsu ba bare suyi ma magana don haka ta zuba mata ido tana jiran sanda zata nutsu ta fidda komai daga ranta. ********kwanaki uku da dauko fadeela,da safe yana shirin fita ya kaita gurin dr raheema tayi mata checkup,daga can ya biya da ita daya daga cikin guraren wasa na yara wai don ta warware sosal ta koma kamar da,yanason ta manta da sãahar da abinda ya danganceta. Ta wani bangaren kuma tunanin daya kwana dashi a daren jiya ne har yanxu bai sakeshi ba. Yaya akayi maji tasa yarinyar nan har irin haka,harma take yabonta da kuma shawartarsa ya dawo sa ita? wai wanne irin abune da ita da har take iya mamayar zuciyar kowa daya danganceshi?,mutane masu kima da daraja a rayuwarsa? kamar amfani da tsafi? "Astagfirullah" ya fada yana gama saka links din hannunsa,dai dai lokacin da akayi masa knocking. Muryan Joshua ne,amintaccen yaron dake masa shara yake kula da tsaftar lungu da saqo na sassan bedrooms dinsa. Daga bakin qofar ya gaidashi ya sanar masa cewa BOSS ne ya shigo. Ajjiye abinda yakeyi a gaggauce ya buda qofar ya fito yana mamakin zuwan Dr iarma din a daidai wannan lokacin. A tsaye ya sameshi, fadeela na lafe a jikinsa "Barka da warhaka abba,bismillah ka zauna" cikin nuna girmamawa yake maganar. Wani kallo Dr jarma ya bishi dashi "Ai bansan na haifo dan da yafi qarfin na gaya masa magana yaji ba sai yanzu" furucin da ya sanya dukka masu akin nasa dake falon yin sum sum suka fice a gurin,sun tabbatar yau boss da fada yazo akan ogan nasu "Abba…” " "Dakata Muhammadu,inason na gaya maka,ka dauki yarinyar nan tun muna shaida juna ni dakai ka maidata inda ka daukota,ni dana kaita ni zan daukota da kaina,bayan ka kaita kuma ka nema alfarmar dawowar sãahar taci gaba da kulawa da ita muddin lafiyarta kakeso,dukka rashin kirkin da kaje kayi sajjad ya gaya min,idan ka koma din ka sake maimaita abinda ka aikata" sai ya zare fadeela da zazzabi ya fara saukar mata yana fita a falon. Baisan zazzabi ya rufe yarinyar ba sai da sukazo fita,kai tsaye ya wuce asibitin da ita yasa jibril ya kira dr anwar yana gaya masa suna hanya. Sanda ya gama dubata drip yace zai saka mata,saboda tayi zazzabin a kurkusa kuma for now jikinta babu qwari. Yana daga gefenta yanajin zuciyarsa kamar zata narke sanda Dr Anwar ke gaya masa har yanxu akwai damuwa tattare da Fadeelan. “No more option,dukka zabi ya qare,dole ya sake maida kansa gidan ya nema alfarma ta dawo?”Statement din da zuciyarsa ta bashi kenan na karshe wanda shi kanshi yasan shine ya rage masa. “_WOHOHO,WAYE ZAI SAUKE NE?😂,MUJE ZUWA_* *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 05 ********Tunda suka taho a hanya yake mata hira cikin nutsuwa tare da son janye hankalinta,dukka a qoqarinsa na ganin ya kafa kansa cikin zuciyarta yadda ya kamata. Kaf tsahon hirar da yake mata tun daga thairaphy beaty saloon din har yanzu da suke gab da shiga unguwar su bata amsa masa sau hudu ba. Ta cika tayi fam,tasan tabbas afifa ta gayawa mahmud inda taje. Tun jiya sukayi zata rakata ta wanke kanta,ayi mata gyaran fuska a kuma saka mata jan lalle iya yatsun qafa dana hannu,tayita jiran afifan bata dawo ba,daga qarshe sukayi waya tace tana da patient data kusa haihuwa,so saidai taje,ta sameta acan saita daukota su dawo tare. Maimakon taga afifa sai taga mahmud,hakanan don babu yadda zatayi ta shiga motar,saboda idanu sunyi yawa a kanta sanda take fitowa,dole ta shiga din ya rufe ya jasu,ranshi fari qal,yana jin dadin yadda a yau ta aminta ta yarda ya dawo da ita gida. Zata iya cewa tsahon rayuwarta,tun Karin ma aurenta na farko yaushe ne ta shiga motar wani d'a namiji ba banda yayunta maza,don haka ko a yanzun jinta take a takure qwarai. Taso ya ajjiyeta daga gofar gida amma sai ya giya "Wannan ladan dole na garasashi" ya fadi yana murmushi,da kansa ya buda mata qofar ta fito ya mayar ya rufe "Yanzu sai yaushe kenan ranki ya dade?" "Zan duba" kawai tace dashi tana yin gaba. Kansa ya girgiza,shi sam abinda takeyi bai dameta ba,yasan with time zata daina komai idan ta shiga gidansa,ya soma amfani da kyautatawarsa a kanta wajen kafa kansa. "Madam,oga muhyiddeen yace ki sameshi a dakin baqi idan kin shigo" cewar jamilu yana dan rusunawa. Duban jamilun tayi,kamar zatayi magana sai kuma kawai ta sauya akalarta zuwa can din,wataqila vana wani aiki ne da yasa ya kebe a can,tunda time to time yana yin hakan,sai ya baro gidansa vazo nan yayi aikinsa a nutse,saboda su khalipha basa barinsa. Har zata daga curtains din masu kauri da girma sai ta dakata,saboda wani bagon qamshi da ya shiga hancinta,cikin iiki da zuciyarta takejin kamar tasan qamshin,amma ta kasa banbancewa. Ta kauda tunanin ta sanya hannu ta budesu. Shine yake fuskantar gofa,wannan yasa tana budewar dashi suka fara hada idanu,kwantattun sexy eyes dinsa da yau suke cikin wani irin nutsuwa wadda damuwa kadan ta cakuda dasu. A tare dukkansu suka janye idanun nasu,kowa yana jin zafin dan uwansa a qasan ransa. Itakam sãahar sai da taja siririn tsaki qasan ranta,cikin zuciyarta tana tunanin me kuma yazo yi a gidan nasu?,saboda ita dai ta riga ta yiwa kowanne zuwa nasa gidansu fassara da zuwan da baida alkhairi. "Yauwa kin dawo?,qaraso ciki kinyi bago" ya muhyiddeen ya fada. Cikin nutsuwa take takowa da wani irin rashin sakewa da batasan meye dalilinsa ba,saidai tanajin kamar ido ne a kanta. Tabbas batayi qarya ba,can gasa gasa toufeeq yake qare mata kallo,yanason ya gano meye ne tafi kowa dashi har Dr da maii suke iya magana da bada umarni a kanta? saidai idanunsa basu gano masa komai ba face zara zaran yatsun gafafunta da suka sha jan lalle da yayi radau,suka fito fes gwanin sha'awa. Daga bisani dole ya zare idanun nasa yana sakin tsakin da baisan anji ba ko ba'a ji ba. Yaa muhyiddeen din ta gaisar,can qasan ranta tana juya ta yadda zata gaida toufeea din don batajin zata iya gaidashi sam sam. Kallon da yaa muhyi yayi mata yasa don babu yadda zatayi ta waiwaya sashensa ba tare data dubeshi ba tace "'Barka da yamma" "'Barka" ya furta da gasaitacciyar muryarsa,idanunsa nakan wayarsa da yake qoqarin sanyata a flight mode. "Sun kawo drinks sun wuce,kiyi serving nasa,idan kin gama ki jirayeni wajen maama" yawu ta hadiye sannan ta gyada kaitana qyashin yadda zata yiwa wannan mutumin hidima,wanda baisan mutunci da darajar kowa ba. Dole ta zamo ta sauko qasa daga saman lallausan sofa din,dai dai sanda ta fara serving din nasa yaa muhyi ya juya ya fice daga falon. Mutum ne shi mai kaifin karantar mode din mutum,koda bakayi magana da bakinka ba,yana da saurin fahimtar yanayinka koda ta cikin qwayar idanu ne. Tsaf ya fahimci akan dole take zuba masa komai,saboda mugunta kuma sai daya cika kome taf har bakin cup,ta mige ta koma kan kujerar tayi zamanta ba tare da tavi masa tayin sha ba. Ya fahimci Allah Allah take ya fadi uzurinsa ya tafi,hakane kam a zuciyarta,don ji takeyi kamar ta zura da gudu tabar dakin. Yana sane shi kuma yaqi cewa komai,yanata danna wayarsa ba tare da yace ta tafas ba,yavin da ita kuma keta murza yatsuntsa da sukasha lalle,ranta yanata quna,hancinta yanata zugo mata qamshinsa yana watsa wani irin abu ilahirin jikinta ta kowanne sashe. Kamar ta yayyaba masa magana kan yadda ya barta a zaune haka taji,saidai ta kanne ta cije,don batason yaci gaba da sanin abinda yake bata mata rai. Sai daya mula don kansa,yanata tauna yadda yau a karon farko zai furtawa wata diya mace kalmar ban haquri,bayan maji dinsa da hajiya qarama. Sai daya sauke gafafunsa dake harde ya gyara zamansa yana zuba mata narkakkun idanunsa. Ba abinda yake hangowa saman fuskarta sai tsiwa fal,shi kansa bai san me yasa duk sanda zai dubeta ba yakejin kallon kamar ya bambanta da sauran kallon da yakewa kowa. Kalmar haqurin tana masa maqaqi a wuya,musamman idan ya tuna da kalmar data jefeshi dashi shima. To amma sajjad ya gaya masa tun a hanya,mai nema baya fushi,kuma zaiyi komai ne for the sake of fadeela,indai da gaske yana son diyar tasa. "I hope zaki manta da komaiina neman alfarmar ki dawo kici gaba da zama da angel" yayi maganar da wani irin softness. har yanzu izzarsa tana nan cikin maganganunsa. Nata idanun ta zube masa tana gyara zamanta "Ba komai kudi ke iya bayarwa,kamar yadda ba komai ne darajarsa take hawa mizani daya dana kudi ba. Komai ya wuce a gurina saboda fadeela da nadeeya,but am sorry.....bazan iya dawowa gidanka ba,infact ma am getting married in the next month" abinda ta fada kenan ta miqe tsam tana daukar hand bag dinta. Wani rudu ne ya shigeshi,a hankali yaji zuciyarsa ta motsa da wani irin qarfi ta matse guri daya "Aure zatayi?" Ya tambayi kansa,kamar ba yanzun nan kunnuwansa suka jiye masa abinda tace ba "Idan tayi aure ta tafi,yaya makomar rayuwar fadeela?" Muhimmiyar tambayar data tilasta masa furta abinda ko a mafarki bai taba zaton zai furta ga kowacce diva mace a doron duniya ba "Will you marry me?". Wannan kalmar idan ta kirata da saukar ajali lokacin mutuwar fuju'a a kunnuwanta to batayi kuskure ba. Kalmar data ji girmanta ya wuce girman dutsen dala a kanta. Kunnuwanta suka bada wani shuuu,sai ta kasa daga qafafunta daga gurin,kamar an dasata "Will you marry me?" Ya sake maimaita maimaitawa a karo na biyu. Wannan karon wata faduwar gaba da sautinta yakai har ga kunnuwanta taji,numfashinta yadan so ya fara fita da sauri amma saita yi qogarin saitashi. A nutse ta waiwayo tana dubansa kai tsaye "Absolutely no" ta zare idanun nata daga kansa tana qoqarin ci gaba da tafiya. Saidai taku biyu kacal tayi ya cimmata,ta fahimci hakanne ta hanyar qamshin turarensa da ya mamayeta,taja baya da sauri tana rabewa gefe,saboda yadda yayi bake bake a bakin gofar,kwarjininsa ya daketa da wani qarfi,ya sanya wannan magnet din sosai a kanta da ya sanya ta kasa duban idanun nasa a yanzu. Nasa kallon ya dauke daga kanta yana zaro complimentary card dinsa,yayi taku biyu zuwa inda take,abinda ya kusa dauke numfashinta kenan,saboda bata ga card din hannunsa ba,saura qiris tace masa ya dakata, Allah yasa batakai ga fada din ba ya zura mata card din a gefen jakarta dake maqale a hannunta “Idan kin canza shawara you are always welcome,zamuyi aure don ki kula da fadeela kawai, wannan shine manufar,ni kuma zan baki dukkan 'yanci da mafakar da kike nema" daga haka ya juya a cikin nutsuwa da kamewa ya fice. A qalla sai da yabar gidan ta motsa daga gurin,ta gama tsorata da yadda ya kafeta da kallomsa,batajin ya taba mata irin wannan kallon kai tsaye,yadda ya nufota kanshi tsaye baya ma ko tsoron ya muhyiddeen ya dawo ya ganshi ya bata mamaki. Tsaiwarta ta gyara tana kallon card din, butter milk color da aka yiwa ado da ruwan gold. Tsaki taja,ta sanya hannu ta zaro card din ta watsar a wajen. Wai ta aureshi saboda ya raina mata wayo,shi baisan ko bashi bama ba zata iya auren kowanne namiji ba? ta rasa ma wa zata aura saishi? har abada,Allah yayi mata tsari. Dukka ta gama wadan nan maganganun cikin banbami a ranta ita daya,ba tare da tasan gaddara tana sauya komai cikin qasa da sakanni ba kamar dai qiftawar ido. Kusan hakance ta sameta,bayan ta samu yaa muhyiddeen kamar yadda ya umarceta,ya kuma shaida mata a satin nan mahmud zai turo magabatansa da komai nasu,aurenta duka duka bazai wuce watan gaba ba,so basa son mata auren da bataso,idan tana da wanda takeso tayi gaggawar gabatarwa da abban nasu. Tashin hankali,shin a dazu ta gayawa toufeeq wannan maganar kenan da harshen malaiku? ,wata gudan data ambata shine ke neman tabbata a kanta cikin mintunan da basu wuce talatin ba?. Fadin irin mawuyacin halin data fada ma bata bakine idanunta suka soye sai qirjinta dake zafi, batasan me yasa suka dage sai sun aurar da ita ba,bayan har yanzu bata gama healing ba,tana buqatar lokaci sosai,a galla shekaru goma ma a gaba idan sun bata dama. Ita dava cikin dakin,qarfe biyu na dare tazo ta risketa ba tare da bacci ya ziyarceta ba,sai tarin fargaba da kalmar auren da yaa muhyi ya furta mata daketa yawo a saman kanta. Ta wacce hanya zata samu ta kubcewa wannan qaddararren auren?,dama dukkan wani aure a nan gaba har sai lokacin da taji zuciyarta ta gamsu ta aminta da aure?. "Akwai" taji zuciyarta na gaya mata,amsar da taja hankalinta ta kuma sanyata neman baasin maganar "zamuyi aure don ki kula da fadeela kawai wannan shine manufar,ni kuma zan baki dukkan 'yanci da mafakar da kike nema" kalamansa suka dawo tarwai cikin kunnuwanta,kamar a sannan yake furta mata SU. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI * Book 02 Page 06 Wani irin zuzzurfan nazari ta shiga yi,tanason ta yiwa kalaman nasa duba na fahimta,ta kuma nazarci ma'anarsu da kyau. "Indai hasashenta yayi dai dai,indai ma'anar fassarar tana nufin abinda ta tsinkaya ne.....zai aureta ta kula da fadeela,ita kuma tayi rayuwarta tamkar macen da bata da miji,babu doka,babu oda,babu auratayya,babu sawa babu hanawa...a idanun duniya sunanta matarsa,amma a tsakanin su din bagin juna ne,kowa zaiyi harkar gabansa" wannan hasashe kadai ya haifar da kyakkyawan murmushi saman fuskarta "Yes... yes" ta fada gasa gasa tana sakin murmushi "Ta samu cikakkiyar mafaka,ta kuma samu dama irin wadda zata bata damar yin rayuwarta lya adadin tsahon shekarun da takeso ba tare da takurawa ko sanya idanun kowa ba". Sosai taji al'amarin ya kwanta mata,wanann din wata idea ce me kyau. A daren ta fara laluba card din da ya bata cikin jaka,sai ta tuna ta yasar dashi a falon batama fito dashi ba. Ji tayi a daren kamar ta fita ta dauko card din,amma dole ta haqura zuwa safiya. Haka kawai kuma wani sashe na zuciyarta ke umartarta tayi addu'a. Bata wofantar da wannan shawarar ba,sai ta mige ta daura alwala, don dama ita din gwanace ta wannan fannin,dai daikun darare ne suke wuceta,farinciki ko baqincikinta tana juyeshi ne saman abun sallah, wanda hakan yake qara mata nutsuwa tare da hasken rayuwa,matsalolinta masu yawa kuma warwara take zuwa musu a qanqanin lokaci. Raka'a shida tayi,tana gamawa taji wata nutsuwa na shiga ruhinta,kamar iskar dadin na dada sanyi da dadi,tana yiwa annabi salati idanunta suna lumshewa,a haka har wani daddadan bacci data jima batayi irinsa ba ya sureta. Washegari bata tashi da wuri ba,saboda bacci tayi sosai,bayan ta farka tayi brush tare da alwala,ta dawo cikin dakin nata ta sakawa wayarta charge,ta kunnata ta zauna daga gefan gado,ta buda inbox ta turawa afifa sagon da tasan dole ne ta dawo gida koda bata nemeta ba,duk da jiya da magriba ta tafi zooroad "Bestie aure zanyi"_ abinda ta tura mata kenan ta sauka tabar wayar a charge ta fito falo. Masu aiki keta hidimar kimtsa gidan,da )alama aikinsu na safe yazo qarshe saina rana dana dare. Cikin sakewa suka gaisa kamar yadda suka saba,baaba rabi ta gaya mata maama tace a shaida mata idan ta farka,ta tafi gidan uncle ismail,yau din za'a kawo lefen zeenat qarfe uku na yamma,idan ta gama komai ta sameta a can saisu dawo tare. Tana amsa mata tana ficewa,tanaso ta samu card din kafin masu gyaran gurin su hada dashi su share. Sai data danyi dube dube sannan ta ganshi,ta tsugunna ta dauka tana kallon rubutun dake a jiki. Rubutu ne dake cike da tsari da kuma ban sha'awa,full name dinsa email and phone duka a jiki. Dan tabe baki tayi,tana tuna irin izzarsa da jin kansa,wai yama akayi yasan wasu abubuwa haka a kanta?,ya akayi yasan ita din bazawara ce?,ya kuma akayi yasan gudun auren kowanne namiji takeyi?. lya hasashenta bata iya ganewa ba "Oho masa,shi ya sani" ta fada a fili tana komawa cikin gidan,ta shiga dakinta ta yiwa card din waje,sannan ta shiga hidimar gabanta. ********Sanye yake da long sleeve kaftan thobe button down, wadda daga qasa gefe da gefe yake a tsage,fara ce qal kamar yadda mafi yawa zabinsa kenan a kaya,hannun rigar ya tattareshi zuwa gwiwar hannunsa,yana riqe da mug na coffee kamar kullum yana kurba,idanunsa akan fuskar fadeela daketa faman gogarin zana wani dan tsuntsu. Idan kace hankalinsa baya gurin bakayi kuskure ba,miskilar fuskar nan na hade kamar yadda take a koda yaushe,saidai sassanyan kyan nan da cikakken gashin girarsa zuwa jajayen lips dinsa zuwa kwantaccen gashin dake habarsa zuwa kuncinsa suna sake bayyanar da cikar kyawunsa tare da gara masa kwarjini. Shan coffee din kawai yakeyi bawai don yana masa dadi sosai ba,tun wancan ranar da ya dandana wannan coffee din da kuma shayin gaba daya,dadinsa ya dauke dandanon dadin kowanne irin coffee,hatta nasa kuwa da ya tabbatar ya qware sosai gurin iya hadashi. A nutse ya ajiye mug din,bakinsa na dan fidda tururin ragowar zazzafan coffee din, idanunsa a kafe waje daya. Babu abinda yake masa kai kawo tare da ciwo a rai irin yadda ya zubda dukka makamansa ha gasqantar da kansa ya nema wata diya mace ta aureshi,abinda ya yiwa kansa alqawarin har yabar duniya bazai sake maimaitawa ba,sai gashi dare daya....tazo ta ruguza duk wani abu da ya sanyawa kansa doka da iyakoki a kai. Iska me zafi ya furzar yana dogara gwiwayoyin hannunsa akan qarfen balcony din hadi da fidda zazzafar iska a bakinsa. Ba komai ke sake rura wuta ke zafi a zuciyarsa ba,sai yadda ta tankwabar da tayin da yayi mata. Tana tunanin yana neman wani abu ne daga gareta? ‚bayajin banda fadeela akwai wani abu da zai sanya ya sake kallonta. Abu daya ya sani,koda bata aminta ba,zaiyi dukkan abinda zaiyi,koda tsiya sai ya dawo da zamanta gidan taci gaba da kula da fadeelan Karar shigowar saqo a wayarsa ya dauki hankalinsa,wayace da dukka kira ko sagon da zai shigo ya cikinta to me muhimmanci ne a gareshi,wanan yasa ya miqe tsaye ya sanya hannu a aljihun kaftan thobe din nasa,ya zaro wayar yana dubawa. Sake dafe hannunsa yayi sosai saman qarfen,tuntuni ya sanya jibril ya nemo masa number dinta,ya kuma yi masa saving nata. Haka kawai yaji yana buqatar zama,ya miqa hannu ya jawo wata kujera guda daya me azabar laushi ya zauna,ya lanqwashe gafafunsa a cikinta sannan ya fara karanta saqon _I agreed,i will marry you,but under some conditions,idan ka shirya zaka cikasu.. ..fine,am ready nima"_ dan garamin tsaki yaja,me ya kaishi irin wannan abunne wai "Farinciki da lafiyar fadeela kake nema" zuciyarsa ta bashi amsa,sai ya girgiza kar yana gasgata hakan. Baiyi jinkiri ba ya fara tafa mata amsa _i get the point, duk wasu conditions naki ki rubuta su kawai ki ajjiye basai naji ba,coz i know bani da case dasu,you are going to be my wife for the sake of fadeela,you can do whatever you want"_. Ta kusa a qalla minti guda tana duba amsar tasa,sai kuma ta saki murmushi,saboda abinda takeson ji kenan,zata zama free,zata samu 'yanci. Sauka tayi tana shirin ajiiye wayar wani sagon ya sake shigowa _"Are you ready for the marriage nan da next week?"_tabe baki tayi,yama raina mata hankali, don ta amince kuma sai yayi mata zancan next week?, kwanaki hudu kacal fa gaba "Nooo" kawai ta tura masa tana jan tsaki "Alright,sati biyu kacal na qara,so let's start plan it,ki sanarwa da Dr zan turo magabatana nan da 3days"_. Juya wayar kawai ta dinga yi a hannunta,anya batayi kuskure ba?,anya zai iya cika alqawarinsa?,a yadda maza suke a yanzun?,ba alqawari babu amana. Kai ta girgiza "Batajin komai zai faru,saboda kowa a cikinsu maradinsa yake karewa yakeson cikawa, kamar contract ne yanzun a tsakaninsu. Da zarar fadeela ta warke zata nemi saki daga hannunsa,shikenan contract ya qare,shi da ita kuma kowa zuwa lokacin ya cimma muradinsa. Har washegari zuwa wata washegarin ta rasa wa zata tunkara tsakanin Dr girema da kuma maama dinta,ga afifa still bata nan,dole daga garshe gudun kada abban nata yayi bagin da baisan da zuwansu ba,ta dauki waya ta kira afifa tace ta dawo please. Tunda taji hakan tasan akwai wani Issue daya taso masa may be ta gaza warwareshi,don haka tabar komai tazo ta isketa,lokacin zataci abincin rana ne da yammaci,ta garso musu sukaci a tare: Sai da suka kammala,ta gyara gurin sannan ta dawo ta zauna tana fuskantar afifan "'Bestie na fidda miiin aure" dan dubanta kadan tayi sannan tace "An fidda miki dai,ko ba mahmud ba?,dama ai saura 3days deadline din da abba ya deba mana ya qare" "Ba mahmud bane,wanann zabina ne,MT JARMA" ta fada kanta tsaye tana duban reaction na afifa. Ta fusgi hankalin nata kuwa,don tsaiwa tayi da komai tana kallonta,kalmar na girgiza afifa,hadi da shiga kowanne lungu da saqo na jikinta. Girarta ta dage mata dukka biyun "'Yes,kina mamaki ne?,nima mamaki naso baki dama kamar yadda kikayimin akan SAJJAD" Murmushi afifa ta saki tana kauda kanta gefe "Sajjad banda kina cikin rudani hankalinki ba'a kammale yake guri daya ba,ya kamata ki fahimta wani abu da kanki.....na miki murna da kika samu zabinki,amma bestie,kome zakiyi ki yishi ba'a bisa kowacce manufa,kin sani.....na sani..... dole na garyaraki zuciyata taqi aminta da cewa MT JARMA shine zabinki, kusan kowa yasan dabin dake tsakaninku,yaushe soyayya ta shiga har kuka fahimci juna?" Sam sãahar batason afifa tace zata hanata aiwatar da qudurinta,a yadda ta tsani maza da abinda ya dnagancesu wannan ne kawai option din da ya rage mata,kuma dama a gareta guda daya da zata rayu cikin salama ba tare da wata alaqa tsakaninta da su ba "Allah ya sanya alkhairi,kuma ina addu ar Allah ya maida qogo masaki" bata fahimci maganarta ta qarshe ma,saita watsar,tunda dai bestie din nata bata kawo wani tarnaqi na fine,shikenan. Afifa ce tayi mata rakiya gidan yaa muhyiddeen,ta bawa anty farheen sago ta gayawa yaa muhyi din,shi kuma ya isarwa da abba batun. Sakato anty farheen din tayi cike da zallar mamaki tana kallon säahar din "Yaushe reshe ya juye da mujiya kuma ummin abba?" Dan garamin murmushi ta saki tana kauda kai "Tsarin Allah,haka qaddararsa take" jinjina kai kawaii anty farheen tayi,don ita kanta bata gama gamsuwa ba. A yadda tasan sãahar sarai da kafiya,bata da sassauci akan abinda takeso da kuma wanda takeqi uwa uba kuma gefe guda ga al'amarin daya sauya zuciyarta zuwa giyayya da gaba daga dukkan jinsin maza. Sanda sãahar din ta shiga sallah lokacin afifa dake fashin sallah suka tattauna da anty farheen "'Nafi zaton dukkansu akan wata manufa suka gina auren nan,amma dai koma menene,mu zamu bada gudunmawa waien tabbatuwar komai yakuma dore har abada,so zamu soma shirye shirye,kada ki nuna mata kin fahimci komai" kai afifa ta gyada. To wannan magana da sukayi da Anty farheen sai afifa ta saki jikinta,tun a washegari ita da anty farheen suka soma tsara abubuwa da gabatar da shirye shirye. Ta fannin säahar kuwa jin kanta tayi sakayau,ta tsinci kanta cikin wata iriyar walwala mara misali,hankalinta taji yayi mugun kwantawa,tana ji a ranta yanzu bata da sauran matsala a rayuwa. Saidai harkokin gabanta kawai takeyi,duk wani shiri da su anty farheen sukeyi tana gefe ta zuba musu idanu,gani takeyi bata lokacinsu da kuma kudadensu sukeyi,wani abun saidai ta kalla ta tabe baki,amma batace komai ba saboda abune da take ganin tsakaninta ne kawai da toufeeq din,babu wanda ta shaidawa manufar aurensu. Kwanakin ukun da ya diba matan baqi na musamman cikin girma daga gidan Dr mahmud JARMA suka sauka a gidan Dr girema da kudin auren yaransu guda biyu. Muhammad toufeeq ya bayar da zunzurutun kudin auren Khadija Muhammad girema har naira million daya,yayin da sajjad da ya tsunduma cikin soyayyar afifa tun ganinsa da ita na farko ya bada dubu dari biyar. Sajjad yaso qwarai a qara kudaden sufi haka,amma dr jarma yace sam,hakanma yaso yayi yawa,albarka yake nema musu. Magabatansu sun roqi sati uku kacal,dr girema da gannensa da suka karbi kudin tare basu ja ba,ganin yadda Dr jarma da kansa yaketa roqon ayi masa alfarmar hakan. Da daren ranar dukka su biyun suna dakinsu,afifa waya take amsawa tsakaninta da anty farheen,duka maganarsu akan yadda shirye shirye zasu guda na ne,sayayyar kayan dakinsu zuwa gyaran jikinsu. Cikin satin takeso yaa muhyi ya samar musu da visa su ukun,china turkey ko Dubai,duk wadda tafi sauri da sauqi,su dora kayan ta sama yadda zayazo da wuri "Amma ta sama anty akwai kudi fa" "Karki damu,biyan buqata akeso,indai china ne ma babu matsala,akwai lucky cargo da kayan zasu iso cikin kwanaki galilan har nan kano(me bugatar hulda da amintaccen kamfanin saboda kawo kaya daga china zuwa Nigeria dukka states,sai ya tuntubeni ta wannan number don na hadashi da kamfanin kai tsaye 08187255862)". Sati guda takeso suyi a can,satin da suka dawo kuma sai a fara gyaran jiki da sauran hidimomin da suka shafi amare. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02 Page 7 Har afifa ta gama wayar idanun saahar yana kan wayarta tana chart,ido tadan zuba mata zarginta yana sake tabbata,yadda sãahar me shakulaton bangaro tare da nuna halin ko inkula da dukka abinda ya shafi bikin ya sake tabbatar mata da zarginta,uwa uba ko sau daya ita dai idanunta basu taba nuna mata kiran toufeeq jarma ba "Kina jina muna magana amma bakice komai ba?" Dan duban afifan tayi,sai ta saki murmushi "To me kikeso nace?,salon nayi rash-in kunya?,kuma ma ai kin gama komai,duk abinda nake bugata ko zance ke kin isar min,duk abinda ya samu ayi,wanda bai zama lallai ba ko bai samu ba sai a haqura ko?" Kai afifa ke girgizawa tana kallonta "Amma dai ba haka kikayi ba a aurenki da adamu" ajiye wayar tayi gefe wani murmushi dake cakude da zallar nishadin da takeji gasan ranta ya kubce mata ta zuro gafafunta gasa cikin zummar shiga bandaki sannan ta amsawa afifa "Banda abinki hajiya afifatu,ai kullum dan adam dada wayo da hankali yakeyi ko?,don zanyi aure bawai ba hakan yana nufin na mance da asalin su waye maza ba,ko kuma na manta radadi da daci da suka dasawa rayuwata ba" "'Anzo gurin" afifa ta fada tana zagayowa gabanta da sauri,ta jawo stool ta zauna akai tana fuskantar sãahar wadda ke mata duban mamaki "Bestie bandaki zan shiga,yaa haka?" "Inason nasan gaskiya ne bestie,yau ashe anzo wata gaba da zaki dinga boyemin wani abu a rayuwarki? meye ainihin gaskiyar magana akan aurenki da toufeeq jarma,duk yadda naso na basar nayi kaman ba komai na kasa bestie,ki gayamin gaskiya" murmushi tayi hankali kwance "Ki barni naje nayi fitsarin mana" "Na barki" ta fada tana dubanta. A nutse ta miqe ta wuce bandakin,ba jimawa ta dawo ta koma inda ta tashi ta zauna. Komai ta warware mata,abun sai ya sanya afifa murmushi me kama da dariya "Allah ya sanya alkhairi,abu kuma yay kyau,hakanan hankalina ya kwanta da bayananki,amma ke dashi dukka ku shirya ranar karbar sakamako a tsakaninku" "Sakamakon me?,kefa wani lokacin kin fiya jaye jaye" "Lokaci zai bayyana komai". Tasan halin afifan da iya saqa zance,sai kawai tabar zancanta,ta maida qafafunta saman gadon tayi kwanciyarta cikin nutsuwar data jima bata jita cikin ruhinta ba. Yayin da afifa ke duba kiran da ya shigo mata,sajjad ne,migewa tayi ta dauki scarf dinta ta fice a dakin, sãahar data fuskanci meke faruwa ta bita d kallo tana tabe baki "Hmmm,soyayya manya,mun jima da dawowa daga rakiyarta,mu da ita ko a lahira mun raba jaha" ta fada qasa qasa kamar me qunquni tana gyara kwanciyarta,sai kuma ta tuna zata yiwa maama gyaran wardrobe,don haka ta miqe ta sauko,ta kama gashinta me santsi ta daureshi waie daya,ta dora hula a kanta ta zura slippers ta fice. ********Ya jima a zaune yana juya wayar hannunsa,dukkansu mamaki suke bashi qwarai, nadeeya maji ga kuma mai gayya mai aiki fadeela. Yadda suke nuna tsantsar zakwadi da kuma farinciki akan wannan auren abun daure masa kai yakeyi. A yau sun jima suna waya da majiirin wayar da basu taba yin me tsaho irinta ba,duk da cewa kamar dai ko yaushe itace tayi kiransa bashi ne yayi kiranta ba. Dole bayan ya gama mamakin lamarin ya ajiye wayar gefe,dai dai lokacin sajjad ya shigo gurin bakinsa dauke da sallama. Guri ya samu ya zauna yana kallonsa yana kwance cikin lounge chair "'nata jira naji daga gareka" kyawawan zagayyun idanunsa kawai ya daga ya kalli sajjad din "Game da me fa?" Takaici ya kama sajjad din,kamar bazaiyi magana ba amma ya cije "Ba aure zakayi bane malam?" "Aure zanyi sai mene?" "Bakasan kana da buqatar yin wasu abubuwa ba,mace fa zaka ajjiye cikin gidanka,a ina zata zauna?,ka hada mata lefe?,dinkunan biki da sauransu" kamar bazaice komai ba,sai ya miqe ya zauna sosal sannan ya zura qafafunsa qasa yadda zaiji dadin zaman,idanunsa akan sajjad din "Ce maka akayi wani aure ne duk da za'a tsaya masa wannan hidimar? kawai a daura ta shigo taci gaba da aikinta,ni kuma na bata gurin zama da ciyarwa da suttura that's all,duk wadan nan abubuwan da kake jerowa sai ku masu auren farko,tun wani zamani da ya shude muka rufe wanan batun" sai ya miga hannu ya janyo plate din apple da Jacob ya ajiye masa. Ido sajjad ya zuba masa,kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa,ya saki qaramin murmushi sannan ya miqe "Zaka gane kurenka,indai macece ba'a cika musu baki,i pitty you duk lokacin da ka fada tarkonta,saboda haka kabi a hankali,shawarace kyauta na baka" baice masa komai ba sai qaramin miskilin murmushin da ya subuce akan fuskarsa,wannan maganar ta sajjad bata da banbancin da tatsuniya a gurinsa. Banda fadeela,babu abinda zai sanya ya biya sadakinta ta amsa sunan matarsa a bakunan al'umma bare azo gurin da sajjad din ke magana a yanzu. *********Karo na biyu ya sake gwada kiran qanwar tasa,wannan karon ta shiga sabanin lokutan bava da kiran yake yankewa. Spoon din hannunta ta ajiiye lokacin da kiran ke shigowa,wani hamshagin murmushi ta saki,yadda yayan nata yake bata kulawa tun daga wancan zamanin zuwa yanzu yana y mata dadi matuga,kuma har yau bata canza zani ba sanadiyyar jajircewarta "Assalamualaikum barka da warhaka yaaya" hajiya qarama ta fada bayan ta saka wayar a kunnenta "Yauwa barkanki dai FAUZIYYA" Cikin kulawa suke gaisawa da juna,ya tattambayeta yanayin kayan da taje siyowa a qasar. Tsahon mintuna goma suna tattaunawa sannan ya fara maganar da itace maqasudin kiran "Kwanaki kusan bakwai ina kiranki na kasa samunki har ina tunanin akwai matsala ne" "Babu yaaya wani lokaci ajiye wayar nake a nan hotel idan banason yawan kiran" "To yayi kyau, Allah ya taimaka,amma inajin ai dole ki yanki ticket na dawowa sati me zuwa ko satin sama ma,don yaronki ya tashi aure,Allah ya amsa addu'armu" Wani irin mummunar faduwar gaba me hade da wani tashin hankali ne suka rufto mata,tamkar wadda ake juyewa duwatsu saman kan nata "Yaron....na? wanne kuma?" Ta fada tana qoqarin boye gigicewar da tayi. Dan murmushi dr jarma ya saki "Kina da wani d'an ne bayan toufeeq?,inda 'yarki nace saiki tambaya nadeeya ko HASEENA?" Sarawa kanta yayi da matsiyacin qarfi,wani zazzafan gumi ya karyo ilahirin jikinta ta kowanne sashe,taji kamar an saka allura da zare ana daure kanta,cikinta ya juya take bayan gida ya matsota "Yaya?,ka manta haseena naketa ajjiyewa toufeeq? tunda anyi na farko ba'a dace ba?,ita kanta yarinyar bata taba kula kowa ba saboda ta sanya ranta akan TOUFEEQ din,ko yanzu haka sati uku ne kacal ya rage ta gama karatunta ta baro hannun babanta ta dawo nan nigeria don su daidaita kansu ita dashi" "Banda abinki mijin mace hudu ne faidan yaga yana da ra'ayi uku ne sauran da zai cike ma,sannan ita kanta yarinyar bata da matsala,na santa farin sani,itace wadda ta taba rige president na kamfani na,kuma kema kin santa,wadda ke kula da fadeela kafin tahowarki" "Kanbun uba!" Ta fada gasan ranta har bakinta yana motsawa "Nanny fa yaya!" Ta fadi cikin daukaka sauti "Ba nanny bace fauziyya,kawai tayi sha'awar aikinne,amma badon ta rasa komai ko kuma bata da gata ba,infact 'yar Dr mamman girema ce,wanda kikaso a baya,kikace matarsa ce ta hanashi sauraro da kulaki" wani bala'in kawai bayanan yayan nata suka qara mata,Dr mamman da baya ganin kowacce mace a gabansa sai matarsa?‚buzuwar nijer,wadda koda wasa mamman din bai taba kallon wata mace ya taya da zummar zai aureta ba saboda yadda ya samu kula biyayya da dukkan wani jin dadin rayuwa da d'a namiji yake bugata da muradin samu daga wajen diya mace? ‚matar data wahalar da ita ta kuma kafa tarihi ta zama mace ta farko da tayi mata shamaki da abinda takeso? bayan tafiyarta toufeeq ya koma gidan,yarinyar tayi amfani da wannan damar kenan ta ja hankalinsa? har sai daya kamu da soyayyarta me zafin da ya kasa sukuni cikin sati uku kacal ya nema aurenta?,to itakam fauziyya tana me? wanne irin sakewa tayi haka?. Kamar dr jarma shima yanason canzawa,ta yaya yake maganar idan toufeeq din yana so?,bata saba jin wannan kalamin daga bakinsa ba a duk sanda ta bugaci wani abu daga garesa, komai tsananinsa kuwa "Ya kikayi shuru?" Ya jefa mata tambayar. Cikin duniyanci da wayancewa tace "'Ina lissafin randa zan dawo ne,da abinda ya kamata na taho dashi na hidimar biki,sanann wannan karon abun yayimin banbarakwai ne,ba kamar aurensa na baya ba da akayi komai dani,wanann lokacin labari kawai naji" dan murmushi dr jarma yayi "Kinsan kowanne aure da yadda yake Zuwa,amma dai batun haseena karki damu,indai sun daidaita kansu shikenan,zanfi kowa farinciki da wannan,tuwo na,mai na" rintse ido tayi tana jin zafin abinda yake fadaidan sun daidaita kansu kuma?,ba ruwansa kenan bazai shiga ba bare ya tilasta yiwuwar abun?. Har yanzu batasan me yasa ta kasa bude wata qofa guda daya tal ba,duk da tarin nasarorin da taci take kuma kan ci,amma har yanzu qofar bada umarni ga toufeeq bata kammala buduwa. A duk abinda ta umarta da yayi,musamman abinda ya shafi janibin rayuwarsa akwai yiwuwar yayi ko kada yayi,bata manta lokacin da ta umarceshi da kada ya dawo da Ameesha,sai ganinsa tayi da matarsa a wancan lokacin,ribar kawai da taci shine watsewar lamarin da yayi babu jimawa dutse a hannun riga. Da tana da wannan cikakkiyar damar,to da a yau zata umarceshi da ya dakatar da komal,ya ajjiye batun auren ya saurari zuwan yaruwarsa nan da sati uku masu zuwa. Gefe guda babu abinda ya sake dagula mata lissafi irin haseena,batasan yadda zata tunkareta da zancan ba,bata iya jurewa tashin hankali,bata da juriya sam ko iya cinye abu,ta tabbatar babban bala'i da tashin hankali ne zai biyo baya. Dole tayi iyakar bakin gogarinta na ganin ta toshe dukka wata kafa da zata zamu labarin wannan auren,kafin sannan ta shirya fada mata tare da yi mata bayanin komai yadda zata fuskanta. Bacin ran haseena dai dai yake da nata bacin ran,ita daya qwal ta mallaka a duniya,tafi qaunarta sama da komai a rayuwarta,kai koda kuwa dukiyarta da take mutuwar so,take tattali da fadin tashin tarawa tsahon shekaru,ai dukka tana yine saboda ita haseena din. Migewa tayi dole tsaye,tanajin kamar hawan jininta zai tashi ta zare rigar jikinta tana jin duniyar na juye mata cike da tashin hankali, tashin hankalin data jima bata afka cikinsa ba,tsahon shekaru batasan tashin hankali ba,saboda dukka abinda ta nema tana samu,zallar farinciki da wanzuwar kwanciyar hankali kadai ta sani,sai gashi yau yarinyar da suka dauka aiki a matsayin nanny tana neman ruguza duk wani lissafi nata data dauki shekara da shekaru tana yinsa. Inda ace tana da masaniyar abinda zai faru kenan,da kanta zata koreta kafin tabar gidan,amma inaa.…..sai gashi wani qatoton tsautsayi ya gifta wanda ba zata taba barinsa ya zama qaddara ba. Dole ta qara gaba itama, haseena ce kadai tafi dacewa ta mallaki toufeeq din,yadda ta qarasa rainonsu har suka girma,lallai su sukafi cancanta suci amfaninsa. Qara kadai wayarta tayi amma sai da gabanta ya fadi,bakinta yahau addu'ar Allah yasa ba haseena bace don batason tayi kiranta ta fuskanci akwai wani abu. Hajiya mansura ce,sai da taja tsaki sannan ta koma ta zauna,cikin ranta tana jin me yasa ma ta ¡awo matar nan ta maidata daya daga cikin ahalinta?,a shekarun nan gaba daya tsanarta takeji cikin ranta. Sai da wayar ta kus tsinkewa sannan ta daga. Akwai tashin hankali me yawa cikin muryar hajiya mansura sanda take magana da hajiya qarama "Kinji abinda yake faruwa?" "Naji,menene?" "Baki tambayi halin da labiba take ciki ba,kin ganta can ta kulle kanta a daki,nayi mata maganar duniya taqi fitowa,ki taimaka don Allah ki kirata kuyi magana ko hankalinta zai kwanta" yatsine fuska hajiya qarama tayi tana iin kamar ta rufeta da duka ta wayar "'Mansura!" Ta kirayeta da tsurar sunanta,mamaki ya hanata amsawa,itama kuma bata jirayi ta amsa din ba ta dora da jawabinta "Yanzu labiba ta fara kuka ai,don bata dace sam da toufeeq ba" mamaki ya kusa sanyawa hajiya mansura faduwa,sai data lalubi gurin zama "Me kike fada ne?,ko kin canza daga alqawarin da kikayi mata?" "Tun wacce shekarar?,ai daga lokacin da haseena tazo hutu tun tana da shekara sha takwas,ta nuna muradinta akan TOUFEEQ alaqawarin dake wuyan labiba ya sauka ya koma kan haseena,ko don kinga inata muku kara ke da ita?,ban fito kai tsaye na nuna mata bazata sameshi ba?" Ta qarashe maganar da tambaya,tambayar da rawar da bakin hajiya mansura yakeyi yasa ta gaza amsa mata "Ai na dauka kuna da qwaqwalwar da zata gaya muku gaskiya,me muka hada daku da zamu dauki TOUFEEQ mu jingina shi da yarinyar da har yanzun ba'a da tabbacin ubanta ubanta ne!" "Ke fauziyya dakata!,ya isheki haka!" Hajiya mansura ta fada cikin matsanancin bacin rai. Shu'umin murmushi hajiya garama ta saki tana jinjina kai "Uhmmm,ni kike dagawa murya ko mansura? ni ba? inajin kin manta cewa ba yau na fara fidda matan wana daga gidansu ba,wadda ma take da zuri'a damu na kadata ta koma qasarsu ballantana ke da babu abinda muka qaru dake sai gatoton kashi da kike ajjiyewa suckaway,ki iya bakinki idan ba haka ba nan gaba kadan zakiyi nadamar da zata zame miki har qarshen rayuwarki" *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_ * Part 02 Page 8 gintse kiran hajiya qaraman tayi tana zake jan tsaki mai qarfi sosai,can gasan ranta tana in zafin tsawar da mansura tayi mata "'Lallai duniya tayi lafiya" ta gayawa kanta da kanta,banda haka mansura ko kallon banza bata isa tayi mata ba bare tsawa har irin wannan. Qwafa taja tana dukan tafin hannunta da dayan hannun,ko a yanzun ta tabbatarwa kanta bashi mansurar taci,sai kuma ta biyashi da abu mafi zafi. *_DR JARMA_* Suna gama waya da fauziyya din ya ajiye wayar a gefansa yana binta da kallo,cikin shekarun nan yana samun kansa cikin nazarce nazarce,kamar ana yi masa bitar wasu kura kurai da ya tafka a shekarun raywarsa na baya. A yanzun bayajin zai sake tilastawa wani cikin 'yayansa yin wani abun daya zama ba bisa ra'ayi ko son zuciyarsu ba,hakan yasa duk yadda yaso ga kawo SÄAHAR cikin ahalinsa bai aikata hakan ba kai tsaye,saidai yayi wani abu da ya zama yayi pushing toufeeq din zuwa ga neman auren da kansa,ta yadda ko a gaba sunansa bazai fito cikin wanda yake ganin ya tilastashi ba,duk da yana jin alkhairai masu tarin yawa zasu fita daga gurinta tun saninta na farko da yayi a rayuwarsa kafin ma aje ga ganinta. Wayar tasa ta sake qara a karo na biyu,ya waiwaya yana duban number da ake kiransa. Zumbur yayi yana sake zama sosai yana duban wayar,yakai hannunsa ya murza idanunsa cike da dumbin mamaki number wayar da ya mallaketa shekara guda kenan ya kuma gaza kiran mamallakiyar number, yau sai gashi number tana yawo saman screen dinsa a lokacin da bai taba zata ko kawowa ba. Haka kawai yaji ya gaza daga kiran,sai wani fat fat fat da girjinsa yakeyi,yau shi SHIFA ke kira? ,bayan tsahon was shekaru da suka shude da tarin galubale ZAQI DA MADACI? Kamar wanda aka fuzga bayan tsinkewar kiran va sanya hannu hannun nasa yana rawa ya dauki wayar ta shiga bin kiran. Shuru kaman ba za'a daga ba,yanata addu'a cikin ransa akan ta daga din,ya tabbatar bata da number dinsa ne kuma ko yanzu baya saka ran tayi saving kafin kiran nasa,yadda ta alqawarta masa a can bayan sai data tabbatar da halaccin haihuwarta,ta cika alqawarin,kamar yadda tace ta barshi har abada,amma akwai wata eana da zata waiwayi abinda ta haifa a cikinta. Ta barshi din,wanda kod wasa bata taba gwada nemansa ba,yaranta dai batayi fushi dasu ba ko ganqani,bata bari komai ya shafesu ba. Tana dab da tsinkewa,kamar ba zaa daga ba sai kuma yaji an daga din,shuru ne ya biyo baya,abinda ya tilasta masa yin magana a wani yanayi dake nuni da kamar yana d'ari d'ari "Assalamualaikum warahmatullah" "Waalaikumus salam warahmatullah" ta maida masa amsa har sai da kowanne lungu na jikinsa ya amsa da muryarta,muryar da ya dauki shekaru masu tsaho ba tare da kunnuwansa sun jiye masa su ba,muryar da bazai taba mantawa da ita ba har abada "Barka da wannan lokaci,na kira ke na shaida maka ni da ahalina zamu sauka a nigeria bikin d'ana kuma d'an uwa a garesu,zamu sauka cikin gidan d'ana in sha Allah,bawai ina gaya maka wannan labarin ba saboda neman izini kamar yadda ake bugata,na shaida maka ne saboda kayi magana da 'yaruwarka,ka gaya mata jiya ba yau bace,sannan muna da buqatar zaman lafiya ayi biki lafiya a gama lafiya kowanne bago ya koma muhallinsa,gargadine wannan daga gareni,ina fatan zaka isar mata" iva abinda ta fada kenan ta yanke wayar. Sosai qirjinsa yayi masa nauyi,ya fara jan numfashi tare da fesar dashi "Shifa,har yanzu tana nan da halinta bata canza ba,babu daukan raini ko qasqanci,babu gudu babu ja da baya akan gaskiyarta,sai yaushe abubuwa zasu canza tsakaninta da FAUZIYYA?" wannan din dukka halave da dabi'arta ne. Bata yarda ta sakarwa abokin adawa wasa ba,muddin ita ke da gaskiya sai taga abinda zai turewa buzu nadi. Bai wani damu da maganganunta ba,abinda yake kai kawo tsakanin ruhinsa da zuciyarsa ya shafe wannan. Gaba daya jikinsa ya saki,ya rasa shifa shekaru masu yawa,kuma har yanzu qaryarsa ta sha qarya yace ya samu koda rabi rabin madadinta ne. Shin meye abinda yasa ya kasa haquri da ita a wancan karon ne?. FAUZIYYA sunan da yazo kansa, zalunci suka aikatawa shifa da gudunmawarsa kenan?, tambayar da tasa kansa sarawa har sai da yasa hannu ya riqe goshinsa da kyau. Dai dai lokacin da hajiya mansura ta shigo falon afujajan,zuciyarta cike da tsoro da fargabar abinda fauziyya zata iya aikatawa,gwara tun yanzu tasan wanne tudu ta dafa. Guri ya samu ta zauna ba tare da tayi aakari da sauyawarsa ba "Yanzu fisabilillahi Dr labiba tana da uba kamarka amma har ta rasa toufeeq? yaron da take mutuwar so?" Idanunsa ya aza a kanta,ransa ya darsu da mamakin me yasa kowa sai toufeeq?, cikin daurewa da son sake kashe wannan wutar yace "Bance ya auri kowacce ba kamar yadda ban hanashi auren kowa ba,kawai abinda na sani shidin mijin mace hudu ne,kuma kowacce mace yakeso an bashi damar aurenta" shuru tayi ta rasa abun fadi,ranta na sake zafafa da abinda hajiya qarama tayi mata "Haka ne,amma gaskiya ka jawa qanwarka kunne,na fara gajiya da gadararta da rashin ganin girmana,waishin ni ba matar yayanta bace? matsayin yaya kuma uwa nake dashi a wajenta fa" ji yayi kamar tana son hautsina masa kai,sai kawai ya miqe yana cewa "Kunfi kusa" ransa a mugun quntace, da alama sam bata lura da yanayinsa ba,sai ya tuna wan! lokaci can baya,ko tuntube yayi muddin yaji zafi sai shifa ta gane,ya tuna wani lokaci acan baya sanda zuciyarsa ta afu ga rabuwa da ita. Kamar haka yana zaune saita iskoshi,tayita tambayarsa abinda yake damunsa,a tsawace yace mata "Kinga dalla malama kada ki dameni" bata yi zuciya ba,hakanan bata qosa ba ta juya zuwa daki ta dauko masa magani,ta fuskanci akwai ciwon kai saboda yadda yake riqe da kansa,fauziyya dake zaune a gefe tana masa sannu a jere babu gaqgautawa,ta biya kitchen ta debo ruwa ta dawo ta zauna gabansa,fauziyya na daga gefe tana balla mata harara,amma ko sau daya bata bi ta kanta ba,ta balle maganin ta miqa masa hade da ruwan "Ka sha zaka samu relief, zuwa anjima idan bai sauka ba,akwai ragowar canji cikin salary dina dana yiwa yaro siyayya saika karba kaie asibiti" "Yaaya,kada ka karba,wallahi ban yarda da maganin nan ba,don dazu wata qawarta tazo kuma na ganta da qulle quile a leda,suna ganina suka boye" ta juya da mamaki tana kallon fauziyya,daidai lokacin shi kuma yasa hannu ya tankwabe ruwan da maganin data siya da kudinta. Kallo daya tayi masa ta miqe tana zazzage rigarta data jiqe,ta waiwaya ta kalli fauziyya "Shima wannan ya shiga sahun abinda nake neman haqqi a kansa a gurin Allah" daga haka ta taka ta bar musu gurin. Tunaninsa ya yanke sanda ya isa bedroom dinsa,sai ya zauna yana sake dafe kansa da kyau gami da kiran sunan Allah "'La haula wala quwwata illa billah" ********Tuni sãahar taci gaba da harkokin gabanta,don bata dauki auren a bakin komai ba,bata kuma daukeshi wani abu me muhimmanci ba,sam kai ba zakace itama daya daga cikin amare bace. Komai afifa ta zabar musu sai tace da ita "Yayi?" "Yayi" kawai take cewa,wani lokacin ma kO daga kai ta kalli abun bata tsaiwa yi take amsa mata da yayin,saboda a nata ganin dukka wadan nan abubuwan bata lokaci ne kawai,meye na dukka wadan nan abubuwan akan auren da bashi da maraba da auren haya? Yadda suketa shirye shirye gadan gadan shine ya fara dawo da ita cikin hayyacinta,ya kuma ja hankalinta,tun tana daukan abun da wasa har ta fuskanci da gaske fa ake. Kamar zaa aurar da wata shahararriyar budurwa?, hidimar da sam a aurenta na farko ma baa yita ba,sai gashi yanzun shi wannan auren yanata samun tagomashi. Abun ya fara taba ranta,har taji bata qaunar ma ayi mata zancan auren,saboda ita gaba daya a yadda ta dauki abun,zai kawo sadaki ne akwai a daura auren,ta tattara dan abinda take da ra'ayin dauka ta wuce gidan ta tare a dakin fadeela suci gaba da rayuwarsu kamar baya. Saidai abun yazo da akasin tunaninta,siyayya taga anata yi babu kama hannun yaro. ********Misalin qarfe hudu na yammacin ranarta qule a dakin tayi zamanta tana chart,tun bayan isowar charifa qanwar mahaifiyarta daga nijer gaba daya ta sake quntata a gidan,kullum akwai tsirfar da inna charifa zata tsiro da ita wai da sunan gyaran jiki,abun har ya fara cikata,yau dai tayi mata tawaye tace babu me bata mata jiki da wasu kwabe kwabe. Baki inna charifa ta sake tana kallon säahar din,ba wani shekaru ta bata masu yawa ba,duka duka bazai wuce shekara bivar ko shida ba "Wai nikam wannan auren na soyayya ne kuwa? ina cewa afifa ita ke tayani ma hada kayan,kafin na gama kintsawa ita ta shirya" "ita tanaso inna charifa kiyi mata,ni ki barni hakanan,ban buqatar komai"ta fada tana murie dilka din data fara murza mata a hannu,sannan ta fice a dakin. Ko yanzun da take zaune a dakin sai takejin zuciyarta na mata wani quna,wannan abun da aketayi ita bashi takeso ba,bashi da faida ma sam a gurinta, tamkar ana shelantawa duniya ne,abinda ita a ganinta bai zama dole ba. Turo gofar dakin akayi,kuma koda bata daga kanta ba tasan afifa ce,saboda wani irin gamshi da inna charifa ke jigasu dashi ita da afifan. Duk da taqi bataso, taqi kuma bada hadin kai,amma tana gaunar qamshin sosai,yana mata dadi qwarai. Saman kanta afifan ta tsaya itama tana basarwa "Ummu chamsiyya tace na gaya miki,ki hada kayanki yau,gobe za'a fita dasu tare da kayan kafi gaba daya" a wani matuqar qufule ta daga kai daga wayar da take dannawa ta kalleta "Ya isheki haka afifa,ke idan kina rawar kanki a kan saiiad ki daina sakowa da säahar,kaya na a nan za'a barmin su,ba inda zani dasu" "Hehehe… ...ke kikace kinaso,da bakice kinaso ba da ba'a baki shi ba" afifa ta fadi harda tafa hannaye. Al'amarin daya sake qular da sãahar kenan,sai ga idanu da muryarta dukka sun dauki rawa,afifan sam bata kulata,duk wasu tambotsai da takeyi bata taba biye mata,saidai ma ta manna mata hauka kamar yadda tayi mata a yanzu. Bata da zabi illa ta barwa hawayen damar zuba,zuwa yanzu ji takeyi kamar tace ta fasa auren,to amma tasan qaryarta tasha qarya,babu me kallonta ma bare ya saurareta,kuma ma idan tace ta fasa....wani dole za'a sanyata aura,wanda zata zauna garqashinsa ta zama cikakkiyar mata a gareshi,gara wannan,da an gama wadan nan filile fililen dole kowa ya sama mata lafiya, uwa uba ma kuma bawai binta gidan za'a yi ba bare aga yaya zatay zaman auren. Ranar wuni tayi a daki,don inna charifa tayi rantsuwa indai ta ganta a waje ba abinda zai hanata danneta ta shafeta da kayan gyaran,tasan tsaf zata aikata,don ita din cikakkiyar buzuwa ce wadda ke tafe da tsananta da qiba,tasan kuwa muddin ta tausheta a kalankasin jikin nan nata ko motsi cikakke ba zata iya ba bare ta qwaci kanta. Koda inna charifa bata fadi haka ba dama yau din bata da niyyar motsawa ko ina,hatta da wayarta a silent ta barta,tana daga kwance saman gadon da yake tana fashin sallah,duk wani motsi da kai kawo dake faruwa daga falonsu zuwa farfajiyar gidan tana jinta. Gidan kwanakin nan da bikin ya matso ya fara rayuwa da shige da ficen jama'a. Taji shigowar anty farheen ma amma sai ta qudundune a duvet,don ita kanta anty farheen din nemanta take yau kusan sati amma taqi zuwa,tasan muddin taje fiye da rabin zancanta na auren ne,auren da daga ita har wanda zai biya sadakin nata basu saka a ka ba,amma su anty farheen din duk sunbi sun addabi kansu,wai lallai sai sun gyarata,bayan abubuwan data dinga yi mata sati dayan da sukayi a Dubai, wanda sai da tayi da na sanin binta ma saboda dirke dirke da abubuwan data bata ta tilastata amfani dasu. Acewarta irin gyaran da za'a yiwa afifa ita ba irinsa za'a yi mata ba,amma dai tanason tsakanin afifa da ita a kasa banbancewa acan cikin turaka. Randa ta fadi wannan maganar yini sãahar din tayi batayi magana da kowa ba,idan ta tuno maganar sai taji kamar ta dora hannu aka ta kurma ihu. Wai da waye zata hada gado ma?,da toufeeq?,wannan mutumin da ko sunansa bata qaunar ji? tanata qoqarin danne action dinta akan auren don kada duniya ta fahimci AUREN MANUFA ne,to amma yadda suke nan nan da bikin idan ba'a yi wasa ba zata kai inda zata gaza ci gaba da boyewar. Sake turo gofar dakin akayi,aka dan tsaya kadan a kanta na was mintuna kafin daga bisani ta magantu "Maji nata kiranki amma tace no answer" "Maji”?Ta maimaita sunan cikin ranta,a guri daya tasan me wannan sunan,kakar fadeela,ta kuma san afifa bawai sanin maji din tayi ba. Mamakinta ya gaza bayyanuwa,ta yaye duvet din tana kallon afifa daie tsaye tanata gyalli hadi da baza qamshi "Wacce maji din?" "Uwar mijinki" ta fada gatsal kai tsaye. Duk duniya afifa ce kadai zata yi mata haka ta ayaleta,sai taja siririn tsaki ta ja duvet din da nufin komawa ciki, dai dai lokacin kira ha shigo wayar afifa dake hannunta "'Yauwa gashi ta sake kira" afifan ta fada tana matso da wayar kusa da sãahar din. Koda ta tsani toufeeq tana qaunar fadeela,hakanan tanason maji tana kuma qaunar nadeeya. Mutanene masu wani irin karamci tare da maida dan kowa nasu,suna da wani irin saugin kai tamkar ba daga jininsu toufeeq ya fito ba,ba maji ba,duk wata dake da shekaru irin nata ma ba zata iya wofantar da ita ba,do ta samu cikakkiyar tarbiyyar wannan daga gida,tilas ta miqe ta zauna sosai,ta miga hannu tana amsar wayar tare da jefawa afifa harara sannan ta daga kiran tana karawa a kunnenta,dai dai sanda afifa ta watsa hannunta alamun ko a jikinta ta fita tabar mata dakin. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 09 Muryar maji dake dauke da wani allausan sauti me cike da nutsuwa ce ta mamayi kunnenta. Wata nutsuwa ta saukar mata wadda ta sanyata amsa sallamar cikin tsari. "Ina fatan binty bakiyi fushi da ni ba,inataso na kirayeki amma ban samu damar hakan ba‚nadeeya kamar rowar rak'am(number) dinki takeyi" murmushi säahar ta saki me cike da kunya,ai ita ya dace ace ta nema maji din,don rashin kyautawa tunda tabar gidan bata sake nemanta ba "'Masa'al khair" säahar ta gaidata "Masa'an nur ibnaty kina lafiya ko?,ya iyayi ki?" "Bikhair walhamdulillah" "Ma sha Allah, ya kuma shire shiryen aure? muna hanya cikin satin nan in sha Allah" nauyinta ta sake ji ya kamata,saita kasa magana "Ina fatan za'a yi haquri da halin moha,ya taso me wani irin zafi da rashin son raininaso qwarai na saisaita wannan dabi ar tasa,saidai ban rayu dashi ba,ya sake zuwa kuma bayan ya girma Allah ya jarabceshi da wata irin jarabawa data sanya dabi'unsa suka sake zafafa,ina rogon alfarma ayi haquri da shi,a kuma yi qogari a saita min shi, kyawawan dabi'u da na san dasu na haifeshi su dawo gangar jikinsa suyi tsiro, zuciyarsa ta zama irin ta kowa" "In sha Allah" kawai ta fada,don batasan fadin kowacce kalma da zata nuna ta dauki alaqawarin,saidai daga qasan zuciyarta tana mamaki,dama shi din bai rayu da maji ba”? "Inason diyata tafi kowacce amarya kyau a duniya,don wannan shine karon farko da za'a aurar da moha a gaban idanuna,akwai me gyaran amare da zata iso nan da jibi daga nan gasar tare da 'yar uwata,ina fatan diyata zata bada hadin kai?" Sosai abun ya yiwa sãahar girma,suma da gaske suka dauki bikin?,sun dauka auren gaske ne kenan?,ba yadda ta iya ta amsa a sanyaye da "To,mafi mishkila,jazakillah bi khair" "Nice da godiya da shigowa rayuwarmu da kika yarda zakiyi" maji ta amsa mata cikin qauna da kulawa,har cikin jininta takejin qauna da soyayyar sãaharita din ma'abociyar sallar dare ce,a duk sanda ta roqawa rayuwar toufeeq da nadeeya abokan rayuwa na gari sai taii sãahar ta sake kwantawa qwarai a ranta,tana ta qoqarin ganin yadda zata qulia al amarin tana daga can,sai gashi cikin hikimar Allah komai yazo cikin sauki darajar istikhara din data dinga yi tana neman zabin Allah. Ganin kamar saahar din tana kunyarta ya sanya tayi mata sallama,tare da gaya mata tayi serving number dinta a wayarta,koda tana da bugatar wani abu kada taji komai,kai tsaye ta kirata. Gudun mantuwa da girman majin ya sanya tana ajjiye wayar afifa ta dauki wayar tata ta fara duba tarin miscall din data samu,wasu na cousins dinta ne wasu na yayunta,wasu numbers dinma batasan nasu waye ba. Tana tsaka da saving kira ya shigo wayar tata,kamar ba zata daga ba,saboda batasan number din ba sai kuma ta dauka din ta kara a kunnenta. Baquwar murya ce a kunnenta,ta amsa sallamar da akayi mata "Sunana elyas,ina daya daga cikin ma'aikatan MT JARMA,na kira ne bisa umarninsa,yace na shaida miki,idan akwai wasu kudade da kike bugata na hidindimu ki fada sai a tura miki" wani irin baci ranta yayi qwarai ta mige ta zauna sosai,ma'aikacinsa ne,tasan kuma irin respect din dake tsakaninsu dashi, uwa uba ma shi din dan aike ne gaba daya bashi da laifi sai ta rasa abinda zatace masa,ta lumshe ido takaici yana cin zuciyarta "Hello madam,kina jina?" "Ina jinka,elyas ko?" Kai ya gyada "Yes madam" "Bari na baka shawara,koda gaba kada ka sake yarda ka shiga irin wadannan abubuwan,saboda bai dace ba,kudi kuma kace masa har yanzun dai bashi da kudin da zai bawa sãahar…." Cikin kunnuwansa ta qarasa fadin kalaman,yadda yaga elyas yayi shuru yana qifta idanu yasan akwai matsala,ya fahimci tana da tsiwa da rashin barin kota kwana,zata iya fadin wata maganar ma da zata iya zubda masa girmansa a idanun yaransa. "Da wa kike?" Sautin murvarsa dake da wani irin zurfi da haiba suka sauka mata a kunne a lokacin da bata zata ba,dalilin da yasa batace komai ba kenan har ya sake maimaita tambayarsa. Cikin dakiyarta tare da son fanshe bacin ran da afifa da sauran family ke gasa mata saboda yadda suketa shirin biki tace "Ni ba wulagantacciya bace, kuma bana neman komai a gurin kowa,ka rige arziqinka na rige mutuncina" wani irin zafi maganarta tayi mata,yaji babu dadi sosai a ransa,saidai takaicinsa ragagge ne tunda umarnin maji ya cika "Hey!,watch your words.…karki dauka kiranki yana da alaqa da damuwa da akayi dake.. bazanvi tolerating nonsense ba,don bazan biva sadakinki sannan na dauki wadan nan tsiwar da rashin kunyar ba" daga haka ya kashe wayar yana furzar da iska me zafi daga bakinsa. Lallai idan batayi wasa ba sai ya mata horo me tsanani, ya cire duk wannan jin isar tata da rashin kunya,abinda takeyi masa kaf tarihin rayuwarsa ba wanda ya taba gwada masa irin hakan sai ita. Wani mugun tsaki yaja ya jefar da wayar,maji ce sila,inda ta fahimci maganarsa tun farko da bata sanya yasa ay! kiranta ba. Ya miqe tsaye yana boye hannunsa a aljihun trouser dinsa,yana jin zuciyarsa na sake zafafa,dai dai lokacin da sajjad ya shigo dauke da wasu manya manyan kwalaye shi da jibril. Har suka gama ajjiye kwalayen jibril ya juya ya fita baice musu ta tafas ba. Zama sajjad din yayi ya fara bude kwalayen,wasu irin shegu suit ne da yadiddikan vicuna,qiviut fabric guanaco da baby cashmere wadanda duka aka viwa wani lafiyayyen kwantaccen dinki. Kallo daya zaka yiwa kwalayen zuwa sutturun ciki kasan maqudan kudade kamfanin da yayi kwangilar aikin ya lasa daga hannunsu "Here's our wedding attire,ya ka gansu?" KO duban inda yake toufeeq baiyi ba,don dama yana cike da sajjad din. Tafiya yayi ta sati daya,amma kafin ya dawo sajjad din ya sanya an canza komai na sassansa,an canza tsarin komai ma,ya zuba masa dukka wasu kaya da suke favorite dinsa a design da kuma color,sannan ya fidda sashen da aka zuba jeren säahar din. Yayi masifa kamar zai ari baki har sai da girjinsa ya dinga zafi kasancewar bame doguwar magana ba,yana ganin kaf girman gidan da sassan da yake dasu amma ya rasa inda zaiyi mata matsugunni sai cikin sashensa? haka ya haqura ya gaji,don sajjad ya gaya masa yayi din waye zai aureta da za'a ajjiyeta a wani muhalli na daban,sanann muddin yaci gaba to zai sanarwa da Dr girema auren meye zaiyi,da kuma abubuwan da yaketa yi din,wanda sam basu dace ba,don meye bazai sassauta zafin kansa ba?. Haka ya gama qure sajjad da zazzafan kallon nan nasa ya debe fararen idanunsa yabar masa wajen,yasan indai yaci gaba da tsayawa sajjad bazai gaji da gasa masa magana a fakaice ba,shi kuma bazai iya doguwar magana ba. Yanzun ma key din motarsa ya dauka ya fice daga gidan shi daya,ransa a bace,shi dinma bai duka duka wannan hidimar zaa yita yiba me hana mutun sakewa,hatta da fadeela yanzun ganinta sai lokaci lokaci,duk sun yamutsa gidan da shirye shiryensu,yau basu nan gobe basu can,cire wancan canza wannan siyo wannan ajjiye wancan,duk Dr girema ya daure musu qarqashin ko nawa sukeso zai dauka ya basu. Ko su jibril da sukayi yunqurin biyoshi hanasu yayi,bai tsaya ko ina ba sai bristol palace,ya kama royal suit da ya saba ya wuce ciki bayan ya kashe dukka wayoyinsa yana fatan samun relief ya kuma daidaita kansa,shi kansa yasan yanata misbehaving ne,yana kuma batawa sajjad wanda dama shi kadai yake iyawa dashi,yasan abinda ya faru dashi a baya yake hunting mind dinsa,yanaso yayi cooling temper dinsa kafin ya dawo cikin gidan. *******Kayanta taketa hadawa guri daya,amma fiye da rabin hankalinta ya dilmiya a zuzzurfan tunani. Idan lissafinta yayi dai dai,ranar da zata isa Nigeria ya kama saura kwana biyu rak a fara bikin,kamar yadda kwanan wata ya nuna mata jikin dallelen invitation din me rubutun ruwan gold a jiki, wanda har yanzu hasken katin da tsarinsa basu bacewa idanunta ba,don sam baiyi kama da katin biki ba. Jagwab ta koma ta zauna saman kujera,ba qwarin zuciya ba har gwarin gangar jikinta tana nema ta rasa, komai gani takeyi yana fara zuwar mata a cakude,ko a mafarki bata taba tunanin akwai wani abu da zaizo ya rusa tsarinta ba dai dai da qiftawar idanu, bata taba kawowa wata mace zata shiga rayuwar toufeeq ba baya ga hassenarta wadda aka fi sani da MEENAL YA'AQOUB AJI,saugin abun har yanxu ta tabbatar meenal din bata san da zancan ba,don ko jiya sunyi waya kuma lafiya lau suka gama sukayi sallama. Sautin qarar wayarta ya tabbatar mata da shigowar kira wayarta,ko da ta duba taga sunan baby na kamar yadda tayi saving number meenal haseena sai da gabanta ya fadi,ta zauna sosai tana daga wayar da hanzari,don jikinta ya bata ta faru ta qare. Yadda ta zata din kuwa haka ne,kukan meenal haseena kawai ya tabbatar mata da zarginta,cikin hargagi da daga murya da muryarta da tayi sirantaka da yawa har take bada wani irin amo da ba kowa yakewa dadi ba "Momy? kina ina akaci amanata?, kina raye kuwa momy?" "Ina raye baby meenal,ki kwantar da hankalinki,ba wani abu bane babba" "Ta yaya zakice ba babban abu bane,bayan next week zaiyi aure? zai auri wata bani ba,bayan kinyimin algawarin bazai sake auren kowacce diva mace ba bayan ni?,yanzu duk zaman da nayi shekara da shekaru ina jiransa ya tashi a banza?,duk wani buri na da naci a kansa ya zama mafarki?" "Haseena!" "Momy!!! ba abinda zakicemin,na dauka ina da uwar dana wuce nayi kuka na zubda hawaye na? ta isa ta sharemin kowanne kuka nawa ashe kuskure nayi!" "Meenal ki saurareni mana,kin manta wacece fauziyya?,kin manta waye toufeeq a wajena?,ubansa ma ya yake a gurina barshi?" Maganar ce ta sanya meenal din yin shuru,saidai har yanxu bata fasa kukan da takeyi ba "Wallahi momy idan har ban auri yaa toufeeq ba mutuwa zanyi" "Indai kinga baki aureshin ba saidai idan bana raye,ke ko bana raye saikin aureshi,shine mijinki" hajiya qarama ta maimaita da confidence,tana ajjiye wannan alwashin har tsakiyar zuciyarta "Wani ma yayi rawa bare dan makadi?,bani da qwai a duniyar nan fa sai ke,ke kadai na mallaka kuma duk duniya babu wanda nakeso kwatankwacin yadda nake sonki,idan ban sama miki farinciki da jin dadin rayuwa madawwami ba me nayi kenan?,koda tsiya koda arzigi saikin mallaki muradin ranki,ki rubuta wannan ki ajjiye,alqawari ne dauka" "Ki tabbatar kin cikashi momy,saboda komai zai iya faruwa,inason na auri yaa toufeeq a watannin da muka riga muka tsara tun farko,bazan iya jurewa rashinsa na tsahon wani lokaci ba,bazan iya jurewa ganinsa da wata mace ba bayan ni" "Ki kwantar da hankalinki ki kammala exams dinki,sati biyu fa kacal ya rage,a satin bikin ma zan miki booking ticket,ko Dr jarma banason ya sani,saidai kawai suga isowarki" "Thank you momy” "Naji,amma haka zamu rabu kina wannan kukan don kawai ki hanani sukuni?" "Na daina" "Kin tabbatar?" "Kinsan idan na fadi abu bana canzawa ai" "'Yayi kyau,ki huta da kyau" . Wani qaimi taji yana shigarta tare da karsashin son ganin ta gudanar da komai,don haka ta sake migewa tana qarasa hada kayanta,tare da duba jirgin garfe nawa zata bi. ********Tun daga saukarta farkon layin zuwa shigowarta cikin gidan hankalinta ya soma tashi,ta sake tabbatarwa eh lallai aure MT JARMA zaiyi,irin auren kuma dake nuna cikin wadata da tarin arzigi za'a yishi,ba irin aurensa na baya ba. Abinda ta lura dashi cikin nutsuwa da zurfafa dubanta akan kowa,kamar kowa fuskarsa dauke take da annuri da farincikin auren,komai na gidan an canzashi an sake masa fasali da tsari, hatta da uniform na ma'aikatan gidan kuwa. A ranar kasa zaune tayi ta kuma kasa tsaye,hatta da fadeela da nadeeya bata samu ganinsu ba a ranar,don ba'a basu zama ba,yaa moha zai dawo musu da masoyiyarsu,a wannan karon da a sunan nanny ba,a sunan MATARSA ta sunnah. Tanason ta fita don fara aiwatar da wasu abubuwa,amma baqin da aka fara yi a gidan da abokan kasuwancinta da suketa zuwa ganin kaya sun hanata motsawa,komai kawai yinsa takeyi ba cikin nutsuwarta ba,tana da bugatar zuwa ta sabunta tsonon aikinta,don dama an jima ana gargadinta akan hakan, bata fuskanci da gaske bane sai da taga kwabarta tana shirin yin ruwa. Komai a quntace take yinsa cikin yage da tsabar duniyanci wajen iya boye damuwa da tashin hankali ta kuma bi sahun 'yan murna da Allah ya sanya alkhairi. *_KALLON KALLO * 👀👀👀 *HUGUMA* * _TABARMAR KASHI* Book 02 Page 10 *_KALLON KALLO_*👀👀 Hantsi ne wanda yazo mata a birkice,irin birkicewar da bata taba hasasota ba. Tun safiyar data tashi take jinta sukuku,amma ta danganta hakan da fitar da taketa son yi jama'a na tsaidata,saidai ta yanke a ranta gobe komai matsi taje din,don da zafi zafi ake dukan qarfe. A safiyar a daki tasa aka ajjiye mata breakfast dinta ta tsakura ta ajjiye,saboda kullum damuwa ce ke narkewa a zuciyarta,yadda taga dan uwanta Mahmud jarma ya dauki lamarin auren nan sai yake sake sakata cikin tashin hankali. Kamata yayi ace dukka wadan nan shire shiryen da zumudin akan auren toufeeq ne da meenal 'yaruwarsa,ba wai akan wata nanny ba. Da wannan baqinciki ta kwana ta tashi,da gyar ta samu wajen sha daya da rabi ta shiga wanka,ta fito ta shirya kamar kullum cikin shigar alfahari da fariya na wani dandaqegen lace,ta cika jikinta da turare,ta fito don ganin meye kuma yake gudana cikin gidan gaba daya,wanda kusan wannan din al'adarta ce,komai na gidan idanunta suna kai tana biye dashi saidai idan bata qasar tayi tafiya. Tana takawa ne cikin jin izza tare da yadda take samun komai yadda takeso,idan ka cire yadda al'amuran a yanzu suketa son yi mata gardama,wanda ta tabbatar sako sako da dauke mata hankali da neman kudi sukayi shine musabbabiyyar faruwar hakan. Zuciyarta a cike fal da qunar yadda gidan yake kasancewa kullum cikin hada hada da kai kawo jama'a,duka a shirin fara gudanar da bikin da batasan da meye yafi saura ba?,tana tsoron ma a qare dukka shagalin akan wannan auren data sanyawa suna MATACCE,azo bikin shalelenta abubuwa sugi armashi saboda komai an gudanar dashi a wannan. Dai dai sanda take isowar farfajiyar gidan,biyu daga cikin security din gidan na qoqarin bude qofar gidan,sai ta tsaya cak tana jiran ganin su waye? Wasu laflyayyun range rovers ne guda uku,biyu daga ciki ta sansu farin sani,mallakin toufeeq ne. Tunda ya siyesu suke ajjiye bai hau su ba,to amma ya akayi yau aka fiddasu daga gidan?,ina akaje dasu bata da masaniya?. Waiwayawa tayi tana gogarin kiran daya daga cikin me kula da motocin gidan,saidai kowacce kalma dake bakinta ta qafe tas!,cikin sakannin da basu haura biyar ba yawun bakinta ya dauke,wani abu me nauyi da girma ya daki kanta,abinda ya sanya mata dawo da dubanta zuwa gabanta a hankali kamar me ciwon wuya. Cikin wata lafiyayyar abayar take blue black. lya adon jiki kadai ya isa ya gaya maka daga wanne gabila da kuma kalar nau'in ahalinta "alhamdulillah,alhamdulillah,a'uzu bi kalimatillahit taammati minsharri ma khalaqa,Allahumma anzil ni munzalan mubarakan wa'anta khairul munzaleen" addu'o'in data furtasu dukka a bayyane kuma daki daki,cikin nutsuwa ta haqiga,addu'o'i masu qarfi da tsananin tsari. Wata mummunar faduwa gaban hajiya qarama yayi,ta runtse idanu da kyau tana kuma budesu,suka sauka fes akanta SHIFA CE,maji,matar yayanta Mahmud,bayan shudewar shekaru talatin da wani abu,sai yau gata a gabanta,sun hade cikin gida daya,sun hade cikin gidan toufeeq,toufeeq din da tace ta sanya a ranta ita ta haifarwa saidai ta haifi wasu a gaba shi da nadeeya,toufeeq din da tace itace dashi har abada... ...kai alwashin da taci suna da yawa,wasu lokaci yayi mata halacci ya bata damar cikasu,wasu kuwa har yanzu walagigi takeyi sun kasa cika kamar yadda taso. Murmushin da ta gani saman fuskar shifa bayan isowarta dab da ita,ita da fararen danginta wanda koda baka tambaya ba zakasan cewa yes,larabawan Algeria ne shi ya sake dugunzuma hankalinta,murmushi?, murmushi fa a fuskar shifa,shin ko yawan shekaru da tsahon lokaci yasa ta manta wace ita a wajenta? ‚bata tunanin zata bari taga koda haqorinta muddin ta tuna ita din fauziyya ce "Assalamualaikum hajja fauziyya" maji ta kawar mata da dukka wata tantama daga ranta. Ko wacce gaba ta jikinta sai data cika saboda tasirin sallama,amma kuma nuna hakan a tattare da ita babbar faduwa ce,don haka itama ta saki nata murmushin,murmushin da ko kadan bai shiga fuskar maji ba bare ya ratsa zuciyarta,tasan wace fauziyya,kuma bata tunanin shekaru zasu canza halinta "Wa'alaikummus salam,baqi ne haka damu? marhaban bikum" wani murmushin maji ta saki har sai da farare tas din hagoranta da toufeeq ya gado suka bayyana,wanda shekaru bai ragesu da komai ba. Waiwayawa bayanta tayi kadan ta kalli 'yan uwanta da suka yo gaba,suka bar sauran suna fidda luggage dinsu "'Baqi? baqi,nidai nafi gaban baquwa,saboda daukan ciki wata tara,naquda ta kwana biyu cur babu sassauci a gasar da babu uwa ko uba,haihuwa zuwa raino har na tsahon shekara shida....kin tuna,su kuma dukka wadan nan da kika gani,bari nayi miki taqaitaccen bayani duk da idanunki na shaida sun gama gaya miki,wadan nan sun zarta baqi,ahali ne kuma halastattun dangi ga d'ana Muhammad toufeeq,d'a na halali ga mahmud umar jarma….mun shigo cikin gidan d'ana da sunan Allah tare da dukkan amincinsa,zamu zauna adadin yadda Allah ya deba mana,amincin Allah a gareki" ta furta tana miga mata hannu. Tamkar an shukata haka hajiya qarama taji,tsahon shekaru yau matar da take kalla a matsayin matsala yau ta sake waiwayarta,ta yarfa mata maganganu a gaban masu aiki da dukka hadiman gidan da sukayi tsaye suna mamakin jin bayanan maji. Tunda suke basu taba ganin gilmawar wata mace da sunan mahaifiya ce ga sir toufeeq ba,kowa yana kallon hajiya qarama ne a matsayin uwar kowa,hatta da Dr jarma. Ganin ta gagara bata hannun sai ita ta kamo nata hannun ta hade guri guda a sukayi musabahar,ta sake sakar mata murmushi tana cewa "Kada ki manta,har yanzu a mazaunin qanwata kike,saboda haka daga zamana zuwa fitata hukuncina zai iya hawa kan kowa,ciki harda ke a mazaunina na uwa ga dan da ake qarqashinsa yake bada ci da sha da suttura harda mafaka ga kowa,saina tabbatar da wanzuwar matar alkhairi a gareshi wadda zata kula da rayuwarsa sanann na sake barwa Allah shi amana,kamar yadda nayi tsahon rayuwarsa ta baya, alqawarin kuma Allah gaskiya ne,ya kulamin da su fiye da yadda zato yayi tsammani" sai ta zame hannun nata daga na hajiya qaraman,kai tsaye ta cusa kanta zuwa cikin gidan ba tare data nema jagoranci daga kowa ba. Wata iska me nauyi da zafi ta zuqa ta kuma fesar,me yake shirin faruwa? "Kada ki damu, kwanaki bakwai kawai zatayi idan ta dade ta koma inda ta fito,ta barki da yaran da take taqamar a kansu,ki kuma sake mantar dasu suna da wata uwa a duniya wai ita shifa har abada" wannan saqar da zuciyarta tayi mata ita ta kawo sassauci cikin ranta,sai ta juya cikin gida tabi bayan su maji din. Dole ne kamar kullum tayi amfani da kissa da kyau Cikin hararrami ta dinga bada umarnin kwashe kayansu maji zuwa dakunan da sajjad ya shirya musu,tun a ranar hajiya qarama taga wani irin banbanci muraran,wato shi tuwo dai ba'a taba canza masa suna,daga nadeeya har fadeela babu wanda ya yarda ya saki maji koda kuwa na minti daya ne,suna maqale da ita,bayan sun gama koke koken su,don koda wasa basu taba sanya ran zuwanta ba,nadeeyan rabonta da gain majin tun kafin ta tafi makaranta karatu,yanzu haka shekara kusan shida kenan dr jarma saidai ya bata haquri yace ba yanxu ba,shi ko toufeeq sai ya dauki zancan da gaske saiya shashantar dashi har kayanta ta taba hadawa da yace mata gobe ko jibi zai siya mata ticket tabi jirgi Zuwa Algeria,amma ranar data kirashi yana airport ma zai tashi zuwa dubai haka taci kukanta ta haqura. A yau din da taga majin sai takejin kamar duk duniya bata da sauran wata bugata,taci kukanta qwarai,amma yadda maji din ke kwantar mata da hankali tare da jaddada mata ta yiwa yaa moha uzuri sai ta samu relief. Duk wani shiga da fita na hajiya qaraman idanun maji na biye da ita,saidai kawai tayi murmushi ta girgiza kai,koda nadeeya ta tambayeta takance "B komai nadeeya, Allah yayi muku albarka,ya tsaremin ku" Tun kafin ya iso gidan labarin zuwanta ya riskeshi daga bakin nadeeya da kuma fadeela data rasa inda zata sanya ranta saboda murna,yau gata ga maji. Yana toilet cikin bathtub amma zuciyarsa na wani irin daka,yana jin doki da son haduwa da mahaifiyar da tayi silar kawoshi duniya,wadda rabonsa da ita shekara gome kenan cif,amma wani irin abu me kama da toro da shakkarta yana tasowa hadi da danne wancan dokin da yake ji. A qalla ya kusa kashe awa guda kafin ya garasa wankan ya fito,ya daur towel a qugunsa yasa qarami yana sharce ruwan dake kwance cikin gargasarsa data yiwa murdadden jikinsa ado. Cikin wani sassauqan yadi mara nauyi ya shirya,duk da ba wani zaman ado yayi ba amma kyansa ya fito ainun,rashin walwalarsa ta qaru a 'yan kwanakin saboda damuwar da dr da sailad sukeson jafeshi a cewarsa. Kamar yau din,bashi da niyyar fita amma hakanan ya fita bayan sajjad ya gama ce masa dangin amarya zasu zo su sake ajjiye wasu kayayyaki. Wani takaici yazo masa wuya ya tsaya masa.don me za'a dinga masa shige da fice a sashe?,bayan shi ya fadi cewa bayason dukka wadan nan abubuwan amma anqi sauraronsa. Hasalima shi sashensa ba gurin shigar kowa bane,wannan ya sanya dai dai da masu aiki kebantattu gareshi, su daya sai sajjad ke shiga masa guri. Baisan me yasa sajjad din be gyara spare part din dake gidan ba suje suyi koma meye a can,key din ya jefa masa ya tattara ya fita ko breakfast dinsa da Jacob ya hada bai tsaya yayi ba. Flip flops slippers masu taushi ya saka,wadanda suka bayyana sirrin fara tas din doguwar qafarsa,ya jefa wayarsa a aljihu yana fitowa. A falon suka hade da Jacob wanda yake sanye da afron "Welcome sir,the food is ready" a ga'ida ya zauna din yaci,to amma haka kawai yakejin bashi da nutsuwar hakan "Not now i will be back" daga haka ya Sanya kansa yana fita daga sashen nasa cikin takun nan nasa na nutsuwa da kamewa. Lokacin da muryarsa ta bada sautin sallama maji na zaune fadeela na saman gafafunta kamar zata koma cikinta,fadeela na tare dasu nawwara,houria hessa,minafah ,maysam,banaan,amjad,taraneem,tayma da saneem,kusan su sha biyar 'yan mata kamar nadeeva akazo dasu,sai manya masu dan shekaru kusan saannin maji,wasu kuma basu qarasa shekarunta ba suma sun kusa su takwas. Dukansu suna taya nadeeya shirya gifts da kayayyakin bikukuwan al'adar al'ummar gasar Algeria da maji ta shirya gabatarwa. Sarqoqi ne na wuya hannu da gafa na alfarma,dukkansu na gold,coins na gold da kuma wasu irin velvet gown tare,pakistani bride gown masu azabar kyau da tsada,wanda aka samar daga zare mafi tsada da kuma daraja,tare da wasu duwatsu masu tsada. Ga trousseau package dake dauke da dukka nau'in jewellery na gold da zatayi amfani dasu throughout bikin gaba daya. Kudi sosai marasa misali maii ta kashe, kamar yadda tayi gayya sosai ba tare da jin kudin jirgi ba,duk da kusan kowa shi ya yiwa kansa kudin jirgi,banda 'yammatan da tace suna wuyanta,family ne da sukayi suna a qasar,saboda sun hada komai malanta da kuma dukiya. Dakuna manya manya guda biyu masu girman gaske a wadace ya ishesu,aka zuba musu kuma dukka nau'in abinda zasu bugata bisa jagorancin baaba ramatu data kasa zaune ta kasa tsaye,takaicinta ya cika zuciyar hajiya garama,saidai babu damar yin magana ko wani motsi kada abinda ke lullube a zukata ya bayyana. Kusan babu wadda idanunta bai sauka a kansa ba cikin 'yammatan,zukatansu suka fara raurawa.wasu suka samu nasarar kau da kawunansu,wasu suka kasa,tamkar babu tsala tsalan mazan larabawa a Algeria. Kallon kallon suka yiwa juna shi da maji din,kowa a cikinsu zuciya na motsawa da wani irin yanayi,kewa da soyayyar d'a da mahaifi ta fara aikinta. Duk yadda maji taso daurewa saida qwalla ta cika idanunta,amma tayi namijin goqarin hanasu zubowa duk da basu koma ba. Ta tafi tabar moha din nata dan qanqani a gabanta da qananun shekaru,sai gashi yau ya bayyana a gabanta a matsayin magidanci harda d'iya. Nadeeya ce ta janye 'yanmatan suka fice bayan sun gama gaidashi,sunata daburtawa su sa nadeeya,ita bata qware a larabci ba,su kuma hausar tasu duka kame kame,kai tsaye ma idan kace basu iya ba bakayi kuskure ba. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 11 Wani irin mugun sanyi dukka qafatunsa sukayi,cikin nutsuwa yake takowa gabanta bayan ya sake jaddada sallamarsa kansa a qas,yana jinsa a matsayin wani gagarumin me laifi. Qoqarin zubewa yake a gabanta amma sai ta miga masa dukka hannayenta,baiyi jinkiri ba ya sanya nasa hannuwan a ciki,tayi masa mazauni a gefanta fuskarta dauke da murmushi me hade da hawaye "Kar kace komai,basai ka nemi gafarata ba,na riga nayi maka dukkan uzuri har a gaban Allah,na yafe maka kai da dukkan zuri'arka" majin ta fada tana dauke hawayen fuskarta lokacin da yake zaune a gabanta kansa a qasa har yanzu ya gaza cirashi,yana jin kan nashi yayi masa wani irin nauyi,kunya da nauyinta suna cikashi. Dai dai lokacin hajiya qarama ta hadiyi yawu da gyartaja da baya a hankali ta koma inda ta fito, zuciyarta na wani irin gonewa "Bani labarin yadda rayuwa ta kasance" ta fada tana sakin murmushi,abinda ya sanyashi daga kansa,ya sauke idanunsa cikin na mahaifiyarsa,wani siririn murmushi ya sauka saman miskilar fuskarsa. **********K'arfe biyu da rabi na ranar juma'a,babban masallacin juma ar dake iya daukar dubban jama'ar musulmai a wannan ranar a cushe yake da garin baqi daga qasashe daban daban da kuma garuruwan dake QASATA Nigeria domin halartar shaida daurin auren MUHAMMAD TAUFEEQ JARMA da amaryarsa KHADIJA MUHAMMAD GIREMA,bayan gama daura auren AFIFA AHMAD da MUHAMMAD SAJJAD a asalin garin mahaifinta da dr mamman yace lallai aje tushenta ayi don karramasu. Duk yadda takeso taii cikin ranta da jikinta cewa yau din ba wata rana bace ta daban da dukka sauran ranakunta na rayuwa ba,yau din sunanta amarya a karo na biyu dukka taron al'ummar dake gidan da masallacin sunzo ne don su shaida ta zama matar MT JARMA hakan ya faskara,tana gayawa kanta akasin hakan zuciyarta na jaddada mata qarya take fadi,a haka ta dinga jin rauni,raunin da yakai ga zubar hawaye a idanunta masu yawa da zafi. * MUHAMMAD TOUFEEO RESIDENT * Kai kawo takeyi cikin dakinta,wanda a qalla ta kusa awanni biyu cur tana yinsa ba tare data zauna ko kuma ta huta ba. Tashin hankalin da take ciki ya zarta duk yadda hankali zai iya dauka,ya kuma shafe tunanin me tunani. Asara mafi muni tare da faduwa muraran take gani a gabanta,a dai dai lokacin da tafi bugatarsa a dai dai lokacin da mummunar labarin shudewarsa ta sameta?,batasan haka zata faru da ita,batasan haka zata kasance ba,da babu shakka ba zata bashi baya har na tsahon shekarun nan ba. A nata ganin da hangen bugatarta ta biya,ya kuma tabbatar mata da cewa qulli me dan karen garfi da warwarewarsa ba'a nan kusa ba,nasara biyan bugata da cikar muradi suna ta zuwar mata fiye da yadda tayi zata,hakan ya sake bata qaimin bazama cikin duniya,taci gaba da rayuwarta ta kuma karbeta a yadda tazo mata tana moreta yadda ya kamata. Knocking qofarta a kayi,a mugun fusace take,don haka har ta buda baki zata tambaya cikin zafi,sai kuma ta tuna,a yanzu gidan yana cikin yanayin da bai kamata ta bari aga alamun matsala ko wata damuwa a tattare da ita ba,wanann yasa ta furzar da iska sannan tayo tattaki ta bude qofar. Hajiya mansura ce,ita da hajiya qaraman sukayiwa juna kallon kallo,duk mutumin da ya sansu a shekarun baya,a yanzu idan yaga kallon da sukewa juna zai garyata hakan,duba daya kacal zaka yi musu ka tabbatar da abubuwa masu yawa dake qunshe a zukatansu. Abubuwa biyu itama ke neman zame mata barazana,labiba dake neman zauce mata saboda auren toufeeq,ga kuma saukar shifa a nigeria,labari mafi muni ga kunnuwanta. Abune da bata taba kawoshi ga ranta ba,saboda tana da tabbaci daga gurin masu bata tabbaci. ..ita da Nigerian har abada,tamkar yadda jinjiri yake barin cikin mahaifiyarsa. Ita kadai tasan abinda take gani take kuma karanta daga gurin Dr jarma,bai cancanci shifa ta shigo Nigeria ba ma sam a irin wannan lokacin "Amarya na dab da shigowa cikin gidan nan,ya kamata a ajiye zafin rashi ko ayi abinda ya dace" sarai ta fahimci mansurar magana take danqara mata,amma sai ta sake mata wani murmushi,saboda ta tabbatar tana wasa ne kawai da wuta me tsananin ruruwa da azabar turiri cikin rashin sani,tayi imani bata gama sanin ita din wacece ba,da tabbas! batayi wasa da ita har haka ba,saidai kuma zata dandana kalarta ta ainihi, wala'alla a nan gaba kome irin sunanta ta gani da gudu zata gusa daga wajen "Karki wani damu,dama ni nafi cancanta da karbar matar toufeeg" hajiya qarama ta amsawa mansura. Ciki ta juya tana duban suturar jikinta. Girman kanta ne ya motsa,taji tafi gaban fita haka,don haka ta bude makekiyar closet dinta ta fara laluben suturar alfarma. llahirin jikinta lullube yake da wata irin suttura da aka yiwa dinki na mussamman da lafiyayyen yadin silki me tsananin tsada da daukar hankali,sannan akabi adon doguwar rigar silk din da wata rigar me zubin alkyabba ta baqin yadin velvet me adon zaren da aka tsomashi cikin ruwan gold. Tun daga nesan nesa da ita hancinka yana iya jiye maka kwantaccen qamshi me tafiya da tunani da takeyi,ba abinda ke fita daga jikinta sai wani irin haske da walwali ke kashe idanu. Babu abinda ake iya gani a jikinta,sakamakon yanayin shigartata daya rufe ko ina nata ruf,rufewar data bata damar yin kuka me yawan gaske ta qasan hular rigar da aka Tullubeta da ita. Ba abinda ke mata yawo a tsakiyar kanta sai nasihar Dr girema,maama yaa muhyi yaa Saifullahi da yaa zaid,da kuma shaqigan 'yan uwa sannan masoya irinsu anty farheen anty samreen. Can cikin jikinta take jin wani yanayi me kashe zuciya, maganganun da sukayi mata sun shiga jikinta sun kashe duk wani karsashi da rashin damuwa da auren,sun dora mata nauyi me yawa, kalaman da suka furta a gareta,banda tana da aminci da afifa zata ce tabbas ta gaya musu manufarta a auren. Ido ta lumshe tana jin wata matsananciyar fargaba lokacin dajerin gwanon lafiyayyun motocin dasuka daukota suka fara cusa kai cikin gidan,a baya qaddara ta sanya ta shigo gidan a sunan nanny,a yanzu a karo na biyu qaddarar ta sake dawo da ita d sunan matar aure kuma matar me gidan,abinda ko kadan bata taba tunanin faruwarsa ba. Wani irin yanayi taji yana bin sassan jikinta lokacin da hannunta ya game da na hajiya qarama da ta karbeta daga hannun yakura yayar Dr girema,zuciyarta ta motsu lokaci guda. Haka kawai takeiin matar kwata kwata bata kwanta mata ba ko kadan. Saidai har suka doshi sassan da ita kanta sãahar batasan wanne bane saboda kanta na lullube tana iya tsintar muryarta fes tana sake marabtar danginta "Maji tace a wuce da ita sashenta ta huta,ita 'yar gida ce a gurinta basai an bata wahala ba,kuma ko yaushe zasu kasance tare" sagon da baaba ramatu ta matso ta shaidawa hajiya garama kenan qasa qasa. Kai ta jinjina,a gasan ranta zuciyarta tana bata tabbas akwai dalilin da yasa shifa ta aikata hakan,amma koma meye har yanzu sauran akaloli suna hannunta,kuma ita zata ci daga da yin nasar kamar yadda tayi a baya. Tunda ta tsoma gafarta a sashen jikinta da hancinta ta TABBATAR mata wani guri ne daya banbanta da kowanne sashe na gidan,guri ne me tsari da koda idanunta suna a lullube amma hakan bai hanata ganin lallausan carfet dan gasar turkey da qafafunta ke nutsewa a ciki ba. Qamshin da wajen ke fiddawa kawai ya isa ya saukarwa da zuciya tare da ruhi salaama,uwa uba dukka hayaniyar gidan sam sam babu ita a nan,bisa alama ma sun baro mutanen dake dauke da hayaniyar a can baya,sai wani irin shuru da sautin muryoyin da basu wuce biyar zuwa shida ba dake magana da sauti mara hayaniya. Bata gushe ba tana biye da hajiya qarama dake ci gaba da cusa Kai zuwa hallway din da dakunan baccin sashen suke a jere,wanda aka sake narka kudi aka masa mugun gyara na fitar hayyaci,duk kuwa sa cewa babu abinda ya sameshi, amma a yanzun an masa gyaran da zai dace da rayuwar maaurata. Zuciyarta dake qirjinta takejin kamar ana hurawa wuta saboda ruwan kudin da taga toufeeq din ya barnatarwa gurin,bayan ta samu dukkan bayanai da huijoji masu qarfi daje bayyana mata cewa ba auren soyayya yayi ba,auren sadaukarwa ne ga diyarsa fadeela,a qalla tafi shekara goma batasha maganin hawan jininta ba,amma a yau batajin zata iya kwana ba tare da tasha din ba. Wasi wasi yaso cika zuciyarta taf,tunda suke mata aiki tsahon shekarun basu taba kawo mata labarin da ba haka yake ba,amma a yau ta shiga tantama,yadda taga komai ya canza,tayi imanin muddin babu son ron taoufeeq bata zaton akwai wanda ya isa ya sakashi yiwa bangaren irin wanna tsarin da kowa zaiyi burin kasancewarsa a ciki. Bata fahimci cewa babu kowa a tare da ita ba sai bayan shudewar mintuna goma da sumaira ta shigo tana gaya mata yaa Saifullahi ya bada dokar kada wanda ya zauna. Hannun sumaira ta riqe da kyau,qwalla na sauko mata. A irin wannan gigitaccen yanayin da take ciki inama acw afifanta tana kusa da ita? itace qwarin gwiwarta,saidai kuma inaaa,zagin soyayya ya sanya dukkan wani qarfi nasa ya nesantata da afifan,tana can itama domin fuskantar sabuwar rayuwa, rayuwar da säahar ke mata fatan ta zama me tsananin zaqi,ba me daci ba kamar yadda ta fuskanci tata. Bude gofar da taji alamun anyi a karo na biyu ya sanyata kasa kunne. A nutse take takowa zuwa cikin dakin, idanunta akan rufaffiyar fuskar sãahar,zuciya nata yi mata saqe saqen abubuwan da zata iya aiwatarwa a kanta,saidai duk abinda zuciyar ke gaya mata tana ganin bai dace da ya faru a wannan muhallin ba,a kuma dai dai wannan lokacin ba. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 12 Gyaran murya ta danyi,idanunta akan sãahar tana sake takowa kusa da da ita,daga gefan lallausar sofa bed ta zauna tana dubanta da kyau "Maraba da shigowa mahmud JARMA family,na tayaki murna qwarai bisa samun wannan nasara da kikayi,sannan kuma ina miki alhinin cewa....nasararki zata kasance ta gajeran zango ce,sakamakon toufeeq ba mallakinki bane,dukka tsahon rainon da nayi masa,na raineshi ne don ya zama mallakina,wato mallakin 'vata meenal haseena" wani dan banzan haushi maganar hajiya qarama ta saukar a zuciyarta,tayi qoqarin tsaida hawayenta tana son fahimtar abinda matar take fadi, idanunta na kallon tafukan hannayenta ba tare data yaye rufin kanta ba "Na jinjina miki yadda kika shirya komai ya kuma tabbata lokaci kadan bayan tafiyata,to amma ki sani,sauyawarki daga sunan nanny boyi boyi zuwa ga matar auren toufeeq babu abinda zai canza daga dokoki da tsare tsaren gidan nan,fatan da nake miki ki iya kiyayewa,sannan ki jirayi sakamakon da zai biyo baya nan da kwanaki bakwai masu zuwa,batun jikata fadeela,banason ki fiya zaqewa cikin lamuranta saboda shine samun lafiyarki,kiji kigi ji ki gani kigi gani,na barki lafiya,asha amarci lafiya" tana kaiwa nan ta mige,saidai taku uku kacal tayi sãahar da zuciyarta ke a dugunzume ta gaza daurewa kalaman hajiya qaramar,ta tunzura qwarai,itama irinsa ce kenan? me tarin Izza taqama da izgili,ashe ga inda ya debo dabi'arsa,lallai akwai wani boyayyen abu cikin taku da rayuwar matar cikin gidan,jikinta da zuciyarta sun gama aminta da hakan,adam ya yiwa rayuwa ruhi zuciya da gangar jikinta mugun horon da yasa nan da nan take iya fahimtar wani abu daga wasu mutane da dama. "Inda kinsan abinda ke qasan zuciyata da baki bata bakinki kina wannan b'ab'atun ba.don haka na roqeki ki kama girmanki,zan nanata miki tun a daren farko na cikin gidan nan saboda daga ke har shi ba zamanku nazo yi ba" zallar madarar mamaki ya saukar mata.wani abu yayi mata tsawa a kanta,ta waiwayo tana son tabbatar da abinda kunnuwanta suke jiye mata,sai sukayi idanu hudu da saahar data dage hular kanta,wanda hakan ya bawa kyakkyawar fuskarta data sake wani sassanyan kyau saboda gyara data ci kamar babu gobe,da kuma haske da annurin AMARCI dake sauka a fuska da jikin kowacce diya mace data amsa wannan sunan. Kamar ko yaushe yanzun ma kwarjini tayi mata,amma hakan bai hana hajiya qarama ritsata da ido ba,tana mamakin qarfin halin yarinyar. Tabbas dole ta shiga cikin mutanen da take targeting,ta yiwa kanta wannan alqawarin,sai ta gyada kanta ta juya ta fice a hankali daga dakin. Qaramin tsaki säahar ta sauke bataii zata zauna matar ta sanya mata wata damuwa,ita sam bata cikin damuwarta bare tace zata takura mata,ba ita ba,koda shi kansa toufeeg din ba zata yarda ya zamar mata damuwa ba bare wata ganwar mahaifi data fuskanci zuciyarta akwai ayar tambaya. Ta jima zaune a gurin tana saga da warwarar yadda zata tafi da rayuwarta cikin gidan,zata bawa kowa girma,amma sam ba zata dauki raini cin zarafi ko cin fuska ba. A yadda taji gidan ya fara shuru ya tabbatar mata dare ya fara yi,sai ta dubi agogon dake jikin bangon dakin nata,fitsari takeji sosai hakanan ta tabbatar wadan nan kayan jikin nata ba zasu barta sakewa ba,don haka ta miqe ta zare rigar saman,tanar doguwar rigar wadda ta fidda shape dinta qwarai da gaske,tun daga girji zuwa qugunta,ta tattareta ta nufi qofar da take tunani bandaki ce da zummar idan ta fito tasan yadda zatayi ta raba kanta da rigar itama yadda zatafi jin dadin kwanciya. Ya kusa mintuna talatin zaune cikin motar tasa bayan fitowarsa daga gurin maji,a yau addu'o'in da yasha a bakinta zai iya cewa bai taba jin makamantasu ba daga bakinta.farincikin da ya gani kwance a fuskarta ya taba zuciyarsa,duk yadda yake zaton ta dauki auren ya wuce nan,ta mashi wani babban matsayi da yayi imanin ba nan kusa ta ajiyeshi ba. Motar na a kunne ac naci gaba da aikinta,hakanan fitilun cikin motar. Sanye yake da wani baqin yadi da aka yiwa dinki tamkar na buzaven qasar nijer,dinkin ya zauna matuqa da gaske a jikinsa, kamar yadda baqin yadda ya kwantawa farar fatarsa ya sake fidda ainihin haske da kyanta tare da bayyana zallar hutu da in dadi hadi da kulawar da take samu,bagar sumarsa ta ainihin halfcast na nannade saman kansa tana bada wani sheqi me kyau da sassanyan gamshi kamar ko yaushe. Waiwayawa yayi a nutse ya kalli tarin ledojin alfarma dake gefansa,wanda duka maji ce ta bashi tace ya shiga gurin iyalinsa dashi,don shi babu abinda ya riqo a hannunsa,duk da yanajin sanda abokansu ke hadawa sajjad,sunyi la'akari da cewa shi din tsohon aure ne,sunsan zai tanadi abinda ya kamata ba sai an gaya masa ba. Su kansu kayan qarin nauyi ne a wajensa,don ya tabbatar tilas ya sadasu da wadda aka siya saboda ita kodon cika kima da martabar maji. Sashen nasa ya sake saukewa idanunsa a karo na barkatai,sam baya gaunar shiga sai don babu yadda zaiyi,a duk sanda ya tuna cewa akwai wata mace a ciki me amsa sunan matarsa duk sai yaji kamar dai an takureshi ne kawai. A karo na gaba da qarfi yaja tsakin hadi da balle murfin motar a zafafe ya fito,jibril dake jingine jikin motar ya qaraso da sauri,kafin yace komai toufeeq din ya rigashi magantuwa "Ka gayawa Jacob ya shigomin da kayan cikin falo, ka kashe motar na sallameka,sai kuma da safe" "Sir,da safe kuma? na dauka zakaje hutu ko?, ko don madam" jibril din ya fada zuciya daya yana murmushi,saidai kallon da toufeeq din yayi masa ya tabbatar ya tafka baranbarama,sai yayi saurin jan bakinsa ya tsuke yana yunqurin bude daya side din ya fiddo kayan kamar yadda ya umarta. Hannayensa zube a aljihun wandonsa yake qarewa falon kallo,ya sake jan qaramin tsaki, komai nashi sajjad ya canza masa,duk da kyawun da sassan ya qara ya kuma zuna favourite colours dinsa,to amma shikam bai shiryawa dukka wadan nan abubuwan ba. Da kansa ya gaji da tsaiwa,ya sunkuya ya kwashe kayan da jacob ya shigo masa da su,ya nufi hallway din da zai sadashi da dakunan baccinsu,ransa yana sake baci,komai a yanzun sai yayi sharing da wani,gurin mallakinsa ne a baya,shi daya yake shiga yayi rayuwarsa,idan zao shekara bai fito ba motsin kowa bazai dameshi ba,amma a yanxun bashi da wannan tabbacin. Tsaye tayi a gaban madubi bayan fitowarta daga toilet din tana kallon fuskarta data fito sosai saboda qananun kitson da aka zauna aka yarfawa gashinta me santsi,abinda zata iva cewa tsahon rayuwarta ba zatace ga lokacin da irin hakan ta faru ba,hasalima kwata kwata kitsonta baya wuce manyan kalba guda hudu,saboda tsaho da santsin gashinta, amma a yanzun an samu wata gwana jarababbiyar iya kama gashi ta kitse mata kan tsaf,kuma hakan ba qaramin qarawa fuskarta kyau yayi ba,jelolin kitson gaba daya sun kwanta sosai a gadon bayanta har tsakiyar bayan nata. Hannu ta sanya tana qogarin zuge zip din rigarta wanda afifa ce dama ta zuge matan,da qyar hannun nata yakai,ta fara jan zip din ya fara saukowa,har yakai rabi taji an taba qofar,saita tsaya cak tana kallon madubi dake haska mata bakin gofa,tanason tantance qofar dakin nata aka taba ko kuma sauran qofofin dake wajen. A hankali qofar ta bude,ya bayyana daga bakin qofar da daurarriyar fuskar nan tasa,tashin farko qamshin da dakin ke fiddawa ya marabci hancinsa kafin a sannu idanunsa su suka a bayanta da fara qal don brassiere dinta ta bayyana. Sosai ta razana don batayi tunanin ganinsa ba wannan lokacin,tunawa tayi da zugaggen zip dinta data tabbatar a vadda ya sauka har brassiere dinta za'a iya gani,wanann tunanin ya sanyata juyawa da sauri kamar numfashinta zai dauke ba tare data tuna yadda rigar ta fidda tudun qirjinta ba da kyau. Kamar daukewar majigin tv,gushewar baya zuwa bayyanar qirjinta ga idanunsa duka sun faru cikin abinda baiyi damanda second uku ba,bazaice ga yadda akay ba ya samu idanunsa dumu dumu suna kallon qirjin nata ba da suke a cike,farar fatar dake lullube ko ta ina ta jikinta ta bayyana daga samansu tana nuna mizanin cika da suke da ita. Wani mugun fusga ya yiwa numfashinsa da idanun nasa ma gaba daya yana sanya qarfin zuciya dana ruhi gurin janye kallonsa daga kanta. Yayin da sãahar din gaba daya ta qarasa rudewa,ta fisgi dankwalinta dake ajjiye saman madubin ta yafa ranta a bace. Tamkar baiga komai ba ya sanya kansa cikin dakin yana furta sallama can qasa,kanshi tsaye yake takowa dakin tamkar dai mallakinsa bawai nata ba,bai tsaya ba har sai da ya isa kusa da bedside drawer ya zube dukka ledojin a kai ba tare da ya dauki ko daya ba,sannan ya juya abinsa zai fice daga dakin. Kasa jurewa tayi,tadan daga muryarta kadan "Ba kowanne daki bane mallakinka a yanzu,kafin shiga kowanne daki a gidan nan ya zama dole ka nema izini" tsaiwar mashi maganar tayi masa bisa kansa,har ya rage saurin tafiyar tasa,sai kuma yaci gaba da ficewar,saboda wata kasala dake sauka a kowanne sashe na jikinsa,muddin kuma yace zai tsaya cewa wani abu,a matsayinta na me aure na biyu dole zata fuskanci wani sauyi tattare dashi, wanda hakan mugun abun kunya kasawa da kuma gazawace a tattare dashi but yayi alqawarin zai saita mata bakinta da wasu dabi'u nata,bazai yarda da rashin girmamawa ba,she can live duk yadda taso,amma dole tasan girmansa. Tsuka tayi ta murguda bakinta saboda baqincikin da ya cikata,batasan tsautsayin da ya sanyata barin qofarta a bude ba,bata taba kawowa wai zai shigo ba wannan shine dalili,amma dole daga wannan karon ta tabbatar bai sake shiga mata daki ba. Har tayi banza da ledojin daya shigo dasu,sai kuma taga duk abinda ta bari ya lalace zai shiga sahu ne na almubazzaranci. Short note din data gani jikin wata leda ya bata tabbacin babu abinda ya siya da kansa ko daya,dukka sagon maji ne. Murmushi ya subuce mata,tana qaunar mata sosai har cikin ranta,sonta majin take da gaske har hakan baya iya boyuwa,ta miqe ta adana komai ta dawo ta rage kayan jikinta ta kwanta. "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI_* Book 02Page 13 Cikin nutsuwarsa ya gama komai na shirin bacci,saidai gaba days baccin ya gagara zuwa a idanunsa,ganin dazun yayi affecting tunaninsa sosai,abinda bai taba kawowa cikin ransa zai zama wani abu har haka ba. Da kansa ya buda qofar dakinsa ya wuce kitchen ya hada coffee ba tare daya bi takan abincin dake jere a dining ba,aikin jacob kenan, baya wasa da aikinsa,duk wata hidima da ake muddin yana qasar yana kuma gari baya fashin dafa masa abinci,ko a yanzun duk hidimar da akeyi cikin gidan part dinsa baisan anayi ba,shi yasa yakeji da jacob din shi da wanda yake tsaftace masa sashensa.basu da wasa sam a aikinsu Dakinsa ya dawo,ya buda balcony din dake manne dashi,duk da cewar dare ne amma bai damu da hakan ba,bacci kawai yake nemawa idanunsa tare da hutu da nutsuwar ruhi da gangar jiki. Kurba daya yayi masa kamar lokutan baya ya ajjiye saman dan qaramin table din dake a gefansa,tun daga waccan ranar daya dandani taste din coffe dinta kowanne ya daina masa dadi a harshensa,saidai yasha Black tea Kawaltunda bava snan madara kwata kwata,ko ya gwada shan madaran da nufin ko zai yi masa irin taste din milk tea dinta sai yaji gaba daya basu hada hanya ba. Tafin hannayensa ya hada yana murzawa guri guda da sauri da sauri,lokaci guda ya dakata yana furzar da iska daga bakinsa,dai dai lokacin da wayarsa tayi qara. Mamakin wanda zai kirashi a dai dai wannan lokacin da sha daya na dare tayi ya kamashi,ya qarasa inda ya aje wayar a hankali ya dauka yana duba me kiran,sai kuma kiran ya katse,sagon da ya gani da number sajjad yaja hankalinsa,yayi sliding ya bude wayar ya shiga saqon _Duk wani nutsuwa farinciki walwala da kwanciyar hankali yana tattare da diya mace muddin ka dace,ka raya darenka na yau da kyau da soyayya da kawo jituwa da fahimtar juna tsakaninka da iyalinka,zaka fahimci inda maganata ta dosa_ tsaki yaja,sajjad yana bashi ciwon kai,baisan mata bane,amma yana da tabbacin zai dawo daga mararin gardin da yake ganin ya samu. Muddin diya macace tabbas wataran sai ta bashi madacin da zai maye gurbin zaqin zumar data lasa masa a harshensa,duk kuwa da cewa baya taba yiwa wani wannan fatan bare sajjad din da dadi wuya ko tsananin yana tsaye tare dashi. Kira ne ya shigo wayar tasa lokacin da kwanyarsa ke shirin nutsawa duniyar tunani. A nutse ya dauki wayar ba tare da tantama shakka ko mamakin kiran da akayi masan a dai dai wannan lokacin ba,saboda waya ce da dukka kiran da zai biyo ta cikinta ya tabbatar kira ne me muhimmanci da ya shafi duk wani makusanci a gareshi. Cikin lallausar muryarsa da ta gara yin wani irin sanyi saboda yanayin da yakeji yana bibiyar kowace gaba ta jikinsa. Saidai a maimakon amsar sallamar,sai sautin kukanta cikin siriryar muryartan me matugar siranta qwaral ta maye gurbi. Wayar yadan cira yana duba number din ya tabbatar babu wanda zai kirashi da number wannan qasar sai mutum daya wato HASEENA "Yaa toufeeq wai da gaske ne?,da gaske ne don Allah?, kayi aure?" Tambayar tata ta daure masa kai,meye manufar wannan tambayar? duk da ya jima zuciyarsa da hasashensa suna son kaishi gurin,amma sai ya jaddadawa kansa ba hakan bane,saboda sam baya fatan yarinyar ta jefa kanta shingen da bazata iya samun aminci ba a cikinsa "Yaa toufeeq,wallahi bazan iya jurewa ba,yaa toufeeq kai na yiwa zuciya tanadi,dukka tsahon shekarun nan,mommy ce takeyimin burki" sai ta sake sakin kukan da yake nuna ciwone daga zuciyarta na gasken gaske yake motsawa. Mamaki gaba daya ya sanyashi kasa cewa komai, yarinyar da yake kallonta bata da maraba da nadeeya a gurinsa saboda rainonsu da hajiya qaraman tayi? ‚bugu da qari sam babu hira da tayi kamanceceniya da wannan a tsakaninsa da ita "Relax meenal,calm down" ya fada ta sigar lallashi,saboda gaba daya abun nata yana daukarsa ne kamar wani wasan kwaikwayo "Ta yaya zan iya kwantar da hankalina yaa toufeeq,kasan yadda kake a zuciyata?" "Are you okay?" Ya samu kansa da tambayarta kai tsaye wannan karon,saboda gaba daya mamaki ya gama cikashi "I lost what i love most,i can't keep calm" "Kisha magani ki kwanta,Allah ya sawwaqe" ya fadi yana sauke wayar a nutse daga kunnensa. Kafin ya kashe yana iya jin yadda take kiran sunansa,ya sake kallon wayar yana sake tabbatarwa kansa kodai akwai abinda tasha,ko kuma lallai dole ya dauki tsattsauran mataki a kanta,muddin dai meenal zata ce tana sonsa,to ba shakka raini ya fara shiga tsakaninsu kenan saboda yadda yake treating nata like nadeeya. Qarar shigowar tex ya sake sanyashi waiwayawa ga wayar. Dukka saqon ya gama bayyana saman screen din, kasancewarsa gajeran sago bame tsayi ba BARKA DA WARHAKA ANGON NANA KHADIJA,KA MOREWA WANNAN DAREN TARE D AMARYARKA,AMMA KA SANI AMEESHA NA NAN DAWOWA CIKIN RAYUWARKA,SABODA BA ZATA IYA BARWA WATA KAI BA HAVE A NICE NIGHT_ Samun kansa yayi da maimaita karanta saqon,a hankali a hankali wani abu me zafi yana taba zuciyarsa, emotions dinsa marasa dadi sunason motsawa,how and when ameesha ta samu wannan courage din da zata masa saqo haka kai tsaye?,saboda ya daga mata qafa? ya bata damar taje ta rayu ta tuba?. Har ya dauki wayarsa da zummar nusar da ita kuskurenta,sai kalmar "La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" ta subuce daga harshensa. A hankali yaji yana komawa daidai dinsa,sai ya maida akalarsa zuwa blocking number tata,sannan ya goge saqon,ya jefa wayar a aljihunsa yana migewa daga gurin,yana ji a zuciyarsa bashi da lokacinta Sam,bama yanzu ba,har abada baya jin zata sake samun lokacinsa,bawai ita kadai ba,dukka wata diya mace ma idan ka debe jininsa dinnan daya zama lazim ya rayu dasu,yake kuma da yaqinin babu cutarwa a tsakaninsu har abada. Cikin wani yanayi yake fita dag balcony din har ya riski lafiyayyen bedroom din nasa,cikin qanqanin lokaci ya gama shirin kwanciya,ya maida hasken dakin zuwa dim light,idanunsa na lumshe yana jin kewar rashi ganin fadeela saboda cinkoson gidan,yau din tun sassafe da ya fita yabar musu gidan,duk da sashen nasa baisan me cikin gidan ke ciki ba,amma sai yakejin kamar hayaniyar gidan a tsakiyar kansa take. Bacci yake da bugatar yi sosai,to amma yanayin da yake ciki ya tabbatar idan baiyi wasa ba zaici wuya ko ya dade a haka,wannan ya sanya yana daga kwancen ya miqa hannunsa ya jawo wata mp4 me siffar qwallo fara qal ya kunnata,take sautin karatun alqur ani me girma ya karade dakin da muryar sheik mahir almu'aiqaly,karatun ya fara saukar masa da nutsuwa sosai a zuciya ruhi dama gangar jikinsa,sannu a hankali baccin da bai taba zata ba yayi awon gaba dashi. _sai muce asuba ta gari angon nana kadija_ **********A nutse ta ajiye wayarta data gama karatun qur'ani ta ciki saboda rashin hado mata da qur'aninta da ba'a yiba ta mige tana kallon agogon dake manne a bangon dakin daidai algiblar sallarta. Qarfe shida da mintuna talatin,tana da buqatar ruwan dumin da ta saba sha a kowacce safiya,bata qaunar fita sam sam saboda batason koda tsautsayi yasa su hadu dashi,duk da bata tunanin a dai dai wannan lokacin akwai wanda ya farka cikin gidan. A nutse ta ninke abun sallar tayi masa guri,sannan ta zura lausasan slippers din da suke set da kayan jikinta,wanda couple prayer set ne,ta zari nata ta saka. Blur black ne masu taushi,kala ce ta farare, don haka ta fidda hasken fatarta da kyau wani irin haske dake cakude da amarci da kuma zallar gyaran da tasha daga hannun me gyaran jikin da maii ta ajjiye mata. Duk yadda taso dauke idanunta daga kallon yadda aka tsara hallway din hakan ya gagareta. Wani irin kyakkyawan tsari aka yiwa gurin wanda hatta weather da qamshin da yanayin iskar dake kai kawo a gurin na musamman ne. Fitilunsa na musamman, kamar yadda kome da akayi amfani dashi wajen qawata gurin ya zama favourite colour dinta ne,zaka rantse da Allah ita ta zauna ta rubuta yadda takeson a shirya komai din. Qafafunta na nutsewa sosai cikin Tallausan carfet din da aka malale gun dashi har zuwa sanda ta sada kanta da falon. Hallway din yafi burgeta, amma kuma yadda falon ya tsaru da wasu irin kujeru curtains da carfet carfet sai ta rasa wanne guri ne yafi wani?,nan dinma komai dake dake cikinsa zabin kalolinta ne,kamar tana gurin aka shirya komai. Duk qoqarinta da son ganin abun sam bai burgeta ba hakan ya faskara,ta dinga ratsa falon tana laluben inda kitchen yake,lallausan qamshi me kwantar da zukata yana yawo a hancinta har zuwa zuciyarta. Bata jima ba ta hangi hanyar da zata sadata da falon wanda ke daura da waje na musamman da aka tanada aka kuma qawatashi da dining na alfarma. Bata fahimci da mutum a ciki ba saboda girman kitchen din har sai data kammala shiga "Good morning madam" jacob daketa aikin kintsa kitchen din don shirya abinci na musamman da zai burge matar ogansa ya fadi a ladabce. Turus ta danyi tana dubansa, ya afron da zungureriyar hular kansa kadai ta isa yi mata bayanin waye shi,saidai duk da hakan baiyi qasa a gwiwa ba wajen gabatar mata da kansa "'Sunana Jacob,nine cook din sir,akwai wani abu da kike bugata ne yanzu?" Mamaki ya saukar mata,shi komai nasa ya banbanta dana kowa?,ya kawo qatoton gardi kuma arne ya ajjiye cikin gidansa yana dafa masa abinci yana ci?, iyakacin zamanta a gidan ma bata taba ganinsa ba,ko don ita din bata fiya zurfafa kanta a lamuran da basu shafeta bane?. Ta yaya zata zauna itakam wannan qaton yana mata girki tana ci?. "Bana buqatar komai, just warm water zan diba,and i can handle it" ta furta tana matsawa sashen da aka jere glass mug cikin tsafta da burgewa ta cire guda daya,ta taka a hankali ta isa ga dispenser ta debi ruwan. Saidai yayi mata zafi da yawa,batason kuma sirkashi, wannan ya sanya ta jingina bayanta da kitchen cabinet tana motsa ruwan a hankali,tana so ya rage zafi tasha tabar masa cup din a wajen. Cikin kamewa tare da tarin nutsuwar da sallar asuba ke haifarwa ga zuciya da ruhin kowanne musulmi yayi sallama a kitchen din. Wannan al'adarsa ce,yakan manta da cewa jacob ba musulmi bane,shima Jacob din tsabar sabo da hakan ya sanyashi ya koyi cikakkiyar amsa sallama. Lallausar muryarsa da bacci yasa ta qara zama husky and deep voice ta ratsa kunnuwanta,idanunsa ya fara sauka a kanta,zagayayyar fuskarta dake tsakiyar hijabi tayi fayau da wani irin haske. Zare idanun nasa yayi daga kanta yaci gaba da takowa ciki a hankali, daura da ita ya tsaya shima yana daukar glass mug din ba tare daya sake duban sashen da take ba "Good morning sir" jacob ya gaidashi cikin tsantsar girmama "Morning Jacob" "Kana bugatar wani abune sir?" "Warm water" shima ya fadi a taqaice yana sake cirar spoon bayan mug din. Wani mugun kusa taji sunyi ita dashi, duk da kuwa akwai tazara a tsakaninsu,yadda ya ganta a jiya ke dawo mata fes cikin kanta,a hankali haushinsa ya soma sauka saman zuciyarta,tanason ta matsa daga gurin amma ta gaza,wani irin kwarjininsa da bata taba ji ba ya mamayeta. Ta lumshe ido tana kai cup din bakinta duk cikin son nuna bata ganshi a kitchen din ba gaba daya,gefe guda na zuciyarta yana mata bitar abinda afifa ta taba gaya mata "Aure yana da wata irin daraja,yana garawa namiji kwarjini a idanun macen daya aura din albarkacin wanann igiyoyin guda uku, kibi a sannu bestie, toufeeq ba irin kalar mazan kike kalla bane ba irin adam bane,yadda banbaci da tazara yake a bayyane muraran tsakanin sama da qasa,haka yake tsakanin adamu da toufeed" a lokacin tsaki taja,akwai abinda take son saurara amma gaba daya afifa ta hanata sakat,motsi kadan ta fara mata wa'azin aure "Kina tsammanin don kawai ya biya sadakina sai yayimin kwarjini afifa?" "Bestie" bata barta ta gama magana ta dakatar da ita "Bestie, idan akwai mutumin da ya cancani a duniva nayi masa kara na aureshi ma to mahmud ne,amma saboda har yanzun zucivata bataii akwai wani amintaccen namiji a duniya ba na gwammace na kawoshi,izzarsa dagawa da tsantsar jin kansa ba zasu taba razanani ba,zai kuma ci gaba da tabbata ne a mijin AUREN MANUFA, yayi rayuwarsa nima nayi irin rayuwar da nakeso" a lokacin murmushi afifa tayi ta miqe tana cewa "Ba zaki gane ba" "Ke kai ba zaki taba ganewa ba". *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 14 Lokacin da yake amsar ruwan dumin daga hannun Jacob sai ta juya tana fita a kitchen din. Bai waiwaya ya dubeta ba,amma yana iya tsinkayar adadin takunta har zuwa sanda ta kammala fita. Zare cup din yayi daga bakinsa yana jin zuciyarsa na motsuwa da abinda tayi. Idan abaya shi din bai hada komai da ita ba,a yanzun musulunci ya danqa masa igiyoyi ukunta bayan an zarga mata su aka bashi ragamarta,ko ba komai a yanzun akwai suna me girma nashi a kanta wato MIJI, zai dauki kuwa wannan dabi'ar?,a gaban wadanda ke martabashi tare da ganin girmansa?. "He deserve respect from her" ya gayawa kansa yana jin gamsuwa da hakan har qasan ransa. Saman sofa bed ta yiwa kanta mazauni tana kurbar ruwan dumin nata a nutse,bangarori biyu na zuciyarta kowanne akwai sagon da yake qoqarin kai mata. Sashe guda na zuciyarta na gaya mata rashin dacewar abinda tayi na wuceshi ba tare data gaidashi ba,saboda hakan sam baya cikin tarbiyyar gidansu. Fuska ta yamutse tanason amintar da kanta rashin aibun abinda ta aikata din. Gefe guda na zuciyarta na hasaso mata yadda ya shigo da wanann murtukakkiyar miskilar fuskar tasa,tana iya tuna yadda yake takowa da jin izzar nan tasa,sannan kuma ya dauke kansa tamkar baisan tana a kitchen din ba. Tsaki taja ta dire cup din abinta,bata jin tayi ba dai dai ba,don har abada ba zata dauki duk wani izza tasa da tsarinsa ba,don aure sukayi na yarjejeniya da biyan buqatar kowannensu,ba batun boos ko oga. Kiran da ya shigo wayarta ya dauki hankalinta,mamaki sosai ya cikata sanda taga sunan anty farheen,sai ta nutsu da kyau tana amsa kiran tare da fatan jin lafiya?. A galla akwa biyu suka kashe suna maganata cikin wayar,sanda sukayi sallama jikinta a sanyaye ta ajjiye wayar a gefanta,tabbas wannan dai tasan agenda ce afifa ta shirya mata,don dukka maganganun da anty sukayi da anty farheen din sai tga sunayi mata kama da mutumin da yasan AUREN MAFAKA tayi. Duban lokaci ta sakeyi bayan ta gaji da zaman tunanun,ta shafa cikinta plate tummy dinta da babu komai a ciki sai ruwan dumin dazu rabonta data zauna taci cikakken abinci har ta manta,tana ta kasa kunne taji motsin fadde ko nadeeya amma shuru,sai ta mige da mug din don maidashi kitchen ta hada coffee ta sha. Sanye yake cikin gym wear na company track Smith dan gasar england,qaramin hannu ke da rigar daya tsaya a damtsensa ya kamashi tsam tare da fidda qirar jikinsa data jiqe da zufa har tana nunawa a jikin rigar,hakan ya sanya rigar ta sake manne masa,shafaffen cikinsa dake lullube da wasu muscles ya fita ta cikin rigar,dogo wando ne da kayan sai qafarsa dake sanye da wani irin takalmi dava dace da shigar tasa. Yadda fuskarsa da jikinsa suka hada zufa hakan ya bawa gashin kansa damar kwanciva sosai daga goshinsa zuwa qeyarsa,jikinsa sai fidda sassanyan qamshin turarensa yakeyi, yana rige da qaramin towel a hannunsa yana sake goge zufar hannunsa zuwa wuyansa. Kai tsaye ya doshi kitchen don yasha mutumin nasa wato coffee,duk da cewa tun wancan ranar bai sake samun dandanon da yayi dai dai da nata ba. Kamar dai dazun jacob da ya kammala hada breakfast yana tsaftace gurin ta shigo. Batayi zaton ganinsa ba shi yasa a yanzun Vail ne kawai saman kanta wanda santsin gashinta duk da cewa a kitse yake yake haduwa da santsinsa yake zamewa daga kan nata lokaci lokaci "No,ci gaba da aikinka" ta sake cewa wannan karon,sai yaci gaba da gyaran gurin,ita kuma ta matsa gaba kadan wajen coffee maker machine ta soma hadawa. Yana zare safar hannunsa da yakanyi amfani da ita saboda daga qarfe yana sako gafarsa kitchen din,dukkansu sun bawa gofa baya ita tana nata aikin shima yana nasa. Daga inda yake tsayen yana iya hangen doguwar jelar kitsonta ta cikin mayafin nata wandda ta hadesu cikin wani siririn band,ya janye idanunsa a hankali ya dora kan jacob dake aikinsa,wani abu yana dan taba zuciyarsa "Jacob" yayi kiransa with husky voice dinsa,sarai ta jishi,amma hakan bai sanya koda motsi tayi ba,sai Suger cubes da take qoqarin dauka ta jefa a hadin coffee din nata "Sir" ya fada da sauri yana waiwayowa. Da ido kadai yayi masa nuni da ya fita,sai ya ajiiye cups din da yayi nufin shiryawa ma'adanar kwanukan kitchen din dake ajiye daura da saahar din. Da ido yabi Jacob har ya kammala fita daga kitchen din,a nutse yaci gaba da takowa ciki yana ajjiye hand socks din nasa saman fridge. Sanda ya iso ta gama hada komai,hannuwanta na harde a qirjinta ta zubawa na'urar idanu tana jiran ta gama tafasa mata shi ta juye abinta ta wuce ciki. "Ke" taji ya furta da kakkaurar muryarsa dake cike da wani irin sauti me ratsa kunne da fusgar hankali sanda yake kunna tap din kitchen din ya tara hannayensa yana wankesu. Bata motsa ba kwata kwata,tamkar babu kowa a wajen har zuwa sanda ya kammala wankewar yasa kitchen towel ya goge farare tas din hannun nasa da babu wata alamar datti. A nutse ya zube mata idanunsa,fuskarta sam bata a wajen,amma duk da haka yana iya ganin gefan fuskar tata dake da wani kwantaccen gashi da baya iya kitsuwa,wanda hakan yake masifar qara mata kyau. Sarai yasan fa jishi,wannan halin nata ne kuma abinda yafi tsana kaf rayuwarshi rainin hankali da halin ko in kula "'Dake nake magana" ya fada a zafafe saidai cikin nutsuwa. Sai a sannan fa sauke hannuwanta ta kuma sanya nata idanun cikin nashi "Baki iya gaida na gaba dake ba?" Yayi mata tambayar tana sake nutsa idanunsa cikin fararen qwayar idanunta. Second biyar ta dauke dubanta daga kansa,ta karanci izzar da girman kan nasa ne ya motsa da safen nan,bata kuma da ra'ayin kulashi saboda ba zaman da tazo suyi dashi ba kenan,a yanzun jira kawai takeyi gidan ya zama daga shi sai masu shi,bata tunanin ma zai sake ganinta a wanann sashen nasa,zata koma inda tafi wayo ne. Batasan ya akayi ba,bata kuma san daga ina ba,tana tsaka da juye coffee din nata tajishi dab da ita tamkar zai take yatsunta kwatankwacin abinda ya taba yi mata a company. Wancan karon taji babu dadi qwarai da gaske,don haka a yanzun cikin hanzari taja da baya tana dubansa da razanannun idanunta da suke nuna yadda ta firgita,coffee din data fara juyewa yayi tangal tangal ta fantsama a gasa da jikin machine din. Wani irin duba yake mata dake nuna fushi cikin idanunsa "Ko naira biyar na biya a matsayin sadakinki tana da daraia da kima a wajena,saboda halal dina ce gumina ce,sannan nasan zafin nemanta.bazan bari a keta alfarmarta ba,don munyi auren biyan bugatar kawunanmu hakan ba yana nufin nidin sarakai bane,bazan dauki rashin kunya ko tsiwa ba,koda zaman dadiro mukeyi dake,daga yau ya zama dole ki gaidani kamar yadda kowa cikin gidan nan yakeyi,kamar yadda nima ya zama dole na bawa duk wanda vake samana girmansa" wasu hawaye ne suka fara taruwar mata cikin idanu,shi kuma irin nashi salon kenan?,tun daga ranar farko?. Kai ta girgiza,cikin jarumta da dakiya ta ajjiye cup din hannunta a gefe "Ai ba haka mukayi da kai ba mr jarma,ba auren gaishe gaishe mukayi zamuyi da kai ba,zan kula da fadeela,ni kuma zan rayu independently" taku biyu ya qaro gaba ya sake rage kusancin dake a tsakaninsu,sai a sannan ma ta fuskanci ba dab da ita yake ba,akwai sauran tazara a tsakaninsu,tsoratar da tayi yasa taji kaman yayi kusa da ita "Idan kina tunanin zan nemi wani abu daga gurinki ni ki cire wanann memory din daga kwanyarki ki qoneshi,har abada,saboda nidin tataccen dan iska ne da nake iya samun budurwa kowacce rana nayi disvirgin nata,kinga ko ke kinyimin kadan,abinda nakeso ki fahimta shine,har abada sama nake dake, you must give me a respect, koda ban saka kudina na biya sadakinki ba,ko kece ne kika biya sadakina mrs Khadija?" Ya jefa mata tambayar yana dubanta irin kallon kai tsaye,hannuwansa cikin aljihun wandonsa. Idanunta dake walainiya da gyallin hawaye ta daga ta dubeshi,yadda ya kirata kai tsaye da sunan da dukkansu suke sakayawa suke mutuntawa saboda sunan mahaifiya ce ga mahaifinsu ya bata ranta,taci gaba da tsirashi da ido haushinsa da tsanarsa tana kamata,duk yadda tace zata buda baki tayi magana ba shakka hawayen idanunta ne zasu balle,abinda kuma bataso ya sake gani daga gareta "Maganata itace dai dai,ni dinne kenan na biya,so that's all i need from you ba wani abu can na daban ba" yayi maganar yana dage faffadan kafadunsa guda biyu,sannan ya zare hannunsa daga aljihun ya sake matsowa kadan gaban na'urar dafa coffee din,ya dauki mug din data fara juyewa a ciki ya juye dukka coffee din a nutse ya juya yana barin kitchen din,sai kuma ya tsaya cak ba tare da ya juyo ba "Ki shirya nan da hour daya zamu shiga cikin gida,maji nason magana dake" sai ya sanya kai yana ci gaba da ficewar,can qasan ransa yana jin wani nishadi da dadin yadda yau ya samu coffee din daya jima yana mararin sha ba tare da ya zubar da kansa ya nema a dafa masa ba. Wani baqinciki ne yazo mata iya wuya,ga mari ga tsinka jaka? ta rasa me zatayi masa ta huce,sai kawai tace dashi "Idan ka shamin coffe ban baka ba,gaisuwa kuma ni ba auren gaisuwa mukayi da kai ba,so kayi harkar gabanka kayi abinda ya dameka nima nayi nawa,idan hakan bazaiyiwu ba ka fadi nawa ka biya na maida maka abinka kowa ya kama sabgarshi yaji da damuwarsa" ido ya lumshe yana sipping coffee din, dadinsa ya ratsashi,ya sake dakatawa daga tafiyar da yakeyi ya hadiye sannan ya juyo "Ki ragewa kanki rashin kunya da tsiwa,if not kuma zakisha mamaki tare da wahala a hannuna,zaki rayu ba tare da na shiga harkarki ba,but dole ki bani respect, you get it?" Yayi mata tambayar bawai don yana bugatar amsa ba,sai yasa kansa ya fice. Yana fita hawayen data riqe yana silmiyo mata,tabi jikinta da yadan baci da coffee din da kallo sai kawai ta sake sakin hawayen nata sosai,magoshinta ya cika da wani abu,anya batayi kuskuren aurensa ba?,anya ba shirya wannan abun yayi ba?,anya bawai ya shirya aurenta bane bawai don fadeela kawai ba?,bai shirya hakan bane anya don ya gasata saboda ta samu kubcewa daga kamfaninsu?. Wannan tunanin ya sake daga mata hankali,amma kuma sannu sannu wata murya daga can gasan zuciyarta ke gaya mata "Kema kina da taki damar karki wani damu da koma meye ya shirya" famfon ta kunna ta tara hannuwanta ta daurayesu ta kuma dauraye jikinta ta baro kitchen din, kamar zuciyarta zata fashe. Da yake zancan jacob ma ita ina ruwanta da wani kukunsa,bashi ya ajeshi ba?, shi yaga zai iya,amma itakam ba zata dauki wannan abubuwan ba sam,don ba wannan auren suka tsara zasuyi shi da ita ba. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 15 Kayan jikinta ta zare kaf ta shiga wanka,tanata qoqarin controlling kanta da fushin da yakeson taso mata a kansa,batason taje wajen maji fuskarta da wani yanayi maras dadi. Cikin miti hamsin ta kammala Shiryawa cikin wata qawatacciyar lallausar atamfar exclusive super me matugar kyau da tsari, dinkin tea boubou akayi mata wanda ya zauna mata a jiki qwarai da gaske, ya kuma fidda sigar kyau da dirin da Allah yayi mata,siririyar sarqar dake wuyanta ta gara fidda tsaho da hasken wuyanta. Medium chantilly vail ta yafa wanda ya dace qwarai da shigarta,ta wadata iikinta da turarukanta masu sanyin qamshi. Har tayi taku biyu gaba qafafunta sanye da wasu plate shoes na kamfanin saint Laurent sai ta dawo ta tsaya gaban mudubin tayi folding hannayenta a qirji,kenan yanzun tare dashi zasu jera zuwa cikin gidan?. Qaramin tsaki taja tana juya abun cikin ranta,ita sam ko hanya batason hadawa dashi,duka yadda ma ta lissafa abubuwan yadda zasu kasance sunata zuwar mata da sabanin hakan,totally ma bata taba kawowa zatayi koda rabin kwana bane a sassansa bare kwana guda cur,saidai ta riga ta tsarama kanta yadda komai zai tafi,bata yarda da wannar tsarin ba. Duk da tare suke da jibril suna tattaunawa akan ayyukan da ya fara a Australia ya barosu ya taho nan,amma hankalinsa yana kan agogon hannunsa,lokaci lokaci sai ya daga ya duba,ransa yana sake baci. Ya tsani jira, kuma yana tsammanin ya sanar mata zasu shiga maji na son ganinta. Sam baiso ma main ta umarci ganinsu a tare ba,to amma yadda ya fuskanci maji na cikin murna matuga da auren nasa,bayason sam abinda zai tauye wannan farincikin nata. Mintunan da ya diba mata suna cika ya miqe hannayensa zube a aljihun wandonsa yana yiwa jibril bayanin abinda zai tattara masa ya kuma tura masa duka bayanan ta email,sannan kai tsaye ya fice daga falon zuwa farfajiyar gidan yana takawa majestically kamar yadda ya saba. Dab da zai isa ainihin sassan gidan nadeeya ta fito dauke da wasu trays. Har zata gota taji husky voice din nan nasa na kiranta. Da sauri kuma cikin murmushi ta sauya akalarta zuwa gareshi,idanunta a kan miskilar fuskar nan da kullum take a dinke tsaf,banda ita,kaf duniya batajin akwai wadda ke iya tunkararsa haka,sau da dama ita dinma yana mata kwarjini,wannan dalilin ne ya sanya ko yaya tayi masa wani laifi take shiga uku,iya idanunsa kadai sun isa sakaka a tara "Good morning yaa moha" "Morning" ya amsa mata a taqaice yana duban trays din "Kayan dasu banaan sukayi breakfast ne na debo,kasan sun wuce" "Ban tambaya ba.. ki wuce ki taho da ita, kusameni a nan zamu shiga tare" ya fada cikin basarwar nan tasa. Dadi ne ya Kama nadeeya,dama tun dazun take jiran shigowarsu,don ta matsu taga aunty N din,fadeela kuwa baccin daya debeta da safen shi ya kawo sauqin rigimarta,maji ta hana kowa zuwako kai abinci ma tace a gyalesu tunda akwai cook a sassan. Cikin azama ta qwalawa daya daga cikin masu aikin gidan kira,ta qaraso ta jingina mata trays din tayi gaba "Idan kuka dade ranki ne zai baci" ta jiyo muryarsa, saita gyada kai tana qara hanzari kadan. Muryar nadeeya da taji tana sallama bayan knocking din da take mata ya sanyata miqewa tana murmushi,ta isa bakin qofar ta bude. Rungume juna kawai sukayi,fuskar nadeeya cike da fara'a kamar wadda ta shekara bata ga sãahar din ba "Ina faddee na?" "Tayi baccin gajiya,tun da safe tafarka tana rigimar zuwa gurinki,amma maji tace ba yanzu ba,babu wanda zai tasheku" murmushi säahar ta saki tana in nauyi da kunyar majin tun kafin ma su hadu "Yaa moha ne yace muje nayi miki jangora,yana jiranki a bakin part dinmu" nadeeya ta fadi tana qarewa sãahar kallo. Wani sassanyan kyau da tayi ita kanta yaja hankalinta ina ga yaayanta? tayi imanin nan kusa za'a yi barin wannan jan ajin da kamewar tasa tayi fata fata,fatanta dai daya lah ya kawo komai da sauqi,saboda ta sani shi din bai iya Kama komai da sauqi ba. Tare suka jera nadeeya din tana ta mata hira,kamar yadda suka saba a baya ba amsa sai murmushinta me sanyin nan da yake sake qawata fuskarta. Tun daga nesa inda yake tsaye ya hangi tahowarsu bayan ya daga kai daga latsa wayarsa da yakeyi. A hankali ya zare idanunsa daga kansu ya mayar ga hadiman gidan,wanda kusan duka maza ne suna kai kawo kowa yana gudanar da nasa aikin. Qwayar idanunsa ya juya kadan ya rufeta sannan ya bude a lokaci guda yana gogarin controlling kansa game da mayafin jikinta. Cikin jininsa qin mayafin yake,tun daga lokacin da ya fara ganinsa jikin nadeeya ya hanata amfani dashi,bata kuma sake ba. Iska yaja sosai yana fesarwa hadi da dauke kansa yana kallon gefansa,so yake ya lalubi zuciyarsa yayi kaya control,meye nashi na shiga sha'anin shigar da duk taga dana ta zabawa kanta? nadeeya qanwarsa ce,jininsa ce wannan kuma fa?. "'Matarka ce" yaji ana bashi amsa daga can wasan zuciyarsa. Kai ua girgiza a hankali •ya juya da kansa yana sake maidawa kansu sanda suke gab da qarasowa inda yake. Sarqewa idanunsu sukayi cikin na Juna, kallon second biyu rak suka yiwa juna kiwa ya janye idonsa yana jun haushin kansa, toufeeq kam kasa jurewa yayi sai da ya saki qaramin tsaki yana jin hausnin abinda ya sake maidashi ga kallon fuskarta da tayi wani haske,skin dinta data dauki gyara fiye da zato ta hadu da hasken ranar safiyar,ranar da bata kammala budewa ba saboda gajimare daketa haduwa yana alamta haduwar hadari, irin hadarin farko farkon damina. Suna isowa nadeeya bata tsaya jiran komai ba ta zame ta wuce ta barsu a gurin. Shuru ya ratsa gurin,kowa a cikinsu yana ji da kansa,yana jin kuma faduwa ce ya yiwa dan uwansa magana. Iska ya sake furzarwa yana son abinda ya tsaya masa a maqoshi ya wuce,kamar bazai motsa ba kafin daga bisani ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Bayansa ta gallawa harara,ta motsa bakinta zata ia tsaki amma saita hadiye abunta saboda tunawa da tayi da abinda ya faru da ita company sanadin tsakin,ta murguda bakinta wai duk ko zata huce sannan ta bishi a baya tana gunaguni gasa gasa "Girman kai,fadin rai,bagin rai duk mutum shi daya" ta furta can qasan zuciyarta ba tare data bari ya fito sarari ba. Tun tana hararar bavan nasa har taji kamar idanunta na neman juyewa,a hankali ta janye idanunta,tana dan rufesu kadan sannan ta sake budesu,kai tsaye saman baqar sumarsa da a kullum take cikin gyara ta sauka,ta kwanta sosai da wani irin gyara daya dace da shigarsa ta wani creamy color din yadi na maza,mara nauyi wanda kana iya hangen vest din jikinsa ta zallar cotton fara qar gar da ita. Yadda yake dauke gafarsa da saukewa kadai zai nuna maka yawan kuzari da baiwar lafiya da Allah ya bashi,wani irin taku me cakude da 'yar sassarfa kadan wadda take sanyawa yake danyi mata nisa,har sai tadan qara nata saurin kadan. Shi kansa takun gani takeyi kamar akwai izza da gasaita a cikinsa "Aikin kawai" ta furta tare da jan tsaki. A wannan karon tsakin nata ya bayyana,sai taga ya rage adadin takun nasa da yakeyi. Gabanta ya fadi,ta dora zara zaran yatsuntsa da suka sha lallae saman bakinta tana dan fidda idanunta waje,ba tare da ya waiwayo ba sai taga yaci gaba da tafiyarsa,ta sauke boyayyar ajiyar zuciya yaci gaba da bin bayansa tana kame kallonta daqa kansa,kada wani tsautsayin yasa ta sake wani abun da dukkansu shi da ita zasu raba hali gaban suruka. Da sallama a bakinsa ya tura gofar dakin maii,ita da 'var uwarta wassila suka hada baki wajen amsawa. Fuskar maji din fal da murmushi,wani farinciki yana sauka a zuciyarta. Ganinsu kadai tare ya haifar mata da farinciki me tarin yawa,tana ii a jikinta sãahar din itace addu'ar data jima tana yiwa toufeeq wajen roqa masa ubangiji yayi masa musaya mafi alkhairi da zai wanke dukkan quncin da ya samu kansa a ciki "Qaraso mana ibnaty" maii dake duban sãahar cikin kulawa da murmushi ta fada. Tsananin kunya ce ta dabaibayeta,ta tako a hankali ta qaraso gabanta,sannan ta zame saman gwiwoyinta tana fadin "Barka da asuba" gogarin dagota maji keyi amma sãahar din ta kasa sakewa bari ta mige kamar yadda maji keda buqata,dole ta barta fuskarta da murmushi tana dubanta tace "Barkanmu ibnaty,ya kwanan bagon waje?" "Alhamdulillah" ta amsa da gyar tana wasa da yatsunta "Allah yayi muku albarka,yasa albarka a tarayyarku" maji ta fadi. Kasa amsawa tayi,sai daga kanta da tayi a hankali tana gaida wassila wadda suke magana qasa qasa da toufeeq,bata kuma iya jin ainihin abinda suke fadi. Itama kamar maji din,tana da matuqar kirki,hakanan ta karanci kamar akwai kyakkyawar mu'amala tsakaninta da toufeeq. Qasa qasa maji ke janta da hira,saidai sam ta kasa sakewa da ita,surukuta sosai takeji,a gefe guda wanzuwar sa a waien yasa take jinta gaba daya a takure,saboda basu saba zama a muhalli guda ita da shi ba har irin haka. Duk da ta gefen idanunta tana lura da yadda ya karkata hankalinsa ga wayarsa,abinda ta karanta kwata kwata babu sabo ko shaquwa me yawa tsakaninsa da mahaifliyarsa. Inda itace tayi missing maama haka,ta tabbatar zuwa yanzu tana magale da ita. Cikin harshen larabci wassila tayi magana da maji sannan ta juya ta yiwa toufeeq shima magana,ta cewa da saahar cikin gurbatacciyar hausarta "Zanje na dawo surukata" sai ta gyada kai caking jin nauyin sunan data kirata dashi. Zata fita baaba ramatu na shigowa, fuskarta itama yalwace da fara'a tayi musu barka da fitowa suka kuma gaisa "Ki hado mana breakfast din duka tare dasu,a nan zamuci" maji ta bada umarni, cikin girmamawa baaba ramatu ta juya ta fice. Ba jimawa ta shigo ita da masu taimaka mata dauke da manyan trays guda uku,ta ajjiye a gabansu ta juya ta fita. Wayar hannunta maii ta ajjiye bayan ta kashe,ta jawo dukka trays din tsakaninsu ta dubi sãahar "Matso maza diyata,cin abinci tare da juna yana gara dangon gauna soyayya da kuma fahimtar juna. ..tafaddal moha" ta garasa fada tana sauke idanunta akan fuskar toufeeq,cikin zuciyarta tana juya halayyarsa da har yanzun bata barshi ba,a gefe guda kuma tana sake yarda da hirarsu da nadeeya ta daren jiya. Tabbas akwai aiki a gabanta,wanda kuma zata aiwatar dashi. Sãahar nada kyakkyawar zuciyar da bazataso ahalinta su rasata ba,zatayi dukkan me yiwuwa ta tabbatar ta riqeta cikin iyalinta. Bata taba kawowa zai sauko din kamar yadda maji ta buqata ba,sai gashi ya ajiye wayar tasa,ya kuma zamo daga saman sofa din da yake zaune,ya balle links din rigarsa yana tattare hannun rigar tasa sama. Bugun zuciyarta ne taji yana qaruwa saboda kusancin da suka samu sosai dashi,ya zamana yana tsakiyarsu ita da maji,qamshinsa me wani irin taushi,irin gamshin nan dake tashi a hankali ya fara karakaina a wajen,yana cakuduwa da nata qamshin. Dukka su biyun suka kai hannu lokaci guda a tare saman fararen plate din da baaba ramatu ta hado dasu don fara zubawa maji abinci,ya damqi saman hannunta a tausashe yana tsammanin plate din zai dauka. Karon farko kenan da hakan ta fara faruwa a tsakaninsu,a tare kowannensu ya dauke nashi hannun,wani irin abu yaji ya tsarga yarrr a jikinsa,tun daga hannun nasa ya aika sagon kowanne sashe na jikinsa. Yayin da saahar taji kamar wutar lantarki ce ta jata,cikin rashin saninsu kowannensu sai ya shiga yarfar da hannu,maji dake karantarsu a fakaice tace "'Zuba mana moha" sake maida hannunsa yay,,ya buda komai ya zubawa maji ya ajjiye a gabanta "Wannan yayimin yawa,kuci kai da matarka,samu plate ka zubamin kadan" ta fada idanunta akan wayarta kamar batasan ta fadi wani abu ba. Sam bai taba mata musu ba,don haka ya dauki wani plate din ya zuba matan ya ajjiye mata,ya sanya cokali biyu cikin plate din kamar yadda ta umarta,sai ta ajiye wayartata tana gyaran zaman glass din fuskarta,ta jawo nata plate din da cup din tea tana murmushi tace "Toh.... bismillah ko?" "Dangari" sãahar ta furta a ranta,maji ta gama daureta da dukka jijiyoyin jikinta,batasan ta inda zata fura buda baki tana cin abinci a gaban wannan dan rainin hankalin ba,tana jin ta bata wani babban aiki ne da batasan yadda zata alwatar da shi ba. Idanunsa ya lumshe shima vana budesu duka lokaci guda,ya motsa bakinsa kamar zalyi magana,sai yaga idanun maji din a kansa,don haka ya cinye duk wani uzuri da yaso bata,ya gyara zamansa yana lanqwashe gafafunsa ya dauki spoon daya tare da fara motsa abincin,ya riga ya fahimci abinda majin keso,zai kuma amintar da ita. Yadda taga yayin itama hakan tayi,saidai a nata bangaren ko loma daya ta kasa kaiwa bakinta,abin yayi mata yawa tako ina,gefe daya ga maji da takejin nauyi matuqa,daya bangaren kuma ga uban 'yan girman kan nan da takejin yadda ya sanya mata ido sosai. A nutse yake juya lomar abincin a bakinsa,duk da cewa bawai wani yunwa yakeji ba,amma saboda ya faranta ran maji din yake cin abincin. Yadda ta takura din shi hakan yayi masa,yana karantarta tsaf ta gasan idanunshi,wanda ba lallai bane ka karanci hakan kai tsaye. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 16 Ko a fuska ba zaka taba zaton karantar tata yake ba,har zuwa lokacin da maji ta magantu "'Ki saki ilkinki dani khadijatu,ina jinki ne tamkar moha da nadeeya,ke yanzun diyata ce halak malak,zan iya raba kowacce damuwa tawa da sirrina dake" garamin murmushi ta saki tana jinjina kai. Tabe baki yayi kadan yana matsawa gefe daga gaban kwanukan alamar ya qoshi,duk wadan nan abubuwan gani yakeyi kawai salo ne irin na mata wanda kaidinsu ba qarami bane,sai yanzu ya karanci dalilin da ya sanya dukkansu ta tafi da hankalinsu,cikin ransa yake gulmarta,ta wani sadda kai qasa,tamkar ba itace wannan mara kunyar ba me shegen tsiwa dake iya yarfa masa maganar da duk duniya ba macen data isa ta gaya masa bayan maji "Ban baku kowacce gudunmawa ba ko?" Maji ta fada tana murmushi,a nutse toufeeq ya waiwaya ya dubeta "Wacce iri maji?" "Ta aurenku mana" kasa cewa komai yayi,don baisan wacce gudunmawa kuma maji keson bayarwa ba bayan dukka abinda tayi da uwar kudaden data kashe,tamkar zaiyi auren fari ne ko kuma auren autarta nadeeya takeyi. Wani envelope ta ciro ta ajjiye a tsakaninsu "Maldives, turkey Malaysia,su sajjad ya zaba muku as Honey moon destination" bashi daya ba,hatta da sãahar sai da taji gabanta ya fadi,yayin da toufeeq din yaji abun gazo masa a mugun ba zata,yayi imanin akwai gudunmawar sajjad a zancan,tunda yafi kowa sanin abinda ke gabansu,duka duka da niyyar yij sati hudu kacal wato wata guda yazo,amma gaddarar da baisan da faruwarta ba ta rigeshi har yayi watanni biyu. Bayajin zai iyayin wannan tafiyar da yarinyar,ya dauketa duk inda suka shiga suna tare idanuwa a kansu,dauriyarsa ta qare don haka a tausashe .ya hada envelope din da hannun maji ya riqe cikin nasa hannun "Indai bakiyi booking ba sannan baki biya kudaden ba ki zaremu a ciki please maji,na tara ayyuka da yawa da suke jirana,inason na idasu cikin watan nan" idanu ta sanya masa sosai tana kallonsa tare da gasgata zarginta "Moha,sabon aure fa kayi,akwai Cabinda yakai iyalinka muhimmanci?" Kai ya girgiza a tausashe "Ba haka nake nufi ba maji,koma inane kikeso taje din zata je,amma a yimin uzuri na kammala ayyukan gaba na,zan biya da kudina na kaita ko ina ne ma indai yawo ne,amma kinga tun yanzun bai kamata nabar ayyukana na tafi ba" ran sãahar ya dan sosu,indai yawo ne wato gata shanshani wadda bata taba hawa jirgi ba. "Shikenan,amma wannan tafiyar bata soku ba,koma wanne aiki ne ka kammalashi nan da watanni biyu kacal zaku tafin, daga nan inason ku sauka a Algeria" "In sha Allah" ya fada yana lumshe idanu yana jin nutsuwa na saukar masa ta yadda yayi nasarar soke tafiyar ba tare da wani dogon turanci ba,yasan ya taki sa'a ne kawai,amma maji har yau tana nan a yadda ya santa tun yana da gananun shekaru. A nutse ya bude fararen idanun nasa,baisan yadda akayi ba suka sauka saman fuskarta. Tsaf ta gama fahimtar manufarsa ta soke tafiyar,koda baiyi hakan ba ita sai tasan yadda ta bulowa maganar ta rushe,don ko dogon zama ba zata iya yi dashi ba bare doguwar tafiya ta satittika,idan kowa baisan me ya dawo da ita gidan ba,ita da shi duka sai sun sani. Cikin jikinta tai idanun nasa saman fuskarta,wani abu ne da ita kanta batasan ta yadda yake faruwa ba,a duk sanda yake kallonta sai taji a jikinta,tun haduwarsu ta farko. Nata kewayayyun idanun masu cikar eye lashes ta daga,sai suka hadu guri daya da nasa,sai ya basar yana shirin kau da kallonsa,saidai kuma hararar data watsa masa ya sanyashi kasa aiwatar da hakan. Take ransa ya sosu,mamaki kuma ya cikashi. Ita ba abinda ta iya daga tsaki sai harara?,me yasa ta maidashi kamar sa'anta,da gaske dai ya fuskanci sai yayi maganinta ya saita zamanta. Tarko ya sanya mata da idanun nasa,saidai tunda ta harareshin bata sake waiwayowa sashensa ba,hasalima ta maida hankalinta kan maji dake magana da ita qasa qasa. Migewa yayi cikin nutsuwar nan tasa yana ware hannun rigarsa da nufin fita yabar musu dakin,saboda yadda maji din ke magana da ita kamae bataso yaji ne. knocking qofar akayi,maji dake gab da säahar wadda kanta ke a sunkuye tace "A shigo" A hankali aka murda handle din gofar aka turo aka shigo tare da sallama. Ba maji kawai ba,hatta toufeeq yayi mamaki qwarai da ganin mahaifinsa dr mahmud kai tsaye cikin dakin. Tsakanin toufeeq da sãahar ne kadai aka amsa sallamar banda maji da ta dauke kanta gefe kamar bata ga shigowarsa ba,ta kuma tsuke fuskarta,wannan kyakkyawan murmushin dake saman fuskarta ya bace bat. Sanye yake da wani irin yadin cashmere da aka yiwa dinkin manya,riga da wando 'yar ciki me dogon hannu,sai wata a sama kamar gown ta maza me gajeran hannu Tun daga rigar cikin wandon da kuma gown din aikin hannu na sarauta aka zauna aka zuba masa me matugar daukan hankali da masifar tsada,saman kansa hular dara ce maroon color. Ya sake fitowa sak mahmud din data sani shekarun baya da suka shude,matashin saurayin da ya zuba tashen kyau da farinjinin 'yammata wanda take da imanin a yanzu shi toufeeq ya debo,abu daya ya dakushe wannan a wancan lokacin,akwai wadatar kunya me tarin yawa ga 'yammatan wancan qarnin ba kamar yanzu ba. Gurin zama toufeeq ke gyara masa,amma dukka idanunsa da hankalinsa suna kan majin,wadda ita dinma babu abinda ya sauya daga gareta tsahon shekaru ashirin da bakwai da suka shude sai shekaru kawai da suka dan nuna kansu kadan. * HAJIVA OARAMA_* Tunda gari ya waye bata zauna ba,sai data tabbatar an kammala shirya breakfast na alfarma a babban dining din dake sassanta,bayan an kimtsa ko ina ta tabbatar komai yayi yadda ya kamata sannan ta shiga wanka ta shirya kanta cikin wani Swarovski lace dake ta fidda walwalin Swarovski crystal dake manne a kowanne pattern na lace din. Ta riga ta sani ma,koda bata fadi ba kamar wancan auren nasa,a nan zasuyi breakfast shida matarsa kafin ya shiga kowanne sashe na gidan,don haka ta shirya ta koma falo ta dauki wayarta tare da saka me aikinta ta canza mata channel tanata dakon shigowarsu. Tun tana chart a wayarta don rage lokaci har ta gama lissafe lissafenta ta maida hankalinta ga tv tana dan bibiyar program din da akeyi din. Sannu sannu ta fahimci lokaci yana tafiya,ta duba wayarta ko zata ga kiran toufeeq amma babu komai,mamaki yadan kamata,to me yake faruwa? aure dai ba na soyayya bane bare tace itace ta hanasu fitowa. Zuciyarta nata yi mata kokwanto ko yana wajen uwarshi?to amma batajin hakan zata faru,saboda sam babu wannan sabon a tsakaninsu,hasalima yaushe rabonsa da ita da har zai iya wuceta ita ya tafi gurinta? har ta dauki wayar zata kira taji alamun bude gate din gidan,dai dai shigowar 'yar aikinta,sai ta maida dubanta kanta "Waye ya shigo?" "Boss ne" ta amsa mata cikin girma mawa,maida wayar tayi ta ajiye ta fasa kiran toufeeq din,don tayi amanna nan din Dr jarman zai fara shigowa,kuma dole toufeeq din ya biyoshi. Duk bayan minti daya sai ta kalli agogo amma bataji shigowar yayan nata ba kamar yadda ya saba yi a duk sanda ya kawo ziyara gidan,duk da cewa abune mawuyaci ka ganshi a gidan. Zuwa lokacin haqurinta ya gaza,ta kasa jurewa,sal ta miqe tsaye tana gyara daurin dankwalinta hadi da qwalawa me aikinta kira tace ta rigo mata wayarta ta biyota da ita. Tabbas Dr jarma ne ya shigo,don ga galla gallan motocinsa da vake amfani dasu nan guda hudun a fake a parking lot na gidan. Abun ya sake daure mata kaita maida dubanta ga sassansu fadeela. Gabanta ne taji yadan fadi,saboda jikinta ya gama bata yana can,don son tabbatarwa saita nufi sashen kawai kai tsaye. A parlor din farko ta samu baaba ramatu tana qarasa kintsa dan abinda bai gama gyaruwa ba a sashen, kasancewar yadda tsafta ta ratsa kowa cikin gidan harta da ma'aikata maza da mata,basa barin koda tsinke a waje bare qura "Yaaya ya shigo?" Ta tambayi baaba ramatu kai tsaye "Eh suna ciki" "Shi da wa?" Ta tambayeta fuskarta adan yamutse "Toufeeq amarya da alhaji sai hajiya maji" "Danqari" ta furta har yana furucin nata yana fitowa fili. Daga kai baaba ramatu tayi ta kalleta,suka hada ido,sai hajiya qaraman ta basar kamar ba ita tayi maganar ba,ta sanya kai ga hanyar da zata kaita qaramin falon sassan gidan wanda daga can sai hallway na bedrooms dinsu. Kai baaba ramatu ta girgiza "Allah ya kyauta" ta furta qasa qasa taci gaba da aikinta, zuciyarta cike fal da mamakin dabi'un fauziyyan da har yau suka gaza sauyawa. Ganin idanun TOUFEEQ da sãahar dake a mazaunin suruka yanzu a gurinta shine kadai abinda ya sanya ta gaidashi da harshen larabci a taqaice,kamar yadda suka saba shekarun baya da suka shude. Wannan abunne yayi masa mugun fami hadi da tuna masa wani lokaci can baya. Majin ta mige zata fice tana cewa "'dan kun gama Khadija ki sameni a falo mu qarasa ko?" "Da kinyi haquri kin koma kin zauna akwai maganar da zamuyi" Dr jarma din ya fada a tausashe,wanda shi kansa baisan da haka yayi maganar ba. Cak hajiya qarama ta tsaya tana jin qirjinta yana bugun uku uku,sautin da yayanta yayi magana da maji din a yanzu,wani tsohon sauti ne da yake mata amfani dashi a shekarun baya idan yana son lallashinta. Wai meye yake faruwa ne?,sannan wacce magana ce da yau yayan nata ya hada iyalinsa,harda bare aurowar jiya amma ita babu ita aciki? koma meye za'a tattauna din ba zata iya Jurewa a tattauna ba tare da ita ba. Sai data dorawa fuskarta fara'ar dole sannan ta buda qofar dakin hade da yin sallama. Maii itace ta farko da idanunsu suka fara haduwa waje daya. Dauke kai maji din tayi kamar yadda ta yiwa dr jarma din da a yanxun ma ya samu nasarar dawo da ita ya zaunar duk saboda idanun mutum biyun dai,toufeeq da SÄAHAR Sam bata ko gaunar jin muryar fauziyya a rayuwarta bare ganin gilmawarta,itace silar da har yanzu take zaune ba tare da wata gagarumar katangar dake qara cikasa daraja da kimar diya mace ba wato AURE,ko tuna abubuwan da fauziyya tayi mata a rayuwa batason yi,amma duk da haka tana godiya ga Allah da ya bata wasu damarmakin,duk da wasu sun subuce mata,amma still har yanzu tana rige da lambar mutum ta farko data zamewa fauzivya qadangaren bakin tulu,tsare tsarenta suketa tafiyar wahainiya,wasunsu ma su gurgunce ba tare da sun cimma gaci ba "Ashe duk kuna nan,abun na ahali ne,ko mu koma?" Ta fada da sigar tambaya. "A'ah,qaraso mana,you are the part of duk tattaunawar da za'a yi din" dr jarma ha fada yana fidda gyara zamansa,har yanzu idonsa na kan maji din wadda ta baiwa banza ajiyarsu shida 'yaruwar tasa. Guri ta samu ta zauna a tsakaninsu,a sanann majin ji tayi kamar ta miqe ta fice a wajen,to amma kuma yin hakan kamar bada qofa ne ga fauziyya,so far kuma ita din tana jin a shirye take akan sake maido yaranta ilkinta,wanann na daya daga cikin boyayyun dalilan da yasa batabi ayarin family dinta da sukazo biki sun koma tare ba. Kamar yadda suka saba toufeeq ya gaidata,tayi gogarin gagaro murmushi "'Lafiya lau ango,idonka kenan?" Gaisuwar da sãahar ta migo ita ta katse tuhumar da take masa ta sigar tambaya a fakaice. Wani irin shu'umin kallo tayi mata,tadan kada qafarta kadan "Amarsu,lafiya ya kwanan baqunta?,koda yake ma ai 'yar gida ce na manta" ta furta tana sakin wani murmushi me dauke da ma'anoni da dama,gasan ranta kuma zuciyarta ke sake cika da alwashi da algawura iri iri akan sãahar din,sai ta biya baqincikin da ta sanya ta kwana dashi a jiya sanadiyyar maida mata maaganganun da tayi. Maida dubanta tayi ga yayan nata Dr jarma tana gaidashi. *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_ Book 02Page 17 Amsa mata yayi yana tambayarta hidimar da aka qare jiya "Alhamdulillah, duk da wata tana tafe in sha Allah nan kusa,saura kwanaki shida kacal meenal ta dawo,karatu ya qare sai aure in sha Allah" tayi maganar tana murmushi,kai dr mahmud ya jinjina "To Allah ya zaba abinda yafi alkhairi" "Ameen ameen,tuwona mai na in sha Allah" da kyau sagon ya isa kunnuwan maji,sai ta saki wani qaramin murmushi tana sake juya kanta gefe. Fauziyya ta riga ta makara,tayi makarar da bazata sake yin sammako ba daga nan har illa ma sha Allah,ta rigata isa gaban Allah,ta rigata kuma shiga kotun Allah,ranar yanke hukunci kawai take jira. Hamdala dr jarma yayi sannan ya fara da yiwa toufeeq nasiha hadi da tunasar dashi nauvin da ya rataya a wuyansa "Amana ce ita muka karbo maka,sai kayi qoqarin sauke haqqin Allah a wuyanka,duk da cewa ba wai yau ka fara aure ba" shikam gaba daya wa'azin dr jarma mamayarsa kawai yakeyi,duka abubuwan da yake lissafa masa a yanzun kamar an buga masa gudumar mantuwa,sai yanzun da yake masa bita suke dawo masa a kai, gaskiya ya fada,babu yadda za'a yi suyi wasa da Allah,shi kuma aure koda wasa akeyi,koda wasa aka daurashi to ya dauru kenan. Sai yaji lema tana tsatstsafowa daga gaban goshin sa yasa tafin hannunsa ya gogeta. Kan sãahar ya koma,itama yayi mata abida duka zai gayawa nadeeya,sai da ya kammala sannan yace "Komai na kamfanina ya gama dai daita kamar yadda nake zato sanadin tubalin ginin aikin daku kuka farashi,so saboda haka nayi hiring naku duk da ban tuntubi ra'ayinku ba,zaku je kuyi conclusion na aikin da ku kuka kafa harsashinsa na wata guda,ku tabbatar da gyaruwar komai din,saiku miga ragamar ga sabbin shugabannin da zan nada kuyi tafiyarku,zaka riqe matsayinka na CEO,ke kuma diyata zaki taimaka masa ne a matsayi PA dinsa saboda ya samu saugi da saurin kammala komai kada na riqeku da yawa a company din,hutun sati biyu kacal gareku na hutun aure kafin ku fara aikin" Kusan a tare suka kalleshi,sai ya sakarwa kowannensu murmushi yana gyada kai alamun tabbatarwa. Maida kansu sukayi ba tare da kowa ya iya musa masa ba,saidai ba abinda qirjin sãahar keyi sai bada wani fat fat. Ya tana qogarin nesanta kanta dashi amma al'amura nason sake kawo kusanci a tsakaninsu? Duk yadda hajiya qarama taso daurewa ta gaza,suyar maganar takeji har tsakiyar zuciyarta,tayi gyaran murya sannan tace "Amma yaaya, kana ganin hakan ya dace kuwa?,ya zaa yi harka ta dukiyar iyali a dauko bare a sakata a ciki?, next week haseena zata dawo,sai nake ganin ita tafi dacewa da wannan matsayin" sosai zuciyar maji keson maidawa fauziyya martani amma ta dakata taji wace amsa mahmud zai bayar? ya canza ko har yanzu ita ke riqe da akalar steering na rayuwarsa kamar yadda yake faruwa a baya? Dan qaramin murmushi ya saki sannan yace "Banda abinki fauziyya,ya zaa yi mutum ga matarsa ta sunnah kuma da ita aka fara aikin,tasan makamar aikin sosai sannan a ajjiyeshi a hadashi da wadda ba matarsa ba?" Mamaki ya kama haiiya caramar hadi da rudani, dama sãahar din ma'aikaciyar MT JARMA GLOBAL ce?,me ya kawota aiki cikin gidan?,anya anya ba turota akayi ba?,dukka wadan nan abubuwan dake faruwa ba shiri bane ba kuwa?. "Yaaya,naga tuwona mai na mukeson ayi,hakan ai zai gara musu ma fahimtar juna yadda komai zaizo da sauqi ko?" Ba maji data karanci fauziyya shekaru masu yawa ba take kallonta fes a tafin hannunta ba,hatta dr jarma yayi mamakin yadda take iya furta wannan maganar a gaban saahar,amaryar da kwananta daya tal a gidan miji akewa zancan kawowa kishiya nan da wasu watanni KO satittika?. Toufeeq ne mutum na farko da ya fara miqewa,don ya gaji da jin soki burutsun hajiya qaraman. Ba tun yau ba ta sani shima ya sani,ba kowacce magana tata yake iya bawa muhimmanci ba tun dazun da taketa zubarta baima gama fahimtar inda ta dosa ba sai yanzu,ta barshi yaji da danyan hukuncin da abban ya yanke masa na komawa company har na wata daya,kuma wai shi da yarinyar da ta riga tabar company din a gaban kowa,a yanzun zasu koma shi da ita a mazaunin miji da mata?. Iska kawai yake furzarwa a bakinsa,ya akayi komai yakeson ya dinga juyewa daga ainihin yadda qwaqwalwarsa ke wassafa masa zai tafi?, matsalar hajiya qarama da dukka maganganunta bai daukesu a bakin komai ba,don ita kanta haseena din da take magana a kanta bai dauketa wata cikakkiyar mace ba bare wani wasan kwaikwayon hajiyan ya tabbata,damuwarsa yanzun yadda yarinvar ke gara kusantoshi cikin lamuransa,ya gama da case din maji na tafiya honey moon ashe wani yana tafe. Qaramin tsaki yaja,sai ya sauya akalarsa zuwa dakin fadeela ya dubata,yana jin baccin da akace tana yi din yayi yawa,yasan ba kasafai ta fiya baccin safe ba. Baice da kowa komai ba ya taka a hankali ya fice daga dakin,maji ta waiwaya ga sãahar da kunya ta hanata motsawa "Tashi kibi mijinki kinji, Allah ya yiwa aurenku albarka,ya tsone idon asara da hassada qyashi mugunta d mugun abu". Cikin ranta sai data yiwa maji addu'a sosai data bata damar barin wajen. Ajiyar zuciya me sanyi ta sauke tana lumshe idanunta,tanason ta zauna tayi bitar abubuwan da suka farun amma kanta ya dauki zafi,ba yanzu take da bugatar hakan ba, saita waiwaya sassan dakin fadeela tana duban qofar dakin,qaramin murmushi ta saki,tunda tazo gidan bataga fadeelan ba,tayi kuma kewarta sosai,don ba kadan ba tana jin yarinyar qwaral a zuciyarta,sai ta soma takawa zuwa dakin itama ba tare da tasan yana ciki ba. Da gaske baccinta take lakadan hankali kwance,da alama tayi nisa sosai kuma tana jin dadin hakan,a tausashe ya zauna daga gefanta ya sanya hannu ya kama hannuwan ta yana kalla,kusan komai nasa ta daukeshi banda kamannin fuska da wani lokacin take yanayinsa,wani lokacin kuma yanayi take da maji. Sake damqe hannun nata yayi a tausashe yana sauke numfashi me zurfi daga hunhunsa,ko meye yake faruwa yanzun da shi ta sanadinta ne,lalurarta jarrabawa ce a gurinsa daya tabbatar akwai abinda Allah ke nufi a gareshi,kuma koma meye yana fatan ya zame masa kaffara da nasarar rayuwa. Cikin jikinsa yaji alamun an bude gofar,da yake dakin ba wadatar haske nadeeya ta kashe mata kowanne fitila sansa zasu fita sal ya sanya bata hangeshi a gurin ba sam. Ta gefen idanu yake dubanta sanda take takowa cikin dakin,sassanyan turarenta yana kwararowa tare da cika dakin. Sanda ta ganshi already ta iso tsakiyar dakin,taja ta tsaya dai dai sanda ta mige a nutse,saita juya da nufin fita a dakin,don ba zata iya zama dashi daki guda ba. Batasan ta ina ya iso ba,batasan yaushe yayi dogon takun da ya rigata isa bakin qofa ba,ta dai ganshi yana maida key din jikin gofar yana kullewa. Batason ta nuna tsoro ko firgita,sai tayi kamar bata ga abinda yakeyi din ba,taci gaba da takawa zuwa bakin qofar,ta Kama key din zata bude,wanne tudu wanne gangare sai ji tayi an mata wata wawiyar fusga an ajiyeta tsakiyar dakin. Yadda ta tsorata yasa gudun numfashinta ya qaru sosai,ta fidda idanunta waie tana kallonsa sosai sanda yake tsaye a gabanta hannuwansa cikin alihun wandonsa,ya zuba mata narkakkun idanunsa dake cike fal da bacin rai. Qara taku yayi gaba ya fara hade Gap din dake a tsakaninsu,sai ta fara ja da baya tana dubansa cikin zallar mamaki "Meye haka?,ka bani hanya na wuce" ta fadi ganin ta qure bangon babu kuma sauran inda zata sake goce masa. Kamar da kurma take magana,bai fasa nufota ba yana dubanta da tsimammun idanunsa,miskilar fuskar nan tasa a mugun hade cikin rashin walwala. Idanunta ta mayar ta runtse sanda ya qaraso dab da ita taku daya kacal zaiyi ya hade da ita. Cak ya tsaya yana kallon yadda fuskarta ta soma yin ja,soft lips dinta suke shacking kamar tanason furta wani abu daga dan mitsitsin bakinta na rashin kunya amma tsoron da taji ta kasa fadin komai. Sannu a hankali idanunsa suka sauka kan qirjinta da yake a cike sosai a kuma tsaye,bugun zuciyarta na nuna alamun ya qaru ta yadda qirjin nata yake sama da gasa da sauri,ya lumshe idanunsa saboda yadda dumin numfashinta dake gauraye da qamshin jikinta ke sauka a wuyansa,wani abu yaji kaman ya fusgeshi,sai yayi taku uku baya a hankali yana jin jikinsa yana saki. Irin wannan yanayin ya taba ganinsa sau kusan hudu cikin mafarkinsa,sak kamar irin haka,irin wannan dukiyar fulanin da yasha kai hannu zai taba amma mafarkin ya katse a dai dai wannan lokacin,ko a yanzun sai daya murza hannuwansa dake cikin aljihunsa da kyau,yaja numfashi sosai yana son daidaita kansa,cikin husky voice dinnan tasa dake da wani irin kwarjini yace "Open your eyes" a hankali ta fara bude idanun nata har ta kammala budesu gaba daya "Ke wacce irin mara kunya ce?,ban gaya miki banason tsaki ba,kinyimin tsaki kin harareni me navi miki? ni sa'anki ne? ko don na aureki shine garamar qwaqwalwarki take gaya miki yanzun dai dai muke kamar yadda take gaya miki a baya?" Ya jefa mata tambayar yana tsareta da kallon nan nasa me ladabtar da kowa ba tare da yayi magana ba. Kalaman da ya gaya mata sai suka tunzurata,ta danne tsoratar da tayi din ta sake galla masa harara "Waye yace ka dinga shiga gonata?,ba haka mukayi da kai ba,munyi da kai kowa zaiyi rayuwarsa ne ba yare da ya shiga rayuwar dan uwansa ba.. tunda nazo kagan na. bata ida garasawa ba saboda wata muguwar ba zata da yayi mata,dumu dumu ta tsinci harshensa cikin tsakiyar bakinta wanda shine ya toshe sauran maganganun da tayi niyyar gaggaya masa. Wani irin zuqa yakewa bakin nata yana hadawa sa lips dinta cikin wani irin salo da zata iya cewa ta mugunta ce kawai. Cikin sakanni gaba daya kwanyarta ta birkice da tsananin tsoro gami da firgicin abinda yake faruwa din. Kaf rayuwarta babu mutumin data taba hada baki dashi irin haka baki cikin baki,gefe guda kuma yadda labbanta suka dauki radadi ta gama saddaqarwa sun tsage ne kawai. Duk yadda take tunanin zata iya tureshi ta kasa,sai kawai hawayen da suka tarar mata suka budewa kansu da kansu hanya suka fara sauka,danshinsu ya gangaro zuwa kumatunta ya fara taba skin na fuskarsa. A hankali yaja da baya qafafunsa na wani irin sanyi da laushi,ya kalleta lokacin da take dugewa a waien tana cusa kanta tsakanin gafafunta tana sakin kuka a hankali don kada ta tashi fadeela dake baccinta batasan ma wainar da ake toyawa ba, yatsuntsa biyu saman lips din nata da ko da bata kallesu ba tasan sun tasa sosai "Idan wancan karon na takeki wannan karon bakin tsiwar zan cinye gaba daya,kuma bani zan hadiye ba karnuka zan sa a kaiwa,as from today karki sake cewa zaki sakamin wata doka taki,nine gaba dake so nine me sanya kowacce doka nayi niyya,ko zaman dadiro nake da mace bata isa ta kafamin doka ba bare sadakina na biya,ki aje a ranki bazan taba neman komai daga gurinki ba idan ma shi kikewa,don nafi qarfinsa,ko yanzun bakina da kika lasa saikin biya hakan" daga wannan ya juya a hankali ya fita a dakin. "HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 18 Hawaye sosai takeyi tana shafa labban nata da suke mata zugi, anya ba baki afifa tayi mata ba? ‚idan ba haka ba me yasa yake mata kwarjini har haka? "Martabar aure" amsar da zucivarta ta sake nanata mata kenan kamar yadda afifa ta gaya mata. Motsin fadee ne ya sanyata saurin share fuskarta da daidaita kanta. Ai tana hada idanu da sãahar din ta wantsalo gaba daya daga saman gadon ta qanqameta tana kiran "Anty N,good morning" rungumeta itama tayi sosai cikin jikinta,a hankali takejin wani farinciki, bacin ran dake lullube a zuciyarta ya dinga zagwanyewa. Sun jima a haka sannan ta dagata tana kallonta "Chubby fadeela ina wanka?" Kai ta langabe a shagwabe "Sai kinzo ke zakiyimin" dariya tadan saki "Kin fara girma fa,muje na gani" sai ta riqe hannunta suka wuce toilet din. Sanda suka fito tana tsane mata jikinta aka tura gofar aka shigo. Baaba ramatu ce suna hada ido da sãahar ta tambayeta "Ya akayi baaba" dab da ita ta iso, ta dan waiwaya ta kalli bakin gofa ta tabbatar a rufe take sannan ta warware bakin zaninta, wata leda ta ciro tayi saurin migawa sahar,sai sãahar din tasa hannu ta karba tana jinjina kai "Kome ya tafi dai dai, tun bayan tafiyarki wannan magungunan take sha, ina lissafawa a cikin wadancan ina cirewa ina zubarwa kamar vadda kika kwatanta min, amma an samu matsala daga dawowar hajiya" baaba ramatu ta fada fuskarta tana canzawa, tadan sharce gumi, sãahar ta zuba mata ido gabanta yana faduwa "Matsalar me baaba?" "Daga dawowar matar nan da kanta take sanya fadeela a gaba da magungunan nan,yau kwana biyu nata take bata tana sha,duk wata hanya da zanbi na kauda afkuwar hakan wallahi nayi amma baiyuwu ba" baaba ramatu ta fada hawaye yana cika mata ido, tana jin bacin rai har cikin ranta na vadda tsahon shekaru tana zaune ana wasu abubuwan amma rashin ilimin zamani yasa bata fahimta. Sosai säahar taji hankalinta yayi mugun tashi,ta dinga jinjina kai tana jin tsohon bacin ranta yana motsawa, a lokacin ta'addancin da adam yayi mata sa qwayoyin magani ne suka dinga dawo mata, ba zata bari ba kuwa haka ya faru tare da innocent fadeela ba "Zan yiwa tufkar hanci" ta fada a sarari, cikin zuciyarta tana jin zatayi amfani da nata power din da take dashi a yanzu na matar uban fadeela, duk da bawai tana tutiya da wannan matsayin bane. Kwanaki biyun da maji ta qara cikin gidan säahar gurinta take wuni, tun daga ranar basu kuma haduwa da toufeeq ba saidai a wajen maji,idan ya shigo din ba wani dogon zama yakeyi ba,sosai ta fuskanci abubuwa da yawa,kamar rashin sabo da sakewa tsakaninsa da maji din,duk majin tana bakin qoqarin gain ta jashi a jikinta amma wasu abubuwan basu yiwuwa. Gurinsu maji take yini tare da fadee dinta ga nadeeya,rana ta uku majin ta gama shirin tafiyarta,a safiyar da zasu wuce airport, dukkansu suna gaban motar da zasu wuce da rakiyar nadeeya fadeela da toufeeq. Su libril ke shirya komai,toufeeq din yana sassansa bai kammala fitowa ba,suna tsaye dukkansu gaban motar cikin alhinin tafiyar maji,ji sukeyi kamar su hanata tafiyar, säahar a cikin jiki da zuciyarta takejin babu dadi qwarai. Hannun säahar maii ta kamo tana murmushi "Karki damu d'iyata,bazan dauki dogon lokaci ba zan dawo, dawowar da nake kyautata zaton zan jima ban koma Algeria ba,akwai kasuwancin da na fara processing nasa a nan, bana tunanin zan wuce wata uku ko biyu ma ban dawo ba" wannan albishir din shi yafi komai faranta ran säahar, ta rige hannun maji sosai tana murmushi dai dai lokacin da yake takowa zuwa gurin. Sanye yake da wani baby cashmere da aka yiwa lafiyayyen dinki wanda yabi jikinsa ya dace da yanayinsa, ya kuma fitar da structure dinsa sosai yau din ya saka hula saman kanshi, abinda sãahar din bata taba gani ba kenan,hakan sai ya sake canza fuskanshi,ya fito a cikakken shuwa dinsa ya tashi daga launin larabawan Algeria. Ido suka hada,sai ta janye daga kallonsa tana hade rai,can gasan ransa ya murmusa a karon farko bayan da ya karanci wani abu saman fuskarta. Ta kalleshi ne ba tare da kowa ya tilasta mata ba,amma kuma bayan ya ganta tana kallon nasa sai ranta ya baci tana tuhumar kanta da kanta. Yau kwana biyu cur bai ganta ba,baisan a wanne bigire zai sakata ba, amma tuni ya fara karantar wasu halayen nata,bayan tsiwar da ya samu ya rage mata run randa ya yuwa labbanta wawan kamu,ya fahimci tana kafiya taurin kai da tsaiwa akan ra'ayinta. Zarmewa idanunsa sukayi da kallon labbanta,sun koma normal,wasu irin soft and tiny lips, masu wani irin pinky color me dan duhu. Idonsa yayi hanzarin daukewa yana lumshe idanunsa tare da budewa duka lokaci guda cikin kaucewa gamuwar idanunsu, kada taga yana kallonta ta rainashi. Isowarsa gurin ya dawo da hankalin maji kansa,ta saki garamin murmushi lokacin da yake duqawa har qasa saman gafafunsa yana gaidata,abinda ya sanyawa guard dinsa saurin juyawa suka basu baya. Ido itama sãahar ta dauke tana jin wani abu yana ratsa zuciyarta,karon farko da bataji feeling na rashin burgeta ba tattare dashi. Dabi'arsa guda daya da zata iya zanawa tace me kyau ce,daga kan maji har dr jarma ba zatace ga lokacin da taga ya gaidasu a tsaye ba. Fadeela ce ta matso tayl kissing kumatunsa dake da wani kwantacciyar qasumba me laushi wadda bata cika yawa ba,tana ta fitar d qamshin hair mist da kuma qyallin mayukan da tasha gyara dasu,sai ta zame ta tsugunna tana gaidashi kamar yadda taga ya yiwa maji,dama kusan tun bayan zuwan sãahar gidan ta dorata akan hakan "Barka da asuba abby" ta fada da salon da sahar din keyin gaisuwa, murmushi ya saja yana dan jan kumatunta "Barka da asuba abby, a ina kika canza yadda aje gaisuwa?" Tana dariya ta kalli sahar da sam tagi tsaida idanunta a sashen "Aunty N ce, haka take gaida mutane" basarwa yayi kamar bashi ya tambayu fadeela ba. Hannunsa maii ta kama ta migar dashi, tasa daya hannun ta kamo hannun sãahar,rigota din da tayi shine ya sanyata waiwayowa tana duban maji din. Hade hannayen nasu tayi guri daya,lallausan tafin hannunsa ya sauka cikin nata tafin hannun me wani irin taushi da dumi. A take tsigar jikinsa ta zuba wani irin dumin hannun yana ratsa jikinsa da wani gudu kamar gudun jini a kowanne sashe na jiki. Itama motsa hannun nata tayi saidai ba damar ta janye saboda maji ta lullube nata hannayen da nasu tana duban idanun kowannensu "Na baki amanar d'ana da jilkata na baki amana" sai ta waiwaya ga toufeed "Na baka amanar diyata, ka kula da ita ka kula da mutuncinta, ka tsare mata dukka buqatunta,mutuncinta naka ne, amanar Allah ce a wajenka daga gurin iyayenta kamar yadda abbanka ya gaya maka". Dukkansu babu wanda baiji ta dora masa wani nauyi ba,ba wanda jikinsa baiyi sanyi ba a cikinsu. Karo na biyu hannuwansu suka sake gamuwa wajen qoqarin da kowa keyi tsakanin shi da ita na budewa maji qofar mota, sahar dince ta fara janye hannu kamar wadda wuta ta jata, tayi gefe da hannun tana yarfarwa,ya ganta amma sai yayi kamar bai ganta ba,saida maji ta shiga ya sakewa nadeeva gofar suka shiga ita da fadeela. Da hannu ya yiwa elyas magana, sai gashi ya matso da sauri ya bashi key din motar,ya shiga seat din driver duk sai sukaja baya,don haka yana nuna musu da kansa zai tuga mamarsa kenan. "Yayi wuri ki fara fita diyata,da sai nace kema ki shigo." maji ta fada tana murmushi, cikin alkunya sãahar tayi qasa da kanta taja baya tana daga musu hannu sanda motar ta fara fita a gidan. Ana kammala rufe makeken gate din gidan ta juya cikin jin kewa,muryar daya daga cikin masu aikin gidan taji a bayanta "Madam hajiya garama tana kira" da mamaki ta waiwayo tana kallonta,mamakin kiran da take mata na meye? batajin zata iya taka sassan matar bare ta saurareta,gaba daya babu wata daraja tata data rage mata yanzun a idanunta sai 'yar kadan, ita dinma ta dosaneta ne a dalilin martabar dr jarma "Kice mata zan shigo" kawai iya abinda ta fadi kenan ta wuce sassan su fadeela tana juya kiran a ranta. Gyaran dakin fadeela ta soma,wanda ya tsaye mata a rai,tun lokacin takeson gyarawar, amma nauyin maii bazai barta ta sake ta gyara din ba. Ta kammala gyara komai tana goge dressing table na fadeela tare da kwashe hoodie towels dinta na wanka taji an buda gofar,a nutse ta waiwaya, idonta ya sauka kan hajiya qarama,sai ta ajjiye dukka towels din dake hannuta ta juyo tana goye hannunta a qirjinta tana dubanta kamar vadda itama take kallon nata. Tunda take bata taba jin qwarin gwiwa akan kowanne mutum ba kamar yadda takeji yanzu akan hajiya qaraman ba,daga sanda ta fahimei magungunan bogi take baiwa fadeela taji tayi mata wata muguwar tsana,sai take mata kallon kamar wata jini ko 'yaruwa ga adam, amma har yau tana cike da mamakin dalilin da yasa take bawa fadeela magungunan da ba likitanta bane ya rubutasu ba, meye a cikin ranta? me vasa take yiwa yarinyar da take qaunarta haka?,a zahiri kowa.yana yaba yadda fadeela ke sonta kowa kuma vana yaba yadda itama take nuna damuwarta da kulawarta akan yarinyar. "Fada da aliani fa ba dadi......Ina kyautata zaton baki taba sanin wacece ni ba ko?" Tsaf tayi karatun fuskarta na wasu 'yan mintuna "'Me sanin hakan zai amfana min?" Ta maida mata amsa kai tsaye, a yanzun bata jin zata qyale duk wani wanda baisan darajarta ya takata ba. Wani shu'umin murmushi hajiya qarama ta saki "Yaro baisan wuta ba sai ya taka,sanin ni wacece bazai miki dadi ba sam,abu daya zan zaya miki,ki samawa kanki lafiya da salama,ki watsar da dukka wata huduba da uwar mijinki tayi miki muddin kinason ki qarasa kwanakinki da suka rage miki a gidan nan lafiya lau" murmushi sãahar ta sakar mata ta juya tana ci gaba da aikinta,zatonta da zarginta akan matar yana sake qarfafa,dukka wani haushi nata dake tattare da adam tana jin a yanzu ta samu damar saukeshi akan hajiya qaraman ne,tayi imanin idan akwai banbanci tsakanin hajiya garama da adam to na jinsi ne kawai ,komai nata ya gama bayyana a idanunta,a yanzun tana jin zargi me garfi da rashin yarda da matar yana shigarta "Duk wannan ba matsalata bace, matsalata daya kibar rayuwar fadeela ta samu salama,ki daina ci gaba da birkita kwanyar da take neman ta rayu da cikakken hankali da bawa gangar jikin data mallaketa kariya da ingatacciyar rayuwa" Wani mugun shock hajya qarama taji "What!" Ta furta a rude tana duban fuskar säahar. Kallon tsakiyar idanu sãahar din tayi mata tana gyada mata kai "Basai kince min eh kinayi ko a'ah ba haka bane, umarni dava ne zan bayar, a matsayina na matar ubanta...wadda a yanzu take a mazaunin uwa a gareta,daga yau kula da lafiyarta da alhakin shan magungunanta yana wuyana,ban yarda ba ban lamunce kowa va sake baiwa fadeela magani ba, koda uban da ya haifeta ne!" Ta fada da kakkausar murya. Kamar ba zatayi respond ba saita saki murmushi tana duban saahar "Kada ki qirqiri game din da bazaki iya kai qarshenta ba" "Ba game nakeyi ba,ba kuma maganarta nakeyi ba, saboda ni din ba 'yar wasa bace, ina gaya miki magana ne ta zahiri" ta sake jaddadawa hajiya qaraman ba tare data dubeta ba bata kuma fasa aikin da takeyi ba "Idan kina ganin abune me sauqi yin hakan ki gwada aikatawa" hajiya qarama ta fada tana juyawa ta fita a dakin,don dukka kalaman bakinta sun gama qarewa,abu daya ta sani ya zame mata dole ta fara gamawa da saahar. Sai a yanzu ta fuskanci ba qaramar barazana bace a gareta, ita din wata babbar barazana ce da zata iya wargaza shirinta na shekara da shekaru. Abinda ta yita gudu kenan,ta sake tsanantawa wajen gain toufeeq bai rabi kowacce mace ba sai d'iyarta MEENAL AJI. Dogon tsaki säahar ta sauke bayan fitar hajiya qaraman, gefan kanta ya saara tadan dafeshi kadan,a duk sanda zata tuna abinda ya shafu rayuwarta a baya saita shiga yanayi,ashe har yanzu akwai ragowar azzaluman mutane irin adam a duniya? bama cikin jinsin maza ba kawai harda wai mace?,macen da aka santa da rauni? waishin meye dalilin hajiya qarama ne?, me take shiryawa?. "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 page 19 Da gyar ta garasa gyaran dakin, zuwa lokacin kanta ya fara ciwo sosai saboda damuwoyin da take ta tunawa ta kowanne sashe wanne rayuwa fadeela zata fuskanta daga gurin hajiya garama lokacin da zata rayu babu wani a gefanta da zai zame mata garkuwa?, meye shirin hajiya garama ne? me dame ta sarqa a rayuwar wadan nan bayin Allah wanda basu da babanci da marayu?, tsananin tunanin da ya tsananta mata ciwon kenan. A nan dakin fadeela ta duqunqune ta kwanta tana fatan bayan wasu mintuna kan zai sauka. Bata wuce awa guda kwata kwata da dawowar ba taji muryarsu da alama sun dawo, ba jimawa kuwa sai gata ta iso tana kiran sunanta. Daurewa tayi ta bude idanunta ta zauna sosai, garasowa tavi ta kama hannunta ta riqe "Anty N gidan uncle sajjad zamuje ni da sister nadeeya,tace na gaya miki, tana cikin mota tana jirana abby ne yace kada mu batawa driver lokaci" murmushin garfin hali ta saki, tana tunawa yau kwanaki shida kenan amma sau daya tak sukayi waya da afifa, abinda bata taba kawowa ba akwai randa zasu dauki kwanaki basuyi waya da bestie dinta ba,saidai bawai hakan yana nufin ta qullaceta ko taji haushinta ba, ko kadan, uzuri kawai ta bata. "Ki cewa bestie na ina godiya da kulawa,a gaidarmin da uncle sajjad" maimakon taga yarinyar ta mige ta tafi sai ta kama hannunta sosai tana kallonta "Anty N. kaman baki da lafiya" kai ta girgiza "Gajiya nayi sai kaina dake dan ciwo kadan" säahar din ta fada tana kallon tsakiyar idanun yarinya zuciyarta na karyewa,tare da mamakin meye tayi da za'a cutar da ita ne? ita ba kudi ko dukiya ba kaman dai ita,ita ba wata babba ba bare ace ta aikata wani abu,bata mallaki komai ba sai rayuwarta da numfashinta da soyayyar makusantanta, a ciki me ake nema?. "Bari na gayawa sister nadeeya‚mu zauna dake" yarinyar ta fada a karye. Kai ta jinjina mata "A'ah, karki gayawa kowa,inajin sauqi,kafin ku dawo na warke in sha Allah" saita sakar mata murmushi don bata qwarin gwiwa. Duk da haka yarinyar tana tafe tana waiwayenta har ta fice a dakin, abinda ya sake karya zuciyar säahar din kenan, ta koma ta kwanta tana lumshe idanunta zuciyarta a cunkushe. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi yana duban hajiya qarama dake sharar hawaye hadi da fyace majina bayan kukan data sharba, fuskarta na nuna zallar alhini da bacin rai. Har cikin ransa baiji dadin vadda take kuka tana gaya masa sãahar ta zageta ba tare da gaya mata bat iva kula da fadeela ba, daga yau kuma kada ta sake kusanto inda take, magungunanta da komai nata ta haramta mata tabawa saboda wai bata yarda da ita ba. Iska ya furzar me dumi daga bakinsa "I will talk to her,stop crying mommy" ya fada calmly. Kai ta girgiza "Kada kaie ka tareta da zancan toufeeq taga kamar na hadaku rigima kuna zamanku lafiya " baice mata komai ba,ya dai fara takawa yana barin wajen. Bayason kuka gaba daya,bare kukanma na babba,babban ma macen data rainesu har suka kawo haka. Amma kuma ta wani gefen zuciyarsa ta kasa nutsuwa da statement na abinda ya farun,haka kawai kuma yakejin zuciyar tasa ta gaza karba. Ba kasafai yake yanke hukunci kai tsaye ba ba tare daya ji ta bakin mutum ba,wannan ya sanya ya wuce sassansa kai tsaye. A parlor ya samu Joseph yana sake tsaftace falon,duk da bawai yayi datti bane, a'ah wannan tsarinsa ne, ko yana nan ko baya nan,sharar safe data yammaci irin haka. Rusunawa yayi ya gaidashi, ya amsa sama sama ya wuce yana jiyo motsin jacob daga kitchen,shi kuma yaci gaba da aikinsa yana maida earpiece din kunnensa. A nutse yake takawa cikin hallway din har ya isa bakin gofar dakin, hannu vasa ya murza handle din sannan ya tura qofar baya ya shiga a nutse. A kintse dakin yake,komai fes fes cikin wadatacciyar tsafta da kulawa,ba abinda ke tashi a dakin sai wani nau'in qamshi me sanyi d kwantar da zuciya. Tsaiwa yayi yana qarewa dakin kallo karon farko tunda aka shirya dakin cikin gidan, komai cikin favourite colours dinsa yake ya sauke hannunsa yana takawa zuwa ciki, duk kuwa da ya fuskanci ba kowa cikin dakin. Gefan gadonta ya qarasa ya zauna,haka kawai yaji weather din dakin tayi masa qwarai, ta kuma saukar masa da kasala,ya cire hannuwansa daga aljihun wandonsa da zummar dorawa saman gadon,sai yaji ya dora saman wani abu ne taushi da santsi. Waiwayawa yayi yana duban gurin. Panties dinta ne da braziers dukkansu farare gal gal kamar hannu bai taba tabasu ba. Janye hannun nasa yayi da sauri tsigar jikinsa tana zubawa,sai ya kauda kansa,idanun nasa suka sauka saman bedside drawer dinta. Hannunsa ya miqa ya dauki litattafan da suke kai na farko al-qur'ani ne ya maidashi ya ajjiye, na biyun littafin azkar dinta ne,ya buda ya karanta wasu daga cikin addu'o'in da suke ciki na wasu mintuna sannan suma ya mayar ya ajiyeshi,na ukun kuma MY DIARY shine abinda ke rubuce a fuskar littafin da manyan harufa da aka yiwa aloo da ruman azurta. Har ye maida ya ajiye ya mige sa ya koma ye sake dauka, ya bude shafin farko. Rubutu ne ekin tsari da daukan hankali kamar haka -the worst feeling in the worid is knowing you've been used and lied to by someone you trusted, and the saddest thing about betrayal is that it never comes from your enemies_ Ya maimaita kalaman sun kusa sau biyar yana jin wani abu yena taba zuciyarsa yana jin kamar saboda shi akayi duke weden nan maganganun, akwai wani abu clin reyuwarta bayan wanda ya bincika ya saniyes... ya san da hakan duk da a wancan lokacin yace bashi da bugater ya sani din, amma a yanzun sai yaji yana da she'awar haken. Maida littafin yayi ya rufe, a maimakon ye maidashi wajensa sai ya fice dashi daga dakin gaba daya Guri yayi masa a davinsa sannan ya juya ya fito, tunda bai ganta a sassansa ba ya tabbatar tana sahensu nadeeya. Zai iya cewa a kwanakin shida su biyu rak yaga gilmawarta a sashen kwata kwata,duk da cewa shima din ba wai zama yake a gidan ba, yanata qoqarin ganin ya fara hada kan ayyukan da zaiyi a company din dr, so yake yana cika wata guda yabar qasar dawowarsa kuma sai baaba ta gani, abu daya zai masa cikas,ya tabbatar Dr shine mutum na farko da zai fara masa maganar yana da iyali a yanzu, amma yasan yadda zai tafi da komai,yanason ya danyi nesa kadan ya samu zafin da kansa ya dauka ya sassauta. Sanda taji anyi knocking migewa tavi ta zauna sosai duk da yadda kanta yake ciwo kamar zai cire ta dauka baaba ramatu ce, da muryarta da tayi sanyi qwarai tace "Shigo" ya murda gofar ya turata ya sanya qafarsa. Ta lumsassun idanunta da kanta data jinginar a fuskar gadon taga shigowarsa, bata tsamamci ganinsa ba,ta miga hannunta a da hanzari ta jawo dankwalinta ta budeshi tana rufe gashinta. Kansa ya dauke kaman bai gani ba,ya qarasa shigowa ya jawo stool zuwa gaban gadon ya zauna sosai yana dubanta. Kwarjini taji yayi mata kamar yadda yake mata wasu lokuta,kanta ta juyar wani bangaren gasan rabta tana mamakin abinda ya shigo dashi. A nutse ya kafeta da kallonsa, mayun idanun nan nasa suka dinga ratsa jikinta suna bata alamun akwai kakkaifan idanu a kanta,batasan me yasa ba,duk sanda zai kalleta sama da second biyu sai taji kallon har cikin jininta,abinda kaf rayuwarta bata taba ji ba akan wani. Yadda baice komai ba haka itama,bataga amfanin zuwan da yayi ya sakata a gaba yake mata kallon daukan alhaki ba,wannan ya sanya ta yaye duvet din ta fara yunqurin saukowa daga saman gadon "Koma ki zauna" ya fada still idanun suna kanta. Kamar ba zata koma din ba kamar yadda yace,sai kuma ta tuna da gargadinsa, batason wani abu da zai kawo haduwar jikinsu waje daya ya sake faruwa,don haka ta dakata daga gogarin saukar da takeyi fuskarta na kallon gabanta,baya iya hangen fuskarta da kyau,sai gefen fuskarta dake dauke da kwantaccen gashi ta gefen kunnuwanta. Kansa yadan gyada kadan ya fuskanci gwanar taurin kai ce "Kina da masaniyar matsayin hajiya a gurina?" Ya tambayeta adan kausashe, tun kafin ya gara komai a kai ta fahimci inda maganar tasa ta sanya gaba "Ko na sani ko ban sani ba ba wanna bane ya kawo ni gidan nan ba,nazo ne don kula da fadeela, kuma na dauki alqawarin bata dukkan kariya da dukka iyawata,bazan taba barin wani abu ya cutar da ita ba alhali ina da ikon dakatar da shi, saboda haka na dakatar da ita daga bata magani don aiki nane". Fuskarsa ta dan sauya yana mamakin qarfin halinta "Kika dakatar da wa?‚are you in your sense?" Zuwa lokacin kasancewarsa a gurin kawai matsi ne da takura a wajenta don haka ciwon kan nata zuwa lokacin kamar an ninka mata shi, har ya fara sauka zuwa idanunta kamar yadda yake mata a yawancin lokuta idan yazo da tsanani. Waiwayawa tayi ta dubeshi kai tsaye "Yes, na fada na dakatar da ita, bama ita kadai ba kowa a gidan nan, ciki harda kai mahaifinta". Karon farko kuma lokaci na farko da garfin halinta tare da qarfin gwiwarta ya burgeshi yaso kuma bashi dariya har ya murmusa da wani kalar miskilancin murmushi wanda gefen bakinsa ne kawai ya motsa, saidai hakan ba qaramin qara masa kyau yayi ba. Gefe daya kuma yana karantar yanayinta da ya canza, tabbas akwai abinda yake damunta,yasan kuma ba zata taba fada ba,sannan muddin ya barta ta kwana a haka kota galabaita yayi imani daya daga cikin haqgoqinta kenan da ya gaza saukewa ne. Ci gaba tayi da sauka daga gadon, tana ganin ta gama bashi amsa,no need ta tsaya wani dogon magana,gefe daya zuciyarta na sake cika da mamakin hajiya qarama,tare da jin cewa ta shiryawa tunkararta da dukka wani nau'in abu da zatazo dashi. Sai daga gama sauka kaf yana kallonta ba tare da ya sake cewa komai ba yana sake nazartar garfin hali da kafiva irin nata. Sunkuya tayi da zummar gyara takalminta ta saka,sarawar da kanta yayi ya sanyata tallafeshi tana furta "Wash" ba tare data tuna ma yana wajen ba. Sai a sannan ya mige a nutse, ya tako a hankali zuwa inda take,qamshinsa ya tabbatar mata da garin kusancinsa da inda take *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Book 02 Page 20 Bude idanunta tayi a hankali ba tare da ta daga kanta ba,saboda tsaiwarsa a gabanta dava gefe ya bata damar ganin doguwar fara qal din qafarsa. Sake yunqurawa tayi da nufin tashi "You can't do it,lemme help you" ya fada yana miqa mata hannunsa. Kau da kai tayi,ta yaya zata bashi hannunta?,gobe yayi mata sharri yace ta taba masa hannu?. Wannan abun ya sanya ta qarfafawa kanta gwiwa,ta yunqura a karo na biyu ta miqe gaba daya,saidai ko taku biyu bata yi ba duhu ya mamaye idanunta,wani irin jiri ya debeta yayi baya da ita zai zubar a wajen. He is ready akan kome zai faru already,saboda yanayinta ya gama nuna masa babu lallai ta iya barin dakin kamar yadda taso,tsabar dai taurin kaine da kafiya irin nata,don haka cikin zafin nama ya tallafota,yayi mata kyakkyawan masauki saman qirjinsa. Duk da yanayin da take ciki amma hakan bai hana hancinta zuqar ni'imtaccen qamshin dake fita tun daga ainihin skin da gargasar qirjinsa,vest zuwa rigar jikinsa ba. Wani irin abu taji wanda ya tilastata damqe gaban rigarsa da hannunta,ya lumshe idanunsa kadan yana sauke ajiyar zuciya saboda yadda dumin jikinta ya fara ratsa rigar jikinsa zuwa fatarsa yana ratsa jikinsa sosai "stubborn girl" ya furta qasa qasa da wata irin murya me taushi. So take ta tureshi daga jikinta amma ta kasa saboda jirin da takeji,yasa hannunsa ya tallafeta sosai,sannan ya fara takawa da ita sannu a hankali suna fita a dakin. Hankalinta a tashe yake,bata son kasancewarta cikin jikinsa,tana jinta ne kamar a kan qaya,batason wani ya gansu a haka,to amma yadda takejin garin yana juya mata tasan tayi qarya tace zata iya takawa da kanta. A hankali suke takawa,bugun zuciyarsa na sauyawa da wani irin bugu na daban,qamshin turarenta na shige masa hanci,kamar yadda qamshin hair mist dinta ke ratsa dan kwalinta yana fitowa zuwa qofofin hancinsa. Duk taku daya da zatayi sai tudun qirjinta ya gogeshi,idanunsa yake rufewa yana jin abun yana tabashi har tsakiyar kansa,hakan ya sanya jikinsa ya fara weakening,ya dinga kokawa da kansa ya sake aro jarumta ya yafa,sai ya dinga Allah Allah su isa ya zareta daga jikinsa. Dab da zasu shiga sassan nasa yaja ya tsaya saboda muryar Joseph da yake jiyowa,ya tuna ya barsh ne yana goge goge. A nutse ya juya gefan damansa yana kallonta,rigar atamfa ce a jikinta,duk da dinkin boubou ne amma hakan bai hana tudun qirjinta fita ba sosai,da alama tana daga cikin matan da suke da baiwar cikarsa da kuma tsaiwarsa,ganin sun tsaya sai ta danso janyewa baya kadan,ya dauka zata fadi ne,da hanzari ya zanya dukka hannayensa ya tallafota don kada ta fadi inda kai tsaye yayi mata masauki a karo na biyu cikin qirjinsa ya maida hannuwansa ya rufeta gam a tsakiyar faffadan qirjin nasa,jikkunansu suka mannu guri guda dumin jikinsu kuma ya sake gauraya yana ratsa jikinsu da kyau. A tare suka sauke ajiyar zuciya wadda ta fito duka lokaci daya,sãahar ta lumshe idanunta zuciyarta na quna ta yadda yau din ya samu damar hada jikinsa da nata,jikin da yake iqirarij batasan darajarsa ba. Tattara dukka hannuwanta tayi ta tureshi daga gareta,abun yazo masa a bazata don haka ta zamu nasarar raba kanta da shi,idanunta da suke adan jirkice ta dubeshi dasu "Kada ka sake tabani,zan iya taimakon kaina" daga wannan ta fara takawa zuwa cikin gidan kai tsaye hannunta riqe da dankwalinta daya zame. Binta yayi da kallo cike da mamaki,wanne irin taurin kaine da ita?,tana tafe tana layi amma duk da haka bata fasa tafiya ba,normally yana da wani irin tausayi ga mara lafiya. Dab da zata shiga parlor din muryar Joseph ta qara tashi da alama suna hira ne shi da jacob cikin dariya da kakaci,sai a sannan ya tuna suna falon,kanta kuma babu dankwali,kuma a haka zata ratsa ta tsakaninsu ya tabbatar,wannan tunanin ya sanyashi daga qafa don ya risketa ya tsaidata,saidai tun kafin ya isa tuni ta shige abinta. Sanda ta shigo din da kallo Joseph ya dan bita dashi,kallo daya yayi qas da kansa yana ci gaba da mopping din da yakeyi,lokacin da yake yunqurin dauke dubansa daga kanta dai dai lokacin toufeeq din ke shigowa. Cak ya tsaya yana zura hannuwansa a aljihun wandonsa tare da hadiye wani irin yawu. Haka kawai yaji ransa yayi mugun baci. "Joseph" yayi kiran sunansa da wata murya me kaushi,cikin rawar jiki ya amsa ya kuma ajjiye mopping stick din ya qaraso da sauri ya zube a gabansa. Fada sosai ya shiga zubawa cikin bacin rai,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Daga Joseph har jacob tsuru tsuru sukayi,don sautin fadan nasa ne ya fiddo Jacob daga kitchen shima,at last yace "Get out from here,you All" ba wanda ya sake cewa komai sai ajjiye kayan aikinsu da sukayi suka jera suka fice,su duka suna mamakin abinda ya bata ransa,iya tsahon zamansu dashi bai taba musu fada irin haka ba. Wayarsa ya fidda daga aljihu ransa a bace,ta yaya zata ratsa tsakanin masu aikinsa a haka?,tsabar taurin kai ne kawai da kafiya irin nata,kuma zaiyi maganin wannan taurin kan nata surely. Har ya fara kiran Dr anwar,sai ya katse ya koma kiran Dr raheema,bugu uku kacal ta daga "Ki sameni gida yanzu" abinda ya fada kenan ya gintse kiran. A hankali ya koma saman hannun kujera ya zauna,har yanzu yana jin zuciyarsa na masa quna,ya daga hannunsa ya kalli tsadajjen agogon dake maqale a lafiyayyar fatarsa. Yana da schedules da yawa yau dinma,akwai baqin da yasa aka ajjiye a tahir guest palace amma cikin jikinsa yakejin kamar bazai samu zuwa ba. Kamar kuwa jibril yasan abinda yake saqawa sai ga shigowar kiransa,ya kalli wayar da kyawawan fararen qwayoyin idanunsa,sai ya daga wayar ya saka a kunnensa "Sir,i think kamar ka manta,we have an important with the guest who is staying at the guest house,sunce morning flight zasu bi gobe,seven pm dot,They asked me to tell you, if you don't mind, the conversation should be over tonight" kai ya gyada "Alright,kazo ka daukeni after one hour,banason rakiyar kowa" "Yes sir" jibril ya amsa masa cikin girmamawa. Yana sauke wayar dr raheema na shigowa. Kai tsaye yayi mata nuni da hallway na dakunansu. Nauyi taji sosai,saboda bata taba yin nan gefan ba hasalima part din nasa yaune karon farko data fara shigowa,so sai abun yayi mata kwarjini da yawa. "Don't mind,ki shiga tana ciki" ya furta calmly "Okay madam ce?" Tayi tambayar tana murmushi,kai ya gyada mata,sai ta gyara box din kayan aikinta tana cewa "It's better to let her know first sir kafin na shiga" kansa ya daga a hankali yana duban hanyar,ya yadda da idea dinta,don haka ya miqe a nutse yana maida wayarsa aljihu ya nufi hanyar. Tana jingine da fuskar gadon idanunta a lumshe,zara zaran gashin idonta sun yiwa idanun nata rumfa da kyau,sau daya ta bude ido ta kalleshi ta mayar ta kulle,ya qarasa kanta ya tsaya yana dauke dubansa daga kanta "Ki shirya ga dr nan zata shigo,ki gaya mata matsalarki,i don't want rudeness" ya qarasa maganar yana turawa Dr raheema gajeran tex akan ta shigo. Bude idanun nata ta sakeyi a hankali ta sauke a kansa,me ruwansa da rashin lafiyarya da zai kira mata likita,saboda tsabar girman kai da izza kuma yazo yana kafa mata dokoki kaman ita ta buqaci ganin likitan?. Tare da nadeeya sukayo sallama da fadeela duka a tare. "Oh sannu anty N" nadeeya ta fada cikin nutsuwa,tana gudun kada tayi misbehaving yanzu a sendata waje. Qaramin murmushin data fusgo da qyar ta sakewa nadeeya tana gyada kai,ta miqa hannu a hankali ta sanya hannun fadeela da duk take a dame cikin nata,ta tabbatar lokacin dawowarsu baiyi ba,tayi yaqinin fadeela ce taqi sakewa,ta gayawa nadeeya ita kuma ta tattarota suka dawo. "Sunnu madam" Dr raheema ta fada cikin murmushi tana sake yaba kyan da sãahar din ke dashi "Dama MT JARMA din sai mata irinku" ta fada a ranta tana murmushin gulmarsu da tayi. "Yanzu ukhtie fadeela ta yaya za'a duba maman naki ehnn?" Dr raheema ta fada tana murmushi ganin yadda ta kafa ta tsare ta nannade hannun sãahar da kyau "Karkiyi mata allura please dr" ta fada a shagwabe,dariya tadan saki "Ah.....wai da allurar zanyi mata fa,kika sani ko qani maman naki zata baki ko bakiso?" Wani tsalle tayi hadi da sakin hannun sãahar da maganar Dr din ta sanyata kasa bude ido. Tuni fadeela ta maqale toufeeq tana dariya "Da gaske daddy?,wai nima anty N zata haifo min qani?,daddy nima na daina wasa da teddy sai da qanina?" Gaba daya nauyi ya saukar masa,yasan halin Dr raheema ba wai tun yau ba,tana da mugun barkwanci da kuma kirki,amma haka kawai saita hada masa gwarama,ta qala masa abinda bai taba attempting aikatawa ba harda su wani ciki? "Fadeeeeela" toufeeq yayi kiranta ganin ta dauki abun serious. Yadda yayi kiran nata ya sanya ta nutsu tana dubansa "Ki nutsu za'a duba mara lafiya. Nadeeya come and take her,ku zauna a waje ku jira" ya fada yana wani basarwa saboda kallon da yaga nadeeyan tana masa,haka kawai zata janyo yara su rainashi,yadda yaga nadeeyan tana kallonsa itama tayi believing ne da abinda Dr raheema ta fada bisa alama. "Kodai anyi abunne?" Ta fada qasa qasa tana duban idanun sãahar bayan ficewarsu nadeeya "Da wa?" Sãahar din ta fada kai tsaye tana duban dr raheema din,don ko dazun da tayi zancan ciki bacin rai kawai ta dasa mata. Tambayar sai ta saka Dr raheema murmushi,tana zaton kunya kawai sãahar din takeji. Ga toufeeq kuwa ya fahimci sarai ma'anar amsar data bawa dr raheema din sai yayi folding hannayensa a qirjinsa yana duban fuskarta,zarginsa ya saje tabbata sanda ta juya kadan ta jefa masa wani kallo "Ba maza ai a gidan" ta fada qasa qasa hankali kwance bayan ta dauke kai daga dubansa ta maida idonta ta lumshe. Dr raheema batace komai ba,ta bawa ranta zafin zazzabin daya fara hawa mata ne. A nutse ta gama dubata,sai ta fidda PT strip "Ko zaki kawomin fitzarinki zanyi pregnancy test,saboda nasan magungunan da zan rubuta miki" kai tadan juya kadan "Ki rubuta maganin directly kawai" murmushi ta sakeyi mata kamar yadda yake nuna al'adarta ne hakan "Sorry madam,indai matar aure ne dole tayi gwajin kafin karbar magani saboda gudun matsala ga qaramin cikin da ba'a san dashi ba" siriryar iskar ta furzar daga bakinta,itakam ta gaji da zancan cikin nan da taketa jawo mata shi d baki a gaban wannan dan izzar wanda ko a yanzun yana tsaye qyam kamar tsohon soja yana danne danne a wayarsa,sai ka rantse da Allah babu shi a dakin kwata kwata,ko kuma baisan abinda yake faruwa ba "Am on my period " ta fada qasa qasa cikin jin takaicin tona asirin kanta da tayi da bakinta. Duk yadd tayi qasan da muryarta sai da yaji din, sauke wayarsa yayi saboda shigowar kiran jibril "Zan fita yanzu,thanks dr,zan saka elyas yayi magana dake" "Thank you sir,Allah ya bata lafiya" "Ameen" ya amsa sannan ya maida dubansa gareta "Take care" ya furta softly wanda sãahar ta tabbatar na ganin ido ne,bai tsaya jiran respond nata ba ya juya cikin nutsuwar nan tasa yana ficewa a dakin. *H U G U M A* *_TABARMAR ƘASHI_*💔 Book 02 Page 21 Ta kusa mintuna talatin tsaye a bakin window dinta tana jiran feedback na abinda ta shirya,first plan dinta kenan. A gaggauce ta sauke labulen tana amsa sallamar masura me aikinta data aika ta sanya mata ido akan abinda zai biyo baya. Shuru tayi har masura ta gama labarta mata,taja wani numfashi me tsaho ta fesar da me zafi "A taqaice kinason kice ba wani rashin jituwa daya gilma a tsakani?" Kai ta gyada "Dukka ma suna sassan nasa,harda Dr raheema,kamar ma batajin dadi ne" "Tashi kije" ta bawa masura umarni,sai ta miqe tsam ta fice. Hannunta ta dunqule tana dan dukan daya tafin hannun nata dashi. Tayi missing target dinta,a gobe meenal zata sauka a gidan kuma tun a yau taso ta haifar da gagarumin rikici gami da rashin fahimta a tsakaninsu,to amma ya akayi ta kuskure?. A mganganun data gaya masa game da yarinyar tayi zaton har sai ta shiga maganar wajen sasantasu. Mamakinta da daurewar kanta ya sake qaruwa lokacin da taji tashin motarsa,ta sauke labulen nata ta koma ta zauna saman sofa din dake falon. Tayi nisa a tunani har bataji lokacin da me aikinta ke gaya mata ta gama gyaran dakin meenal ba har sai data maimaita "Good,ki wuce sashen su nadeeya,cikin dakunansu ki sake gyara mata daya a can" "Okay hajiya" ta amsa mata a ladabce tana fita. Tayi hakanne saboda ta samar da kusanci na mussamman tsakanin meenal nadeeya da kuma fadeela data tabbatar itace ruhin toufeeq. Qarfe sha biyu saura na dare ya samu dawowa,sanda ya shigo falon babu kowa,har qwayayen lantarki duka a kashe sai masu qarancin haske da aka bari kada duhun yayi yawa. Dining ya duba,kusan a yanzu bazai iya cin komai ba,amma kuma yunwa yakeji,dole ya zauna ya tsakura abubuwan da basu cika nauyi ba,su dinma baici da yawa ba ya ture,inda zai samu wannan hadin coffee din da yafi kowa murna,zuwa yanzu ya fara fita a kansa,saboda yasan idan ma ya hada baya masa dadi kamar nata,abun ya zame masa kamar jarrabi. Cike da gajiya data qarawa tafiyarsa nutsuwa yazo zai wuce,idonsa ya sauka akan qofar dakin nata. Tunda ya tafi meeting din hankalinsa ke a rabe gida biyu wanda shi kansa baisan ainihin dalilin hakan ba. Har ya gota sai kuma ya dawo,ko ba komai haqqinta ne a kansa ya kula da lafiyarta kamar yadda take qoqarin kula masa da lafiyar diyarsa. Haske ne sosai a dakin,da alama bacci ya dauketa ne ba tare data shiryawa hakan ba,don fadeela na kife ne saman cikinta,hannuwanta zagaye da bayan fadeelan. Gabansu ya qarasa ya tsaya sosai yana kallonsu,suna rungume da juna tamkar uwa da 'ya. A hankali ya zame ya durqusa daga gaban gadon inda suke kwancen,idanunsa saman fuskarta da take looking innocent cikin bacci,bayan a idanu biyu cikakkiyar matsiwaciya ce,sassanyan kyan nan nata da babu abinda ke sanyawa ya gushe shinfide akan fuskar tata. Da sauri ya dauke idanun nasa daga kanta ganin yadda suka fara yawo saman pink lips dinta,kwanyarsa nason tuna masa abinda yaji a wancan lokacin da ya nada lips din nata da nashi. Har zai miqe yaji alamun fitar numfashinta kamar ba dai dai ba,alamu suke nuna fadeela kenan tayi mata nauyi,sai ya zare duvet din data lullubesu dashi,ya soma zare fadeelan daga jikinta. A firgice ta farka tare da sake qanqame fadeelan cikin zafin nama tana kiran sunanta. Cak ya tsaya yana dubanta cikin mamaki,gaba daya ta firgita kamar ana zare numfashinta ne. Sakar masa fadeelan tayi a hankali bayan sun hada ido,sai ta tsuke fuskarta tana qoqarin gyara gabab rigarta da ya tattare saboda janye yarinyar da yayi yasa ya bude don rigar me santsi ce,saita juya right side dinta tana sake jan duvet din sosai tana lulluba har saman kanta,cikin ranta tana jin haushin yadda kowanne lokaci yake shigo mata daki ba tare da neman izini ba,dole tayi masa magana,ba zata juri wanann ba,a duk yanayin da kake ciki sai mutum ya ganka kenan a haka?. Shima yana gama gyarawa yarinyar kwanciya ya tofeta da addu'a sai ya juya ya fice,tabi bayansa da kallon harara ta cikin duvet din, cikin sa'a ya waiwayo don ya manta bai kashe musu haske ba,tayi hanzarin maida idanunta ta kulle,sai kawai ya basar amma cikin jikinsa tabbas yaji tana kallonsa,ya kashe wutar yaja qofar ya fice,yadda ta firgita da jin ana jan fadeela na tsaya masa a rai,ya sauke sassanyar ajiyar zuciya sanda ya kammala shiga nasa dakin ya zare takalmansa a gajiye ya watsar dasu a gun ya zube saman sofa bed yana dage kansa saman bayan ya watsa hannayensa. Yana fita ta waiwayo ta jawo yarinyar cikin jikinta,sai yau zasuci gaba da kwana tare,don kullum maji hanawa takeyi tazo,a nata nufin a barsu su sake,kuma fadeela tayi girma da kwana cikin iyayenta. Idanunta a rufe amma tana bitar abubuwan da suka faru wunin yau,bata jima tana wannan dogon tunanin ba bacci yayi awon gaba da ita. ***karfe biyar da rabi ta idar ta farka,a nutse ta sauka daga saman gadon,jikinta ya sake sosai,babu ciwon kan ko kadan,sai dan rashin qwarin jiki dan kadan. Bandaki ta wuce ta daura alwala ta dawo ta shimfida abun sallah,sai data idar sannan ta tashi fadeela,tana gamawa a nan gefanta saman abun sallar ta bingire bacci ya sake daukar yarinyar. Tayi nisa wajen yin azkar dinta,yayin da gefe daya kuma qwaqwalwarta ke cike taf da tunani daban daban. Wayarta ce tayi haske kadan,ta jawota tana dubawa, afifa ce ta turo mata saqo,murmushi ya subuce mata tana girgiza kai,wato sajjad yana so ya sanyata ta manta da ita,lallai sunci bashi,bari a gama amarcin ta nemeta saita tsigaleta tas. Tana shirin buda saqon sautin knocking ya ratsa kunnuwanta,ta tsaya tsam daga qoqarin bude saqon da takeyi tana son tantance daga inda sautin yake fitowa,don dai tabbas ba qofar dakinta akewa knocking din ba. Har ta basar jin cewa ba tata qofar ake bugawa ba,ta buda saqon afifa tana dubawa,wanda saqon sannu da jiki ne da kuma ban haquri,saidai har ta gama karantawa ta maida mata reply ba'a daina buga qofar ba. Maida idanunta tayi ta rufe bayan ta kalli agogo,duka duka yanzun qarfe takwas ne da wasu mintu na safe,to waye zai shigo har nan din yana irin wannan nacin qwanqwasa qofar?. A hankali bugun ke qara yawa,qaramin tsaki ta ja,ba kasafai ta fiyason hayaniya da safe ba,ta miqe a hankali tana gyarawa fadeela kwanciya ta nufi qofar dakin nata. Cikin nutsuwa ta murda handle din ta bude qofar,ta kuma sanya kanta tana leqen tsahon hallway din don ganin me bugun da kuma dakin da ake bugawar. Hakan yayi dai dai da sanda shima ya buda qofar tasa,ya kuma sanyo kansa waje,fuskarsa tayi wani fresh da hasken sallar asuba tare da wani irin tarin nutsuwa da kamala da yake da ita. Ido suka hada shi da ita,manyan fararen idanunsa da bacci yadan qara musu haske da girma,a tare suka janye dubansu sannan ta sauke kallon nata akan matashiyar dake tsaye gaban qofar dakin. Sanye take da skinny jeans da wata t.shirt da iya tsahonta qugunta,qafafunta dogayen takalma ne masu tsini da igiyoyi a jikinsu,sai qaramin Scarface dake kanta wanda iyakarsa wuyanta,ba wani abu da ya rufe mata,bata iya ganin fuskarta,amma duk da haka zaka iya gane tsananin sirantar da take dashi da kuma hasken fata. "Yaa moha" ta fada da muryarta me tsananin sirantaka, muryar na dan rawa kadan alamun kuka takeson saki. A nutse ta maida jikinta ta kuma maida qofar dakin nata ta kulle,kwanyarta nason tuna mata wacece ita?. Gefan gado ta koma ta zauna tana qarshe cikon hailalarta da take guda dari duk rana safiya da maraice 200 kenan. Gefe daya kuma yarinyar na mata yawo a idanunta "Haseena,'yar hajiya qarama" wani lungu daga qasan zuciyarta ya cillo mata amsar,bayan ta gama qirga kwanakin da hajiyan tace mata zata dawo,haka yake,indai lissafinta yayi dai dai kenan. Qaramin murmushi ne ya qwace mata a fuskarta,tadan girgiza kai kawai,wanann itace haseena din da hajiyar keta kururuta zuwanta?,saita girgiza kai kawai,ta sauka a hankali ta dauke fadeela ta maida saman gadon itama ta koma ta kwanta tana jan musu duvet. Dakin ya dauki shuru na wasu sakanni,tana ci gaba da salati qasan ranta idanunta a lumshe,dukka hallway dinma shuru,babu alamun motsin mutum kwata kwata. Sanda ta maida qofar ta rufe duka akan idanunsa,a nutse yana kuma qarawa fuskarsa rashin walwala ya sauke dubansa akan yarinyar. Idanunta cike suke taf da qwalla,ta ritsashi da idanunta tana kallonsa da kyau,sai kawai ta zame jakar dake rataye a kafadarta ta ware hannunta da zummar rungumarsa. Da sauri yaja da baya yana jifanta da wani kallo "Meenal,meye hakan?" Ya furta a mugun dake,tsaiwa tayi sak tana kallonsa,hawayen da take maqalewa na gangarowa "I want to be in your arms yaa toufeeq please" ta furta tana sake sakar masa kuka. Tsaiwa kawai yayi yana kallon ikon Allah,yadda qanqanuwar yarinyar da aka haifa ta taso a gabansa ta zama haka,totally ma ta canza,tun daga yanayin halittarta kawo dabi'unta,tayi wani irin girma kamar sa'arsa,duk da cewa 'yan watanni ne tsakaninsu da nadeeya,amma sai ka rantse gaba take da nadeeya. Ganin baice komai ba sai hannunsa sa ya goye kawai a qirji yana mata wani kallo da batasan inda ya dosa ba,saita sulale a gurin ta duqa saman qafafunta tana sake sabon salon kukan "Yaa toufeeq,i can't take it anymore,duk tsahon wanann lokacin da naqi kula kowa kai nake jira,na saka raina da duka burina a kanka" sai taci gaba da gaya masa abinda ke ranta kai tsaye ba kunya ko kwana kwana,gaba daya kansa sake daurewa yayi,yaushe ta zama mara kunya haka?. "Look meenal" ya kirata yana sake hade ransa da kyau,a hankali ta daga idanunta da suka jagale da hawaye ta kalleshi "Dama ina wasa dake?" Ya fadi da wani irin tone da ya fidda kwarjininsa har ya kusa bugar da ita,qoqarin tattaro dukka dauriyarta tayi,da gasken gaske takeson toufeeq fiye da lokacin baya kafin dawowarta da ganin da tayi masa yanzu,a wannan lokacin da tayi ido hudu dashi,bawai cikin hotunansa da take faman wallafawa ba,ta sake jin cewa a shirye take ta karba toufeeq din daga hannun kowacce mace "Kaga alamar da wasa nake yaa moha?,kaga alamun wasa cikin soyayyar da nake maka?" Ta tambayeshi idanunta cikin nasa hawaye na sake wanke mata fuska. Abun sai ya koma bashi mamaki qwarai,yayi shuru yana karantarta "Yaa toufeeq please say something,kayi magana mana,da gaske nake maka,bazan iya jurar rasaka ba,i can do anything a kanka,ciki kuwa harda kashe kaina muddin na rasaka!" Cikin 'yan mintuna qalilan ya gama fahimtar da gasken take fa,duk abinda take fadi din da gaske ne zata aiwatar,shi sai yake ganin ma kamar ba cikin saitinta take ba. "Muje parlor" ya fadi yana nuna mata hanya,dole tana buqatar guidance and council,ya kamata ta fahimci shi din a matsayin yaaya yake a wajenta bawai masoyi ko mijin aure ba. Kamar ba zata tafin ba har sai da ya maimaita mata yana sake hade fuska,sai tayi gaba tana qoqarin tsaida hawayen nata. A hankali ta bude idanunta saboda gajiya da tayi da rufesu din,baccin kuma da take sanya ran zuwansa baizo ba,batasan me zuciya da kunnuwanta suke jira ba,sai ta miqe a nutse tana gyara top din rigar baccin jikinta me rubi biyu,ta jawo dankwalinta me santsi daya dace da rigar ta daure kanta ta zuro qafafunta ta sauko daga saman gadon. Gaba daya ta manta da batun shan ruwan duminta,ta zura bedroom slippers dinta ta nufi qofa. Duk yadda taso ta dauke kai daga kallon qofar dakin da a dazun yarinyar ke tsaye amma ta kasa controlling din idanunta. Ba kowa yanzu a qofar dakin,saidai kamar a bude take bawai a rufe yadda ta saba ganinta ba kullum. Batasan dalili ba amma sai ta samu kanta da jan qaramin tsaki,ta juya tana fita a gurin. Muryarsa a tausashe kunnuwanta suka fara jiyowa,a lokacin da yake magana da haseena cikin son kwatanta mata abinda ke cikin zuciyarta ba me yiwuwa bane "Ka fahimceni yaa toufeeq,nima ba yin kaina bane,bansan lokacin da zuciyata ta kamu da matsanancin sonka ba,a yanzu kuma ba abinda kunnuwana zasu iya fahimta sai yaren sonka kawai" daidai lokacin idanunsa dana sãahar dake qoqarin wucewa kitchen suka hadu waje daya. Har tsakiyar kanta taji kalaman yarinyar da muryarta me bala'in sirantaka,ta lumshe idanunta tana daukesu daga kan toufeeq din,wani tsanarsa na darsuwa a ranta. Shikenan shi bashi da aiki sai jefa soyayya a zukatan 'yan mata?,su kuma basu da aiki sai zub da kima da martabarsu?,shin wai basajin kunyar roqon soyayya daga gurin namiji?, namijin ma irinsu toufeeq din me zafin kai izza da jin cewa shi din wani ne?. Bata sake bari kunnuwanta sun jiye mata komai ba ta daga qafarta ta shige kitchen din da dan sauri kadan,sai a lokacin ya dauke idanunsa daga kanta,baiga komai saman fuskarta ba kamar yadda ya saba gani a baya akan fuskar AMEESHA a duk lokacin data fahimci wata mace tana ra'ayinsa,koda kuwa bata furta ba,a ranar babu zaman lafiya ko kuma kwanciyar hankali. Idanunsa dake dauke da wani irin maganadisu wanda ke sake dasa mata kakkaifar soyayyarsa cikin zuciyarsa ya zube mata cikin kowanne lungu na jiki da zuciyarta. "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 22 • "Kije ki huta tukunna" ya fadi wa meenal din yanason shawo kan matsalar ta lumana,bayason akai ga ta qure dan garamin haqurinsa a kanta. "I will be back to you koda baka nemeni ba" bai iya cewa komai ba don shi har yanzu yarinyar na bashi mamaki ne. Banda ita din itace tabbas inda watace bata isa ya tsaya bata lokacinsa wai yana saurarenta ba. A abinda ma tayi masan na binsa har bedroom dinsa,abinda fadeela ce kawai ke da wanna damar, tabbas zafafan maruka ya kamata ya bata,to ko a yanzun ma baisan meye ya sanyayashi har haka a kanta ba. Iska ya furzar a bakinsa,yana shirin migewa Jacob ya shigo. Cikin matuqar girmamawa ya gaidashi "Sir do you need something b4 i prepaid breakfast?" "Warm water as usual" ya furta yana murza yatsansa a goshinsa. "Jacob" ya kirashi da wani hanzari wanda har sai da Jacob din ya dan zabura,sam ya sha'afa tana cikin kitchen din,sannan idan ya tuna da kyau sleeping dress ne kaman a jikinta,duk kuwa da cewa ko ina nata a rufe yake, amma ya tabbatar indai silky clothes ne dole su fidda wani abun koda baka sani ba. "Come" ya fada yana gyara zamansa cikin sofas din. Gabansa ya qaraso ya tsugunna "Daga yau na canza maka kitchen, zaka koma amfani da extra kitchen dake backyard" "Okay sir, but inason gaya maka ma,if possible zanje gida gobe, momma na bata jin dadi" mutum ne shi mai bada uzuri ga ma'aikatansa,musamman idan ya shafi lalurar iyali ko ta iyaye "No worries* ya amsa masa a taqaice. Yana zaune har zuwa sanda Jacob ya dauko key na kitchen din,ya juya yana fita ta qofar gaba don yace kada ya bude ta qofar dake cikin main kitchen din. Har ta tafasa ruwan tana jira ya huce sai taji batajin shansa, tayi taku biyu zata fita sai taja ta koma tana jan tsaki, kwata kwata bata qaunar sake giftasu bare taga kayan takaicin dake faruwa a falon. Tana mamakin yadda mace zata zub da kanta tayi tallan kanta a inda ba'a san daraja ko kimarta ba,me yasa suke rufe idanunsu.ne wai kaman basusan halinsa ba?. Sake jan tsaki tayi a karo na biyu,ta bude daya daga cikin locker's na cabinet din inda aka jera duk wani kayan tea,ta fara hada milk tea, ko bata sha ba ta ajiyewa fadeela,ta tabbatar kwana biyu tayi missing girkinta. Sai data gama hada komai tsaf sannan ta javo. daya daga cikin kyawawan kitchen stool din dake kitchen din wanda suke iri daya sak da jikin cabinet na kitchen din. ta zauna a kai. Hannunta a qirjinta tana duban tukunyar da ta fara tafasa,qamshin cardamom na 'ana'ana da madara da flavour yana tashi kadan kadan yana cika kitchen din. Zuciyarta nason fadawa tunani amma tana turewa daga ranta, don batason yau kwata kwata ta kwana da wani ciwon kai bare a gobe ta rasa karsashin fita office a goben kamar yadda Dr jarma ya umarta Tun kafin ya qarasa shiga qamshin yayi masa maraba,ya lumshe ido yana sanya kai a kitchen din, bakinsa dauke da sallama gasa qasa. Bata waiwayo ba ta amsa sallamar tana sake gyara yafen dankwalinta,kadan kadan yake dora idanunsa akan fuskarta,da gaske baiga alamun komai saman fuskartata ba. Ya garasa shigowa yana dauke kansa,ta qasan idonsa kuma vana satar kallon coffee pot dinta dake shirin fara tafasa wadda va tabbatar a nan gamshin da ya game sassan yake fita. "'Ina kwana" ta fada ciki ciki tana murza yatsunta wadanda ke da sauran shatin jan lallen biki a jiki "'Idan mutum vace bakisan daraiar ilkinki ba fitsarrun bakin nan naki yace zai qaryata right?" Ya fada yana kafeta da shanyayyun idanunsa. A bazata maganar tazo mata,sai ta daga fararen idanunta ta zubesu a fuskarsa wani abu me gyalli daga tsakiyarsu ya fusgeshi da qarfi ya maida nasa idanun ya lumshe, abinda dama yaketa son gani kenan, tsakiyar qwayar idanunta "Ya kamata Jacob ya ganki a haka?" Yayi mata tambayar da wani yanayi da ya tunzurata "Ya kamata Jacob ya zama yana shiga kitchen dinan?, Kai ka damu dashi,ni dukkanku ban damu da wanzuwarku ba" shine abinda takeson gaya masa,amma sai wani sashe na zuciyarta ya kwabeta,uwa uba kuma a yau batason bashi damar da zai shanye mata tea ya barta da zafin lebe don haka sai ta kauda kanta kamar ba da ita yake ba. Hakan da tayi sai yaji abun ya zafafeshi "Am talking to you" ya fada adan kausashe,har ta dago kamar zata kalleshi sai ta fasa, ta sauka daga kan stool din tana nufar tukunyarta sannan tace "To" ta dauki garamin rariya ta fara tace ruwan madarar da ya tafasa yasha kayan qamshi. A nutse ta gama juyewa,ta ajiye kayan ta juya tana barin kitchen din. Tukunyar data bari a wajen ya kalla,ya danja tsaki yana tambayar kansa tsoron yace ta dafa masa yakeji ko kuwa?. Kai ya girgiza "No, bayason raini ne kawai" dole qanwar naqi ya jona coffee maker din yana hada kayan tare da addu'ar Allah yasa yayi dadi. K'arfe sha biyu da rabi na rana suna zaune a falon, ranar farko kuma karon farko da ta taba zama a falon bawai wucewa ba,hakan ya faru ne saboda nacin da fadeelan ta dinga yi mata "Please anty N mu zauna kawai a nan,nan din yafi dadi, kuma sai nafi sanin abby ya dawo,daxun yayimin alqawarin kawomin cookies" kumatunta ta kama taja tana murmushi "Bakin kwadayi,shi yasa kike qara kumatu" hirar da suke ne ta tsaya cak, fara'ar fuskarta kuma tayi gaura duka lokaci guda. A nutse ta tashi daga durquson da tayi tana duban fuskar IG celebrity MEENAL YA'AQOUB AJI,wadda ta shahara da dora mabanbanta hotuna da fuskokin MT JARMA da Instagram basa gajiya da recommending mata ita tamkar ta buqaci haka daga garesu. Ta bangaren MEENAL itama sanda take takowa nata idanun suna kan fuskar säahar din, wani irin abu me girma yana zarta mata tun daga tsakiyar kanta har zuwa tafin qafarta. Jikinta dukka ya fara fidda gumi tana jin wani rudani yana shigarta. Addu'a takeyi qasan ranta. Ya Allah ya sanya ba wannan bace matar yaa moha, Allah ya taqaita wahalarta ya sanya ba ita bace,muddin hakan ta kasance tasan babu ta inda zatakai labari wajen hada kyanta da take taqama dashi dana sãahar din. Duba daya tal ta yiwa meenal din ta dauke idanunta daga kanta,saboda cikin qasa da minti daya sautin muryarta ya tabbatar mata itace haseenar hajiya qarama. Yadda ta debeta ta watsar itama ya bata amsar cewa ita dince, itace matar da tasha gaban burinta takeson kawowa cikar burinta barazana,wannan tunanin ya sanya ta sake tsuke fuska itama "Ukhtie....abby dinki yana ciki?" Ta tambaya don gudun karya tsarinsa, kamar yadda a dazun ya gargadeta kan bayason irin wannan zuwan "Ya fita" fadeelan ta amsa mata a taqaice don ba wani sabo ko shaquwa bane me yawa a tsakaninsu,don meenal din na hannun mahaifinta tun tana da shekara goma sha biyar, kawai lokaci lokaci ne take zuwa musu hutu,tunda kuma ta shiga university ma bata sake zuwa ba sai yanzu data kammala "Okay" meenal din ta fada, cikin satar kallon sahar ta samu waje ta zauna, ta kuma dora qafa daya saman daya ta fidda tsadajiyar wayarta ta fara dannawa. Tamkar batasan Allah yayi ruwanta a gurin ba sukaci gaba da hirarsu da fadeela, nadeeya duka yau din bata nan, don haka sai su biyu. Har zuwa lokacin sallar azahar yayi ta janye fadeela suka wuce dakinta suka bada farali, sannan suka fice daga sashen don komawa sashensu,saboda yau tana da sha'awar yi musu abincin dare abinda tunda ta dawo gidan batayi ba. Bayan sãahar din meenal tabi da kallo, tana da izza fiye da tata tana kuma da miskilanci da jin kai da yafi nata yawa yanzun ta ina zata fara quntata mata? ta wanne bangaren ya kamata ta fara ajiyewa rayuwarta bacin rai?, sai kawai ta gyara kwanciyarta cikin qayatattun kujerun falon tayi kwanciyarta hankali kwance,ta dauki. waya ta turawa hajiya qarama tex don kada tayita bulayin nemanta cikin gidan. _tambayoyin dani kaina bansan amsarsu ba,saidai lokaci zai bayyana mana komai "HUGUMA* "TABARMAR KASHI' Book 02 Page 23 *****Tsaye take cikin kitchen din tana qoqarin rufe lunch bag din fadeela dake dauke da tarkacen kavan beak dinta na makaranta. Sanye take da wata lafiyayyar tattausar abaya sagar dubai, da aka sagata da zare da kuma yadi me tsananin kyau da tsada. Maroon color ce wadda aka yiwa ado da bagi da kuma zaiba a jiki. Daga ciki kuma wani lallausan cotton lace ne maras nauyi wanda aka yiwa dinkin riga me dogon hannu da straight skirt. Daurin kanta ya zauna das sakamakon yadda ta yiwa gashin kanta gammo daga baya ta kuma daura dankwalinta ya zauna mata dass da samfurin daurin dankwalin nan da ake kira zahra buhari. Wani irin tattausan gamshi take fitarwa,wanda ya zame mata al'ada ya kuma kama suturunta da kyau. Turaren wuta na kaya me asalin tsada wanda take samu takanas daga masu abun wato garin mahaifinta BORNO. Wani irin sassanyan kyau tayi a safiyar kyau me ratsa idanu da shiga zuciya,ba tun yau ba shigar laffaya na daya daga cikin shigar dake matuqar qara mata kyau da matuqar da kwarjini, takan koma kamar balarabiya tare da fita a ainihin yarenta na SHUWA-ARAB. Dai dai lokacin da dukka motocinsa da suke fita zuwa kamfani suka gama komai, fitowarta kadai suke jira, harda toufeeq din dake zaune cikin motar. Sanye yake da wasu kurtas charcoal color da suka dace da farar fatarsa,hankalinsa duka suna kan system din dake cinyarsa yana shigar da wasu bayanai akan meeting din da sukayi a daren jiya shida board members na sabon kamfaninsa da zai fara aiki wata me kamawa, dai dai lokacin da yake sanya ran ya kammala da kamfanin MT JARMA. Ta cikin eye glasses dinsa ya daga agogon hannunsa daya kwanta luf cikin gargasar data zama tamkar rumfa wa fatarsa vana duba lokaci. A galla sunyi zaman jiran mintuna goma kenan zuwa sha biyar,baya cikin tsarinsa bata lokaci da saba lokacin zuwa aiki,gashi tana son zama silar haka a ranar farko. Qaramin tsaki yaja yana ajiye system din, sannan ya buda gofar side dinsa a hankali yana zura gafafunsa waje. Da sauri elyas ya matso,sai ya daga masa hannu,ya fahimci me yake nufi don haka ya koma da baya yaci gaba da tsaiwa a gurbinsa. Har ya sako daya qafar ya hangi tahowarsu,fuskokinsu gaba daya cike da wani irin walwala da annuri ita da fadeelan, tana riqe da lunch box din fadeelan,ta kuma rataya school bag din nata still a daya kafadar, daya hannun kuma na riqe da hannun yarinyar. Sak suka fito a 'YA da UWA,wani abu ya taba zuciyarsa ya kuma tuno masa shekarun baya,a lokacin da yake da shekaru kwatankwacin na fadeelan,lokaci da maji ke riqe hannuwansa kamar haka ta kaishi makaranta sannan ta wuce gurin nata aikin. Anutse ya zare idanunsa daga kansu,ya maida qafafunsa cikin motar tare da jan murfin motar. Karo na biyu idanunsa suka sake sauka a kansu. Dai dai sanda ta zame hannunta daga na fadeela tana gyara yafen lafayar jikin nata,zara zaran yatsunta da aka sakawa lalle a jiya suka bayyana hakan sai ya tuna masa da wani lokaci can baya, ranar farko data mige cikin taron ma'aikata kamfani don ta gabatar da nata aikin. A ranar dukkan wanda ya kalla cikin mazan dake hall din idanunsa vana kanta, daya bayan daya ya dinga bin fuskokinsu da kallo ba tare da sun sani ba,haushi da takaicin da ya sanya yace ta hada file din kenan zai duba a gida ko office ba tare data garasa cinye mintuna goman da suka rage ba. A yau ma sal ya samu kansa da sauke dubansa saman fuskokin guards din nasa dake tsaye suna dakon fitowarta. Daya bayan daya yake nazartarsu,sai ya janye idonsa yana furzar da iska daga bakinsa. Kusan mutum biyar a cikinsu idan idanunsa sun gaya masa dai dai kamar ita yaga suna kalla. Jamal daya daga cikinsu ya hanga yana gyara tsaiwarsa tare da gyara zaman glasses dinsa. Haka kawai yaji wani abu me nauyi yana sauka a hankali saman qirjinsa. Jamal na daya daga cikin mazan da Allah ya jarabta da son mata,mutum ne me yawan kule kule, abinda ya sanya tasu sam batazo daya da toufeeq ba. Kusan sau biyu yana dakatar dashi kafin ya samu ya maida hankalinsa ya kuma dai daita kamar yadda tsarin duka yaransa suke. "Madam…madam" muryar adama daya daga cikin masu aikin dake aiki a sassan hajiya qarama ta ziyarci kunnenta. Cak ta tsaya tadan juya kadan har adama ta qaraso "Abincin makarantar fadeela ne......inji hajiya qarama" ta fadi a ladabce. Sosai ta kalli qawatacciyar lunch bag din dake rige a hannun adama, mamaki yana sauka a ranta. Yaushe har aka canza tsarin baiwa fadeela abincin makaranta?, lallai da gaske matar nan take, qaramin murmushi ya subucewa fuskarta wanda ya sake qara bayyana kyanta "Ki gaya mata ummarta ta riga ta tanadar mata komai" ta furta tana daga mata lunch bag din hannunta. Kalla adama tayi saita juya tana komawa ciki. Saita juya tana ci gaba da tafiya tare da jan siririn tsaki, tsanar matar yana samun gurbi cikin zuciyarta. Idonsa ya dauke daga kanta yana lumshesu,yadda ta juya tsukakken bakinta da yasha Marron lipstick yana wulgawa ta cikin idanunsa,ya rasa me yasa tsiwa take mata dadi,idan tayi tsiwar kuma sai ta sake maidata kamar wata qaramar yarinya. Tun kafin ta garaso tayi noticing motar da yake ciki,don haka sai ta tsaya daga motar da aka kebe saboda kai fadeela makaranta da kuma sauran uzurorinta, budewa fadeela gaba tayi,ita kuma ta shiga seat din baya. Jibril ne ya duga vana rufe motar sannan ya zagayo yana gogarin tashinta "Madam tace zamu fara sauke fadeela a makaranta sannan mu wuce" jibril ya fada cikin girmamawa. Mamaki ya kamashi, me kenan?, bayan yarinyar nada driver?,so a lokacin bashi da lokaci dogon surutu,don haka ya gyada masa kai kawai,motocin suka fara tashi a nutse suna ficewa daga gidan. Sanda security na gidan ya kammala rufe qofar bavan fitarsu a sannan hajiya garama ta garaso farfajiyar gidan a birkice, cikin matsanancin fushi take bin shatin tayoyin motar da kallo "Uban waye yace ki dawomin da abincin saboda ta fadi haka? me yasa baki tsaidasu ba kin kuma shaidamin kafin fitarsu daga gidan?" "'Kiyi haquri hajiya,ban zaci...." Kyakkyawan mari ta sauke a fuskar adama tana wani irin huci,wanda hakan da tayi dai dai yake da haushin kaza huce kan dami. Har ta buda baki zatace wani abu sai kuma ta fasa,saboda koma meye yanzu zata fada din bashi da amfani, saboda komai ya riga ya ruguje, amma tabbas ba zata taba bari komai ya tafi a banza ta ruwan sanyi haka ba. Tana takawa cikin qida take gava mata "Ki cewa bala va shirya nan da awa daya zai kaini makarantar su ukhtie " bata tsaya jiran amsa ba tayi gaba cikin tsananin fushi. A kan idanunsa yana ganin sanda ra budewa fadeela gofa ta rataya mata jaka da lunch bag dinta,ta tsugunna tayi kissing dinta ta kuma rada mata wata magana dashi kansa baisan me tace mata ba,fadeelan ta doso motarsu,ganin haka ya sanyashi bude murfin motar tun kafin ta garaso. Murmushi fal saman fuskar yarinyar, saboda hirar da sukayi da säahar din cikin motar, tana jaddada mata daga yau itace zata dinga kawota tana kuma maidata gida. Kidding goshinta yayi sai tace "Yau abby ka rakoni makaranta, inajin dadi sosai " hannunta da a yanzu suka zama masu kauri ba kamar a baya ba ya kama yana murmushi ya jinjina kai, sai ya sanya hannunsa saman kanta ya shafi kan "'Barakallahu fiik, ayi karatu da yawa" hannu ta daga masa tana masa bye bye, idonsa ya sauka akan motar fadeelan, säahar ta koma ta zauna cikin motar,har fadeela ta juya ya kirata "Angel" sai ta dawo da sassarfa,ya danyi shuru yana juya maganar a ransa,bayason ya fadi ta dauki maganar da wata manufa daban,haka kawai cikin zuciyarsa yakejin bai dace su zauna mota guda daga ita sai driver ba,yayi gogarin hana kansa gain baiken hakan amma ya kasa,idanunsa nata sake dawo masa da irin kallon da ya gani daga idanunsu jamal a dazu "'Kije ki gayawa autynki ta dawo wannan motar". Shuru tayi tana duban fuskar fadeela sanda take gaya mata saqon toufeeq din, kafin takai ga yin komai fadeelan ta dauki handbag dinta tayi gaba da sauri tana cewa "Nima bari na tayaki aunty" bata da sauran zabi illa bude murfin motar da tayi ta fita a hankali tabi bayanta. A nutse ta zauna elyas ya maida murfin ya rufe, qamshinta ya mamaye motar,ta gyara zamanta sosai tana maida dubanta ga bakin qofa sannan tace "Good morning" a taqaice, saidai ko uffan bataji yace ba. Ranta ya baci sosai, ba abinda a yanzun yake takura mata irin wannan gaisuwar data zame mata qadangaren bakin tulu,idan tayi ya amsa mata da qyar,idan kuma bata yin ba tana tsoron abinda ya furta zai aikata mata. "'Good morning" ta sake fada adan qufule, idanma bata maimaita ba tasan tsaf zaice bata gaidashi ba. Dukka gaisuwan nata yaji sarai, amma yadda ta juya baya tana fuskantar gofar sannan ta gaidashi kamar dole ya bashi haushi, yadan dauke idanunsa daga kan system din ya aza mata su "Wani ne yace dole saikin gaidani?, ki riqe kayarki bana so daga yau,don ba qanfar gaisuwa nakeyi ba,na saka miki dokarta ne saboda na saitaki kan abinda ya dace" daga haka ya maida dubansa ga allon system din. A yau din karon farko taji jikinta ya sanyaya da yadda yayi mata magana,babu wannan fadan Sam cikin muryarsa sai wani irin softness har cikin ranta taji abun bai kamata ba,don haka ta gyara zamanta da kyau tana dan fuskantarsa "Barka da asuba" fa furta itama da sanyin muryarta. Tsigar jikinsa ne yaji ta zuba,ya daga idonsa a nutse sai suka hada ido,kowannensu ya janye dubansa da sauri "Barkanki" "An tashi lpy" "Alhamdulillah" ya fada ba tare da ya sake dubanta ba, daga haka ta rasa abinda zata sake fade, saita ja bakinta tayi shuru tana maida dubanta ga hanyoyin da suke ratsawa da gudu. "HUGUMA* • TABARMAR KASHI Book 02 Page 24 Har suka isa company din babu wanda ya sake cewa da dan uwansa komai. Jibril nayi parking a parking lot na company din ya kashe motar sannan yayi magana ba tare da ya waiwayo ba "Akwai employees da suka shirya welcoming naku,da tayaku murnar aurenku,suna entrance na main building" system din ya sauke daga saman cinyarsa yana ajiiveta gefe daya,idanunsa akan jibril "'Waye ya sanar musu da hakan?" Ya jefa masa tambayar da salon tambayarsa din nan me cike da dakewa. Cikin dan daburcewa jibril din yace "Yallabai sajjad ne" dauke dubansa yayi daga kan jibril,ya gama gano abinda sajjad din ya shirya, sai kawai ya bada umarnin bude gofofin motar. Kusan dukka manyan ma'aikatan company dinne suka jeru sahu biyu hagu da dama, kowanne dauke yake da gift a hannunsa,wasu flowers wasu boxes,mafi akasari sunyi hakanne saboda säahar din, don babu wanda baii cadin mu'amalarsa da ita ba,basu sake tantance muhimmancinta ba sai bayan tafiyarta,yanzun kuwa data dawo musu a karo na biyu sai hakan yayi musu dadi gwarai. Ta tsakiyarsu suka fara takeaway a nutse,duk wanda zasu gifata sai ya ranqwafa cikin girmamawa. Mr hamza shine mutum na biyu a sahun, sunzo dab dashi ya ranqwafa idanunsa akan fuskarta "Sir, congratulations, congratulations sir" ya fada da dan murmushi saman fuskarsa,sannan ya miqa flower din ga sãahar. Baisan ya akayi ba,yadai tsinciki kansa da sanya hannu ya karba flower din daga hannunsa ya miqawa elyas tare da yi masa inkiya, sannan a hankali ya sanya hannunsa ya lalubi hannunta, ba zato ba tsammani sai jin tafin hannunta yayi ya manne da lallausan tafin hannunsa guri daya,ta waiwayo da hanzari tana dubansa idanunta kuma suka fada cikin zagayayyun fararen idanunsa. Zame hannunta taso yi cikin hikima da dabara amma ya matseshi tsam cikin nata,saboda ya fuskanci idanun mr hamza na kan hannayen nasu "All eyes are on us" ya fada qasa qasa,a hankali itama tayi noticing hakan, musamman daga idanun mata da yawa da dama can ba huldarsu take shiga cikin company din ba, da masu goqarin shiga gonarta amma tayi musu iyaka irinsu saima. A gaggauce suka dinga wucewa,hakan ta bishi saboda hannunsu na cikin na juna. Bai sakar mata hannu ba har suka isa bakin elevator. Zame hannunsa yayi a nutse,abinda sãahar keta qoqarin yi kenan,ba tare da ya dubeta ba kuma ba tare da yace da kowa komai ba ya danna button ta bude. Baya yaja kadan tare da yi mata nuna da hannu akan ta shiga. Cikin nutsuwa tabi ta gefansa,har kafadarta na gogar hannunsa saboda yadda ya tsaya yayi bake bake a bakin elevator din,wannan ya sake bawa turarenta damar bugun fuskarsa,ya damqe hannunsa da kyau kamar wanda ya boye wani abu. Waiwayawa yayi baya,kallo daya ya yiwa su elyas taga sun janye baya,ya taka da sassanyan takunsan nan ga shiga ya rufe dasu suka fara haurawa. Shuru elevator din yayi sai qamshin jikkunansu daya cikata. Yana tsaye daga gabanta dai dai bakin gofa,wannan ne ya bata damar gare masa kallo da kyau,duk kuwa da yadda taso dauke kanta,amma halin zuciva, sai taji a karon farko tana son yin hakan. Tun daga kan lallausar nannadaddiyar sumarsa,murdadden hannunsa dake boye a aljihunsa, daya hannun nasa dake rige da waga qawatacciyar briefcase dinsa zuwa bayansa da takalman dake gafarsa wanda suketa daukan idanu. Tana gama satar kallon dai dai sanda elevator din ta iso dasu floor din da suka nufa wato gini na garshe na kamfanin. Ya danns button din sannan ya taka yana shirin fita "Ki ringa kame ganinki,karki manta ni dan iska ne me yiwa mata fyade, muddin kika cika kallona zan iya dauka cewa ranki ya biya ne da ni, komai kuma zai iya faruwa". Idanu ta fiddo waje cikin mamakin maganarsa,sai tasa hannunta guda daya ta dafe kanta haushin kanta yana kamata,meye ma ya kaita tsaiwa ta kalli wannan mutumin idan ba jawowa kai matsala ba ta fahimci shi kullum baiso a zauna lafiya,batasan meye tayi masa ba,wai shi kunyar furta kalmar fyade ma baya jinta sam?. Gani tayi idan ta barshi ba shakka ya sha da ita, saita tako itama tana biye dashi sanda yake scanning key din a jikin qofar "Wai shin me ma zan kalla hala? wannan kodaddiyar fatar ko kuma wanna gashin mara kyan gani?" Ta furta tana nuna singalilin hannunsa dake riqe da handle din gofar. A karon farko dariya taso qwace masa amma ya rage kaifinta ta hanyar murmushin gefan bakiya kalli hannun nasa data nuna sai ya sanya daya hannun yana shafarsa "U'uzubi kalimatillahit taammati minsharri ma khalaga, da gasken dai qaremin kallo kikeyi, banda haka ta ya kika san da zaman gargasata iyee?" Ya jefa mata tambayar data sanyata fara raba idanu amma ta basar "Bayan gashina mara kyan gani sai kuma meye kika gano?,oya tell me" ya fada yana murza handle din tare da tura gofar baya ta bude. "Eheenn, ina jinki da meye da meye?" Ya kuma jefa mata tambayar yana matsota idanuwansa akan lips dinta da suke haifar masa da wani irin abu a jikinsa wanda yake sanya tsigar jikinsa zubawa,a duk sanda yaga lips din sai ya tuna da santsi da kuma laushinsu. Ba zato ba tsammani taii va cafketa ya kuma finciketa zuwa office din ya maida murfin da qafarsa guda daya. Jefata yayi jikin bango yana bin bayanta "Saifa kin gayamin, kada naje wadan nan marasa kunvar idanun naki sun ganemin sirri na" yadda ya matseta da bango ya sanyata jin kamar iskar dake wajen tayi mata kadan,ta tabbatar ko da wasa ta motsa ba shakkan qirjinta shine abu na farko da zai fara gogar jikinsa. Qangame jilkinta tayi guri daya tana rufe idanunta sanda taga ya taho da hannunsa saitin fuskarta, ta gama taga ya taho da hannunsa saitin fuskarta,ta gama saddagarwa may be maruka zata sha,sai taji yatsunsa guda biyu saman lips dinta suna zagayasu. Tsigar jikinta ne ya zuba lokaci daya taji kamar wayar wuta ta jata "'Waye ya baki izinin shafa wannan abun?" Kusan daukewa numfashinta vayi, saboda a saman fuskarta yayi maganar muryarsa can gasa kamar me shirin rad'a mata, hucin furucin bakinsa dake cakude da mint scent ya daki fuskarta. Bata gama kokawa da wanna ba ta tsinci lausasan lebunansa masu dan tudu a saman nata siraran labban, ta gama fahimtar abinda yake shirin yi mata, saita tattara dukka qarfinta ta sanya hannunta saman girjinsa ta turashi baya tana gocewa gefe cikin bacin rai. Idanunsa da wani abu ya sirka a cikinsu ya daga yana dubanta "Duka wannan baya cikin sharudanmu,koma meye zanyi ko zan sakawa fuskata ba damuwarka bane, na kula kawai da fadeela,i will do my very best, that's all" ta fada muryarta tana rawa. Kafin yace komai yaji qofar na bada alama na shigowar wani,don haka ya juya da dan hanzari kai tsaye ya wuce cikin office dinsa. Saima ce rungume da files, gaba daya fuskarta zuwa zuciyarta babu wani sukuni ko annuri, ido suka hada da säahar, sai säahar din ta dauke kai tana gyara rufin lafayarta sannan ta durfafi office din itama kai tsaye,cikin ranta tana jin kamar ta zura da gudu tabar office din, a karo na biyu ta sake dawowa aiki da wannan mutumin da bashi da kirki ko kada,ko yaya zata kasance musu?. A nutse ta buda ta shiga da murtukakkiyar fuskarta,har hanzu office din yana nan kamar yadda ta sanshi,saima sake qawatashi da akayi da gyare gyare. Guri ta samu ta tsaya tana harde hannuwanta a girji, bugun zuciyarta har yanzu bai daidaita ba. Bashi a office din,amma taji qarar ruwa daga toilet, sai ta zabi taci gaba da tsaiwa kawai. A galla mintuna kusan goma sha biyar ya shafe kafin ya fito,kallo daya ta masa ta dauke kanta, gaba daya fuskarsa ta sauya,ya koma real MT JARMA dinsa data sani,kamar ba shine yanzu yanzu yaso matseta yayi mata mugunta ba,ya jade fuskarnan da kyau,abinda ya sake qara masa kwarjini kenan "Have a seat" ya fada yana jan tashi kujerar baya tare da shirin zama a kai,har yanzu bai kalleta ba. Batason suia magana da vawa,don haka ta garaso ta zauna din, ya buda wani file dake gabansa ya ciro wata takarda ya ajiye saman file din "As my new P.A,aikinki zai zama a qarqashina ne, zai kuma zamana kan umarnina,na baki access da duk wani kira mo email da ya shafi office dina, sauran abinda zakiyimin idan ta kama zan sanar miki, koda ya fita daga tsarin aikin PA" •_HAJIYA QARAMA_* Ita da masu aikinta biyu suka isa makarantar, kai tsaye har zuwa office din shugabar makarantar. "Abincin jikata ne FADEELA Muhammad jarma" dubanta headmistress din tayi "Cute angel,ko ba ita ba?" Ta fadeta da sunan da yawanci ake kiranta dashi a makarantar. Murmushi hajiya garama ta saki tana gyada kai "Eh ita fa" "'Amma dazu mamarta ta kawota da kanta,kuma da abincinta tazo kamar yadda aka saba" kai hajiya qarama ta jinjina,tana jin dacin kiran sãahar da sunan mahaifiyar fadeela "Ba itace mamarta ba,matar ubanta ce,nanny dinta kuma ada" ta qasan glass matar ta dubeta "Eh amma ita muka sani a yanzu,don ko last week da za'a shiga sabon session itace tazo tayi updating data na fadeela,da sunanta muka cike komai,so ko yanzun ba zamu iya karbar abinci daga hannunki mu bata ba,sannan koda daukarta ma a yanzu ita ke da alhakin hakan,idan fana da uzuri kuma zata kiramu da kanta ta bamu shaida akan wanda ta turo din". "Turqashi!" Ta furta tana dukan hannun kujerar da take zaune a kai ba tare da tasan ta aikata hakan ba "Madam kinsan da waye kike magana kuwa? hajiya fauziyya ce ni fa qanwa ga Dr mahmud JARMA, uwa ga MT JARMA, sannan kaka ga fadeela,kinaso ki gayamin matsayin matar uba ya wuce na kaka?" Ita kanta matar mamaki sai daya darsa mata a rai, saboda bataga meye abun tashin hankali ko bacin rai ga gin karbar abinci ba,amma duk da haka ta basar ta girgiza kai "Ko kadan kuma wannan ai family issue ne ma hajiya,abinda na sani dai kawai, duk wanda aka sanyashi cikin data na dalibi shine zaici gaba da juyawa da kulawa da komai nashi,dama kusan ita fadeelan ce kadai bata da wannan record da muke dauka a duk shekara,so wannan karon kuma ta samu,haqginmu ne mu kula da lafivar dalibi da tsaronsa, ki koma da abincin hajiya idan kuka sasanta a gida sai kuzo asan sunan wanda za'a cike dashi, ko kiyi kiranta muji hakan daga bakinta". Tsantsar bacin ran da take ciki ya hanata sake cewa komai sai kawai ta miqe tana fita dava office din, adama na biye da ita da lunch bag din. Sai data kusa minti ashirin a tsaye jikin motar tana juya abun a ranta, ita yarinyar zata dinga shigewa rayuwa haka? lallai zata nuna mata kurenta,amma kafin sannan bari taje ga mataki na gaba. "Gida zamu koma hajiya?" Driver dinta ya tambayeta,saita girgiza kai "Gidan yaaya zaka kaini" •_DR MAHMUD JARMA RESIDENT_ Yana duge gaban garamar luggage dinsa, daya daga cikinsu wadda duk sanda tafiya ta kamashi yake amfani da ita. Yana tsaka da zugewa hajiya mansura ta shigo dakin dauke sa tray data shiryo masa kayan abinci a ciki. Idanunta a kansa har ta garaso ta ajiye,ta koma gefan gado ta zauna "Kwanaki uku kenan inatason yin magana da kai, amma sai nake ga kamar baka da lokacin kanka a 'yan kwanakin nan" ba tare da ya dago ya dubeta ba va iiniina kansa "'Inata shire shiryen yin tafiya ne kuma a galla tafiyar zata dan iya daukana lokaci wala'alla me dan dama kafin na dawo,duk da bana fatan hakan" ya bata amsa yana tsaida luggage din bayan ya gama rufeta. Sosai take kallonsa,cikin kwanakin gaba daya kamar ma cikin nutsuwarsa yake ba,to amma ita abinda yake gabanta a yanzu yafi tasa a damuwar a gunta "Labiba gaba daya na kasa gane kanta,yini take ta kwana tana kuka,ta daina fita ko ina,ta daina walwala ta daina magana da kowa" "Duka akan me?" Yayi mata tambayar yana zama saman stool. Mamaki yadan kama hajiya mansura yadda yayi kamar baisan komai a kai ba, duk da haka ta hadiye cikin lanqwasa murya da karyar da kai "Akan yayanta toufeeq mana, tunda yayi auren nan ita kuma ta koma haka" idanunta yake kalla kai tsaye,yama rasa abinda zaya fada, baisan me yasa daga mansura har fauziyya kowacce idanunta ya rufe akan batun hada auren toufeeq da 'yarsa ba,duka duka ma yaushe yaron yayi auren da har za'a tsaya rakito masa wani auren?,shi yasan abinda su basu sani ba yadda haseena take zabin fauziyya,labiba take zabin mansura, haka säahar take ZABINSA, ya riga taoufeeq nema masa auren sãahar ba tare da shi kansa ya sani ba. Bayan ya samu dukkan labarin aurenta da adam daga bakin muhyiddeen,ya tabbatar ya kuma yi imanin SÄAHAR itace macen da tafi dacewa da toufeeq,itace kuma madadin AMEESHA data sanyawa rayuwarsa dafin da yasa yake kallon mata amatsayin ABU GUDA. SAAHAR itace tayi masa kamanceceniya da SHIFA, dabi'unsu suna gogayya da juna,yafi kowa sanin wacece shifa da halaccinta a garesa,wannan ya sanya ya yiwa toufeeq sha awar mallakarta. "HUGUMA* _TABARMAR KASHI* Book 02Page 25 "Yanzu ba zaka sanya baki ba ko don a samu hankalin yarinyar nan ya dawo jikinta?" Agogon hannunsa da ya manta bai cire ba ya soma zarewa "Bana shiga lamarin da ban isa na hadashi ba, daga ke har fauziyya na gaya muku, toufeeq yana da ido so ba sai an tursasashi ba,ko ni bani da ikon bashi umarnin ya auri wance,idan ya gani yanaso bazan hanashi ba" maganar tasa ta tabata sosai, kuma dama fauziyya tana can tana nata yaqin kenan? ya tabbata ta shirya cin amanarta da gaske,iska ta furzar a bakinta tana gangance idanu "'Wallahi wallahi wallahi tsautsayi yasa ta yimin kan kara sai nayi mata na itace, idan tana tutiya da ita din gwanace ni uwarta ce a wannan fannin, zatasan ni mansura cikakkiyar KARA DA KIYASHI ce daukan mara sani" abinda ta furta kenan qasan ranta, kafin daga bisani muryar dr mahmud ta mamayi kunnenta "An samu ticket din? na ranar yaushe ne?, alright zanyi managing na jira ranar" sai ya sauke wayar daga kunnensa a hankali yana furta "Alhamdulillah" yadda fuskarsa ke nuna annuri yaja hankalinta "'Wacce tafiya ce haka me muhimmanci zakayi?" "Ni kadai tafiyar ta shafa,so ba wani abu bane na daban" ya fada yana kashe wayarsa. Binsa tayi da kallo,haka kawai taji jikinta bai bata ba,so amma koma inane zatabi diddigin tafiyar har ta san inda zashin. Hannuwanta ta sake tajuya tana ficewa don dauko masa plate din abincin data manta. Tana saukowa daga stairs din hajiya qarama na shigowa falon,kallon kallo suka yiwa junansu, kafin hajiya garama ta buda baki da qyar tayi sallama. Kamar yadda tayi sallamar da gyar haka mansura ta amsa mata da gyar tare da dauke kanta, tazo zata wuce ta gabanta tamkar batasan da wanzuwarta a wajen ba. Matuga da gaske abun ya daure mata kai,don bata taba kawowa a duniya akwai lokacin da zaizo mansura tayi mata irin wannan abun ba "Ina yaya yake?" "Tunda kinsan kan gidan ai kinsan inda zaki sameshi" ta amsa mata da gatse, tunda ta sani aduk sanda tazo gurinsa itace ke shaida mata yazo din "Idanma da gatse kika fada yanzun zaki ga cikar aikin irin na fauziyya" tana kaiwa nan ta kama stairs din tana hawa,hajiya mansura ta bita da kallon zallar mamaki baki bude. Ya danyi mamaki da yaji ana knocking,ya miqe ya buda qofar, mamakinsa ya qaru da ganin fauziyya da safen "Muje falo" yace da ita ha fito ya biyo bayanta. Nan falon saman suka zauna,yana qoqarin zama ta fashe masa da kuka "Subhanallahi, lafiya me yake faruwa?" Hajiya Mansura da tayi gaggawar dawowa don taji abinda ke faruwa duk da tasan fauziyyan bata taba wata magana me muhimmanci tsakaninta da yayan nata a gabanta ba,ta saci kallon fauziyyan cikin sa'a suka hada idanu "'Maganace ta ahali yaya,zan samu sarari?" Kai ya jinjina vana karbar plate din daga hannun mansura yana cewa "Mansura bamu guri" "Tom" ta fada zuciyarta kamar zata fado daga qirjinta saboda tsananin takaici. Shekara da shekaru har yanzu babu abinda ya sauya a irin wannan abubuwan dake faruwa,a wannan shekarar kadai ta soma gain abinda fauziyya ta nema dr jarma bai bata ba AURAWA TOUFEEQ HASEENA. "Me ya faru?" Ya sake tambayarta,sai ta sake sakin hawaye "Ba shakka yaaya toufeeq ya auro yarinyar da zata rabamu dashi" mamaki ya kamashi "Kaman yaaya? wai säahar kike nufi?" Kai ta jinjina masa "Itafa,tun daga lokacin da tazo gidan komai ya canza,shi kansa toufeeq ya sauya,a yanzun ban isa da shi ba,sai abinda tace,hatta da gaisuwa bankai ta shigo ta gaidani ba,saidai idan mun hadu a compound na gidan" Shuru yayi hannunsa saman bakinsa yana mamaki, vasan wanne aure akayi da manufar auren dake zukatansu dukka su biyun,to yaushe hankulansu suka hadu guri guda har suka fara mu'amalar da mutum me taurin kai da kafiya irin toufeeq sahar zata fara juyashi ya soma daukan maganata? "Yanzun me va faru?" Hawaye sosai ta matso "Waini yarinyar zata kalla tace daga yau tanamin kashedin babu ni na fadeela, ta soke bata duk wata kulawa da nake bata,ta shiga ta fita ta canza komai har na makarantarta,abinci bata magani,hatta da daukan yarinyar yanzu babu wanda yake da wannan ikon idan ba ita ba,hatta kaita makaranta yanzun ta maidashi wuyanta". Ga mamakinta murmushi ne ya subuce akan fuskarsa yana dan girgiza qafarsa,cikin ransa aminci da gaunar sãahar tana ratsashi "Banda abinki da rigima irin taki, kefa yanzun kin girma,da meye kikeson kiji? da shekarunki koda kasuwancinki koda kula da fadeela? ina cewa ke sauqinki ne ma,aiki aka rage miki da nauyi ko?" Sosai ta girgiza,amma kuma ba zata saare ba sai taga abinda ya turewa buzu nadi "Haba yaaya,haba yaaya, ubanta ma nina raineshi bare diyar? ta yaya kawai don an aurota zamu sake mata kula da diyarmu haka sakaka? yadda yanzu duniya ta zama babu gaskiya,sai a hada kai da mutum a cucuka" "'ah dakata fauziyya,duk ba za'a samu wannan daga sãahar ba ina kyautata mata zato, banda abinki meson naka ai shima naka ne,ki bar musu diyarsu don Allah, ki cire ranki daga wannan qanqanin abun,duka ba damuwa bane" "Yanzu ba zata tsawatar ba kenan yaaya?" Murmushi ya saki yana girgiza kai "A'ah ni bazan shiga wanna maganar ba, diyarsu ce, inda ace kina qorafi ne akan nadeeya to itace 'yarki sai kuma inda qarfinta ya qare" Boom 💥 taji wani abu cikin kanta,karo na farko data fuskanci haka daga gurinsa, bai taba ganin hawayenta ba ba tare daya zartar da abinda take muradi ba. A yanzun shurun da tayi ma kamar bai fuskanci bacin ranta ba,janta ya shiga yi da hira yana yi mata tayin abinci "Alhamdulillah na qoshi, zan wuce gida na baro meenal ita kadai,kasan kuma baquwa ce har yanzu" "'Gaskiya ne ya kamata tazo tayi kwana biyu su saba da mamarta da yar'uwarta" "Zatazo" ta amsa masa a taqaice,saboda ta qagauta ta fita daga cikin gidan ko zata samu damar yin kyakkyawan tunani akan yarinyar,sai takejin kamar wata masifa ce ke tunkarota. System ya tura mata da tarin wasu ayyuka da zata tattara masa bayanan guri guda. A nutse take aikin tamkar ma bata office din, lokaci lokaci tana ji a jikinta tamkar yana kallonta ne,amma kuma duk sanda ta daga kan nata don ta tantance sai taga idanunsa yana saman system. Mintuna goma sha biyar kacal suka rage lokacin break ya cika,har a lokacin bata motsa ko ina ba tana zaune tana gogarin tattara aikin da ya bata hatta da wayarta ma a kashe take, don batason tayi wani abun ma da magana zata shiga tsakaninsu. A karo na barkatai ya sake satar kallonta, shi kansa bazai iya tuna wani abu a rayuwarsa da ya yiwa adadin satar Kallon da yayi mata ba ba tare da shi kansa vasan satar kallon yake ba. Dai dai lokacin data zura hannuwanta ta cikin lafayar ta kuma bayan wuyanta tana gogarin tattare gashin data nannade, santsinsa ya sanya ya ware da kansa yake kuma damunta a wuya. Hakan ya baiwa laffayar damar zamewa, lallausan gashin nata dake da wani irin bagi da daukar idanu ya ware a kafadarta ta hagu. Tana qoqarin mayar da mayafin kira ya shigo ta wayar office din. Ta daga kai zata kalleshi suka hada ido, basarwa yayi cikin shan gamshi va kuma hade rai sosai, don bayason ta fahimci tun ba yanzun ba idanunsa ke kanta "Kin manta aikinki ne?" Ya fada a dake,har ta dan juya idanunta zata sauke masa harara sai tayi saurin gyara kallonta,tayi rolling qwayar idanun tamkar me yin fari. Wani irin ayalli idanun nata suka bada,a dole ya rusunar da kallon nasa daga kanta. Migewa tayi a nutse ta isar ga wayar ta daga,ta kara a kunnenta tare da yin sallama da nutsatsiyar muryarta me sanyi da taushi. Cak ya tsaya daga singing din da yakeyi sautin yana shigar masa kunne "Idan kuma namiji ne fa?" Yaji tambayar ta fado a ransa,sai ya rige biron a hannunsa yana juyashi tare da son tsinkayo muryar waye a wayar. "Ma sha Allah, ina fatan Khadija Muhammad girema ce?" Mamaki ne qwarai ya kama sãahar, ta yaya za'a yi kira a wayar office office din da ba nata ba amma farat daya a kama sunanta? "Eh itace" "Good,na buga dai dai kenan.....kina magana da Ameesha,ex_wife din mijinki muhammad toufeeq,maama ga FADEELA" sosai ta gyara tsaiwarta ba tare da tace komai ba " Zuwa yanzu nasan fes kin fahimci wacece ni din" "Me kike bugata" garamar dariya ta saki "Naji dadi dana sameki me saurin fahimta,hakan na nunamin bazan sha wahalar fahimtar dake lokaci yayi na dawowata gida na ba" "Dashi ya kamata ku garasa wanna maganar" tà gintse ameesha din daga abinda ta kira da soki burtsu a waienta. Waiwayawa tayi gareshi bayan ta dauke wayar daga kunnenta suka hada ido dashi, idanunsa zube fes akan fuskarta yana son ya karanci wani abu. Bata bashi dama ba don dauke kanta tayi, ta qarasa gabansa ta rangwafa daga saman table din tana gyara masa zaman wayar a gabansa,wannan ya baiwa ragowar gashin kanta damar qarasa warwarewa,iskar dake shigowa daga window ta buso masa dukkan gamshin dake magale a jikinsa harda tsarabar shafar gefan fuskarsa. Ido ya lumshe a hankali yana jin yadda zuciyarsa take bada wani sautin bugu, sanda zai bude idon harta ja da baya tana sanya takalmanta ba tare data dubeshi ba tace "'Baguwa keson magana da kai" bata tsaya sauraronsa ba ta dauki hand bag dinta da wayarta ta fita daga office din. Kamar zaman jiran ganin me shiga da fita daga office din saima tayi tana fitowa suna hada ido,saita dauke kai tana nufar living room dinsa dake cikin office din. Ta dora hannunta zata murda handle din living room din sai aka budo ainihin gofar da zata sadaka da sashen saima. Sai ta waiwaya tana duban qofar. Sanye take da wata gown na Vintage clothing, saman kanta lullube da siririn scarf data nadeshi daga kanta zuwa wuyanta kawai,fiye da rabin fuskarta sun glasses ne ya mamayeshi, sai wani rufaffen takalmi me tudu data sanyawa qafarta, daya hannun na maqale da hand bag yar mitsil, daya hannun kuma wani foldable basket ne da aka shirya qananun warmer's masu kyau a ciki. MEENAL YA'AQOUB AJI kenan,sananniya ga duk me ta' ammali da kafofin sada zumunta,wanann dalilin ya sanya saima miqewa tsaye cak suna kallon kallon a tsakaninsu. Koda batace ba tasan gurin toufeeq tazo,don duk wanda ya santa,yasan ita daya ce tallin tal dake wallafa hotunansa kusan koda yaushe saman shafukanta na sada zumunta. Batayi mata kallo na biyu ba ta murda gofar room din ta shige ta barsu suna kallon kallo tsakaninta da saima. "Madam ina zuwa haka?" Saima ta tambayi meenal cikin gatse. Dawowa tayi da baya tayi qasa da glasses dinta ta qarewa saima kallo,sai ta saki wata dariyar rainin wayo "Jealousy"' ta fada cikin nishadi sai kuma ta dora "Zanyi mamaki gwarai idan kikace wai baki sanni ba… Meenal ta fada cikin izza da jin cewa ta kai ta kawo ta kuma shirya gogawa da kowa akan TOUFEEQ,tasan da saima already tasan kuma zaman me takeyi a gurin… *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 26 .. Anyways, nazo wajen masoyina ne kuma mijina" daga haka ta juya ta nufi office din kai tsaye. Zallar mamaki ya hana saima cewa komai,sai kallon zallar mamakin da ta bita dashi. A cikinsu wace ainihin matar tasa?,ko mata biyu ya aure lokaci guda basu sani ba?. A nutse take takawa cikin living room din dake tsare da sofas masu tsada da aka sake zubawa,sofas din da kake da ikon lanqwasa su duk shape din da kaso,daga kujera me qaramin table a hannunsa zuwa matsakaicin gado tare da pillows. Jakar hannunta ta ajiye saman sofa din a hankali. Kalaman ameesha ne suka fara dawo mata fes cikin qwaqwalwarta. Siririn tsaki taja gana jin zafi a zuciyarta da matar ta kasance mahaifiya ga fadeela, juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta, kuma ita din ba qanqanuwar yarinya bace, dukkan alamu sun nuna zaiyi wahala a samu karamci kamun kai da sanin ya kamata daga gurin matar, kalaman bakinta kawai sun gama gayawa säahar wacace ita din. Sake jan tsaki tayi tana nufar gofar da aka rubuta Toilet daga samanta da wani irin rubutu ruwan azurfa. Tura bandakin tayi ta shiga tana binsa da kallo komai kar kamar ka zuba abinci a ciki kaci. Fitsari tayi ta daura alwala sannan ta fito ta tayar da salla. Ko' bayan ta idar zamanta tayi saman lallausar abun sallar dake ajjiye har guda uku a wajen. Tana azkar kadan kadan tana tunanin abinda zata ci. Fuskar haseena dake shigowa da kwanukan abinci ne ta dawo mata,cikin shigarta dake nuna halittar sirantakar da Allah yayi mata tako ina wanda wala'alla ita bata ganin hakan. Gefe daya kuma fuskar saima ta fado, duk yadda takeson kore tunanin komai daga ranta amma sai ta gaza aiwatar da hakan?. Wai meye tattare da shi da sauran maza basu dashi suke wannan parade din a kansa,kamar qarar wayarta shine amsar tambayarta sai kira ya shigo mata,wanda shine ya zama silar yankewar tunaninta ta dauki wayar tana dubawa. Bestie afifa ce, saita saki murmushi sannan kuma ta tura baki gaba,tabbas sai ta fanshe shakulaton bangaron da afifan tayi da ita ta daga wayar ta koma saman abun sallar. "bestie bana yi, bestie kinci amanata" sãahar ta fada tana harara wayar tamkar dai afifa na wajen "Don Allah bestie kiyi haquri, wallahi ban taba experiencing irin wannan yanayin ba a rayuwata" afifa ta fada da muryarta data gama komawa me sanyi. Ta fahimci maganar afifan, don haka ta sanya hannuita toshe bakinta saboda dariyar da take cinta "Na miki uzuri bestie, Allah ya bada lafiya" "Wai Allah bestie, naga rayuwa,sai yau na samu space da hayatee ya taho company" baki sãahar ta tabe, ita kwata kwata wadan nan sabgogin basa burgeta ko kusa ko alama,kafin tace wani abu afifa tace "Amma bestie lafiyanki qalau kuwa? ,kina cikin hankalinki kike shirin sakarwa mata mijinki?,wannan na ciki wannan ta shigo?" Maganar tadan baiwa sãahar mamaki "Kamar yaaya? dama na aureshi ne don na kula sa sabgoginsa ko kuma na kula da diyarsa?" Ta jefawa afifa tambayar. Goshinta ta dafe tana lumshe ido, sãahar dai bata canza ba?,a kwanakin d sukayi tare ta dauka komai ya fara canzawa dangane da junansu a zukatansu "Saahaaarrrr....... please ya kamata ki koma cikin hankalinki,hayatee yazo office dinsa ya taras da hakan, saboda yana kishinsa yana kishinki kuma yana kishina yasa ya gayamin....i was so shocked... ...nasan ba haka bestie na take ba, aure ai ba abun wasa bane bestie, ko banza igiya ce me girma a tsakaninku... ...moha ba normal irin gama garin maza bane,wannan abun da kike na shakulaton bangaro ba komai zai haifar miki ba sai d'a maras ido, ki tsaya kawai kiyi abinda ya kamata ki manta da komai" baki sãahar ta tabe "Yaushe kika koma me bada shawari?, kinje kin kurbi giyar aure ko?,hmmm sannu farin shiga,to na gode da shawara,amma ni ba ruwana da abinda ya shafi rayuwarsa,wannan shi ya zabarwa kansa,ya auri mata dubu ma ya kula million a yau duka shi yaso, zan wuce gida yanzu lokacin tashi ya kusa,idan na isa zamuyi waya,inason mu tattauna akan wani abu daya fara tunani a kai" "Allah yasa maji ta aura masa uku tsala tsala larabawan Algeria" "And so what!" Ta fada da lafazin da ya sanya fifa shegewa da dariya "Allah sarki bestie,Allah ya baki lafiya,sannu" mamaki ya kamata,me afifa ke fada?,kawai sai ta sauke wayar ta kashe,taga alama so take kawai ta tuburata. A nutse ta maida wayar jakarta,ta fidda wata siririyar roba doguwa da bata rabo da ita ta murza turare,ta warware lafayarta ta gyara zamanta sosana ilkinta,ta kuma gyara daurinta,sai gashi ta fito d'ass da ita,wani sirrintaccen kyan amarci da batasan dashi ba yana bayyana saman fuskarta. Jakarta ta dauka ta rataya a hannunta ta fito daga resting room din. Wayam mazaunin saima yake, ba kowa sai takardu da na'ura a gurin. Kanta ta sanya kai tsaye office din nashi, ta murda qofar ta turata. Idanunsa na zube fes akan qofar yana qarasa jin abinda ameesha ta fadiwa sãahar a waya ta a dazun data kira kafin ta ajjiye masa wayar ta fice. Can qasan maqoshi ya amsa sallamar,ta tako zuwa ciki ba tare data dubi fuskarsa ba kamar tasan ita din yake kallo,hakanan bata kalli ko sashen da meenal ke zaune ba,wadda ta ajjiye basket din saman table dinsa ta kuma zauna saman kujeru biyun dake gaban table din nasa,idanunta a kansa tana qoqarin shanye maganar daya gana gaya mata,tana jin zata iya jure koma meye, tunda ta sanshi,ta kuma yi imanin dama bawai zata sameshi ta sauqi haka ba. Dan binta yayi da kallo,sai itama meenal din ta rakashi da kallon, ta kuma janye idonta daga kan sãahar bayan ta tabbatar sãahar din idanunsa suke kalla. Haka kawai wani irin bacin rai ya cika masa maqoshi,yana datse kiran ameesha ita kuma haseena ta sanyo kai da tarkacen kayan abincinta. Can cikin ransa yana jin zafin me yasa zata daga wayar ameesha har ta bashi?,me kuma yasa ta barwa meenal damar shigo masa office da kayan abinci?. Ido meenal ta qangance, tun daga zuciyarta har ruhinta tana jin matsanancin kishin kyan da säahar ke dashi,yau ne tayi mata kallon fes ta gefen idanu,duk yadda takeji da gayu da kyau sai takejin a yanzun ta muzanta idan aka kwatantata da säahar din. Duk da shigarta shigace ta gargajiya a wajen meenal,don ita bata taba kwatanta sanya suttura full irin hakan ba,to amma ayau sai taga shigar tayi mata mugun kwarjini, abinda bai taba faruwa da ita ba. "Ina da abunyi so zan wuce gida, inason tsaiwa na dauki fadeela" ta gaya masa tana sake matse agogon hannunta ba tare da ta kalli fuskarsa ba. Zare idanunsa yayi daga kanta a hankali yana dai daita zamansa. "Tana da abunyi ma take ce masa?,waye bashi da abiny kenan" Bata jira amsarsa ba ta tako a hankali ta qaraso gaban table din nasa amma ta left side dinsa, akwai file da take da bugatar dauka kuma suna ta wajen,abinda ya qara kusanci kenan a tsakaninsu sosai,sassanyan gamshinta na haurawa hancinsa yadda ya kamata,tsaiwar da tayin kuma a wajen ta baiwa haseena damar ganinta sosai fiye da dazun. Zara zaran yatsunta da suka sha lallae tabi da kallo a sace, kamar yadda shima nasa idanun suka sauka akai,launin kalar tana bala'in jan hankalinsa. Hannu yasa da sauri ya dafe wani file da take shirin cirowa,wanann ya baiwa hannuwansu damar haduwa guri guda,take haseena taju zuciyarta tamkar zata fashe,ta dauke idanunta daga kai tana migewa. "Ki koma dasu gida,bana da enough time da zan iya cin abinci har haka a office" ya bata amsa yana maida file din tare sa cirowa sãahar din na gasansa daya tabbatar shi take nema. Tana karba ta soma takawa zata bar gurin,lokacin meenal ke maida kwanukanta cikin kwandon tana jin wani bacin rai ranta kamar zai fashe. Bata taba zaton zai watsa mata gasa a ido ba yace ta koma da abincin ba,ta hada komai a gaggauce ta nufi hanyar fita tana qoqarin danne fushinta da hawayen da ya cika mata idanu,saboda batason matarsa taga karayarta. Meenal na fita tabi sahunta,saidai kafin takai ga fita ya amsa mata zancan dauko fadeela daga school,har yanzu ransa na susa,tare da jin bacin rai da mamakin yadda ameesha ta samu number wayar office dinsa bayan yayi blocking nata a dukka wani layi da yasan zata iya samunsa. "Fadeela nada driver,so ba buqatar kije daukota,ki tsaya kiyi aikinki" waiwayowa tayi ta kalleshi sosai,sai lokacin taga yadda yanayin fuskarsa ya canza da kyau "Ba dole bane ace driver kullum shike da alhakin jigilarta,daga yau shima na soke wannan saidai idan da wani dalili me qwari" barin aikin da yakeyi yayi, ya dauke hannunsa yana soke yatsunsa guri guda, idanunsa a kanta. Cikin ransa yana jin kamar ba wannan aikin ya kamata ta bawa muhimmanci haka ba,yayin da wani sashe na zuciyarsa kuma yake son daga martaba da kimar abinda tayin tare da son gamsar dashi "Zauna muyi magana" yayi furucin cikin rashin son wasa a fuskarsa. Kai tadan dauke, kamar ba zata zauna ba kuma ta dosana kadan a saman kujerar "Kome zakiyi kiyi qoqarin kare martabar hajiya,saboda ita din kamar maji take a gurinmu" kai ta girgiza "Ba maji bace,ba kuma zata taba zama maji ba,am sorry to say ban yarda da kowa ba akan fadeela,saboda nayi experiencing wani abu da yaso tarwatsa rayuwata shigen abinda fadeela ke shirin fuskanta daga gurin mutumin da yafi kowa kusanci dani" ta qarashe maganar muryarta tana rawa. Har cikin jikinsa yaji wani abu ya tsarga masa,ta miqe tana qoqarin boye qwallarta,batason zubda hawaye a gabansa "¡ have to go" kamar bazai amsa mata ba sai taga ya mige,ya tura kujerarsa baya ya fito a hankali daga gurin ya zauna saman resting chair yana maida takalminsa,ya daura agogonsa sannan ya dauki wayoyinsa da system dinsa sannan yace "Let's go" sosai tayi mamaki, saboda bata taba kawowa zaice suje din ba. Danne mamakinta tayi tayi gaba yana biye da ita a baya. A hankali take takawa da irin takunta nan qafafunta akan tsari,wanda sai kayi tsammanin tana sane take shirya takun nata daya bayan daya. A hankali a hankali sai taji kamar gafafunta suna neman hardewa wannan va sanya ta sake rage saurinta sannu a sannu har ya cimmata suka dai daita kafada. Kusan a tare suka daga idanu suka kalli juna,sai kuma kowa ya dauke kansa yaba basarwa, itakam harda qarin matsawa gefe. Ihun murna kawai fadeela tadinga saki sanda taga sãahar harda abby dinta wai sun biyo daukarta,abinda bata taba samu ba kenan. Yana zaune vana kallonsu ta cikin glass din yana jin wani farinciki na ratsashi saboda walwalar da ya gani saman fuskar fadeelan,wai me ya hanashi yin hakan shi tsahon shekarun da suka shude? ya barwa driver komai da komai na hidimar daukota da kaita?. Ido ya lumshe yana jin wani farinciki. Duk yadda yaso ga dannewa amma ya kasa sai da ya furta "Thank you"sanda take maida murfin motar tana rufewa. Cike da mamaki ta kalleshi sai kuma ta basar "It's my pleasure" ta amsa masa tana dire school bag din fadeela da tuni ta haye jilkin Abby dinta tana cewa yau itama 'van class dinsu sunga abby dinta da mammanta sunzo daukarta kamar yadda ake daukar kowa. Sanda suka isa gida ko sassanta bata shiga ba suka wuce sashensu, nadeeya daketa zuba idanun dawowarsu ta tarbesu suka dunguma,shi daya ya wuce ciki, sai daya shiga yaga dining wayam sannan ya tuna Jacob fa bava nan, garamin tsaki yaja ya wuce bedroom dinsa. Duk abubuwan daya aiwatar tun daga wankansa canza kaya da fresh milk da yasha ba hakan bai mantar dashi tunanin dake magale a kwanyarsa ba,meye yasa tace bata yarda da kowa ba? me yasa wani irin rashin jituwa yake gudana tsakaninta da hajiya qaraman cikin dan lokaci kadan?,da wannan tunanin ya gama hutunsa cikin sashen,har aka kirayi magariba yayi alwala suka fita sallah shi da jibril. Bayan ya dawo sallar sashen hajiya qarama ya shiga,don bayan ya fito jibril ya shaida masa sau uku tana aikowa kiransa, ba'a gaya masa bane sabida sunsan dai dai lokacin hutawa yakeyi. Yaji dadi da bai samu meenal ba a sassan,ya samu guri ya zauna yana gaidata "Ka kusa fin garfina ai toufeeq" hajiya ta fada tana tara hawaye cikin idonta. Mamaki abun ya bashi qwarai "Me kuma ya sake faruwa,i thought kun gama magana da Dr ko akan komai?" *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02Page 27 "Amma toufeeq kamar ni?, meye amfanina a cikin gidan idan ban kula da fadeela ba" ido ya lumshe sannan ya bude,ya gaji gaba daya bayason wani daru "Karki wani damu, tattaromin magungunan ki bani, ni zan ci gaba da kula da hakan" a bazata maganar tazo mata,har hakan yaso ya rudata amma ta daure "Haka ma zaka ce dani toufeeq? yayi kyau shikenan, kaje kawai" ya dauka ya kawo qarshen maganar, amma sal ta sake cewa "ya kuke ciki da meenal?,dazu ta dawo tana kuka,ta bata lokaci tana bada direction na abincin da za'a dafa maka,sai kuma naga da takai maka babu abinda ka taba a ciki,me yake faruwa?" Idanunsa yadan rufe kadan,a yadda ya fuskanci yanayinta ko meye zai fada mata a yanzun zata bata masa lokacine ta qara masa hayaqi akai, saidai duk da haka yana bugatar ya datse dabi'ar daukar abinci takai masa company,alhalin suna da kitchen, sannan kowanne kalar abinci yakeso yana daga office jibril zai iya masa order dinsa "Mun fita da madam dauko fadeela daga school" idanu tadan bude da kyau tana kallonsa. Tunda suke dashi bata taba jin ranar da ya zarce daga office dauko fadeela makaranta ba sai yau,yau din kenan har hakan ta fara?, har yarinyar taci nasarar juyar masa da hanakali da sauya masa ra'ayi da tsari?,duk kuwa da tarin taurin kansa da kafiyarsa akan tsarinsa?, wanda ko ita ba kasafai takecin nasarar canzashi ba?. Bata gama wannan mamakin ba ta ganshi ya miqe sannan yace "So please hajiya ki fahimtar da ita basai tayi wahalar kawomin ba,i will be alright, bazan rasa duk abinda nake bugata ba" mamaki ya hanata cewa komai,shi sam baima wani zurfafa dubanta ba bare ya gane ya dora mata "Zan wuce ciki.da wuri nakeso na kwanta" "Jacob baya nan,ko a kai maka dinner?" Ta sake garfin halin fada tana ritsashi da ido tare da son tabbatar da zarginta akan säahar . Hannu yasa ya shafi tattausar sumarsa "No, ba damuwa,i will get something to eat" sai yayi mata sallama yana ficewa. Labiba da haseena, tabbas yana gab da yi musu mummunan warning din da ko sunansa sukaji zasu san nayi,yana musu kara da alkunya ne kawai saboda iyayensa, hajiya qarama da dr jarma,don kwata kwata baya saka mansura a lissafinsa. Yana shirin fita a sashen adama na isowa, hankalinta yayi gaba sosai don haka bata lura da shi ba har sai da yayi dab da ita, cikin zafin nama ta kauce masa abinda ya sanya ta bugi bango ledar dake hannunta ta. yage,magungunan ciki suka zubo qasa. Cikin tsananin rudewa tare da tuna kakkausan gargadin da hajiyan tayi mata wajen kula da maganin har zuwa sanda zata kawo mata shi,sai ta sulale a gurin tana tattarosu tana zabga salati. Kansa ya dauke yana ci gaba da tafiya. Har ya gota yá dawo da baya sakamakon wani tunani da ya darsu a ransa. Akwai masu aiki a gidaje kamar haka da suke ta'ammali da kayan maye qwayoyi ba tare da iyayen gidansu sun sani ba,wasu ma idan aka samu tsautsayi har su koyawa yaran gidan "Ke.. zo nan" kiran da ya sanya hantar cikin adama juyawa,ta dawo da hanzari ta zube a gabansa "Wadan nan magungunan fa?" "Eh... na'am" ta fada a rude tana tuna gargadi na biyu data yi mata,kada ta nuna cewa maganin yana da alaqa da ita ko fadeela "Uhmmnn" ya fadi yana tsuke fuskar nan tasa me sanya shakka da tsoro a zukatansu "Ko kin fara shaye shayen muggan qwayoyi?" Ya fada kansa tsaye yana tura hannunsa cikin jallabiyyarsa ganin bata ds niyyar amsawa. Fassarar da yayi matan ta razanata matuqa,har batasan sanda ta daga kai da sauri tana rantse rantse ba "Wallahi A'ah yallabai,magungunan fadeela ne hajiya tace na karbo daga bakin gate" "Bakin gate kuma?" Ya tambaya cike da mamaki, saboda yasan duka magungunan da fadeela ke sha ba na nan bane, hasalima order dinsu ake mata na kusan million daya,yana damqasu a hannun hajiya qarama har sai sun qare sannan ya sake yi mata order din da kansa (nasan zakuyi mamaki,maganin million daya?,harma fiye da hakan sukan sha,sannan kamar yadda nace wasu da yawa masu gata a cikin masu lalurar EPILEPSY order magungunan nasu akeyi musu,a qalla a shekara sukan sha maganin million daya din, fatanmu Allah ya rabamu da dukkan wasu cututtukan zamani,ya qaremu da lafiya,su kuma ya basu lafiya,wadanda ya zame musu na har abada ne kuma rabbi yasa ya zamar musu kaffara "Eh.. .eh" kai ya jinjina,ko sun qare ne tayi order ba tare data sanar masa ba, sai ya samu kansa da lissafa adadin kwanakin da suka rage su qare din. Har ya daga qafarsa yaci karo da roba,ya tsugunna yana dubawa sai yaga daya daga cikin robar maganin da ya gani ne yanzu,ya waiwaya zai kirayeta amma tuni har ta bace a gurin,ya juyata a hannunsa,kwata kwata tasha banban da robar magungunan fadeela,sai kawai ya jefata a aljihun rigarsa ya wuce. ******Dukka qafafunsa ya zuro waje yana juya zaman agogon hannunsa. Yau din shigar suit ce yayi wadda tayi matugar dacewa dashi,ta fidda kyana kai kace daya daga cikin jaruman Indian films ne. Yau din har da wani extra eye glasses daya mannawa fuskarsa me duhun kala,wannan ya sake qawata fuskar tasa qwarai. Karo na uku va kalli agogon nasa,ya fahimci tunda suka fara ajjiye fadeela a makaranta suke shanyashi,a kullum sai yayi zaman jiransu,duk sanda zata iso kuma tana yine kamar batasan ta sanyashi zaman jiran ba. Kaf duniya idan ka dauke Dr jarma babu wani mutum da yake iya zaman jira,sai ita data karya masa record. Dago kan da zaiyi suna fitowa daga sassan, kamar kullum tana rataye da school bag din fadeela tana kuma riqe da lunch bag dinta, yarinyar itama na dauke da hand bag din sãahar. Sati kusan na biyu kenan da yake ganin fitowarsu a hakan, amma har yau ya gaza saba ganinsu a irin wannan yanayin,duk lokacin da suka fito din sal sun fisgi hankalinsa qwarai, saidai yau din hankalinsa ya dauku fiye da ko yaushe. Tuni ya sanyawa guards dinsa dokar zama cikin motocinsu a duk lokaci irin wannan har su fito su wuce. Shi kansa bazaice ga dalilin da yasa yayi hakan ba,kawai dai yana ji a jikinsa hakan shine abinda yafi dacewa. •Yau din kamar murmushi da fara'ar fuskarta ya banbamta da na ko yaushe. Cikin shigarta da ko yaushe take fita zuwa office din da ita ta laffaya. Saidai kuma a yau din laffayar ta musamma ce. Wata irin lallausar farar laffaya ce me yarfin ruwan gold,wadda ta dace da siririn takalmin qafarta me tsinin dunduniya maras tsaho,wanda zara zaran dogayen yatsunta suka kwanta luf a ciki,komai nata a ranar kusan gold colour ne, sai hakan yayi masifar qara mata kyau da wani irin haske,lafiyayyar fatarta ta fita shar. "Wow" yaji an fada cikin wani mugun zumudi, furucin da yaja hankalinsa aka fusgeshi har cikin kwanyarsa. A nutse ya waiwaya,ba kowa bane tsaye a wajen sai Jamal. Saidai kuma wayace a hannunsa da alama wani abun daban yake kalla. Haka kawai yaji wani abu yazo ya tsaye masa a wuya. Ba yaune rana ta farko da yakejin kamar shigar bata dace da ita ba,amma sai yake gayawa kansa rayuwarta ce,bai kamata yayi mata shishshigi a ciki ba. A yau din duk yadda yaso ya share kaman yadda ya saba sai yaji ya gaza dannewa. Wow din da Jamal ya furta sai yakejin kamar a kanta ne "Dole ka kare martabar aure, ko ba komai sunnar ma'aiki ce daya kamata ace an tsare kimarta" wani sashe na zuciyarsa yaji yana gaya masa. Cikin nutsatsen takunta ta iso bakin motar a hankali, kallo daya tayi masa ta janye idanunta tana rage kaifin fara' arta,wanda wanna din wata dabi'arta ce da tuni ya gama ganeta. Hannu tasa a nutse ta budewa fadeela seat din ta daya side din, qasan ranta tana gulmarsa. Zata iya cewa tsahon lokacin da ta dauka dashi zata iya rantsuwar bata taba gain dariyarsa kamar yadda sauran mutane sukeyi ba,wannan baqin eye glasses din da yasa ko yau din kuma tsautsayin kora da sauke kwandon masifar akan wa zai fada?. Tambayar da ta yiwa kanta kenan, wadda tayi dai dai da saukar sautin muryarsa "Ji mana" ya fadi yana zube mata zagayayyun idanunsa dake da haske qwarai. A nutse ta juya suka hada ido,a hankali idanun nasa suka sauka akan lips dinta daketa ayallin lip gloss. Tun wancan ranar bata sake maimaita saka jambaki ba,tunda yayi mata wannan abun. Bata fata ya maimaita kusanto jikinta,shi yasa ta daina sakashi kwata kwata a bakinta. Dubansa ya sauka daga cikin idanunta zuwa lausasan lips din nata,haka kawai yaji ya hadiyi wani yawu. Sai kuma ya fara qoqarin saita kansa yana sake hade ransa "Wannan shigar bata yi ba,go and change" sosai mamaki ya kamata,sai ta sauke dubanta a nutse ta a kallon kanta tun daga yatsun qafarta zuwa ainihin gangar jikinta,bataga ta inda ake ganin wani abu nata ba. Yana daya daga cikin abinda ya sa take yawan zabar shigar laffaya saboda yadda take suturta kaso saba'in na surarta "But......me shiga na yayi,is like fa kana shiga hurumin da ba naka ba" ta fada tana hade ranta da kyau. Wani kallo da ya dago ya aje mata sai da taji tabbas tayi subutar bakin bashi amsar da tayi a yanzun. Bai sake bata damar yin tunani na biyu ba taji kawai ya damqi hannunta,bai tsaya jiran komai ba ya nufi sassansu yana riqe da tsintsiyar hannun nata,yana jin zuciyarsa na wani irin zafi,ba tun yau ba shigar ke tsole masa ido,daga yau kuma ta bar yinta kwata kwata. "Ka sakarmim hannu mana,kama wuce ga'ida fa" ta sake fada da nata zafin sanda suka isa qofar dakinta. Fusgota yayi ya jefata jikin qofar yana binta da kallo. Take tsoro ya kamata cikin ranta tana mamakin abinda ya Sanya farar qwayar idanunsa sauya kala lokaci guda "Idan na sake jin bakinki sai na shayar dake mamaki" ya fada da zafinsa shima,sai yasa hannu ya murda handle din dakin ya buda qofar ya tura saahar din ciki. Tamkar kurma haka ta zama,tayi tsaye tana kallonsa sanda ya bude closet dinta yanata debo kaya yana zubawa saman gadonta. Batace masa komai ba har ya kammala,ba tare da ya rufe ba ya tako a nutse ya tsaya gaban kayan "Ba kwalliyar ki akace kije ki nuna musu ba da zaki dinga sanya wannan abar,tun randa kika fara zuwa aiki har yau,ki cireta ki zabi wasu daga cikin kayan nan ki saka ki fito" Sosai ranta ya baci, ita ko kadan bata taba sanya laffayar da sunan kwalliya ba,hasalima tana sakata ne saboda tsaro, batasan yawan kallo, tana da tarin kaya lace atamfa shaddodi da sauransu kayayyakin qyale ayale na mata, amma duk ciki tafi qaunar sakata muddin zata shiga taron daya hada hadakar maza da mata. Abinda bata sani ba,a duk sanda ta saka laffayar tana yi mata mugun kyau ne,tare da sake nuna zallar dangantakarta da shuwa "Bazan iya canza kowanne kaya ba" ta fada masa kai tsaye tana dauke kanta daga sashensa zuwa wani sashe na daban hadi da goye hannunta a qirjinta. Ko motsinsa bataji ba bare ta sanya ran yana dakin,har zuciyarta ta fara gaya mata ya fita ne,abun mamaki sai taji hucinsa dab da ita,kafin tayi kowanne motsi taji ya kama daurin lafayar dake qugunta data yiwa daurin zarge ya wareshi,a take ta fara warwarewa daga jikinta. A mugun razane ta kama laffayar ta cukuikuyeta,don tabbas muddin ta warware din ta gama tozarta a idanunsa,zai ga shape na komai nata ne,don wasu rubber material ne a jikinta me golding masu tsayawa dai dai jikin mutum. Hannu daya ya sanya ya zare laffayar a jikinta qwayar idanunsa cikin nata yana karantar yadda hankalinta yayi wani mugun tashi,yayin da ita kuma ta dage tana gogarin tattarota, wani tashin hankali yana bayyana qarara cikin idanunta. Ko kusa ko alama garfinsu baizo daya ba,tayi imanin idan akaci gaba da haka dukka laffayar zata zame ne ta barta gayanta. Dole badon ta shirya ba cikin rawar murya tace "Am sorry i will change it please" yadda tayi maganar da mugun sanyi muryarta na rawa ya karya lagonsa,sai kawai ya sake mata laffayar yana cewa "Kin dauka ni abokin wasanki ne?, Bayan na biya sadakinki duniya ta shaida ke din kin zama halal din da zan iya yin komai dake ba tare da na zama abun zargi ba shine har kike da zarrar tsaiwa kina fadamin wannan maganar na ina wuce hurumina?" Sake rigeta kawai tayi da kyau cikin tunanin mafita "Bakisan zan iya mai dake naked ba kuma nace kiyita zama a hakan a gabana?, kuma banyi laifi ba har wajen Allah?" Daga furtawar kawai da yayi sai taji kamar ma ya maidata tsirarar, abinda ya sake mugun razanata kenan ta kasa cewa komai sai karyar da wuya da tayi. Ya gano ta karaya sosai,sai yaja baya yana qara nisan tazarar dake tsakaninsu "na baki minti daya" ya fada yana sake ja da baya hadi da maida jikinsa ya jingin da mudubi. Cikin rudewa take dubansa,yana nufin a gabansa zata tube ta canza kayan? tashin hankali "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_ BOOK 02 Page 28 "Don Allah ka bani guri, zan canza" ta fadi kamar zata rushe da kuka, idanunta na fidda wani qyallin hawaye, da gaske dai mutumin nan dan iska ne. Idonsa ya lumshe kana ya budesu,duk sanda hawaye suka cika a idanunta wani irin haske suke garayi "Zan dawo muddin kika batan lokaci" yana kaiwa nan ya juya yana fita a dakin. Duk da taso tare hawayen amma saida suka silaloAllah ta yarda baki afifa tayi mata "Aure yana garawa namiji kwarjini a idon matarsa, duk wannan cika bakin da rashin kunyar taki idan baki wasa ba saikin nemeta kin rasa" daya daga cikin maganganun da sukeyi da afifa kenan,wanda ita a nata gurin dai dai yake da tatsuniyar gizo da qoqi. A gurguje ta cire ta sauya da wata atamfa, plain zani da riga ne, ta dora daurinta ta maida mayafin kayan sannan ta fito. Cikin hallway din ya saka wata kujera yar garama ya zauna. Tana bude qofar yana daga kansa daga danna waya. A hankali take takawa saboda bacin ran da yake cin zuciyarta na irin kama karyar da yakeyi mata. Sati biyun da tayi dashi cikin MT JARMA company kawai tana danne zuciyarta ne, amma kama karya kawai yakeyi mata. A nutse ya sauke qafafunsa qasa daga dora daya saman dayan da yayi, still idanunsa suna kanta, kai ya girgiza "Koma ki cireta,batayi ba" sai data kalli kanta,kamar zatayi magana amma kuma yadda ya kafeta da kallon nan nasa yasa ta kasa fadin komai,sai kawai ta juya din tana jin zuciyarta kamar zata fashe. Karo na hudu kenan ta sake fitowar idanunta na mata radadi saboda hawaye,yau din kamar wata wadda kamfani suka dauketa contract na fashion show,ta tsaya a gabansa tana jifansa da harara a fakaice, cikin ranta tayi rantsuwar wannan ce qarshe, muddin yace batayi ba bazata sake komawa ba. Kallon da yayi mata wannan karon yafi na wadancan shigar, duk da abaya ce me sulbi “yar qasar Turkey amma ta fiddata a balarabiya zamm.Janye idanunsa yayi yana miqewa tare da jan sirirn tsaki "Ba zuwa office yau" ya fadi yana fita a nutse yana barin hallway din. Hakan itama yayi mata,saboda ita kanta yau ranta a bace yake. Yau din ya raina mata hankali ya kuma bata mata lokaci yadda ya kamata,inda ace sunje office din to bata jin zata yi komai saboda haushinsa da ya cika mata zuciya. Baqinciki ya sanyata yin zaune a bakin gadonta kawai ta kasa fidda rigar ma daga jikinta, tana jin qarar tashin motocinsu,sai kawai ta koma saman gado ta nade abinta ta kwanta tana jan qwafa, kallonsa a kanta yaqi bacewa daga idanunta,babu wani namiji baya ga adam data taba tsaiwa va kalleta har haka saishi, duk da kowacce shiga jikinta yane yake da mayafi, amma har gangar jikinta tana jin kallonsa shi din me zurfine, don ya banbanta da yadda takejin idanun sauran mutane idan suna kallon nata. Wayarta kawai ta jawo ta bude data tahau online, ta samu afifa kuwa a lokacin "'Bestie yau ba office?" Tsaki ta tura mata, sannan ta fara bata labarin rainin wayon da yau din toufeeq din yayi mata. Abinda ya bata mamaki dariyar da afifa ta dinga aiko mata da ita "Banason wulaqanci bestie, idan ba zaki tayani ba ki barni da bacin ran da ya dasa min" sai a yanzun afifa ke sake yarda cewa akwai fa autanci da gaske, da taga gayyar na shirin watsewa sai tace "Ba shiga sabgar da ba tashi yayi ba, banda abinki bestie duk duniya kallon miji da mata na haqiqa sukeyi muku,kinason ki tona muku asiri ne?, kinga dole yayi komai don ya tabbatar da ingancin aurenku a zuciyar kowa" "Shi ya sani,bazan sake bari ya rainan wayo irin na yau ba" "'Nima ina bayanki" afifa ta fada tana boye dariyarta. Gyara kwanciyarta tayi "Bestie na fara wani tunani cikin raina,inason kiyimin cikakken bayanin yadda za'a magance epilepsy magani na har abada" "You mean surgery?" "idan har ta kama da hakan hakan za'a yi" gyara zama afifa tayi "Idan nau'in epilepsy dinta yana cikin nau'ikan wanda za'a iya yiwa surgery din zaki iya taking risky na hakan? bayan family dinta ma dake tare da ita basuyi mata ba?" Ido tadan rufe tana tunanin maganar afifa, sannan ta bude tana maida mata amsa "I can take the risk afifa indai za'a dace.....anjima zamu tattauna akan ciwon if you are available" "Ba damuwa" ta amsa mata itama, tasan tsaiwa da rashin tsoro da va jima da dasuwa a zuciyar sãahar, indai tace zatayin to zatayi babu fashi. Ta jima zaune a daki abinta, har akayi sallar azahar, ta bada farali tana zaune tana duba lokaci. Batabar gurin ba sai data daidaici lokacin dawowar fadeel daga school ya kusa,sai ta miqe ta ninke abun sallarta, ta sauya kayanta zuwa wata gown sassauqa, don kitchen takeson wucewa kafin su qaraso. Ita ko nadeeya yanzun sun daina cin abincin kowa sai nata. Gown din tayi mata kyau sosai,ta maidata kamar wata baby musamman da gashin kamta ke fake a tsakiyar kanta cikin wani pink ribbon. Gown din me siririn hannu ce, kuma bata gama saukowa ba sai ta dora hijab da ya sauka har gasan gafafunta,ta zura wasu takalma masu laushi ta fito a sashen nata. Dab da zata isa ga sassansu fadeela hajia garama ta fito. Kamar ko yaushe cikin shigar fariya da alfarma, mayafinta a kafada don ita din ba ma'abociyar yafa mayafi bace. Wani kallo tabi sahar din dashi sannan ta saki murmushi tayi gaba "A'uzu bi khalimatillahit taammati minsharri ma khalaqa,Allahummakhfinihim bima shi'ita" ta samu kanta da furtawa saboda wani faduwar gaba da saukar mata sanadin murmushin murmushin da ta gani akan fuskarta. Baaba ramatu ta samu da zuwaira suna hira a falon,ko ina a tsaftace kamar ko yaushe,suka gaisa cikin girmamawa sannan ta wuce kitchen bayan tace da zuwaira da ta mige zata bita suyi zamansu,abu me sauqi zata hada. Veggies couscous ta shirya tare da egg souce, tasan fadeela da son kayan zaqi,ba kuma kasafai take barinta vanzu tayi ciye ciyen kayan kwalin nan na banza da wofi ba,sai ta bude freezer ta fidda kankana ayaba yoghurt ta hado da madara ta zuba sugar tayi mata blending water melon smoothie data cikawa madara sosai. Tana juyeshi a wasu madaidaitan drinking glasses masu bamboo lids bayan ta zare glass straw din da suke dashi nadeeya ta shigo. "Aunty N,yauma akwai special abu da alama, qamshi tun daga compound" tayi maganar tana legen smoothie din da take juyewa "Abincin faddee ne" dan fuska nadeeya ta bata "Amma ana wasa tare ci banban, nidai wannan smoothie din za'a tallafeni dashi,yau nasha rana, inajin ajiye aikin nan zanyi" ta fada tana narke fuska. Murmushi säahar ta saki ta maida murfin ta rufe ta zura mata straw din ta miga mata. Zuqa daya tayi ta lumshe ido "Anty N,bazan iya shan wannan abun a tsaye ba bari na garasa daki" "A fito lafiya " ta fada tana murmushin santin da taga nadeeya din tanayi. Cikin fridge ta maidashi inda sanyi bazaiyi masa yawa sosai ba,saboda ta saka ice cube qurin blending din so da sanyinsa. Muryarta taji tana qwala mata kira "Tom an dawo kenan" ta fadi a ranta tana murmushi, a hankali taii sautin nata yana matsowa kitchen din,sanda ta lita dab da gofa saita waiwayo tana murmushi hadi da dan harara a idanunta na yadda ta tafi school bata nemeta ba yau din. Maimakon fadeela sai idanunta suka hadu da nashi,gabanta ya fadi,ta dauki hannunta tana nadeshi a girjinta saboda yanayin rigar da take sanye dashi, already ta cire hijabinta tun shigowarta kitchen din, saboda tasan babu wanda yake shigowa, daga ita sai baaba ramatu sai zuwaira. Sam bata kawo zai shigo ba,saboda bata taba ganinsa cikin kitchen din ba sam. Duk yadda yaso yiwa idonsa shamaki a kanta amma hakan ya faskara,sambala sambalan singalalin hannunta dake da lallausar fata me santsi yabi da kallo, a hankali ya zarce da kallon qirjinta data lullube da kyau da singalalin hannun nata,saidai duk da hakan hannun nata bai wadatar ba,saboda cikarsu da tsaiwarsu ya sanya suka fito ta saman rigar fam dasu. Kadan kadan zuciyarta ke bugawa tana duban fuskar fadeela tare da qoqarin waskewa da nuna bata damu da shigowar tasa ba. A kasalance ya dauke idanunsa yana cewa da fadeela "Sauka angel ki qarasa" saboda dama ha daukota ne a bayansa da kansa yau din. Kafada ta maqale "Abby ki qarasa ladanka please,ka shigar dani ka kaini gurin anty N" ta fada tana maqale kafada "Ya salam" ya furta a ransa,wannan rigimammiyar ruwa takeson ballo masa. Magiya ta dage da yi, hakan ya sanya ya fara takowa da ita cikin kitchen din yana gogarin hana idanunsa kawai wanann gurin da ya zame masa kamar wata jarrabawa akan yarinyar. "'Matso abby ka gani" fadeela ta fada tana miqewa daga bayan nasa,nufinta ta taka bayansa sannan ta maqalewuyan säahar "What?, sauko angel" ya fada yana dan daga kansa yana dubanta. Sake marairaice fuska tayi "Please mana abby, munyi algawari fa kace yau bazan taka qafafuna a qasa ba" kai ya girgiza yana tuna sunyi hakan, amma shi bedroom dinta yace zai sauketa. Idanunsa ya lumshe ya gara taku biyu gaba yadda yarinyar keso,saahar na tsaye tana murmushi idanunta akan fadeela, saidai can qasan zuciyarta wani mugun gudu takeyi kamar wadda tayi gasar tsere, taku biyunsa su suka hade dukka wani tazara dake tsakaninsu,wadan nan abubuwan da suke tone masa idanu,suka zame masa idanunsa barazana suka samu kyakkyawan masauki saman girjinsa. Yadda yaji saukarsu saman likinsa haka tail vadda girinsa ya tokare nata. Dukkansu jikkunansu suka karbi wani sago me nauyi da bala'in ratsa zukata,yayin da säahar jikinta ya dauki rawar da saura kadan fadeela tasha gasa, banda toufeeq yayi zafin namar taro yarinyar,ya saka dukka hannuwansa ya sauketa a gasa yana duban fuskarta "She's not brave enough,ba zata iya daukanki ba" ya fada muryarsa tana dan sargewa wanda shi kansa baisan da hakan ba. Itakam fadeela da batasan dawar garin ba dariya takeyi tana sake magale säahar "Anty N,abby na ya fiki qarfi, amma zamu hada qarfinmu waje daya muma ko?" Kai ta gyada mata a sanyaye tana jin qafafunta babu qwari sam. Tsaiwa yayi kawai a wajen yana duban fuskarta,yadda lokaci daya hankalinta ya tashi fuskarta kuma cakude da bacin rai kadan. Kasa motsawa yayi shima yana qoqarin controlling kansa kafin yakai ga takawa yabar wajen,jikinsa a sanyaye ya ja da baya ya jingina da kitchen cabinet din yana sake binta da kallo sanda take rige da hannun fadeela bayan ta maida hijabinta jikinta. "Ungo wannan ki fara sha kafin kiyi wanka,kizo kici abinci na gama" sãahar tace da fadeela tana bata drinking glass din. Harda tsallenta, ta dawo gurin toufeeq bayan zuga "Yummy abby sha kail" ta furta tana miga masa. Hannunta ya dafe yana girgiza kai,ta fahimci me yakeson cewa saita maqale wuya "Please mana abby" a nutse ya durqusa ya sanya straw din a bakinsa ya zuqa. Har cikin kwanyarsa dadi da gardin fruit dana madarar ya ratsa masa,ya lumshe idonsa yana jin smoothie din yayi masa matuqa,saidai kafin ya sake sha fadeela ta janye abinta ta kafa a baki. Su suka fara fita a kitchen din yabi warmers din da kallo daya tabbatar abinci ne a ciki,ya shafi cikinsa yana jin yunwa tana taso masa, tunda jacob yaje gida yake wahalar abinci,tun asali mutum ne shi da bakowanne abinci yake iya ci daga hannun kowa ba, gidan cike yake da masu girki da kuma nau'in abinci kala kala amma bai iya ci ba, da abincin jacob kadai ya aminta. Ba mai yawan ciye ciye bane, amma kuma baya wasa da cikinsa ta fannin abinci, idan ya tashi zaiyi masa ci me kyau,daga nan kuma sai lokaci na gaba. Da qyar ya shawo kansa sannan ya fita a kitchen din shima. Sassan nasa babu kowa kamar ko yaushe,bedroom dinsa ya wuce,ya soma zare kayan jikinsa cikin wata muguwar kasala,ya zauna yana zare takalmansa idanunsa suka sauka aka robar maganin. Hannu yasa ya sake daukota yana juyawa,sai ya maida ya miqe yana dauko system dinsa daga inda ya ajiye ya kunnata,akwai result da zai karba yau game da maganin daga gurin Dr anwar,don haka yabar system din tana daidaita ya wuce toilet don yayi wanka kafin ya fito. "HUGUMA* '_TABARMAR KASHI* Book 02Page 29 Sai da ya gama shiryawa tsaf cikin wasu lausasan pyjamas bagaqe a yau amadadin farare da yafi amfani dasu komai ya zauna luf a jikinsa,yaja stool ya zauna vana duba system dinsa. Dukka hankalinsa va bayar akan bayanan da Dr anwar ya turo masa. Lokaci daya yaji wani gumi yana tsatstsafo masa,yasa hannunsa a tausashe ya share yana dungule hannunsa ya rufe bakinsa yana tsurawa system din ido "'Yaya akayi maganin ya kasance daga hannun haliva qarama? me yasa maganin da bai kasance na lalurar fadeelan ba amma take shansa? me hakan ke nufi?" Ya viwa kansa tambayar yana jin hankalinsa yana tashi "Take it easy" wata zuciyar ta gaya masa "'Kayi bincike wisely" aka sake nanata masa. Miqewa yayi yana fita a bedroom din nasa a hankali, ya ciro wayarsa da ya bari a parlor ya fara kiran layin nadeeya. Bugu daya ta daga "Yaa moha" "Me sunan matar nan baga wata gajeriya me jiki dake aiki a sassan momy?" Dan shuru kadan nadeeya tayi sannan tace "Ko adama?" Kai ya gyada "Yes, kiyimin kiranta, amma banason kowa yasan na nemeta" "To yaaya" ta fadi tana ajiye wayar, saita dubi su sãahar wanda suke zaune zasu fara cin abinci "Ina zuwa AUNTY N" kai ta gyada mata,saita koma daki ta dauki mayafinta ta fice. Tun daga yadda ta shiga parlor din zakasan a mugun razane take,ko ina na jikinta rawa yakeyi,gumi kuwa ya gama jiga mata jiki sharkaf. Yau ta shiga masifar da me fiddata sai Allah, dazun nan hajiyan ta gama yi mata kakkausar jan kunne kamar yadda ta saba a duk lokacin da aka karbo maganin, saidai kuma jan kunnen yau din yafi na kullum, kamar tasan abinda ya faru a hanyarta na kawo mata maganin. Da hannu ya yiwa nadeeya nuni akan ta tafi,ba musu ta juya,cikin zuciyarta tana taya adama alhini,ko wanne tsautsayi ne yasa ta shiga gonar toufeeq din? wanne irin laifi tayi masa haka?. Tun kafin yace ta zauna gafafunta suka kasa daukarta, saita sulale tayi zaman dirshan a gurin. Kallo daya yayi mata ta fashe da kuka, tama mance da wani jan kunne na hajiya qaraman "Wallahi bansan komai a kai ba indai batun magungunan ne" idanunsa kawai ya zuba mata yana mamakin rudewar da tayi. Sake debo rantsuwa tayi "Na rantse da ikon Allah bansan komai ba" “Tun yaushe ake kawo maganin?" Ya jefa mata tambayar Shekara biyu…shekara biyu a cikin ta uku* ta bashi amse kowanne sashe na jinta yana kakkarwa. Wani irin zafi idanunsa yaji sun fara yi masa, abinda zuciyarsa ke hasaso masa har bayaso sukai ga kwanyarsa bare ta sauya masa su ga dayan sashen na zuciyar tasa *ki hada kayanki gaba daya,na sallameki daga aiki a gidan nan" abindia ya fada kenan. Faduwa tayi a gurin tana hurwa tana kuka sosai, saboda tasan muddin tabar aiki a gidan asirinta ya tonu,mutane masu yawan gaske ne suke neman damar yin aiki a gidan amma basu samu ba Tsawa ya buga mata wanda ta sanya ba shiri ta tattara zaninta ta fice tana kuka. Shuru yayi yana maida jikinsa ga kujerar idanunsa a lumshe "To maganin meye?" Tambayar da Dr anwar dinma bai bashi amsa ba, yace masa baida alaqa sam da ciwon fadeelan, suna kuma ci gaba da bincike. "Wanne magani kenan ake bata yanxu?" Tambayar da tazo kansa kenan,ya kuma miqe a nutse ya sanya flip flops slippers dinsa yana baro sashen. Tuni ta gama cin nata abincin ita da fadeelan, nadeeya ce tayi saura,don haka suka barta a falon suka wuce daki don ta shiryata ta bata maganinta tasha. Toilet ta kaita, kamar ko yaushe yanzu ta fara canza pattern na wankanta, zata hada mata kayan wankan gaba daya,tayi mata tsarki ta wanke mata bayanta da sauran inda hannunta bazai kai ba,sauran kuma saita tsaya tana kallonta tayi da kanta, tanayi tana gyara mata har su kammala. Sanda yayi sallama dakin basuji shi ba,suna bandakin tanata tsokanar fadeelan saboda yau ta dage bayan nata ma zata wanke da kanta. A nutse ya garasa shigowa,ya maida murfin qofar ya rufe, idanunsa suka sauka akan dressing table din fadeelan inda kayan baccinta maganin nata da sauran tarkacen kayan nata suke. Kai tsaye ya dauki robar maganin yana dubawa,sak irin maganin da yasan yana siyowa da kudinsa va damgashi ga hajiva garama har na tsahon watanni shid,bayan wata shidan kuwa baya taba batan lissafi zai sake kawo wani na wata shidan. Bude robar yayi ya zazzago maganin. Shine asin da asin babu banbamci, sai ya maida murfin maganin ya rufe ya maidashi inda vake vana fadin "Hasbunallahu wani'imal wakil" wane sashe na zuciyarsa kuma na tambayar sa,waye yake bata kudin siyan maganin?. Lokaci daya komai ya rikice masa,lissafi yaso qwace masa,ga hajiyan da wani magani sabanin wanda ake baiwa fadeelan, ita kuma gata da irin maganin fadeelan ba tare da yasan waye yake siya ba. Komawa yayi ya zauna saman sofa bed,har ta gama wankan suka fito tana tsane mata gashinta da hoodie towel din data rataya mata saman kanta. "Abby...." Fadeela ta fadi, abinda ya jawo hankalin sãahar sal tadan ja da baya tana boye jikinta a qofar. "Abbyyy..." Maganar yarinyar ta magale mata a maqoshi,a hankali yatsun hannunta dana gafafunta suka fara motsawa suna shacking. Dukkaninsu suka fahimci abinda ke shirin faruwa da ita,lokaci guda kuma kowanne ya taso da mugun hanzari suka nufo fadeelan,shi ta gaba sãahar ta baya,suka kuma isa gareta lokaci guda tare da rarumota cikin jikinsu saboda kada tayi mummunar faduwar da zata ji ciwo. Shi yayi nasarar rungume fadeelan,yayin da säahar ta saki wani irin kuka mara sauti cikin narkewar zuciya tana kiran sunan fadeela "Shshshsh" ya fada yana dora yatsansa saman lips dinsa duk da cewa shima cikin tashin hankalin yake "Stop crying" ya sake fada da muryarsa da taynkaushi.va mige a nutse ya kaita saman sofa bed ya kwantar da ita sosai yana ambaton sunan Allah a ransa. Ta dauki tsahon kwanaki masu dama rabon da ta samu wannan attack din,kusan zai iya cewa harma ya manta,ya kuma tsammaci lalurar ta tafi kenan. Idanunsa suna kan agogo yana yana lissafa adadin mintunan kamar yadda ya saba,yayin da sautin kukan säahar ke shiga masa kunnuwa,sai ya dinga jin kamar ana soka masa allura cikin qwaqwalwarsa,wani irin ciwon kai ya fara saukar masa kadan kadan har cikin idanunsa. Wannan karon bata gara ba akan mintunan data saba yi, ta bude idanunta a hankali tana kallonsu. "Aunty N,faduwa nayi ko? ‚na dauka na warke na daina faduwa" furucin da ya sanya sãahar tsananta kukanta,hawaye masu yawa suka jige mata fuska ta kasa controlling dinsu, gaba daya hannuwanta suna cikin na fadeela ta rigeta tsam "Zaki daina daughter, zaki daina in sha Allah very soon, in sha Allah,in sha Allah, i promise" duk da yadda kansa yake sarawa hakan bai hanashi dubanta ba,bai taba ganin hawayenta da kukanta ba kamar yau, kamar ma ta fishi shiga tashin hankali. A nutse ta mige ta dauko tissue ta dawo ta zauna a gefanta tana share mata majinar data zuba daga bakinta hade da yawu. Hannu fadeelan ta miga tana share mata fuska "Ki daina kuka anty N,na dauka na warke ne, amma ai na saba" migewa tsaye yayi yana saka hannunsa a aljihun wandonsa kansa yana sake sarawa,yanajin kalaman fadeela har cikin zuciyarsa,yana jin kamar ya gaza. _WASHEGARL Cikin jikinta fadeelan ta kwana a daren jiya,da safe ma tace yau ba school, tunda juma'a ce ta zauna a gida ta haqura. Da safer tayi mata duk abinda ya kamata, duk da cewa Zuciyarta babu dadi,haka gangar jikinta babu kuzari, amma haka ta daure ta koma sashensu. Me share share ta samu yana aikinsa,kamar yadda toufeeq din ya maidashi akin sassafe, shida zuwa bakwai ya gama komai,idan kuma ya makara saidai ya bari kuma sai bayan sun fita office. Gefe yaja yana sadda kansa gasa sanda yaji sallamarta "Good morning maa" ya fada ba tare daya kalleta ba "Morning"' ta amsa masa tana wucewa. Samun kanta tayi da kallon gofar dakin nasa, ba alamun da mutum a ciki,duk da cewa daman kusan kullum kamar haka qofar yake, amma yau sai taji abun yadan ja hankalinta, duk da haka ta watsar ta isa nata dakin tana shiryawa a hanzarce don kada tayi late. Ta zarta lokacin shirin nata, amma ga mamakinta har ta kammala shiryawa ta fito bataji wanann sassanyan qamshin nasa da duk safiya yake gaya mata kammala shirin boss din ba. Ta iso parlor babu kowa, dama jacob ne zaka samu ya raya falon da qamshin abincinsa, shima tunda yaje gida wanna yayi qaura. Yankewa tayi ta fita farfajiyar gidan saidai kafin ma ta qarasa duka taga babu motocin da suke fita din ko guda daya "Good morning madam,ya jikin oga din?" Muryar jibril dake magana cikin girmamawa ya furta. Da dan sauri ta waiwayo "Jikin oga kuma?" Ta tambayi kanta da kanta,ta tambayi jibril din kamar zubewar kimarta ne, saita amshe kawai "Jiki da sauqi alhmdlh" "Allah ya qara afuwa" "Ameen" ta amsashi. Qafafunta babu qarfi sam ta koma ciki, taja burki a falon ta tsaya tana tunanin meye abunyi?, at last taga babu wani abu da ya rage illa ta shiga dakin da kanta. "HUGUMA* "_TABARMAR KASHI_' Book 02 Page 30 Sau biyu tana dora hannunta akan handle din tana janyewa. Tana tunanin yadda zata shiga dakinsa yau a karon farko, tana kuma tunani da tsoron kada ya fasarata. To amma kuma zuwan ya zame mata tamkar wajibi,don kowa a gidan da zai buqaci jin yanayin lafiyarsa ita zai fara tuntunba daga bakinta kuma za'a so aji komai. Uwa uba fadeela, data tashi ta tabbata abby din zata nema. Kuma ko babu komai rama alkhairi sai dan halak, shine mutum na farko daya fara kulawa da kuma lura da sauyawarta lokacin da ciwon kanta ya motsa. Sama sama ta soma jin kamar muryar meenal daga falonsu,wanda daga shi sai hallway din da kuma bedrooms dinsu. Bata sake tunani na biyu ba ta murda gofar kawai ta shige. Dai dai lokacin da yake kwance cikin duvet, bai jima da komawa ya kwanta ba,saboda a jiyan bai samu wani cikakken bacci ba,gaba daya idanunsa ne suka soye yanata hada lissafin da bai samu nutsuwa a kansa ba sai da zuciyarsa ga bashi gamsuwa da rinjaye akan bangare guda. Koda ya samu baccin sai tashi farkawa ba sai qarfe shida na safe, alfijir ya fara ketowa sosai. A razane ya sauko, hanzarin da ya sanya kanshi sarawa ya rige kan yana takawa a hankali ya wuce toilet. Alwala ya daura ya zauna yayi sallarsa,ya duba first aid kit ya balli maganin ciwon kai yasha. Yana gama lazumin ya lallaba ya koma gadon yana sake qudunduna a duvet din. Idanunsa ya lumshe a hankali,yanayin da vake tsintar kansa kowacce asuba ya fara sauka ga jikinsa, abinda bai taba tunani ba saboda ganin yadda ya kwana yana fama da tunani bacin rai da kuma ciwon kai. Matse jikinsa yayi guri daya vana lumshe idanunsa,abun mamaki sai ga hotonta kar cikin duhun idanunsa sanye da farar gown dinta me qaramin hannutsigar jikinsa ta zuba lokacin da ya tuna yadda jikinta ya gogi nasa,sai ya runtse idonsa da kyau ya juya yayi rub da ciki yana gangame pillow da hannunsa tare da ambatar sunan Allah a sarari. Duk yadda yayi zaton na wasu mintuna ne zuwa awa komai zaiyi narke masa amma abun ya wuce tunaninsa,maganin ciwon kan da yasha sai yakeiin kamar maganin wani garin garfi ya sha bana ciwon kai. Sake tura kansa yayi cikin duvet din yana kiran sunan Allah gasa qasa,jikinsa yayi dumi sosai ,sai hucin numfashinsa da ya cika duvet din wanda ke gauraye da sassanyan night scent dinsa,da ya rufe idanunsa ita yake gani cikin mabanbantan yanayin da yake ganinta, idan kuma ya bude idon nanma ba sauqi, abun kamar wani tsafi ko sihiri. Kamar cikin mafarki yaji tattausar muryarta tana yin sallama cikin dakin. Tsai da numfashinsa yayi na wucin gadi yana cike da mamaki da kuma tantama, idanunsa a rufe ruf ba tare daya motsa ba, kunnuwansa suna jiyo takunta cikin lallausan carfet din dake dakin duk da takun nata baya bada sauti. Koda bata zurafafa kalle kalle a bedroom din baiya iska da gamshin da yake fiddawa kadai ya isa gaya mata na musamamn ne fiye da kowanne daki dake gidan. Wasu irin furniture na alfarma masu tafiya da hankali, luxury curtains da suka mamave dakin suka sanvashi ya sake zama wani luf luf da babu lallai ka iva tantance dare ne ko kuwa rana?. Akwai wadatar hasken fitilu a dakin har kusan color biyu,farin qwai da kuma light blue sai suka hadu suka bada wata kwantacciyar kala me kvau a kowanne sashe na dakin,frames manya manya dake dauke da ayoyin tsari ne a kowacce kusurwa ta dakin. A kallon da tayi masa sai jikinta ya bata bacci vakeyi,abinda zataso tayi shine komawa,to amma zuwa lokacin ta jiyo muryar haseena daga bakin gofar dakin, zuwa lokacin ma har ta fara knocking. Yau daya tak taji wani abu ya taba zuciyarta,wanda bata dorashi a mizanib komai ba sai na haushin rashin hankali da rashin kamun kan meenal din "'Yau zataga qarshen fitsar" ta gayawa kanta d kanta,don haka sai t wuce bakin gadon kai tsaye ta zauna kusa dashi. A yadda ta zauna kawai sai da tsigar jikinsa ta zuba,ya runtse idonsa ta cikin duvet din yana sauke numfashi a hankali. Zubawa lallausan creamy white duvet din idanu tayi tana sauraren knocking din da meenl ke ci gaba da "Koda yayyanka uwa daya uba daya, bai cancanci kazo dakinsu a irin wannan lokacin ba,ko ita da ta taso a mazaunin auta yar lelen yayyenta,har suka gama rayuwarsu cikin gudan ko da safe maama bata bari taje a wannan lokacin. A nutse ta daga kanta jin ta fara murda gofar, tana nufin shigowa zatayi kenan? ta rantse yau saita nuna mata iyakarta, don haka ba tare da tunanin komai ba ta dage duvet din ta tura kanta gaba daya har zuwa rabin bayanta a ciki, abinda ya bawa numfashinsu d qamshin su damar gauraya guri day kuma lokaci daya,kowa ya zuqi hucin numfashin dan uwansa har cikin huhunsa. Idanunsa ya lumshe yana jin yadda numfashinta ke sauke yana garawa duvet din dumi, ko sau daya bai motsa ba,har zuwa sanda aka tura qofar aka budeta. Mugun bugawa zuciyarta tayi, saboda ganin qafafun mutum biyu cikin duvet daya, take zuciyarta ta ayyana nata ga abinda sukeyi "Na shiga uku!" Ta fada da garfi tana sakin qofar, ta kuma juya da hanzari ta fice. Qaramin tsaki säahar ta saki bayan ta tabbatar da ficewarta,sannan ta yungura zata miqe tana qogarin yaye duvet din. Hannunsa ya sanya ya zagaye wuyanta da kyau,a hankali yana warware idanunsa ya saukesu fes cikin nata "Ina zaki?" Ya furta a hankali cikin salon rada da wani irin taushi yana kallon zara zara din gashin idonta dana girarta,wani abu yana tsarga masa saboda ya samu kusanci da ita fiye da yadda ya taba samu tsahon sanin da yayi mata a rayuwarsa,ainihin kamanninta hadi da cute face dinta yau ta zama kusa da shi sosai fiye da ko yaushe jarababben qamshin nan nata gaba daya ya cika duvet din. Tsigar jikinta ce ta tashi saboda iskar daya baza mata saman fuskarta,kasa magana tayi sai ma gogarin sake migewa da takeyi saidai babu dama saboda ya tare ta da hannunsa "Ina zakije nace? bake kika kawo kanki ba?" Ya sake fada yana lumshe idanunsa dake kan fuskarta,yana jin yadda komai na jikinsa ya fara wani irin aiki. Gabanta ne ya fadi,sai yanzu ta fahimci wautar data tafka,ta sauke idanunta cikin toro da d'ari d'ari ga gangar jikinsa. A tube yake babu riga,sai tarin lallausat gargasar data cika girjinsa me santsi da laushi, gabanta ya sake faduwa ta maida idanunta ta kulle gam,qirar jikinsa toro yake bata, saboda jikinsa ya ginu da wasu irin muscles dake nuna yadda ya baiwa motsa jiki muhimmanci "Me kikazo yimin?" Ya sake fada muryarsa na sake karyewa da yin laushi, labbanta dake walainiyar lipstick suna fusgar hankalinsa,yana jij kamar ya cinyesu "Bab.....ba komai, just nazo ne gaya maka na gama shirin fita,saik kum...... "Sai kuma na baki sha'awa ko?, kikaji kinason ki rungume ni?" Ya garasa fada yana dage dukka girarsa sama. Ido ta fidda waje,abinda take gudu kenan zai manna mata sharri "Allah ya kiyaye,meye abun sha'awar a nan?" "Oh really?, dama kince babu maza a gidan nan ai ko?" Shaf ta mance da maganar sai yanzu, amma ganin yana son raina mata wayo saita fara quna quni tana son qwatar kanta "Banyi garya ba.....ka sakeni" ta fadi tana son janye hannunsa amma ko gezau, tako ina ya tsareta tas.va ma sake matso da ita sosai cikin jikinsa. Sai data soma gajiya sannan ya zare hannun nasa,yana jin yadda jikinsa yake fidda gumi saboda saukar zazzabin nasa da kuma yanayin da yakejin jikin nasa a ciki. Da hanzari ta zare kanta daga duvet din tana nishi, tuni dankwalinta ya zame daga kanta, tana gyara yafen mayafinta ya yaye duvet din saman kansa yana dubanta gasa qasa "Coffee please" ya fadi har yanzu muryarsa na cikin wani irin rauni "'Ina kwana?" Ta fada cikin zafin rai da yadda gaba daya ya janyo ta yamutse "Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice yana maida kansa cikin duvet din, don babu abinda ganinta yake qara masa sai shiga wani irin yanayi dake sanyashi birkicewa. "Idan kika wuce baki kawomin ba sai kin gane baki da wayau" ya fada qasa qasa, kamar yasan shirinta kenan. Baki ta tura gaba kamar ta fasa kuka,shi kam ba'a masa abin arzigi sam,inda tasan irin wannan cakumar zaiyi mata da ba shakka bata shigo dakinsa ba. Tayi mamaki sosai sanda ta bude gofar dakin ta samu haseena zaune a gurin. Kallon kallo suka yiwa junansu,sai haseena din ta mige tsam ta kewaye säahar ga mamakinta sai ta kama handle din gofar ta tura ta shige. Karon farko. wani abu mai nauyi ya tsaya mata saman zuciyarta, tabi qofar da tuni haseena din ta maidata ta rufe da kallo, sai taji ta kasa daga qafafunta "Shin meye nawa?" Ta yiwa kanta tambayar, tanason garyata kanta da kanta game da damuwa da takaicin da taji a ranta. Kai ta girgiza tana son tabbatarwa kanta cewa ba komai bane ba kuma abinda ya shafeta bane don haka ta soma takawa tana wucewa kitchen din. Duka duka mintuna biyar sun isheta ta kammala hadawa, wasa wasa sai gashi tana dosar minti goma tana dawurwura cikin kitchen din, kadan kadan wani irin bacin rai ya soma hayewa zuciyarta,wanda ya janye dukka wata nutsuwa da walwalarta,sai data zuba coffe powder din spoon uku sannan ta tuna yayi yawa, ta zare dot din ta zubar tana sake hada wani. A hankali ta saki spoon din sugar ta koma da baya ta jingina da kitchen cabinet din, tamkar yayewar hijabi ta hango abinda ya faru da ita shekarun baya. Adam take gani fes saman gadonta na aure tare da wata,lokacin da ta kamasu a zahiri,yaci gaba da duban qwayar idanunta ba tare da ya bar abinda yakeyi din ba. Sakin cokalin tayi a qasa,kamar wadda aka fusga ta nufi hanyar kitchen din tana in kanta kamar zai fashe lokaci guda zuciyarta na sake haska mata shigar haseena dakinsa cikin wata banzar rigar bacci da wani gantalallen mayafi dan mitsitsi. Da wani irin qarfi ta buda qofar dakin, abinda ya jawo hankalinsu kenan su duka biyun,shi da yake zaune saman gadon da haseena dake tsaye a qasa amma dab da gadon hawaye suna wanke mata fuska. A hankali idonta ya sauka akan jikinsa da babu riga,sai ginannen qirjinsa dake bayyane, saboda duvet din ya dawo iya cinvarsa zuwa gafafunsa "Bacemin a gun" ya fada a tsawace, sai haseena ta juya da sassarfa tana fita a dakin, sautin kukan da taketa cinyewa yana qwace mata. Jiri jiri ta soma ji,tana jin tsawar har cikin kwanyarta itama, fara takawa tayi zuwa gefansa don ta lalubi wayarta da kuma dankwalinta tabar masa dakin itama "Where is my coffee?" Ya tambayeta da muryarsa deep inside fushi yana azalzalarsa "Ban dafa ba" ta bashi amsa kai tsaye tana jin kamar zuciyarta zata tsage. Idonsa ya lumshe kana ya budesu,yana hangen tsiwar nan fal idanunta "Har yanzu ban koya miki darasi ba shi yasa baki fasa yimin rashin kunya ba...... "Me yasa zaki barta ta shigomin daki a cikin yanayin da nake ciki?,idan da a tsaye ta ganni kinsan abinda zai faru?" "Sai kayi mata abinda kace kana yiwa mata, tunda dama budurwa ce ina kyautata zaton indai bawai ka karba yadda kace kana karba ba,qila shine dalilin bibiyar.....waima meye nawa a ciki?,live your life, bani da case" ta bashi amsa da wani irin zafi har cikin ranta tana in qunar da batasan dalilinta ba, kalamansa kuma suna dawo mata. Kamar ta yanki zuciyarsa da reza haka yaji,wani irin fushi ya taso masa, ita batasan dukka laifukan ta ba? ta yaya zata dinga bari mata suna samun access dashi ta kowacce hanya?,a kirashi a waya ta bashi su,su shigar masa office su shigar masa sashe harma ta fita ta barwa yarinyar sashensa? yarinyar da ko falonsa na farko bai taba bari ta shiga ba yau gata cikin bedroom dinsa a lokacin da yake cikin wani yanayi?, banda Allah yasa yana kwance tasan iya dadin zubar da mutuncinsa zaiyi?, koda bai shirya aurenta ba wanna zai zama sanadin da dole ya aureta. Maganganunta suka sanyashi jin he is nothing, bazai qyaleta ba yau sai ya nuna mata BAMBAMCIN DAKE TSAKANINSU. "Kema yau zanyi miki abinda nake musun, kinga daga nan zaki gane dalilin da yasa suke bibiyar tawa" Ya fada yana sanya hannunsa yayi mata kyakkyawar fuzgar da bata dire ko a ina ba sai saman jikinsa. Dukkan jikinta ne ya dauki rawa lokacin da suka samu sadarwa tsakanin ilkinsu a sannan ta gane me yake nufi da yace ya godewa Allah data sameshi a zaune. Cikin kwanyarta taji kamar zata zauce sanda ya riqe fuskarta da kyau a tsakiyar tafin hannunsa,ya kuma hade bakunansu guri daya. "HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_ Book 02 Page 31 Duk yadda tayi zaton zai mata mugunta da labbanta yanda yayi mata wancan karon ba haka bane, cikin wani irin taushi da tsananin qwarewa waien iya sanin kalolin kisses yake sumbatarta hadi da lashe lips dinta zuwa harshenta dama ilahirin bakinta gaba daya,cikin second biyar yanayin fitar numfashinsa va fara canzawa da wani irin gudu har girjinsa yana dagawa. Lausasan hannuwanta da sukayi wani mugun sanyi ta aza saman nasa hannun dake kan fuskarta tana gogarin turewa saidai ko gezau baima ji me takeyi ba, yaji dai saukar wani sassanyan abu me laushi akan hannunsa,wanda ya qara saukar masa da wani yanayi cikin kowanne sashe na jikinsa ya kuma gara masa qaimi. Sai daya tsotse bakinta iya yadda ransa yayi masa,ya kuma tabbatar da mutuwar jikinta da kyau sannan ya juyeta zuwa saman gadon,ya kuma zame mata rumfa, bai sake mata bakin ba duk da haka,sai hannuwansa da ya zame a hankali ya zurasu ta gasan rigarta. Daidai cibiyarta suka sauka,ya fara yawo dasu tun daga nan yana haurowa sama, yana nufar ababen harinsa na tsahon lokaci,wanda a yau yakejin kamar numfashinsa zai fita saboda son isa garesu. Ci gaba yayi da hawa sama da hannuwan nasa,yana isa yaji akwai babban shamaki tsakanin hannun nasa da su,sai ya dagata cikin zafin nama yana neman zip din rigar. Baisha wahala ba saboda zip din gaba ne da rigar, tana jin garar zipping din rigar tasa dukka hannuwanta ta damqe hannun nasa idanunta na malalar da hawaye tana girgiza masa kai,sam bata shiryawa wannan rayuwar ba "'Kada ka karya yarjejeniya......kada kayi cin amana" fararen idanun da suka juve zuwa ruwan goro ya lumshe,CIN AMANA?,SHI DA SADAKI YA BIYA YA AURETA A HANNUN WALIYYANTA DA SHAIDU?. Maganar data furta sai ta zama kamar zuga cikin kunnuwansa, ya tabbatar idan bai tabbatarwa yarinyar ta halasta a gareshi ba wannan bakin nata bazai mutu ba,ba kuma zata daina gaya masa maganganun da basu da tushe a wajen kowa ba tamkar hayarta yayo ba aure aka daura musu ba. Jaa daya ya yiwa zip din sai gashi ya balleshi gaba daya har qarfen ya fice daga jikin zip din fara tas din fatarta ta bayyana da dukiyar fulaninta dake lullube cikin marron din brassiere me lace,sai suka zama tamkar wasu fure cikin fulawoyi. Kalar bresssier din saman fatarta yayi wani mugun haskata, abinda ya sake sanyashi rudewa ba tare da ya tsaya cireta ta baya ba ya janyeta sama take hannuwan da suka kasance irin wadanda ake iya sanyawa da cirewa ne suka zame daga likinta, wannan ya bashi damar cireta fit daga jikinta ta saman kanta vavi wurai da ita aefe. Gaba daya dimaucewa ya sakeyi,wani abu ya zarta cikin kansa lokacin da hannuwansa suka isa ga muradinsa kuma mafarkinsa. Sanda taji dumin hannunsa a nan kukan da take boyewar sai ya subuce mata ya sakar mata nauyinsa ne sosai bata da katabus din iya awatar kanta,duk wani qarfi nata ya gare, yadda yake yamutsata ya wuce abinda hankalinta da kwanyarta zasu iya dauka,ba'a taba yamutsa jikinta tare da cin moriyar albarkatunta ba irin a wannan lokacin. Lokacin da taji ya dauki hanvar tabbatarwa da kansa sadakinsa,tare da dora mata idda da amsa sunan matarsa ta sunnna sai hawayenta ya qara gudu, ba abinda yake dawo mata kai a sannan sai maganganunsa masu ciwo da zafi a zuciyarta "Ka manta bansan darajar jikina ba?" "Am really sorry,afwan afwan afwan" ya fada vana cusa fuskarsa tsakiyar qirjinta da yakejin kamar ya hadiyesu "Kada ka manta,ni bazawara ce "Ta sake fada tana goqarin tuna masa ko zatayi nasara ya qyaleta "Nima bazawari ne" ya amsa mata vana sake gangameta kamar zai tsagata gida biyu, muryarsa na wani irin rawa, labbansa suna haduwa suna rabuwa "'Na taba yin bari har sau bivu fa" "Na haifi fadeela" ya amsa mata vana gogarin sake gusar mata da hankali ta wasu hanvoyi da zaivi wahala hankali ya isa guje musu "Kafin kai wani ya taba aurena ya sanni.. "Noooo!!!" Ya fada da wani irin qaraji wanda ta tabbatar indai da mutum a kusa babu abinda zai hanashi yaji "Ki fadi komai amma banda wannan kalmar, zaki iya kasheni da ita" ta fahimci hakan da tace ya shigeshi da kvau don haka ta gara cewa "Ba garya nayi maka ba‚na taba hada gado!.... "I will punish you!" Ya fada a kausashe yana jin lokaci yayi da zai bata darasi me wuyar mantawa,wanda kuma zaisa ta manta da kowa da komai ko zai sami tabar kunnuwansa su huta. Wasu irin salo ya fara aiwatar mata,wanda ya kusa sanyata shidewa,har cikin kwanyarta ta dinga jin kamar zata zauce,sai daya tabbatar duk taurin kanta da kafiyarta ya kaita inda ba zata iya gocewa ba sanann ya fara sanyata amsa sunan MATAR TOUFEEQ Tun tana fahimtar komai da kuma amsar sagon a dai dai har ta fara gane cewa shayi fa ruwa ne sallarsa sai kuma was sinadarai, idanunsa cikin tsakivar nata idanun ya hanata ko sau daya ta motsa su ko ta saukesu daga kanta,wannan din wani sirri ne daya barwa kansa,har zuwa lokacin da ta fara ji a jikinta, ta fara kuka tana neman garfin tureshi amma abun yaci tura. "Am sorry....afwan, kiyi haquri,na tuba" abinda ya dinga maimaitawa kenan,saidai duk da hakan bai hanashi aiwatar da abinda yakeyi din ba,wanda kafin yakai ga sake mata nauyinsa ya kuma rungumota cikin jikinsa da mugun garfi ita a lokacin ta gama galabaita. Wani irin numfashi yake saukewa a hankali idanunsa a runtse kowanne sashe na jikinsa hatta da iinin dake gudana a ilahirin jikinsa yana jin kamar an wankeshi an zuba masa sabo, qwaqwalwarsa na masa bitar dunivar da va shiga wadda yakejin tamkar bai taba shiga duniyar da tayi shigenta ba yanajin kamar yau ne ya fara aure a duniya, kuma kamar yaune karonsa na farko daya fara sanin diya mace. Kansa ya juya daya sashen "Hasbunallahu wani'imal wakil"" ya furta can gasa yana tuna abubuwan da suka faru daga daren jiya zuwa yau,zuciyarsa na wani irin bugawa,yana jin shakka gami da kokwanton abinda zuciyarsa ke ayyana masa game da hajiya garama. Tafin hannunsa da sukayi wani irin gumi da dumi ya bude ya kutsasu tsakiyar na säahar wadda ke fidda wani irin kuka tsakiyar girinsa ba tare da ta sake yungurin yin komai ba,saboda meye ya rage kuma?, komai ya riga ya gare. Ya kasa cewa da ita komai kamar yadda ya kasa kallon fuskarta, ya sani shi kansa cewa taji a jikinta iyaka,ba ita ba,ko shi da yake namiji ya san cewa yau din yayi wani irin aiki da bai taba kamarsa ba, duka duka auratayyarsa da ameesha bata wuce a irga ta ba tsahon zamansu, duk da kasancewarsa me wata irin mabugaciyar halitta. Karon farko yayi yungurin lallashinta saboda yadda sautin kukan nata ke haduwa da yanayin da yake ciki suna son sake birkitashi. Jawota ya sakeyi cikin jikinsa sosai, fatar jikinsu ta mannu data juna. Shi da ita dukkansu sai da sukaji a jikinsu saboda yadda lokaci guda kowa sago yakai har kwanyarsa,shi kam kasa boyewa yayi saboda ajiyar zuciya ce ta qwace masa har numfashinsa na wani irin rawa. "Its okay,am really sorry, na karya doka da yarjejeniya ko?" Yayi maganar da wani irin taushi da rauni, vana jin wani abu me matugar garfi yana ratsawa jiki jini da jujiyoyin jikinsa,yana saukar da wani abu me sanyi har saman zuciyarsa, zuciyar dake cike taf da rudani, amma a vanzun wani irin nutsuwa da aminci na ziyartarsa. Har cikin ranta taji gatse yakeyi mata,don haka ta dunqule hannunta cikin garfin hali ta soma qoqarin tureshi tana cewa "Dama ku din ai kun qware ta wannan fannin rantsuwar garya,yaudara da cin amana, banyi mamaki ba, amma ka sani yadda ka keta haddina bazan qyale ya tafi a banza ba" murmushi ne ya subuce masa, vadda take maganar kadai ya isa gaya masa lallai wanna dan garamin bakin tsiwar yau anji jiki. Bai kulata ba sai gafarsa da ya sanya ta garfin tuwo ya raba gafafunta biyu ya Sanya tasa a tsakiya,sannan yasa dukka hannunsa biyu ya sake jawota jikinsa sosai yana rufe tazarar dake tsakaninsu,yayi mata kyakkyawar runguma cikin yalwataccen girjinsa da gargasar dake cike da ita ta zame mata tamkar wani bargo "Naji na yadda, kome zakice na yarda,but am sorry maaa" takaici ya gara qumeta,a yadda ya sake gangameta yana shanshana gashinta zuwa wuyanta yana sake sauke wani numfashi sai tsoro ya sake shigarta,wani sabon qarfi yakeji, saboda ya doshi shekara kusan hudu cikin ta biyar rabonsa da ya wasa lafiyarsa haka,yana kuma son mantawa da bacin ran dake cin zucivarsa wanda duk idan ya tuna yakejin kamar zuciyar tasa zata tsinke ta fado. Sakinta yayi a hankali saboda kota ina ya tabbatar yana da bugatar zagaye na biyu,ya sauka daga saman gadon ba tare daya damu da rufa komai a jikinsa ba ya wuce bandaki. Duvet ta jawo ta lullube jikinta da kyau tana hawaye, idanunta a runtse tana jin wani yanayi cikin zuciyarta. Yaye duvet din tayi bayan tayi tunanin gwara ta fice a dakin kafin ya davo, don batasan da wanne ido zata kalleshi ba ya gama da ita gaba daya,yasa ita kanta kunyar kanta da kanta takeji. Tana motsawa tasan tabbas taji ciwuka a gurin, hawaye ya sauko a idanunta, tasan cewa dama hakan zata iya kasancewa,saboda wani irin jiki Allah ya bata, wanda tun baya idan aka samu tazarar mu amala tsakaninta da adam,ko kuma yayi wata tafiyar to duk ranar dava dawo mata sai taji alamun ta sake hadewa bare vanzun data dauki was shekaru, sannan kuma ita kanta tasan ba garamin gyara inna charifa da me gvaran iikin da maji ta aiko tayi mata ba. Idanunta ta runtse tana hawaye tare da tunanin yadda zata fita a dakin tana jin wannan ciwon Alwala ya daura saboda cika umarnin ma'aiki S A W da yace, duk wanda yake bugatar zuwa ma iyalinsa a karo na biyu ba tare da yayi wanka ba to yayi alwala. Damshin ruwan alwalarsa da kuma yadda ya goga mata gashin fuskarsa saman tata fuskar kadai ya sanya tsigar jikinta tashi. Sai ta gangame jikinta guri daya,hakan ya bashi damar daukarta cak ya maidata cikin duvet din. Lokacin data fahimci abinda yake shirin sakeyi sai taji kamar an aza mata duka tashin hankalin duniya saman kanta,a yadda akasha gwagwarmaya dazun, tayi imanin idan ya maimaita babu mamaki tafiya ta gagareta,don haka kai tsaye ta saki kukanta a wannan karon ta kuma aje duk wani zafin kai da kafiya tata ta fara rogonsa. Da kyau ya rigeta yana sauke sheshsheqa ya rungumeta cikin jikinsa sosai yana laluben kunnenta da bakinsa "Please help me, daya kawai..... Daya zan qara,it has been too long rabona da nayi,ban gama satisfying ba,i want to kiss you all over your skin is so soft and smooth, bazan boye miki ba,you are so hot, l've never felt this good before, kada kice a'ah,zan iya jure komai amma banda wannan" yayi maganar sanda hankalinsa ke nisa da gangar jikinsa. Bai sake bata damar cewa komai ba ya hade bakinsu guri guda yana bin dukka hanyar da vasan zai sake sukurkuta nata tunanin. Tana jinsa wannan karon ma yana sake maimaita addu'ar da vayi daxu wadda ke da matuqar muhimmanci ga ma'aurata "Bismillahi,Allahumma jannib nash shaidan,wa jannibash shaidana ma razagtana" ta lumshe ido tana jinsa, zuciyarta na wani irin narkewa. Wannan karon wasu irin hawaye sirara ne suka dinga zirarowa daga idanunsa,yayi mata wani mugun riqo yana jin kamar ya bude cikinsa ya maidata ya boyeta a can ciki gaba daya bakinta ya gama mutuwa murus,ita kanta tasan a ranar gaba daya ta gama moruwa. Shima kansa wanna karon bakin nasa ya mutu murus, sai tafi hannunta da ya sanya saman fuskarsa yana digar da hawayen dake sauka a hankali, idanunta a lumshe,amma tana iya jin saukar sassanyan hawayen cikin tafin hannunta. Kamar yana zuba mata wani abu dake da tasiri ga gangar jikinta haka takeji,don haka ta janye hannun nata tana boyeshi cikin jikinta. Tashi yayi ya zauna ya dagata cak ya azata saman jikinsa yana qoqarin kallon fuskarta amma sai ta juyar da kan nata ta wani sashe ta hanashi hakan "'SAHR" Ya kira sunan nata a karon farko kaf fadin rayuwarsa a iya sanin da yayi mata,ya furta sunan nata da wani irin qwarewa tare da cire wasu haruffa a ciki wadanda suka garawa sunan dadi da kuma sauya masa ma'ana gaba daya. Ita kanta har tsakiyar kanta taji sunan, sautin ya fita tar da wani irin taushi da amo me sanyi da ratsa zuciya. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI * Book 02 Page 32 Da gaske ba zata kalleshi ba,duk iya yadda yake tunanin zai shawo kanta taqi kallonsa,a dole ya ajjiyeta ya miqe don zuwa toilet,ya wuce bandakin yana waiwayenta kafin ya dauke kai ya shige bakinsa dauke da addu'ar shiga bandakin. Koda ya gama wankan ya jima yana kwararawa kansa ruwa,zuciya qwaqwalwa da qirjinsa sunyi wani fresh,dukka wani nauyi rudani da kuma dabaibayewar tunani kamar an sanya almakashi an daddatsesu. Koda ya fito still idanunsa suna kanta,ta cure jikinta sosai cikin duvet din kamar bata bugatar shaqar iskar dakin,qarasawa yayi gareta a tausashe ya danja duvet din,da sauri ta kamashi ta cukuikuye da kyau jikinta har kyarma yakeyi "Ba abinda zan sakeyi miki,gate up na taimaka miki kiyi wanka" tabbas da zata iya da harara zata dago ta galla masa,amma kuma tasan ba zata iya hakan ba,don babu abinda ya jawo mata shan wannan baqar izayar sai bakinta da idanun nata data kasa kiyayarsa kamar yadda yace "Kiyi haquri ki taso na taimaka miki,ba zaki iya tashi ba" "Bazan iya tashi ba sabida kasan ka baje kolin muguntarka a kaina ko?" Ta fada yau din muryar tsiwar ta koma muryar shagwaba qwarai da gaske. Siririn murmushi ya kufce masa yana tuna abinda ya tarar tattare da ita "Kaina bisa wuyana,i apologize fa,zan kuma ci gaba da apologizing din koda yawun bakina zai qare" kafin tace komai sukaii sautin bugu sosai,knocking akeyi da qarfi qarfi,kafin daga bisani muryar hajiya qarama ta wanzu a gurin "Toufeeq, toufeeq" karon farko da yaji wani abu a kanta,wato duk wata kima tata da girmamawa da yakeji a duk sanda ta kirashi a yanzun sai yakejin babu ko daya "Toufeeq ka bude, ko jikin ne?" Ta sake fada tana qaguwa da tsaiwarta a gurin saboda hankalinta a mugun tashe yake,kukan da meenal keyi mata da alwashin da takeci tana jin tsoron faruwar wani abun "Am feeling better,na sha magani" "Ban yarda ba, ina falo inason magana da ku" "Okay" ya amsa mata a gajarce. Idanunsa ya maida ga sãahar "Gate up please" ya fadi a tausashe yana bata hannunsa,sam bata buqatar wani taimakonsa,don haka ta ture duvet din da wani dan guntun qarfinta tana miqewa. Saidai tuni ta maida fuskarta ta kife tsakiyar pillow jikinta na rawa "What's happened?" Ya tambayeta a tsorace yana takowa kusa da gadon "Stay away please,cover your body" sai a sannan ya tuna cewa qaramin pant ne a jikinsa wanda iya gaba da bayansa kawai ya rufe masa, murmushi ya saki wanda yayi masifar yiwa cute face dinsa kyau, murmushin da ya jima bai sauka akan fuskarsa ba akan wata diya mace,bai musa ba yaja qaramin towel ya daura a qugunsa "Okay,zaki iya tashi yanzu" ya sake fada yana sake miqa mata hannun. Koda ta tashi din gocewa hannun nasa tayi,ta dauke kai kamar bataga taimakon da yakeson bata din ba,ta soma sauka a hankali daga saman lallausan gadon da ya kafawa rayuwarta tarihin da bata tunanin wanzuwarsa ba tsakaninta da MT JARMA din ba. Sai data huta a bakin gadon sannan ta soma takawa zuwa bandakin. Bai fasa ba ya bita da kallo yadda take takawa cikin sanyi da nutsuwa har ta shige ta tura qofar. Duk da yana cikin wani razani da fargaba amma murmushi bai kasa boyuwa daga kan fuskarsa ba, hannuwansa ya sanya duka biyun ya kama gashin kansa da kyau ya riqe yana murmushin, kafin daga bisani kuma ya saki kan nasa,ya koma bakin gado ya zauna yana daukar wayarsa tare da laluben number dr raheema,don a yadda yaga tana takawa yasan tabbas zata bugaci wani taimako. Tana cikin ruwan zafin amma hawaye takeyi,tabbas jarma ya mamayeta,ko daya batasan wannan qaddarar zata tarar ba a dakin, da ba ciwo ba,ko suma yayi babu abinda zai shigo da ita. Cikin zuciyarta takejin wani qunci da takura,wannan rayuwar bata shiryawa yinta ba kwata kwata,amma tabbas daga wannan ya gama,ba zata iya ci gaba da zama da shi ba,tunda har yaci amanarta ya karya alqawari da yarjejeniyarsu. Cikin wata irin nutsuwa ya shirya kansa a cikin wasu pajamas masu dogon wando da dogon hannu,gefe guda a ransa yana juya al'amarin hajiya qarama,zuciyarsa ta riga da tayi rawa cikin al' amarinta,yana kuma bugatar nutsar da hankalinsa da zurafafa bincike cikin sirri da takatsantsan, muddin tana da hannu akan ciwon fadeela da gin yankewar al'amarinta baya tunanin zai iya yafe mata. Sai daya waiwaya ya sake kallan dakin kafin ya fita,har lokacin bata fito a bandakin ba,ya ja qofar ya rufe yana fatan tayi zamanta kada tace zata gudu a dakin. Cikin wata sassanyar nutsuwa dake saukar masa yake takawa,har ya isa falon. A tsaye ya zamu hajiya qarama,meenal na zaune saman sofa da idanunta da suka canza launi. Kallo daya tayi masa taji wani mahaukacin kishinsa kamar zai hallakata,sai ta kasa dauke ido daga kansa,yayin da shi kuma ya tattara hankalinsa kan hajiya qarama idanunsa shima a kanta sanda yake zama saman kujera "Me ya sameka haka? yanzu baka da lafiya sai ka zauna a daki baka shaidawa kowa ba?,banason wannan sakacin naka toufeeq" idonsa yadan lumshe yana samun daidaito cikin nutsuwarsa bayan ya kira sunan Allah "Da sauqi alhamdulillah" "Mun godewa Allah" ta sake fada cikin nuna kulawa "Ina ita nanny din?" Ta tambayeshi tana dubansa. Kansa ya sake dagawa ya aje mata wani kallo,sai tadanyi relax kadan cikin mamakin yanayin kallon nasa "Wa fa?" "Nannyn fadeela,säahar" "Bata jin dadi,but she's my wife, not a nanny please" ya fada da wani irin sanyi, sanyin da ya kunna wuta a zukatansu ita da meenal, qarin mamaki kuma ya zauna sosai a zuciyar hajiyan. Lallai da hausawa ke fadin BABA MA DA BABANSA sai yau ta sake gasgata hakan,waye haka ya tsayawa yarinyar?, ko da yake bai kamata tayi mamaki ba,domin qila tarihi ne yakeson maimaita kansa,yadda mahaifiyarta ta hana mata samun mahaifinta wato dr mamman girema,haka takeso ta hanawa meenal samun toufeeq,sanann ta zame dukka wani martaba izza tata da fada aji da take da ita,wanda sam ba zata taba bari hakan ya faru ba koda zata rasa komai nata,toufeeq shine Target dinta,shine plan dinta na shekara da shekaru. "Oh,yayi.....saboda ita kenan ka kori 'yaruwarka data damu da lafiyarka? ta kasa sukuni da haqurin jiranka ka fito tayi tattaki ta sameka har inda kake?" Hannunsa yayi folding a qirjinsa,yayi wani relaxing, kai tsaye idanunsa cikin na hajiyan "Hajiya,ya kamata ki nusasheta bambamci tsakanin jiya da yau,ya kamata ta fahimci ma'anar alfarma ta dan adam da yadda ake keta ta haramunne a shari' ance,ya dace ta dinga banbance hagunta da damanta,sannan ya cancanci tasan yadda ake iya kama zuciyar namiji da wasu nagarta da kyan zuciya nutsuwa hankali da sanin ya kamata" ya furta yana dunqule hannunsa guri daya da kyau. Saroro hajiyan tayi cike da tsantsar mamaki,yau tana ganin wasu baqin halaye da dabi'u daga toufeeq din. Kamin kowa a cikinsu ya sake cewa wani abu takunta cikin taushi da qamshinta ya mamaye gurin. Sahar ce sanye da wata baqar doguwar riga me sulbi wadda keda wani irin ado da wasu zararruka masu daukan hankali, fuskarta tayi fayau,ta sake wani irin kyau da fresh,sannan kuma ta ciko lokaci daya, sassanyan kyan nan nata kamar an sake qara mata shi,fatarta da idanunta sun qara wani haske da girma. A hankali take takawa kamar wadda ke tausayin gasa. Kai tsaye ya bita da kallo yana fahimtar tafiyarta ta canza sosai, kuma yasan hakan baya rasa nasaba da abinda ya faru a tsakaninsu. Idanunsa ya lumshe tsigar jikinsa na zubawa lokacin daya tuna abinda ya farun mintunan da suka shude,yana ji a ransa inama lokacin ya sake dawowa,yayita kuma tabbata a haka ba tare sa ya wuce ba. Ido suka hada dashi,wani qasaitaccen murmushi da yayi matuqar qara masa kyau kwarjini da cikar kamala ya sakar mata yana lullumshe mata idanunsa. Sai take ga kamar dariyar mugunta yake mata,wannan yasa ta langabar da kanta gefe tana jifansa da harara, abinda ya zama kamar wani wasan soyayya ko cusa haushi a zuciyar hajiya da kuma haseena. "Ina zuwa madam?" Ya fada cikin matuqar girmamawa,kanta tadan juya kadan,ta cije tana qoqarin tauna maganar da zata gaya masa,saboda cikin jikinta takejin akwai idanu a kanta "Zanje duba fadeela" "Uhmmmmm" taji muryar hajiya qarama na fadi, idanunta kuma a kanta. Kai tsaye ya miqa mata hannunsa,ta gane me yake da bugata,kuma a lokacin taji ba zata iya wofantar da abinda yayin ba,duk da zuciyarta cike take da haushinsa, amma wani abun kana yinsa ne ko ka barshi saboda wasu idanu masu guda da illa. Cike da mamaki yaga ta garaso a hankali ta dora zara zaran yatsunta cikin nasa,wani irin abu me dadi ya saukahar tsakiyar zuciyarsa,ya maida hannun ya rufe ruf ya kuma jawota a tausashe ya zaunar da ita a kusa dashi cinyoyinsu suna gogar na juna "Ba yanzu ba,bakijin dadi,Dr raheema na hanya" ya fada yana sake game hannuwansu guri guda. Cikin nacin kallo da son tantancewa hajiy qarama ke garewa säahar kallo, gabanta na wani irin faduwa,tana hango canji muraran daga fuskarta,lokaci daya ta qara wani haske da sheqi "Innalillahi,na shigesu" ta furta lokacin da zucivarta ta ayasa mata "Kodai ciki ne?" "'Ina fatan haka" taji muryar toufeeq yana sake matse hannunsa cikin nata. Sai a lokacin ta fahimci a fili tayi maganar kuma a bayyane. Cikin sauri da son gyara takunta ta saki murmushi "Ameen Allah,lallai da duk duniya na kasance mutum ta farko wadda zatafi kowa farinciki,fatana ko yaushe ahalina su qara yawa,don haka nake qoqarin ganin samun dai daito tsakaninka da 'yar uwarka" yadda hannuwansu ke cikin na juna yaci gaba da taba zuciyar meenal din,bata da zarrar cewa toufeeq din komai,saboda ayau din kwarjinin dake kan fuskarsa kamar ya zarta na kullum,sai gani sukayi kawai ta miqe ta fice da sassarfa tana toshe bakinta saboda sabon kukan da yake shirin qwace mata. Hadiye wani abu me tauri hajiya qaraman tayi cikin murmushin yaqe "Allah ya raba lafiya" banbarakwai sahar taji, mamaki ya sake kamata lokacin da taji yana amsawa da ameen, sai ta faki idanun hajiyan ta zame hannunta daga nashi, saboda yadda yake yamutsa hannun nasa cikin nata tamkar yana amfani da damarsa ne. Zaman bai dauki lokaci ba Dr raheema ta qaraso,cikin girmamawa ta gaida hajiya qarama,ta amsa mata cikin izzar nan tata amma faran faran "Ki dubamin ita da kyau don Allah" tace da Dr raheema. Murmushi ta saki kawai "To hajiya,in sha Allah" ta fadi tana maida hankalinta a kansu "Ku qarasa ciki,ko da clinic zakuyi amfani?" Kai Dr raheema ta girgiza "Inajin basai munje ba, indai ba worsening matsalar tayi ba". Tana zaune daga gefan gadon ta rasa ta yadda zata yiwa Dr raheema bayani,wannan wanne irin abun kunya ne shikam,yana neman bata kunya da tona mata asiri. Sai kace wata virgin zai dauko mata likita?. Dai dai lokacin ya buda qofar dakin ya shigo yana sauke boyayyar ajiyar zuciya sanda idanunsa suka sauka a kanta,tsaida shi hajiya qarama tayi tana masa kukan tare da fadin yan wulagantata,ya canza totally mace na son rabasu,shi kam bai iya wannan jidalin ba, bugu da qari a yanzu ma shi bashi da wani guarantee a kanta,tana cikin suspect, bazai kuma taba nutsuwa ba har sai ya samu yaqini da tabbacin komai "Sir batace komai ba" Dr raheema mai yawan fara'a haquri da sanin ya kamata ta fada. Hannuns a qirjinsa ya tako ciki "First night ko first day dinta zance,shi tayi a dazun, so kamar yanayin tafiyarta nake gain ya canza,and jikinta akwai dumi sosai tun dazun, duk da taqi yarda da hakan" ya furta dukka bayanan idanunsa a kanta,yanajin kamar ya hadiyeta. Idanunta fal da qwalla ta dubeshi, tanason sake harararsa ne ko zata zamu relief din abinda yayi mata "Nifa bazawara ce Drya za'a ce saboda na samu wani ciwo dalilin hakan?" Ta fada cikin dan zafin rai. Idonsa ya lumshe murmushin nan nasa dan kadan me taushi na subuce masa,can qasan ransa kuma yana jin babu dadi,don da alama kalmar BAZAWARA din ta tsaye mata a rai. Cikin kulawa Dr raheema ta ajjiye kayan aikinta,ta dawo dab da ita ta zauna tana game hannunta cikin nata "Ba abun mamaki bane yadda kowacce mace ta banbanta haka suma mazan suke da da banbanci kin gane?" Tayi mata bayanin a taqaice,jin tayi shuru sai ta dora "Yadda muka banbanta a halittar jikinmu hama suma mazan suka banbanta,kowacce mace akwai yanayin halittar ta,jikin wata jikinta yafi na wata tsukewa,kamar yadda suma mazan halittarsu ta wani tafi ta wani,zai iya yiwuwa a auren mace na biyu ta fuskanci jin ciwuka da sauransu, saboda qila ta qara samun tightness,sannan shi kansa mijin nata data sake aura wala'alla yafi na farkon cikakken. "Don Allah Dr" ta fada da sauri tana rufe idanunta. Wannan karon sai da dariya ta qwacewa Dr raheema "Kin fahimta kenan ba sai na garasa ba?" Kai ta gyada mata sau biyu da saurinta. Shima murmushi yayi mai sauti wannan karon, wanda ya tsaye ma säahar,taji kamar da biyu yayishi,sai ya juya yana nufar qofa don ya basu guri. A nutse ta sake mata bayani yadda zata fahimta,hakan ya sanyata tunani me yawa "What a difference?" Ta samu kanta kanta da fadin hakan,sai kuma taji haushin kanta ya kamata "Difference din ganiya" ta sake fadi tara fada ita da zuciyarta har tana tsuke garamin bakinta. "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_ Book 02 Page 33 Dr raheema na fita ta maida key jikin qofarta,ta koma ta kwanta saman gadonta tana sauke numfashi, idanunta a lumshe bacci ne fal cikinsu. kuma shi take da bugatar vi saboda a jiyan tashin ciwon fadeela bai bari ta samu isashen bacci ba yau din kuma ta tashi da wuri da zummae zasu fita aiki,wannan gaddarar ta fada mata. Wasu hawave suka sake zarto mata idanunta a lumshe tana bitar abinda ya faru tsakaninta da shi,tun daga sanda ya sanyata cikin jikinsa har zuwa lokacin data wuce bandaki. Kadan kadan taji ana taba gofar, sau biyu aka murda,sai kuma taji an juya an bar gurin ba tare da anyi knocking ba. Wayarta dake saman kanta ta jawo tavi kiran nadeeya "Fadeela ta tashi ne?" "Eh ta tashi, abbynta ya shigo yanzu suna tare, ashema bakuje office din ba" kai ta gyada "Eh" "Amma lafiya?, anty N naji muryarki wani iri?" "Ba komai kawai inajin kasala ne,please ki kula da fadeela, kada ki bari ta fita gaba daya daga sashen,sannan kada kowa ya bata komai sai abinda kika girka da hannunki, shima kaemi motsa daga kitchen din har sai kin gama,idan ta rage kuma a zubar, kada a ajjiye" Nadeeya ta danyi mamaki, amma kuma tasan sahar din kulawarta ga fadeela ta musamman ce, don haka ta amsa mata da "To,in sha Allah, sannu Allah ya bada lafiya,ki huta sosai don nasan akwai rashin samun cikakken bacci ma jiva,gwara ma da yaa toufeeq ya hana zuwa aikin yau,kya samu ki huta" "To nadeeya‚na gode,ki cewa fadde na i missed her " murmushi nadeeya ta saki, sai itama fadeelan dake kan cinyar toufeeq ta saki murmushin, don duk a kunnensu tayi maganar. Maganganunta suka sake sakashi zurfin tunani vana da bugatar zauna ya tattauna da ita, amma ya sani a yanzun kamar ya bar mata wani ciwo ne a zuciyarta,ya tabbatar a quilace take dashi, ba lallai bane ta tsaya ta saurareshi. Special care da take bawa fadeelan wani abu ne da bau taba ganin kwatankwacinsa ba,bata da lafiya amma dukka hankalinta da tunaninta yana kanta. Maida idanunta tayi ta rufe itama ba tare data motsa din ba, tana jin yadda qasusuwanta suke ciwo,cinyoyinta kamar wadda tayi wasan tsere na kwana guda,ko yaya ta motsasu sai tail wannan ciwon,hakanan ta cikin qashinta takeiin zazzabi yana mamaye ilahirin jikin nata,sannu sannu wani gantalallen bacci ya dauketa. Cikin baccinta ta dinga jin kamar muryar fadeela na gwala mata kira. A hankali ta bude idanunta ta miqe ta zauna saman gadon tana sake jin sautin muryarta daga bakin gofa tana hadawa da knocking. A hankali cikin lallaba jikinta da ya qara tsami ta sauko a gadon, ta isa bakin gofar ta bude. Fadeela dince, toufeeq yana tsaye daga bayanta,guri daya idanunsu suka hadu,ita ra fara janye nata idon ta taka a hankali cikin takatsantsan tana komawa cikin dakin gami da laluben dankwalinta da ya zame, sassalkan gashinta me santsi wanda ko ribbon bata samu damar saka masa ba tunda tavi wanka ta barshi a haka don ko Draver bata samu ta saka ta busar da shi ba ya tarwatse iskar dake dan kadawa cikin dakin na mata wasa dashi daga hannun hagunta zuwa dama. Idanunsa a kanta har ta zura garamin hijabi wa jikinta yayi qarfin halin dauke idanun nasa ya biyo bayan fadeela. "Anty N,tun dazun nake nemanki sister nadeeya ta hanani shigowa,wai baki da lafiya?" Ta fadi cikin kulawa. Dan qaramin murmushin da bata shiryawa saki ba shi ta saka, ta saka hannu ta shafi gefen fuskar yarinyar,she was so caring "am getting better fadee na,so karki damu" Idanunsa a kansu har ya qaraso ya zauna saman sofa bed ta yadda zai iya fuskantarsu. Ledar hannunsa ya ajiye ya fidda magungunan ciki sannan ya dubi fadeela "Jeki kawomin cup be careful" "No ta barshi" sahar ta fadi zata miqe, hannu yasa ya maidata, suka hada ido ta kauda kai,sai ya miqe "'Karki rufe qofar before na dawo please" ya fadi da sigar lallashi. Bata ce masa komai ba sai sake kau da kanta tayi,ya gaji da saurarenta ya juya yana fita a dakin. Lokacin da ya dawo fadeela na zaune d'are d'are saman cinyarta tana mata surutu, idanu yadan fidda sannan yasa hannu a nutse ya sauketa daga kan cinyar tata "Noo my angel,anty N bata da lafiya,kinyi mata nauyi da yawa" "Ayyah,sorry anty" ta fada tana kallon säahar, kai ta girgiza mata tana shafa kan yarinyar,a yanzu duk wani tunani nata ya tattara kan yadda zata samawa yarinyar lafiya,yanzun shine abinda kadai ya rage mata tayi, tana jin daga wannan ta kammala zamanta cikin gidan. Tablet din farko va miga mata yana kafeta da idanunsan nan da suke gara mata wani nauyi,sai kuma haushinsa da takeji can qasan zuciyarta "Take it please" ya fada qasa gasa yana sake watsa masa idanun nasa, hannu tasa ta dauka a tsakiyar tattausan tafin hannunsa sannan ta karbi ruwan da ya zuba a cup. Daya bayan daya ya dinga bata tana sha har ta gama,ta ajjiye cup din sanda fadeela take kallonta "Ya akayi fadee?" "Am starving" ta fada qasa qasa daidai sanda yake kwashe magungunan ya dora sanan dressing table, dawowa yayi gabanta ya kama hannuwanta ya rige cikin lallashi "Fadeela" yayi kiranta "Yau ba girki, oya ki yiwa zuwaira ko nadeeya magana,su baki wani abun kici,she's sick kin gani ai ko?" Kai ta jinjina, sai ya fiddo wayarsa yayi kiran nadeeya. Mintuna kadan ta shigo, suna hada ido da sãahar din taji wani nauyi ya saukar mata,gani takeyi kamar ma kowa zai gane abinda ya faru, kamar an rubuta abunne a gaban goshinta haka takeji a jikinta "Sannu anty N" kai kawai ta gyada mata tana lumshe ido nadeeyan bata zafafa ta garaso kusa dashi. Bata ji abinda yace da ita ba,yau an magana dasa gasanne suka motsa, ita dai taji ta kama fadeela sun fita a dakin. Ta cikin rufaffun idanunta taga hasken dakin ya ragu,a hankali taji an maida qofar an rufe, ta tsammaci tare suka fita saita gyara kwanciyarta cikin duvet. Saidai ko minti daya ba'a rufa ba sassanyan qamshinsa ya mamayeta,kafin ta gara tuna komai ta jishi a cikin duvet din. Wani wawan juyi tayi da nufin tashi, tashin bai samu ba,sai ma kyakkyawan masauki da yayi mata cikin jikinsa, lallausar fatarsa me wani irin gamshi da dumi ta manne a nata jikin,hucin numfashinsa da ya sauka daga wuyanta zuwa gefen kunnenta ya sanya ta jin wani irin abu na mata yawo cikin jikinta "Karki wahalar da kanki, don ba zaki iya qwacewa ba, dukkanmu bacci mukeji ni da ke, so mu rage baccin koda na one hour ne you will feel better idan muka tashi, and baccinki it will be more comfortable idan tare mukayi,karki wani yunqurin yin komai, just relax please"ya garasa fadin please din yana cooling voice dinsa sosai cikin yanayi na salon shagwaba. Ido kawai ta rufe tana jin yadda bugun zuciyoyinsu ke sauri ita dashi,hawaye ya cika idanunta tana jin zafi cikin ranta. Ya yaudareta,ya karya alqawarin dake tsakaninsu,yayi abinda ransa yakeso, dama jikinta ne yake bashi sha'awa?,hakan kuma bai isheshi ba yanzu ya dawo ya tilasta mata yin bacci dashi. Ta tabbatar yadda ya fada ne, no way da zata iya qwatar kanta, amma kuma bakinta tana ganin zai iya qwatarta "Bamuyi aure da kai don mu dinga wannan abun ba, ka karya yarjejeniya kaci amana" garamin murmushi ya subuce masa,a yanzun son tsiwar nan tata yakeyi,ya fuskanci da tayi masa shuru gwara tayi masa tsiwar,yana enjoying sosai,sai yasa hannunsa ya birkitota,ya sanya tafin hannunsa ya tallafe kansa bayan ya dogare gwiwar hannunsa saman gadon, qwayar idanunsa ya narka cikin tata yana mata wani mayataccen kallo "You are saying na karya alqawari, naci amana,i break the rules,dama munyi alqawari da ke? yaushe mukayi yarjejeniya?, uhmmm madam suna ina? ‚nunamin su" Baki ta saki tana kallonsa tsakanin idanunsa guda biyu,wata qwallar ta sake cika mata idanu. Sai yanzu ta tuna basuyi a rubuce ba,yace baya bugata ta rige kayanta to rami yayi mata a sannan?, ko dama ya shirya faruwar hakanne? yanzu bata da wata huija kenan koda bavan ta gama aikinta akan fadeela ta nemi takardar sakinta?. "Kinzo kulawa da fadeela amma baki yarda ki kula da daddynta ba ko dan gangani?" Ya fada yana langabe mata kai, wanda shi kansa baisan lokacin da hakan take faruwa ba. Ta karanci abubuwa na neman saba saiti, gaba daya kamar ba da MT JARMA take magana bama, sai taji kanta bazai iya dauka ba "I need space please ka sakeni ka fitarmin daga daki" wata wawiyar rungumar yayi mata yana saka kanshi tsakanin boobs dinta da har yanzu yakeji basu isheshi ba "Ki huta hakanan please magani kika sha" yadda yaketa morewa albarkatun girjinta yana masifar gona mata rai,cikin rawar muryar dake nuna kowanne lokaci kuka zai iya qwace mata tace "baka da bugatar bazawara in all ways,so me zakayi da ilkin da ba'a san darajarsa ba?" Bai gara barinta tace komai ba sai tsintar bakinta tayi cikin nasa ya hade bakunansu gam,ya hanata sake cewa komai, sai wani zazzafan mouth to mouth kiss da yake sauke mata wanda cikin mintuna yaso sake birkitashi, da qyar ya zare bakinsa yana jin dumin hawayenta suna taba fuskarsa "Idan kinason zaman lafiya kiyi baccinki kawai" ya fada yana aza mata nauyin girjinsa idanunta kawai taja ta rufe gam, bata sake cewa komai ba, saidai tuni ta yanke hukuncin abinda zata aikata. Ba jimawa bacci yazo yayi gaba da ita, ya gyara mata kwanciya cikin jikinsa yakai lips dinsa yayi kissing goshinta,kamar zai cinyeta da idanunsa wani irin murmushi na fita akan fuskarsa "Rigimammiya ta" ya fada softly yana jin zuciyarsa kamar wadda aka canzawa muhalli. Afwan,yau na baku shi a rarrabe kuma page d'ai d'ai,ayimin uzuri na wuni a asibiti ne. Amma gobe komai zai zama normal in sha Allah, Na gode da kasancewa tare dani. *HUGUMA* _TABARMAR KASHI* Book 02 Page 34 Yamamci lis ta farka, ta samu baya dakin,sai abinci data tarar, toilet ta shiga tayi alwala ta dawo tayi sallar la'asar, kamar ba zata taba abincin ba amma wata irin azababbiyar yunwa takeji, rabonta da abinci tun toasted bread da taci da milk tea. Tana bude abincin tasan nadeeya cs ta girka,ta diba kadan taci ta maida ta rufe. Taji dadin jikinta sosai, hakanan taji ta gaji da zaman dakin, tana zura slippers dinta aka turo gofar. Toufeea jarma ne,cikin sassanyan yanayinsa,yana sanye da shirt da trouser dukkansu baqaqe,shigar data sake gara masa kwarjini qwarai, ta kuma fidda ainihin zallar kyansa,idanunsan nan masu kaifi a yau sun koma masu laushi, saidai cike suke da tasirin was abubuwa masu tarin yawa. Qarasa shigowa yayi cikin dakin qamshinsa yana mamaye ko ina,ta dauke kanta tana jin haushin yadda tabar qofar a bude har yaketa samun damar shigo mata kai tsaye. Hannunsa goye a qirjinsa ya garasa ya jingina da dressing table,da lallausar muryarsa din nan yace "How are you feeling?" Ta qasan idanunta ta gasa masa harara. kamar ba zata amsa masa ba sai kuma tayi magana ciki ciki kamar wadda aka viwa dole "'Da sauqi" "Ma sha Allah Alhamdulillah" ya furta a nutse "Su sajjad suna parlor suna jira" ya fada yana dubanta still, don tunda ya shigo ko sau daya bai dauke idanunsa daga kanta ba. Da sauri ta daga kai suka hada ido,sai kuma ta basar, tana jin zumudin ganin afifa har cikin ranta, ta garasa sanya slippers dinta ta mige tana takawa. Har ta gotashi taji an riqe hannunta a tausashe, da dan mamaki a fuskarta ta juyo suka hada ido ta watsar da kallon nata gefe "Tsayani mana" y fadi yana sakar mata hannun. Dole ta dakata har ya cimmata suka jera,tare suka ratsa hallway din har suka isa falon. Idanun afifa akanta, murnarta itama ya gaza boyuwa. Rungume juna sukayi suka zube saman kujera tana gaida sajjad Lokacin da yake ce maya ya jiki? Allah ya sawwaqe sai da taji kamar gasa ta tsage ta shige, tadan saci kallon toufeeq shima ita yake kalla. Ya fahimci kallon da take masa,sai ya tabe baki ya kuma watsa hannayensa alamun ba ruwansa baisan komai ba,a kunyace ta ja afifa suka shiga kitchen tana nemana abinda zata basu. Karon farko data fara baqi kenan, afifa da ta lura tana ta wani bove dariya ita ta tayata suka shirya komai cikin tray, tana shirin dauka toufeeq din ya shigo. Har saman fuskarsa taga yaji dadi, yasa hannuwansa ya tallafe nata hannayen dake dauke da farantin yana mata wani irin kallo "Jeki huta, thank you" banda tana gudun jiwa kanta ciwo da tuni ta zare hannunta daga qasan tray din, amma dole ta jira ya karba sannan ta zame nata hannuwan a hankali. Koda ya fita ta laluba kitchen din ba afifa ba dalilinta, ta tako ta fito sai ta cimmata tsaye a tsakanin hallway dinsu "Ke nake nema ai" "Tuni na yiwa kaina qiyamullaili na fito..... Kai azaba,irin wanna kallo haka kamar babu gobe?, bestie kamar zaku cinye junanku?, kuyi haquri ku ragewa 'ya'yanku fuskar da zasu kalla taku mana karku cinye kanku tun yanzu su su rasa abin kalla... " Batasan ta dimawa afifa dundu ba sai data gantsare tana fadin "Wayyo hayatee,zata wujijiga maka baby" surrender sãahar tayi daga bakin qofar dakin tana riqe da handle tana duban afifa dafe da bakinta "Bestie,ke yanzu har kina zancan daukar ciki?" Harara ta watsa mata "Yo me za'a jira?, daga ni har mijina dukkanmu jarumai ne kuma munason junanmu, ribar auren soyayya kuwa ai haihuwa,ki zauna ke kam,nan da wata takwas zaki rakani labour room in sha Allah" dariya ta kubcewa sahar,abinda ta jima batayi ba, ta maida gofar ta garaso dakin tana neman gurin zama kusa da afifa "Sannu da qogari bestie na yarda har yanzu da sauranki a hankali" "Allah am serious, kedai ba kin zauna ba?, da alama ma sai yau aka bare gyadar" ido sahar ta fidda tana dubanta sosai "Inji wanne munafukin?" "Ba wani munafuki, ina ta kiran wayarki ne naji baki dauka ba,da na nemi nadeeya tacemin yau tun safe baki da lafiya, kina can kina bacci ke da oga,yanzun suka fito ita da fadeela, nasan halin bestie na da taurin kai da tsanar maza,nasan ba abinda zai kaiki bacci tare da MT JARMA haka siddan,saidai idan ya miki qarfa qarfa ne,idan kuwa hakane to ya burgeni wallahi, Allah yasa yayi miki ciki ma yau din ko jiyan, bansan actual ranar ba" ta fada tana ayaqyata dariya abinta, sai kuma ta sassauto ganin fuskar säahar din ba walwala, kamar ma hawaye ne cikin idonta. Kama hannun nata tayi "Me kuma ya faru bestie?" "Amanata vaci bestie,ni bance masa ina da bugatar auratayya ba,yasan auren meye mukayi amma sai ya yaudareni yaci amanata?" Saura kadan dariya ta sake qwacewa afifa,amma ta tabbatar idan tayi dariya gayyar zata watse ne "Hana bestie, kamar bakiyi karatun addini ba?,haduwata da hayatee yasa na sake sanin waye taoufeeq sarai, may be ma fiye da ke tunda ke baki maida kanki ba,na miki imani da Allah jinki yayi kawai da kunne, amma dai baiyi niyyar aikata miki komai ba, kawai an samu akasi ne,wanda dama ba yadda za'a yi kina halalinsa ya zauna yana kallonki, saboda me?,bayan Allah ya bashi damar yayi komai ba komai?" Hannunta ta qwace daga na afifa, saboda ta karanci ba wani goyon baya zata bata ba,zata zartar da abunta ba tare data nemi shawara daga wajenta ba "Kiyimin bayanin ciwon fadeela sosai,inason naji yadda yake fiye da bayanin da kika taba yimin, hankalina yana tashi, inason na kawo garshen ciwon a tare da ita,ina zargin matar nan zargi me qarfi,na tsaneta bestie haka kawai zuciyata ta wayi gari bata gaunarta sam sam" gyara zama afifa tayi "Gaskiya ba'a yimin tarba me kyau ba,masu juna biyu ai sai da abun kwadayi,abani abu na saka a bakina sai naji dadin yi miki bayanin" harararta tayi tana migewa "Zakiyi bayani ne da kyau,me bestie na takeso?" Idanunta ta juya "Me zan zaba ma?, kitchen din bestie din nawa kamar ba na matar aure ba,ba wasu ajiyayyun snacks ba komai,ko girki banga alama ba,ina dukka fikirarki ta girke girke?" "Zaman nazo ma kenan" ta bata amsa tana harararta sannan ta juya ta fice. Mintuna kadan ta dawo mata da abinda ya samu ta ajiye mata bayan ta gama ta tattara hanakalinta ta fara yiwa säahar din bayani "EPILEPSY Ciwo ne na kwakwalwa da ke iva shafar kowacce halitta me rai hatta dabbobi ma suna yin ta Kin San ita kwakwalwa da nerves su ke controlling jikin gaba daya suna anfani da electric signals ne wajen aika sakonni a sassan jikin Dan Adam. Misali ko Abu ka kalla ko kaji sauti nerves din da ke cikin idanun ka da kunne su zasu sarrafa wnn abun da ka gani ko ka ji su Maida shi kwatankwacin electric current su aika ma kwakwalwa ita Kuma ta tantace maka kaza ne ka gani ko ka ji" "Haka zalika idan kwakwalwa na so misali ka daga hannun ka zata Yi relaying sakon ne ta hanyar aika electric signals ne ta nerves zuwa hannun sai ka daga shi kawai,wnn shi ake kira voluntary movement, xaka iya yin shi duk sadda kake so kana da control on kayi ko Kar Kar kayi Amma kamar bugun zuciya kyafta Ido, movements na kayan ciki wajen sarrafa abinci da sauran motsi da sassan Jimi ke Yi Wanda baka iya controlling shine involuntary movement dukan movements din nn akwai sassan kwakwalwa da ake da alhakin Yin su Guiyoyin kwakwalwa, NOTE akwai jijiyoyi kala kala a jikin mutum kamar na jini,na kwakwalwa,na ba jiki kariya daga cututtuka da sauran su suna da sunayen su na turanci, Amma dai bahaushe duka jijiya yake Kiran su). Abun da yake faruwa a epilepsy shine ita kwakwalwar kwatsam zata saki wadannan electric signals din ne lokaci daya sai ta Kuma kasa controlling dinsu shi yasa Zaki ga sun fadi kusan ko Ina na jikinsu Yana motsawa uncontrollably a Hakan was har fitsari ko bahaya Yana kufce masu Yadda electric signal din ke faruwa lokacin attack din is similar to kamar wutar lantarki na spark ne abun da yake faruwa kenan a cikin kwakwalwar Attack din Yana faruwa ne kusan kamar a stages 4 1) na farko ana Kiran shi aural stage wato kamar warning sign ne cewa anytime ka fara Jin wadannan alamun xaka iya samun attack Kuma kowa da yadda yake ji wasu zasu rika Jin cowon Kai,ko su rika gain was abubuwa,ko su rka Jin wava Kara ko harshen su ya rika Jin wani dandano ko jikin su ba dadi kowa dai da irin abun da yake ji sai mutum yayi preparing ya samu waje ya kwanta saboda gudun samun raunuka Sai stage na biyu shi ake kira Tonic clonic stage shine actual convulsions din Zaki ga mutum ya fadi Yana jujiga Yana zubar da miyau da fitsari da sauran su dai actual seizure din Stage na 3 shine post ictal stage kamar recovery k nn bayan seizure ya tsaya zasu zama confused suna ganin Jiri da cowon jiki snn bacci Mai nauyi zai dauke su. Stage na hudu Kuma na farawa ne bayan sun Farka daga wannan baccin was da yawa basu iya tuna ma sunyi Amma zasu tashi da cowon jiki da raunuka na faduwa ko ciccije Baki da harshe da sukayi lokacin sezure din har zuwa lokacin da zasu warware gaba daya. Epilepsy kala kala ne. Akwai Wanda muka sani Wanda mutum zai fadi yayi ta jijiga shi ake kira generalized epilepsy,akwai Wanda Kuma iya sashe daya na jikin shi ke jijigar Kila fuska ko hannun ko kafa,wani Kuma Zaki ga zuru zai Yi ya kura ma wuri daya Ido kamar yy hooking anywhere dai ya danganta da sashen kwakwalwar da ke da, matsala tunda ita kanta kwakwalwar akwai sashe sashe da ke controlling kowane fanni na jiki. Akwai aune aune da ake yi a gane sashen kwakwalwar da ke da matsala da Kuma abubuwa da suka haddasa seizure din Akwai hoton kwakwalwa kamar su CT scan,MRI, Akwai awon dake duba electric signal din(EEG). Ana Kuma auna jini a duba ko akwai infection kamar sankarau (meningitis) tetanus,rabies da sauran infection dai da ke iya taba kwakwalwa. Ana Kuma auna jini a San adadin wasu sinadaral kamar calcium,zine, phosphates,vitamin D,B da Kuma parathyroid hormone da karancinsu a jiki ko Kuma yswansu idan ya wuce misali yake haddasa seizure din, Akasin shekarun baya da ake tunanin seizure shafar aljanu ce ynz an gano cewa ciwo ne na kwakwalwa da zaa iya controlling din shi da magunguna ko surgery. Akwai kalolin maganin da ake sha ko ayi allura da dama da ake kira anticonvulsants da ake anfani da su Kuma da ake nasarar controlling din ciwon da su. Wadanda aka samu gano kamar tumor, ko scar ko fannin kwakwalwar da ke da matsala akanyi surgery a Yanke sashen da ke da matsalar ana Kuma dacewa musamman idan kwararru ne masu kayan aiki na zamani su kayi. Amma surgery na iya zuwa da complications misali bayan anyi ya kasance mutum Bai iya anfani da wani bangare na jikin shi ko ya samu paralysis gaba daya. Yawanci epilepsy na Yara Yana farawa ne dg zafin zazzabi Zaki ga da sun fara fever jikin su ya dau zafi sosai zasu fara convulsing da yawansu sukan warke daga lokacin da suka Kai 5-7yrs haka. Duk da akwai wasu dalilan sake haifar da ita, kamar mummunar faduwa ko buguwa a kai. Masu epilepsy na fama da tsangwama daga wajen mutane Wanda rashin sanin ainahin ciwon ke kawowa. Akwai side effects na magunguna da suke affecting learning da behavioral abilities na musamman yaran, so wannan shine cikakken bayanin". "HUGUMA” *_TABARMAR KASHI Book 02 Page 35 Shuru sãahar tayi tana gyada kai, idanunta dauke da qwalla,tausayin masu ciwon yana ratsata "Surgery shine best hanya nake tunani da fadeela zata rabu da ciwonta,saboda kamar nata ciwon hakan ya nuna a yadda naji daga bakin nadeeya,hajiya qarama ta gara iza wutar ba za'a tabata ba,ba za'a yi mata aiki ba....yanzu kuwa lokaci yayi,ko tanaso ko bataso" sãahar ta fada with confidence. "Bestie,please nan da sati daya ki bincika min best asibiti a kowacce qasa yake da zasu iya yiwa fadeela aiki, zanji da komai,ko sajjad banaso ya sani sai an gama" kai afifa ta mirgina "Anya bestie?,bakya gudun faruwar komai?" Kai ta girgiza "'Na yarda da Allah, kuma nayi imanin bazai tozarta ni ba,kyakkyawar niyya sa tsarkin zuciya shine a gaba da komai" ta qarasa fada tana daukar wayarta, ta bude calendar na period dinta don ta duba kwana nawa ya rage, saboda ciwo da taji mararta tana mata kadan kadan. Qatoton circle ta gani tare da manyan rubutun OVULATION DAY,sai ta sauke wayar tana dan yatsina fuska "'Kina experiencing wani pain ne?" Kunyar afifa kadan tadan kamata,saita kau da kai tana girgizawa "Na sha magani" murmushi afifan tayi, qasan ranta tana jin dadi da hakan ta faru, tana kuma sake ganin kima da martabar toufeeg, don wanna abun da yayi a wajenta ya tabbatar mata yasan abinda yakeyi,kuma shi ba shashasha bane,hakanan ya tabbatar mata cikakken namili ne da tunaninsa ya saba da na diya mace. ********Kamar ko yaushe,qarfe takwas saura minti biyar ta kammala shirinta,har ta fiddo mayafi zata yafa ta tuna da hijaban da ya aiko nadeeya ta kawo mata guda goma sha biyar a jiya. Tun ranar da su afifa suka tafi tunda ta rakasu bata koma sashen nata ba,tayi zamanta a sassansu,kwanaki biyu yau kenan ko fuskarta bata sake bari ya gani ba,ko hijaban ma sai nadeeya taga ta shigo mata dasu "'Inji yaa moha, ki fara using nasu on Monday" tayi maganar tana hadiye dariya. Da kallo ta bita,nadeeya da afifa sun hade kai,sai suyita mata magana suna boye dariya,sun maidata kamar wata 'yar tsanar wasansu,amma taci alwashi itama duk ranar data kamasu ba zasuji da dadi ba. Qaramin tsaki ta ja, batasan meye nufinsa da yin hakan ba,zama tayi ta zazzagesu,ta kuma cire color din da zai shiga da atamfar jikinta,ta qarasa gaban madubi ta saka tana daure igiyar kai data hannun hijabin. Lokacin fadeela ta shigo wadda ta barta ne tana qarasa yin breakfast a dining. "Anty na gama" "That's good girl,oya let's go" ta fada tana goya school bag din fadeelan a bayanta kamar yadda suka saba. Tun daga nesa taga parking space din da yake cin motocin nasa wayam ba kowa, ba kamar yadda suka saba ba,a safiya irin wannan gurin zaka sameshi jere da motocinsa da kuma su jibril suna tsaye suna jiran garasowarsu. Yau din shi daya ta hanga,tsaye jikin BMW dinsa fara sol, wadda a wancan satin ta iso,sai daukan idanu takeyi tana tabbatarwa da me kallonta tsadar da take da ita. Yau din sassaugar shiga ce, amma yadda kayan suka karbeshi sun maidashi wani so hot,ya koma balarabe sosai amma mara yawaitar haske sosai, cikin taupe color button up shirt yake da slim fit trouser medium gray, gafarsa wani tsadadden sneakers ne da ya kwanta sosai a lafiyayyar qafarsa da take qal kamar baya taka qasa. Wayarsa na hannunsa yana dannawa,tamkar hajiya qarama dake tsaye gabansa tana fuskantarsa ita da haseena baya jin abinda ma suke fadi,yayin da haseenan dake rungume da hannayenta ta zuba mishi idanu,sirrin tasirin kyan dake fita tattare da kamilar fuskarsa me yawan kwarjini suna sanyata jin kamar ta rungumeshi a yanxu haka,tana jin kamar ta bude idanu ta ganta ta zama mallakinsa matarsa, kishinsa na sake hauhawa cikin zuciyarta, tana ji a ranta zata iya vin komai zata iya rasa komai muddin shima ta rasashi, ciki kuwa harda rai da rayuwarta. Kai säahar ke gogarin daukewa bayan idanunta sun gama qarewa kowa kallo a cikinsu,wani abu taji na neman tsaya mata a wuya,tsaiwar meenal tayi mugun yin kusa da toufeeq din, ta tabbatar da zaiyi wani wawan motsin tsaf zai iya taba jikinta, qoqarin gayawa kanta takeyi "Ba huruminki bane,meye naki?" Amma ga mamakinta zuciyar taqi karba,kai ta sake kawarwa tana fadin "Wataqila tana tuna cewa dukkansu musulmai ne masu amfani da yaren hausa, bai kamata kuma a samu hakan daga garesu ba" Kamar wanda aka yiwa wahayi da tahowarta,ya cira kansa a hankali idanunsa suka sauka a kanta "Ya salam,ya Allah" ya furta a fili qasa qasa. Idanu ya kafeta da shi yanason banbamce shigar mayafin data hijabin "Ba abinda ya buya" wata zuciyar ta gaya masa,wannan kyan yana nan a muhallinsa d gurbinsa,cikakkiyar halittar da a yanzu yasan ainihin cikarta da zatinta sai yake ganin tamkar kiwa na iya ganinta ta cikin hijabin nata,boobs din da yake qoqarin ganin sun buya sai idanunsa ke nuna masa su muraran,wani abu ne nauyi yaji ya sauka aqirjinsa ya sauke hannunsa yana yarfar dashi sannan ya ratsa ta tsakanin hajiya qaraman da meenal ya nufesu. A hanya sukayi kacibus, kowa idanunsa cikin na dan uwansa,fadeela ta wuce gaba abinta ta tafi gaida hajiya qarama,wadda a yanzu sai zata fita school suke haduwa,sabanin lokutan baya da duk safiya sai an kai mata ita kafin ta wuce makarantar. "Babu ta yadda za'a iya boyesu ne?" Yayi mata tambayar yana riqe qwayar idanunta cikin nasa,wanda taketa shirin gocewa hakan. Cikin rashin fahimta da dan hadewar fuska tace "Me?" Idanunsa ya sauke akan qirjinta, da sauri takai dubanta kai,sai tasa hannu tana daga hijabinta ta saitin gurin hadi da ja baya tana kuma sake hade rai "Ummmm?" Ya sake fada da sigar tambaya. "Bana so" ta fadi cikin jin haushi,taku biyu yayi gabanta yana qare hade tsakaninsu "Nine dai bana so, banason kowa ya kallesu Allah zan iya hadiye zuciyata, they're mine" A mamakance ta kalleshi tana zare ido, tanason tace wani abu ma ta kasa, bai kuma bata dama ba,sai ya sake matsawa gabanta,a hankali yasa hannunsa ya jawo hijabin saman habarta wai ko hakan zai rage mannuwarsa a jikinta yana sake kallon girjin nata "Damn it!" Ya fada gasa gasa,sai ya zura hannu ya karba lunch bag din fadeela,ya sake saka hannu ya zare school bag din nata sannan ya juya ya fara tafiya. Juyowarsa ta sanya hajiya qarama dauke kai daga kallonsu wani abu yana bugun zuciyarta was canje canje take gani a tsakaninsu wanda batasan meye silar afkuwar sa ba. Meenal kuwa kuka takeson saki hajiyan na mata nuni da kada ta sake tayu,haka ta dinga hadiyeshi tana ji kamar tana hadiyar zuciyarta,zuciyar tata kamar zata fashe. "Barka da safiya" sahar tace da hajiya qarama,sai da tayi namijin qoqarin dai daita kanta sannan ta jefa mata wani kallo "Barkanki dai,ya ayyuka?" Yadda ta kira ayyukan ya yiwa säahar kama da gatse, sai tayi kamar bata jita ba, tayi gaba dai dai lokacin da ya bude mata seat din gaba. Sai data kalleshi cikin mamaki ya dage mata dukka girarsa biyun,bata ce komai ba ta shige ya tattara mata hijabinta ya rufe mata motar. "If you are not ready to go ki koma ciki" yace d meenal da takaici va sanyata tsaiwa a gurin, tabota hajiya qarama tayi sai ta taka ta bude murfin motar ta shige. Sahar na kallonta ta cikin madubi, haka kawai yau din taji kanta ya fashe, gyara zamanta tayi tana kauda kanta gefe. "Set your belt" ya furta a nutse yana gyara zamansa. Kasa jira yayi ya miqa hannunsa da nufin jawo belt din ya daura mata,wanann ya bawa hannnun nasa damar shafar qirjinta. Daga shi har ita ba wanda jikinsa bai amsa ba,haushi ya kamata,tana tsammanin zai janye,sai taji ya garasa kwantar da fin rabin jikinsa a kanta. Da sauri ta daga kanta ga hajiya qarama dake tsaye saitin window din nasu,idanunta fes a kansu tana gain komai,ta dauke kan nata da sauri ta maida gareshi, tanason magana ma amma ya matseta sosai jikin seat din, yanata kokawar sanya belt din amma har yanzu baikai ga sakawa ba. Bugun zuciyarta ya fara qaruwa saboda gaba daya kusan a fakaice rungumeta yayi, saita sanya hannunta tana son tureshi, saidai kafin takai ga aikata hakan ya saka belt din da wani irin hanzari,ya kuma kama dukka hannuwan nata ya rige cikin nasa va sauke mata tattausan kiss saman lips dinta abinda ya sanya hajiya garama rufe idanunta da sauri ba tare data shirya ba "Kwana biyu,kwana biyu ko?"' Ya fada qasa qasa, tasan me yakeson fadi ,yanason sakayawa ne saboda meenal dake cikin motar. Da sauri sukaji an bude murfin motar kuma a wani irin fusace,bata iya tsaiwa ba ta kwasa tayi cikin gidan da mugun gudu, abinda ya yanke tsaiwar hajiya qarama a gurin,tabi bayan meenal din cikin sassarfa. Tashi yayi ya koma mazaunin driver yana sakin murmushi "Ko kishin kanki baki dashi? a gaban idonki na bawa wata lift?" Ya fada with softness yana shirin kunna motar "Kishi? god forbid" kadan ya waiwaya ya kalleta, kaman zaiyi magana sai ya fasa murmushi ya sake kubce masa "Alright,zamu gani, amma dai yanzun ai na taimakeki da korar miki ita,ko banza kya shaqi numfashi me kyau" kasa amsa masa tayi saboda gaba daya ya yamutsa ta a fakaice,kuma batason taci gaba da amsa masa fadeela ta fahimci wani abun. Kawai dai abu daya ya bata mamaki driving da yakeyi yau da kansa abinda bata taba gani ba, sai daya fita sauran motocin suka taso suka rufa musu baya,biyun kuma sukayi gaban tasu. A yau din bayan sun isa company,su biyu kadai suka wuce zuwa ciki. Dukka ma'aikatan kowa goqarin gaidashi yakeyi cikin girmamawa,abinda yadan basu mamaki shine yadda yake amsa gaisuwar tasu a yau kadan kadan, musamman ma'aikata mazan. Hatta cikin elevator su kadai ta dauka har zuwa building dinsu. Baya yaja yana kallonta,fa fahimci abinda yake nufi tayi gaba kenan, dauke kai tayi gami da noqewa kamar bata fahimci abinda yake nufi ba. A nutse ya tako ya garaso kusa da ita,ya sanya hannunsa ya rigo nata hannun yana hade tafukan hannayensu guri daya. Cikin sauri ta daga kanta ta kalleshi,ta kuma fara yunqurin zare hannunta daga nashi. Jifanta yayi da wani irin kallo sannan ya girgiza mata kansa alamun a'ah,bai sake saurararta ba ya jata a tausashe suka fita daga elevator din. Kusan duk inda suka gifta sai idanun jama'a sun bisu da kallo,wani irin mugun matching sukayi a safiyar tare da wani sassanyan kyau dake cakude da annuri saman fuskar kowannensu. Wanna kallon da ya lura ana binsu da shi ya sake jagula masa lissafi,sau uku yana canza mata side,from left to right, from right to left. Cikin kamalarsa yayi sallama cikin lobby na office din nasa, mazaunin saima kenan. Da kuxarinta ta dago tana amsawa, harda gyara zamanta, saidai kuma kafin takai ga garasa amsa sallamar komai ya magale mata a wuya,da qyar ta tattaro kalmomin "Good morning sir" "Morning" ya amsa mata yana wucewa kai tsaye ga office dinsa,har a lokacin kuma bai sake mata hannu ba "Sir,kowa kai yake jira,dukka suna hall din" saima tayi qarfin halin fada tana jin wani abu me daci saman harshenita. Sai a wanna karon ya waiwayo,kallo yayi mata irin wanda ya saba yiwa kowa, amma sai taji wani dadi a ranta,saboda takan jima bata samu wannan damar ba "Monday ne dama?" Ya tambayeta cikin kokwanto. Sai data hado wani murmushi saman fuskarta sannan ta gyada masa kai tana lumshe idanu "Yes sir" tana gama fada jibril yayi knocking ya nemi izini sannan ya shigo "Sir, kowa yana jiranka" "Okay" ya amsa yana gyada kai "HUGUMA* • TABARMAR KASHI* Book 02 Page 36 A nutse da wani irin sanyi ya maida dubansa gareta,wani sashe daban take duba bashi ba. Har gasan ransa yaji bazai iya tafiya ya barta cikin office din ba, kamar bai gaji da kallonta ba "Madam" ya kirayeta da wani irin amon sauti me laushi da sanyi. Tsigar jikinta tadan zuba saboda canzawar sautinsa a yau din, amma sai ta fuske kamar bata jishi ba. Ya matsu ya Kalli qwayoyin idanunta,yanason yabar mata wani saqo me nauyi da narka zuciya,kamar yadda ya sani, sauran mata ma suka sani, idanunsa nada wani irin mugun tasiri da maganadisu me qarfi dake narka zuciyar mata da yawa,ya kuma tafi da tunaninsu. Uwa uba yana matuqar qaunar idanunta, tun a shekaran jiya daya qure musu dukkan kallo harda wanda ya wuce qa'ida ma idan akwai,kallon cikin idanunta na tuna masa yanayin da suka shiga gaba daya shi da ita a wancan ranar,yadda komai ya canza cikin lokaci qanqani. A ranar ya fara tabbatar da kyawun qwayar idanun nata. Hannunta ya saki kawai sai ya rigo qugunta, sai gata tsaye a gabansa suna fuskantar juna. Kanta kawai ta sunkuyar ta hanashi kallon fuskarta bare akai ga idanunnata, abinda ya hanata kowanne yunquri na qwatar kan ta shine Karantar da tayi saima tana wajen "Da mutane fa a gurin nan" ta fada qasa qasa wai don kada saima din taji, saidai abinda bata sani ba,yadda tayi cooling voice dinta ya sanya yaji tsigar jikinsa gaba daya ta tashi,yadan ja wani numfashi hade da sheshsheqa "| know, just i want to look into your eyes......please" jin abinda ya fada ya sanyata maida idanun nata ta kulle gam, tana nufin ba zata bashi wannan damar ba,har cikin zuciyarta abinda tayi niyya kenan, indai idanunta yakeson kalla zai bushe a wajen saima ce kawai ta zalunceta data ci gaba da zama a gurin, tana pretending kamar bata ganinsu,ita kuma tayi imanin dukka hankalinta yana kansu,banda ita da tuni ta tureshi daga riqetan da yayi. Zanen fuskarta ya shiga kallo daki daki, tun daga kyakkyawan eye brows dinta,miqaqqen hancinta mar tsaho da tudu, shape din idanunta da kuma eye lashes dinta masu tsaho ya dire zuwa kyawawan lips dinta da suke yawna fuzgarsa,duk yadda yaso ya daure ya kasa "Your lips look so lonely, would they like to meet mine?" Babu shiri ta bude fararen idanun nata tarr bisa fuskarsa da suka cika da tsoron kada ya aikata din. Qaramin murmushi ya subuce masa. Fuskarta ya kama ya hade fuskokinsu guri guda, abinda ya Sanya saima ba shiri cikin rawar hannu ta kwashe takardun da bata gama tabbatar da ingancinsu ba ta bude qofa ta fice "Am dying to have my lips on yours one chance please!" Duka garfinta ts tattaro ta turashi tana yin baya,numfashi take maidawa hadi da sanya hannunta daya tana gyara zaman hijabinta "Why all these ne wai?, why?" Ta tambayeshi cikin zafin rai, zuciyarta na gaya mata shi kuma jikinta kadai yakeso, sha'awar ta kawai yakeyi, bashi da aiki sai burin son taba jikinta?. Da baya da baya yaja ya jingina jikinsa da bango yana rufe idanunsa, tuni kowacce jijiya ta jikinsa ta amsa "You stole my heart" ya fada can qasan maqoshinsa,labbansa kadai sune suka motsa. Itadimma lallabawa tayi ta zauna zaman kujerun dake gurin, tsahon wasu mintuna shuru ba wanda yace da kowa komai,yayi ta maza yana qoqarin binne komai a ransa ya mige ya tsaya saman qafafunsa ya fara takawa "Let's go" ya fada a taqaice, sai ya kasa ci gaba da tafiya sanda ya isa bakin qofa,ya tsaya har ta qaraso. Lalubar hannunta ya sakeyi ya hade da nasa,ta ja zata fincike yace "'Kina cirewa ban yafe ba" laqwas taji zuciya ds gangar jikinta tavi, bata da wani sauran zabi sai ci gaba da binsa da tayi. Kamar ya koma haka yaji lokacin da suka isa hall din, bai dauka zaman meeting din da mutane da yawa ba haka idanu sukayi caa a kansa shi da ita dukka suka mige suna masa barka da zuwa. Da ka ya amsa yana jin nutsuwarsa na raguwa. A nutse y jawo hannunta ya jawo kujerar da aka tanada saboda zaman CEO ya matso da ita gabanta,ya zaunar da ita a kai sannan ya koma bava ya tsaya yana dafe da kujerar, tamkar yaron gidan da uban gidan nasa. A schedule na meeting din one hour ne meeting ne, amma cikin mintuna talatin ya sallamesu. Yadda suka shigo yanzunma haka suka koma office din yana riqe da hannunta,wannan shi ne ya zama muhimmin topic na tattaunawa a cikin company din a ranar. Tunda suka dawo duk bavan minti dava zuwa biyu sai ya daga kai ya kalleta. A duk sanda ya kalletan kuwa sai wani abu mai qarfi ya fusgeshi tattare da ita. Wasu lokutan har sai ya tsaida abinda yakeyi ya zuba mata idanu yana kallonta cikin wani irin nutsuwa da wank lamari me matugar qarfi kaifi da kuma zurfi cikin zuciyarsa. Bata fahimci komai ba, kawai ta fuskanci yau din yana ta sanyata zurga zurgar dauko wancan ajjiye wannan. Yayi amfani gwarai da wannan damar wajen samun damar morewa kallonta ta yadda ranshi yakeso. A karo na barkatai ya sanyata dauko masa wani book cikin tsararriyar book shelf dake gefen table dinsa,saidai akwai tazara tsakaninsa da ita. Sanda ta miqe don isa gurin sai ya daga kansa gami da ajiye biron dake hannunsa,a hankali yake sake qarewa tafiyarta kallo, komai nata unique ne, bai taba cin karo da mutum me uniqueness irin nata ba. Ta maida hankalinta sosai tana duba masa littafin da ya aiketa ta dauko din,ba kuma wai don zaiyi karatu bane,a'ah,kawai yanason yaga wannan kyakkyawan takun nata. Yadda take tura baki da bata rai saboda bataga book din ba ya sanyashi sakin murmushi yana jin wata gajiya da kasala suna bin sassan jikinsa,wanda shi kansa yasan ma'anar hakan a tattare dashi. Ya miqe a nutse yana sanya hannayensa a aljihun wandonsa, har ya isa gareta bata sani ba. Daga bayanta ta tsaya, dab da ita,tazarar data rage a tsakaninsu duka baifi taku daya rak ba. Muryarsa ya sassauta sosai ya kuma rage tsahonsa yana son daidaita kanshi da ita ya dawo da kansa saitin kafadarta,cikin laushin murya tamkar wanda yake a buge yace "Am so tired,can you give me a hug pleasssssse" cak ta dakata daga abinda takeyi tsigar jikinta tana tashi,yadda yayi maganar saitin kunnenta ta shigeta sosai,sam sam bata tsammaci tsaiwarsa a wajen ba,saita qame a tsayen, bata juyo ba bata kuma ci gaba da neman littafin ba. Ragowar taku dayan da ya rage shi ya qarasa, cikin sanyi da tashi ya zura hannuwansa ta saman cikinta.va kuma jawota a mugun slow ya manneta da jikinsa. Kamar wadda aka yiwa allura ta zabura tana juyowa da sauri da nufin kufcewa,saidai kuma babu damar kuncewar saboda yayi mata zobe gaba da hannunsa. Kai tsaye idanunsu suka jone guri daya,ya lumshe nasa idanun tare da budesu lokaci daya yana sakin wani lafiyayyen siririn murmushi da ya sanyata kasa jurewa kallonsa saboda wani tsalle da zuciyarta tayi ta kuma ce mata "He was elegant" kanta takeson kawarwa amma ya hanata wannan damar,ya kama fuskarta ya riqe da kyau yana mata wani duba dake dauke da tarin ma'anoni masu wuyar fassarawa,wanda yakejin tamkar bakinsa bazai iya fadinsu ba "Hold me please hold me so close, that your breath become my oxygen" ya fadi numfashinsa na fita da sauri da sauri saboda yadda ya kwadaitu da labbanta. Bai iya controlling kansa ba kuwa sai daya dangane da bakin nata kaman dazun,ya shiga sauke mata hot kisses ya hanata katabus da dukka wani yungurinta na qwatar kanta. Har tsahon wani lokaci kafin ta samu nasarar tureshi, taja baya tana kallon idanunsa da nata idanun da hawaye ya cikasu taf yana gab da gangarowa. Bai wani damu da kalar kallon da take masa ba, yafi damuwa da yadda bata qaunar ya rabi jikinta,wanda a yanzun yakejin cikin zuciyarsa bazai iya wani dogon zamani ba tare da ya rabeta ba,ji yake kamar wani magnetic ne a tsakaninsu. Murmushi ya sauke mata da idanunsa da suka sakeyin wani irin laushi "Your eyes driving me insane madan ki daina kallona haka" ya furta yana gyara zaman sumar kansa da yatsunsa "Only you can give me that feeling" ya furta a nutse idanunsa har yanzu cikin nata idanun da bata iya gani sosai saboda qwallar cikinsu. Ba tare da kowannensu ya sakeyin komai ba sukaji an tura qofar office din, sautin takalma masu tsinin dunduniya ya soma tashi kafin daga bisani muryarta ta bayyana cikin sallama. Har cikin jinin jikinsa sai da yaji wani abu ya tsarga,lokaci daya gabanin yakai ga juyowa dukka wata walwala da nishadi da ya samu a yanzu suka fara narkewa. Säahar ke fuskantar qofa,don haka da ita idanunsu ya fara jonewa. Fara tas din mata, wanda har haskenta yaso zarce haske na dabi'a,tana da wani irin kyau shimfidadde akan fuskarta,saidai kuma a gangar jiki, irin matan nan ne da basu da hips kwata kwata,duk kuwa da cewa ita din ba wai siririya bace amma rashin hips din nata bayyananne ne ga duk wanda yasan tsarin halitta a gurin mace. A shape gown ce a jikinta ta wata shadda 'var mali komai na jikinta cike yake da ado da gawa "Sãahar, nanny N ko?, i see" ta furta tana jifan sahar da wani irin kallo, zallar kyawun da bata tsammaci samunta a tattare da ita ba yana bugar son bugar da ita,tako ina tana hangen wasu qualities kai tsaye daga gareta ta cikin hijab dinta kai tsaye, kyan suffa ciki da waje wanda cikin qasa da minti biyu wani azababben kishinta daya ninka wanda take ji a kanta kafin ta ganta ido da ido va lullubeta. Farat daya kwanyar säahar tayi mata recalling muryar, take kuma ta fahimci wacece, idanunta ta maida kan toufeeq wanda tashi daya kamanninsa suka canza da wani irin bacin rai da zallar tsana "Barka da warhaka uban 'yata" ta fada tana rangaji tare da jifansa da wani irin shu'umin kallo da tasan yanaso ada "Kar ka damu yanxu am single, naje na dawo kuma dukka don saboda kai" zare idanunta sãahar tayi daga kansu,tanaji a ranta bata da bugatar sauraren kowa a cikinsu,bata son jin komai daga bakinsu, don ba matsalarta bane, kowa yaji da matsalarsa, kuma kowa ya rige damuwarsa don haka ta fara takowa da nufin ta isa ga gurbinta na dazu ta dauki takalminta da hand bag dinta. Cikin jikinsa yaji tahowarta, zuciyarsa kuma ta gama gaya masa abinda zatayin, ficewa zatayi ta barshi da ameesha,fuskar da ya jima da shafe babinta cikin rayuwarsa. Rabuwa yayi da ita har ta garaso dab dashi, bata taba tsammanin yana ganinta ba,sai kawai ji tayi ya tattarata cikin jikinsa yayi mata wata kyakkyawar runguma. Mamaki ya hanata motsawa, sai kuma yadda kunnuwanta suka jiye mata adadin qarfin bugun zuciyarsa da ya qaru matuqa, ala dole tayi luf tana jin bugun sosai cikin kunnuwanta,abinda zai shaida maka lallai yana cikin fushi "'Baki yarda da gargadin dana yi miki ba?" Duk da zuciyarta ta qone sosai da kalar rungumar da ya yiwa sãahar din wanda ita daya tasan gardinta da dadinta, da kuma sirrin dake tattare da wannan ingarman girjin nasa data jima tana kewa,ta kuma gaza samun kwatankwacinsa acan inda take harin "Babu me rabani da kai sai Allah moha..... you are mine forever" cikin nutsuwa ya dauke kallonsa daga kanta,yasa hannu daya ya jawowa sãahar kujera ya zaunar da ita a kai "'Huta a nan" ya fada cikin kulawar da sai da Ameesha taji kamar numfashinta zaiyi skipping na wasu daqiqu. Tasan toufeeg ciki da bai fiye da kowa,soyayyarsa kulawarsa da tsantsar iya ririta mace wani abune da ta gama lalube daga gurin kaffff mazan data hadu dasu bata samu wanda yake da koda rabin rabinsa baya tattara abubuwa masu yawan da sai an tara maza dari ba'a samu qwaya daya rak irinsa ba. Wayar da ake kiran security kawai ya danna ya koma ya tsaya kusa da sãahar kamar wanda yake bata kariya "Inason ka bani dama mu fahimei juna, nayi maka kuma bayani mu yafewa juna na dawo na kula da 'yata" runtse ido yayi,ju yayi kaman ta soka masa wuqa a qahon zuciyarsa,har bayason ta furta fadeela diyarta ce. Bazai iya bata yawun bakinsa ma a kanta ba sai yaja waya yayi kira zuwa wajen saima "Come in" ya fada a kausashe yana ajjiye wayar saima da security uku suka shigo, mata biyu namiji daya Migewa yayi sosai iyakar tsahonsa yana dubansu,hatta säahar satar kallonsa take ta qasan ido,yadda lokaci daya ya koma Muhammad toufeeq jarma din data sani farkon haduwarta dashi, kaman ba shine yanzun nan ya gama karyar da wuya da murya a gareta ba "Who allowed that women to enter?" Kallon kallo aka fara a tsakaninsu,kowa yana tsoron magana yana kuma tsoron gaddarar yau ta fada kansa ta kora daga aiki, duk da cewa tunda ya dawo din ko ma'aikaci dava bai kora ba. "We are sorry sir, don Allah, bamusan bakason ta shigo ba" daya daga cikin matan tayi qarfin halin fada zuciya a karye "Take her outside, and daga yau,idan na sake ganin gilmawar fuskarta cikin kamfanin nan ku tabbatar kun rasa aikinku" yana kaiwa garshe suka cafketa su biyun,don kuwa ba zata jaza musu asara ba,don kaf fadin kano dama Nigeria basajin akwai company da zasu samu me dadin aiki da kuma albashi me tsoka wanda yayi kamanceceniya da kamfanin MT JARMA. "Ni ka wulaganta haka?" Abinda ta iya fadi kenan saboda tuni suka garasa yin waje da ita. Sai a sannan ya waiwayo ga saima ,wadda kallon idanunsa kadai ya sanyata taji kamar zata saki fitsari a wandonta "You are fired" ya fada kansa tsaye. Ya jima yanason rabuwa da zaman yarinyar cikin office dinsa,amma ya rasa da wanne irin laifi zai kamata,sai yanzun da wannan dalilin yazo. "Nan din ba Bar bane ko club da zaki dinga barin mata anyhow suna shigo min,bayan kin sani tare muke aiki da iyalina a ciki" yayi mata bayanin yana juya baya ba tare dava dubeta ba. Kuka ne ya hanata cewa komai, kawai saita juva da gudu gudu ta fice saboda ta gama tozarta tako ina a gaban idanun matar da take bala'in jin zafinta da tsananin kishinta,wanda ita sam saiman bata cikin damuwarta a rayuwa. "HUGUMA* "_TABARMAR KASHI_*® Book 02 Page 37 Yana jin qarar rufe gofar saima ya tako zuwa gaban saahar din, saman qafafunsa ya tsugunna vana dubanta da wannan zafin da har yanzu baibar saman fuskarsa da kuma zuciyarsa ba. Kauda idanunta tayi daga kansa tana jin wata shakkarsa tana shigarta,scene din da ya gabatar yanzu a nan ya sake tabbatar mata har yanzu TOUFEEQ JARMA shine dai,a gareta ne kawai ya sauya. Yatsunsa ya sanya ya dawo da fuskarta saitin tata fuskar, sai ta sake kau da kai,ya sake maido fuskar tata ta sake kawarwa,a karo na uku ya sake juyo da ita a zafafe sannan yace "Idan kika sake juyamin qeya sai na miki hukuncin da na fahimci shi kikafi jin toro,idan baki wasa ba saidai a kawo wheel chair a daukeki, kada ki manta ina da sofas masu taushi a resting room" izzarta ce ta motsa,ya akayi ta bari ya karanci ta tsorata da abinda yayi mata?. So take ta gaggaya masa magana, amma ta sani daga qarshe yamutsatan da batason yayi shi zai aikata mata "Na kusa kawo qarshen komai" ta fada qasan ranta a fili kuma tana hade rai "Wayonki da tsiwarki dukka yau na rainasu, saboda baki kishina saiki bar duk wata karya da godiya su dinga tunkarar mijinki gaba gadi ko 'yar shakkarki basa ji saboda sunsan lusara ce MATAR TOUFEEQ?" Da gayya ya kira mata lusarar saboda ta motsa wani abu dake danqare a zuciyarta,yaci nasara kuwa,don take bacin rai ya bayyana "Ko ba komai ya kamata su dinga jin shakkar tunkarata haka kai tsaye saboda KE" "'Ina ruwana da abinda ya shafi rayuwarka?,rayuwarka daban tawa daban,ka taba ganin anyi kishin abinda ba'a so?, ba'a kuma damu da shi ba?" Ta fada itama gaba gadi. Murmushi ya saki karon farko shima zuciyarsa a yau ta dandana dacin kalmar RASHIN SO da kuma QIYAYYA. Kai ya girgiza "Tashi mu tafi gida" ya furta yans miqewa tare da ja baya ba tare saya sake bi ta kanta ba. Ranta a quntace itama ta tashi tana jin haushin maganar da ya gaya mata, bataso yabar zancan iya haka ba,sai gashi yayi kamar komai bai faru ba. Baice mata ci kanki ba a mota har suka dauko fadeela suka wuce gida yana jinsu sunata sabgarsu,bai ce musu komai ba kuma bai hanasu ba. Yau din sun koma da wuri, yana zaune a motar yana kallonsu har suka qule a sassansu fadeelan, kai ya jinjina "Zanyi maganinki" ya fadi qasa qasa, kafin ya kashe motar,ya barwa jibril key din a jiki ya fito yana cewa "Kada kayi nisa,zamu sake fita kaman nan da one hour" "Okay sir" ya fada cikin girmamawa. Falon wayam,har yanzu Jacob bai dawo ba, hakanan har yanzu bashi da tsayayyen gurin cin abinci. Bai tsaya dogon nazari ba ya wuce bedroom dinsa,don yana matuqar bugatar ganin Dr jarma a yau din,don a gobe yace masa zaiyi tafiya,morning flight zaibi, dukbda dai har yanzu bai gaya masa inda zashi ba, kusan kuma basu saba hakan dashi ba, shima bai matsa da tambaya ba, kasancewarsa mutum ba me bun qwaqwafi ba yasan idan ya dace yaji tabbas zai gaya masa. Ya fara zare kayansa, idanunsa suna bisa gadon Duk lokacin da ya kalli gadon babu abinda yake tuna masa sai wancan moment din, wani abu guda daya da ya tsaye masa a rai, ya kuma kasa mantawa, abinda duk sanda ya tuna sai yaji ilahirin tsigar jikinsa ta tashi, ko me vakevi kuwa. Wani qaramin murmushi ya subuce masa lokacin da ya tuna da sauran abubuwan da suka faru,gaba daya bata da wayo sam ta irin wannan bangarorin, autar ce da gaske "Akwai tsiwa,sai tsoro" ya furta gasa gasa, ya dan kada kai yana jin buqatuwar kasancewa da ita na mamayarsa. Abinda ya farun ya zama kamar ta lasa masa zuma me azabar zaqi ne a bakinsa, kwana biyu rak amma ji yake kamar ya shekara rabonsa da ita, laluben rigimar da zai jawo kawai yakeyi wadda zata bashi dama ya sake kutsawa zuwa wannan alfarmar tata da yake fatan ya dawwama har abada a cikinta. A gurguje ya shirya bayan ya fito, cikin wani yadi me azabar kyau da daukar idanu sky blue,yana da taushi da kuma qarancin kauri, jikinsa sai fitar da qamshi yakeyi me dadi, saidai kuma cikinsa wayam yake yunwa yakeji amma ya bari idan sun fita ya laluba gidan abingi me kyau yayi takeaway. Half cover me kyau ya zubawa gafansa ya dauki wayarsa dake tsuwwa yana duba me kiran. Sajjad ne,ya kara wayar a kunnensa yana ficewa. Har yayi gaba ya tuna yanason magana da nadeeya, don haka ya koma da baya ya shigal sashen. A parlor ya samu nadeeyan tana kallo,gefenta bowl ne da aka yayyanka kankana ayaba da madara,sai abun sugar dake ajjiye ba'a kai ga zubawa ba. "Ina zuwa" yace da sajjad yana sauke wavar idanunsa akan bowl din sanda take gaidashi "Wannan fa?" "Aunty N ce ta hada zata sha, fadeela ta tasheta kitchen wai tayi mata veggies couscous" a nutse ya koma ya zauna,ya dauki bowl din ya fara juyawa "Kun zuba sugar ne?" Kai ta girgiza "Bata saka ba" bismillah yayi ya fara sha, gardin madara dana fruit din dake ciki suka gauraye harshensa,sannu sannu sai gashi ya gama da shi gaba daya ya ajjiye bowl din tare da nufar kitchen din, gamshin da yajeji a ciki yana jan hankalinsa. Tsaye take gaban gas ta bawa gofa baya,sanye take da wata farar gown cotton me hannun vest, iyakar gown din qaurinta,saidai ta fidda shape dinta qwarai,ko a inda yake tsaye yana hangenta,yana iya gain faffadan qugunta da ya zamu ado da tsayayyun mazaunai. Ido ya lumshe vanayin jikinsa ya fara canzawa, qwaqwalwarsa na tuna masa maganar was abokan sajjad "Mace me qugu da hips duniya ce, ai tayi alaji" ya yarda da hakan dari bisa dari, a yanzun ya zama shaida akan hakan. Amma muddin maza suna iya banbance irin wadan nan halittun daga wajen mata bayan ba matansu bane na aure, to ya zame masa dole yayi dukkan me yiwuwa ya bata dukkan tsaro da kariya fiye da yada zai bawa duk wani abu nasa kariya, domin shi yasan me yaji a jikinsa,me kuma ya gani yake kan ganin. Qamshinsa kawai ta shaqa ta tabbatar yana gurin, amma saboda tana kokwanto sai tayi kaman tana gyara jelar gashinta dake fake tsakiyar kanta ta kalli gefanta. Yana tsaye yana kallonsu, fadeela take zubawa abinci,sai ta maze kamar bata ganshi ba,ta kammala zubawa fadeelan ta miga mata,sai ta kwasa da gudu tana ficewa. Maida spoon din tayi cikin tukunyar tana niyyar rufewa. Caraf ya kama hannunta ya riqe, sai ya zagaya ta bayanta ya manne jikinsa ta bayanta yana sake riqe daya hannun nata,ya zamana dukka hannuwanta suna rige a hannunsa "'Na yarda marowaciya ce ke" ya furta cikin hade rai ya miga hannunta dake rige cikin nasa ya dauki plate, ya sarrafa daya hannun nata da nashi hannun ya zuba couse couse din,sannan ya sake mata hannu yana tallafe plate din. Jikinta na rawa ta rufe tukunyar, tayi taku biyu zata bar kitchen din yasha gabanta yana kai lomar abincin bakinsa. Da ido ya tsareta yana ci gaba da cin abincin wani irin taste dadi yana ratsashi, duk yadda jacob yakai ga iya abinci,ya kuma sallama masa akan hakan a yau yaji wadda ta dameshi ta shanye. Yadda baice mata komai ba haka itama bata ce masa ba yadda bata nema ya bata hanya ba shima bai bata din ba,a haka yaci gaba cin abincin yana kallonta,har nadeeya da taji shurun yayi yawa sãahar din bata fito ba, kuma tanason gaya mata ta fiddo wasu fruit din yaa moha ya shanye wancan,da ta leqo ta gansu a haka,sai tasa sawunta a likkafa cikin sand'a ta koma,kuma har ta koma din ba wanda yaji motsinta a cikinsu. Lomomi kadan ya rage ya ajjiye plate din saman freezer wadda tafi kusa dasu "Baiyi dadi ba" ya fada yana yarfar da hannunsa,ya juya ya dauki ruwa ya balle murfin yana sha yana karantar fuskarta. Tayi algawarin daina biye masa, don haka sai ta rabashi kawai ta fita a kitchen din. Murmushi ya saki, yadda yaga ta iya jurewa batayi magana ba,duk da ba haka yaso ba, don bakinta yazo ya sake sha, don hakan ba garamin dadi yakeyi masa ba. Bai ganta a falo ba,cikin dakewarsa wanda ba zakace shine ya gama neman rigima yanzu ba a Kitchen ba yace da nadeeya "Daga yanzu zuwa ko ysuhe, duk lokacin da hajiya ta fita unguwa ko wani guri ki sanarmin, immediately, but ina bugatar sirri,kin gane?" Kai ta gyada sannan tayi masa a dawo lafiya,cikin ranta tana mamakin dalilinsa na bata wannan aikin. Kamar zata kifa lokacin da take sauke masa ruwa da drinks sanda yake zaune a gaban Dr jarma. Tun bayan da yayi aure wanna shine ganinta dashi na biyu,saboda gaba daya ta daina zuwa gidansu. Ko bayan data fita bayan hannunta ta sanya tana share hawaye, ta gaji da zaman jiran nan, ta qagu alqawarin da mommynta tayi mata na cewa nan da wani dan lokaci zai kawo kansa wannan algawarin ya cika,haqiqa akwai mutane da yawa da sai ta dauki fansa a kansu,hajiya qarama data zama mutum ta farko wadda ta yaudareta game da lamarin toufeeg tana cikinsu,koma tace itace mutum ta farko. Tun zamansa gaban Dr jarma ya fahimci kamar cikin farinciki Dr jarma din yake, bai taba komai cikin abinda aka kawo masa ba kamar ko yaushe ya gyara zama,kansa a qasa bakinsa cike da addu' ar Allah ya dorashi kan Dr din "Abba alfarma nazo nema" ya fada yana dan shafa sumarsa dake sheqi. Zamansa ya gyara yana dubansa "Wacece alfarma kenan Muhammadu?" "Abba,don Allah inaso SAHR tayi zamanta a gida,duk aikin da kake tunanin zata tayani, i can do it gaba daya ni kadai,idanma akwai buqatarta, zan ajjiye mata komai a study room dina ta ding aikin daga gida" dan shuru Dr jarma yayi na wasu sakanni, daga yanayin maganar toufeeq kadai ya shanshano wani abu, can gasan ransa dariya tana son kamashi amma ya danneta,sai yadan bata rai kadan "Yanzunma kanason ka koreta ne da baqin halinka yadda ka saba ko kuwa?" Da sauri ya girgiza kai "No, Allah abba ba haka bane" "To yaya ne?" Yayi masa tambayar yana tsirashi da ido tare da son qureshi,don yanason samun tabbacin abinda yake zargi. Sumar sa kawai yayita shafawa,ya kasa cewa Dr jarma komai, baisan ya zai furta masa ba,ta yaya zaiyi masa bayani? abban baisan akwai kunya tsakaninsu ba? "Muhammadu, ka gayan gaskiya” "Abba.... I don't know how to explain, kawai dai..... Banason yadda maza suke kallonta,nayi duk iya bakin gogarina akan hakan ta daina faruwa, har hijabai na dinka mata, amma wallahi abba a banza,abun is annoying me" Dariyar da Dr jarma yaketa boyewa ta kufce masa, yayi qas da kansa yana kallon yadda toufeeq din da magana doguwa ke masa wahala amma yadda ya karkace yanata rattabo masa bayani wanda simple question ne da a amsa daya ya gama da ita. Ta wani gefen sai zuciyarsa ta karye yana tuna shekarun baya rayuwa tsakaninsa da SHIFA MAJI,yayi gogarin dai daita fuskarsa ya daga kal yana kallon toufeeq sanda yake fadin "Don Allah abba a barta, kada kace a'ah" kafadarsa ya dafa yana murmushi "Daina rogona muhammadu,mutum da matarsa?, ko a baya ma ai ni bance dole ba, ta fuskar alfarma nazo, kuma naga kayi accepting, ko a lokacin inda kace ba zatayi yi ba ba komai, matarka ce qarqashin dukkan mulkinka da ikonka take,sai abinda kace zatayi,tunda bakaso na janye ta zauna ta kulamin da muhammaduna" sai a lokacin kuma kunya ta saukar masa,yayi qasa da kansa yana qoqarin tuna da meye da meye ne ya gayawa dr jarma din. "Na gaya maka zanyi tafiya ko? gobe zan wuce Algeria" ya fadi yana duban toufeeq "Algeria abba?" "Eh, zanje na gyaro wata barna, fatana Allah yasa kada gyaran ya daukeni lokaci mai tsaho, don banajin ko da zanyi shekara zan iya dawowa ba tare da na samu yadda nakeso ba" maganar ta dan Sanya toufeeg a duhu,amma duk da haka yayi masa addu'a da fatan alkhairi sosai, suka fada hirarsu irin ta d'a da uba "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 38 Tunda ya shaida mata ta daina fita company ya zamana kamar gaba ita ta kaita. Gaba daya tayi qaura daga sashensa ta koma dakin fadeela ta tattara hankalinta akan yarinyar, gefe guda kuma tana soma musu shirin fita asibiti ita da fadeelan ba tare da kowa ya sani ba. Cikin ilkinsa ya fara jin rashin dadin sassan gaba daya,a hankali ya fara taba ruhi da zuciyarsa,tun yana tunanin ba komai bane, sabo ne kawai da hausawa ke fadin turken wawa ne, har ya karanci lamarin ya fara zarta haka. A hankali ya fara rasa baccinsa saidai ya yita juyi saman gadon yana tuna sweet moment din nan,wanda yabar masa wani irin tunani me yawan gaske da kuma dadi da sanyaya zukata. *******Shi daya ne zaune a falonsu, sai tarin ayyukan da suka sanyashi a gaba,wanda gaba daya sam sam baya jin dadinsu,yana yinsu ne bisa tilas. Gefe daga kuma abinda ya faru dazun tsakaninsa da meenal ke dawo masa,yarinyar ta koma masa tamkar wata zautacciya,tun tana bashi dariya da mamaki abun har ya fara qureshi, bata kunyar fadi masa komai a gaban kowa, ko a dazu sai da yayi kamar zai mammareta ya samu ta fita a sashen. Ajiyar zuciya ya sauke yana ajjiye aikin da yakeyi din,jikin kujerar ya koma ya jingina yana dan lumshe idanunsa, babu laifin wadda yake gani sai nata, itakam wai kamar babu zuciya a qirjinta?, da gaske bata damu da al'amuransa ba,bata kishinsa haka yana nufin bata sonshi fa kenan. Ya baiwa kansa da kansa wannan amsar, abinda ya sanyashi sakin ajiyar zuciya me nauyin. Fadeela ce tayi sallama ta shigo,ya daga kai yana duban yarinyar sai ya saki murmushi. Da gaske qiba takeyi abinta,abinda suka debe tsammani kwata kwata daga shi,sun dauka jikinta ne a haka. Da sassarfa ta iso gareshi, ta fada saman cinyarsa tana kiran sunansa, hancinsa ya shaqi wani daddadan qamshi daga jikin yarinyar "Ya akayi kika fito at this time haka? bakiga dare ya fara ba?" Juyi tayi a jikinsa "Ko aunty N batasan na fito bafa?, hmmm cewa tayi itama dare yayi tunda munyi shirin zamu kwanta, kaj ma har turarenta ta shafa min" ido ya lumshe ya bude,yana jin dadin qamshin qwarai, zuciyarsa ta motsa shi qwarai,sai yaji bazai iya jurewa ba,don haka ya miqe yana cewa ina zuwa Dakinsa ya shiga ya dauki wayarsa ya saka slippers sannan ya kama hannun fadeela suka fito Sassansu suka nufa kai tsaye idanunsa suka sauka a sashen hajilya qarama,yau kwana biyu kenan baiji motsinta ba duka kwanakin ya gaza takawa sassanta ya gaidata kamar yadda ya saba, haka kawai yakejin kamar an cire hakan fit daga zuciyarsa, sake tunawa yayi da kiran da nadeeya tayi masa dazu tana shaida masa,taji hajiyan na magana cikin waya,gobe yinin bikin qawarta, kuma kamar a can zasu wuni. Kansa ya dauke daga gurin,cikin kamewar nan tasa yayi sallama cikin falonsu nadeeya Tun bai gama yin sallamar ba ba kuma tare data daga kai ta dubeshi ba gabanta yayi wani irin faduwa, kafiya da taurin kanta ya sanya taqi daga kai ta Kalleshi,sai taci gaba da sabgarta. Idanunsa a kanta har ya qaraso falon. Nadeeya ce ta fara gaidashi, ya amsa yans miqa mata hannun fadeela tare da yi mata alamar su tashi a gun lokacin yana gaisawa da baba ramatu. Sai a sanann ta dan daga kai ba tare data kalli sashen da yake ba tace "'Barka da dare, ina yini?" Sai ta mige da nufin barin gurin "Inda ban wuni ba zaki ganni?, dawo ki zauna" ya fada da husky voice dinsa. Haka kawai jikinta taji ya mace mata,sautin muryarsa ya nuna a dakensa yake, kamar sautin da ta sani lokacin yana MT JARMA dinsa na asali. "Zaman me kikeyi a nan?" Ya jefa mata tambayar kai tsaye yana soke hannuwansa cikin aljihun wandonsa, tambayar ta sanyata daga kai abisa dole ta dubeshi, sai taji bata da zarrar ci gaba da kallon nasa "Kula da fadeela" ta bashi amsa tana kau da kai,don ta fuskanci izza ce sosai yau din akan fuskarsa. Kai ya girgiza, bayason yayi fushi wani me yawa yayi gogarin dai daita muryarsa "Ki fidda komai naki kizo ki wuce part dinki,can din shine gidanki ba nan ba,karki bari na maimaita miki hakan,just five minutes na baki" daga haka ya wuce ciki. A daki ya samesu ita da nadeeya. Wani kallo ya jefawa nadeeya da ya sanyata shiga taitayinta "Wato kece munafukar ko?" Ido ta fidda tana dubansa a dan tsorace "Yaa me nayi?* Ta fada a karye "Duk ranar da kuka qara bata guri ki tabbatar kashinkl ya bushe,don ba ku na aurowa ita ba" sosai maganar ta bawa nadeeya dariya, amma don dolenta ta cinye abarta, saboda ta san yin dariyar a gabansa ba qaramin match ta tarowa kanta ba. Sai ta karyar da kai "Ayyah yaaya, kayi haquri nima nayi tunanin gaskiya baik. "Will you keep quiet maaa?" Ya furta a nutse "Am sorry* ta furta itama tana kama bakinta. Dan nazarin dakin yayi kadan,sanann ya K'arasa ya tsugunna a gaban fadeela "Yau zaki kwana tare da anty nadeeya?, zan karbi aron nanny N dinki" murmushi fadeelar ta sake tana gyada kanta,sai ya shafa kanta "Good girl" waiwayawa yayi ga nadeeya ya sake wanu hade rai "Ki kula da ita sosai, dole ki koyi abubuwan da take na bata kulawa, kar a bari ta fita, kada ta karbi komai daga hannun kowa,magungunan da antynta take bata su kadai zaki bata good night" ya fadi yana sake kissing goshin fadeela din sannan ya fita. A falon ya sameta a tsaye, da alama fada baba ramatu keyi mata,amma fitowarsa ya sanyata yin shuru. Gaba yayi abinsa,idanunta akan bayansa tayi qoqarin shanye abinda ya taso mata "Fadeela fa?" "Ba tare aka kawoku ba ko" ya bata amsa yana qarasa ficewa, cikin ransa yakejin dole ya zama jalirtacce, dole kuma ya karanta mata da gaske hi din mijinta ne, ita kuma itace matar,ya fahimci fada da baki bazaiyiwu ba, saidai taci gaba da karbar lectures din a karancenta. A shirye yake ya gyara komai ya zama akan shiri, ta lasa masa wata zuma da tafi dukkan zumar duniya dadi zagi da Kuma gardi,baya tunanin jikinsa zai iya ci gaba da rayuwa hakanan ba tare da ta sake ci gaba da fitinarsa ba a rayuwa. Zuciyarta kamar zata fashe sanda take isa sashen,har yanzu izzarsa da jin kansa yana nan,tsantsar rashin adalc da kuma yadda ya karya kowanne alqawari da yarjejeniyarsu. A falo ta sameshi, har cikin zuciyarsa da gangar jikinsa yaji giftawarta,amma bai ko dago kai ba, itakam ko sashen da yake bata kalla ba ta wuce kai tsaye zuwa dakinta. Qamshinta ya gama rikitashi,yayi tsammanin zai iya ci gaba da aikinsa amma hakan sai ya gagara,ya zame takardar da yake dubawa daga idanunsa yana rufe idon,jikinsa da dukkan wata gaba ta jikin nasa suna amsawa "Ya Allah" ya furta yana qanqame jikinsa, sai yasa hannuwansa ya tallafi fuskarsa yana sauraren bugun zuciyarsa da kuma fitar numfashinsa. Ya kusa minti talatin a haka, daga qarshe ya tabbatar aikin bazai yiwu ba,sai ya tattara komai ya rufe, ya wuce dakinsa. Wanka yayi,ya shirya cikin wasu silk pyjama masu sulbi na kamfanin The Natalya masu asalin tsada da kyau, komai nasa designer yake amfani dashi,wannan ya sanya ya sake zama na musamman, kuma duk inda ya ratsa yake zama na daban cikin mutane, Comb ya saka yana gyara sumarsa me santsi da ban sha'awa, ya saka hair mist na sumar da Beard mist dukka ya shafesu. Qamshin ya hade gaba daya daga sassanyan turaren jikinsa suka bada wani qamshi a musamman. Ya kammala ya dauki qaramin towel ya goge hannuwansa,sannan ya fara kiran number wani company wanda suke akin sanya CCTV camera. A taqaice sukayi magana dasu, ya kuma zabi kalar wadda yakeso a sanyasa masa tare da da adadi. Har ya fadi adadin sun gama wayar yayi sake kira,yana buqatar qarin wata guda biyun,yadan saki murmushi wanna karon da ya tuna a inda za'a sanya masan. Sago ya tura musu sannan ya kashe wayar,ya hadata da key din dakinsa ya bude qofar ya fito. Kayan jikinta kawai ta sauya bayan shigarta dakin,tanata kumbure kumbure da ququninta; tsakiyar hakan taji wayar afifa. Sai data fara dauke wayar daga kunnenta sabida ihun dariyar afifa data sajjad "Am sorry hayatee, Allah besty kawai na kira, daga ita zan kashe wayar...ton thanks zataji" sai kuma tayi sallama "Ku fita a idona ke da saljad Allah fa" sahar din ta fada tana bata fuska. Dariya afifa ta saki "Sorry my bestie, kinsan eikin lokacinsa ne yanzun, shi kuma baya gaunar yaga attention dina akan kowa a irin wannan lokacin sai shi, bestie anya akwai abinda yakai aure dadi?, komai na cikinsa me dadi ne wallahi, please ki saki rai da zuciyarki ki tarairayi mijinki ki kula dashi ku more rayuwarku nan da lokaci kadan zaku manta da komai ke da shi he is nice man, kuma idanunsa kadai kika Kalla wallahi kinsan za'a sha soyayya me zafi daga hannunsa, hayatee yana gaya min,idan yanason mace bai iya qaramar soyayya ba, kulawarsa da dukkan lokacinsa nata ne ragama yake migawa,shi yasa da aka cutar da shi abun yayi mugun tabashi" "Bestieeee.....,meye dalilin da yasa kika kirani? don ki bani wannan labarin?" Kai fa girgiza tana qaramar dariya "A'ah your visa is ready, hakanan ticket asibiti da hotel din da zaku sauka, duka hayatee ya kammala,na kasa boye masa besty amma, kiyi haquri saboda tsaro, amma yayimin alqawarin ba wanda zaya gayawa, shima ya jima yana kwatanta shammatar toufeeq,amma shi bashi da qwarin gwiwar da ke kike da ita,zamu biyo bayanki after kun isa, an kuma tabbatar da abinda za'a yi matan" ido ta lumshe tana sake jin qaunar afifa, ta tashi bata da yar uwa mace amma afifa ta maye mata wannan gurbin, ita kanta batasan girman matsayin da afifa ke dashi a gurinta ba,duk wani yanayi na rayuwa da ta zata tsinci kanta a ciki,afifa she's standing by her side a koda yaushe. "Bansa ta yaya zan gode miki ba, saidal nace Allah ya barki da hayatee dinki" "Ya salam,kin gamamin addu'a,rayuwa da mutumin kirki ai ba abinda ya fita dadi" ta fada cikin shauqi, har abun ya sanya säahar murmushi me sauti "Dole naci gaba da yimiki uzuri, kin gama dulmiya* "Wallahi kuma bana tunanin zan fito, jininsu toufeeq suna da iya rige zuciyar mace da sassanyar soyayya, hakanan suna da tsayawa a rai,ke kanki yanzun idan na rantse kin fara sonshi bazanyi kaffara ba,bazan taba yarda yadda ya shayar dake madararsa ba sannan kice bai dasa kowanne irin feeling a ranki ba..." Tana kaiwa qarshen maganar ya tura qofar ya shigo, abinda ya sanya sahar katse wayar ba tare data y sallama da afifa ba, idanunta a kansa .*HUGUMA* * _TABARMAR KASHI *®️ Book 02 Page 39 Fargaba ce ta cika zuciyarta lokaci guda cike da nadamar sanya rigar jikinta,tare da zama da tayi cikin dakin a haka. Wata silk nightgown ce a jikin nata wadda take bayyana shatin komai dake jikin nata,hatta da pant dinta kuwa hakan siffar albarkatun qirjinta da ya bayyana sosai, wanda yake tsaye qyam a cike. Danna wayarta ta soma yi tana amsa sallamar,ita kanta batasan inda take shiga cikin wayar tata ba saboda a mugun rude take. Da qyar ya fusgi numfashinsa yana runtse ido "She's killing me"ya furta a sarari amma kamar wanda baya so a jishi. Gaba daya jikinsa ya amsa,ya qarasa a sanyaye ya zube wayoyinsa da key dinsa saman bedside drawer. A nutse ya miqe yana nade hannun pyjamas dinsa, idanunsa all over her body. Duk yadda yake zaton zai iya jurewa,zai kuma iya controlling kansa yaji ya gaza,bazai iya din ba,step din da yakeson ya fara bi na shaquwa da ita da kuma Koya mata bacci cikin jikinsa kafin komai yaci gaba da wanzuwa a tsakaninsu sai yaji yana rushewa daya bayan daya. Daga inda yake tsayen yana qare mata kallon qurilla, ya karanci yadda qirjinta dake jan hankalinsa matuga da gaske yadda yake dagawa, abinda ke alamta masa cewa bugun zuciyarta ne ya qaru,sai ya sauke hannunsa ya fara takawa gareta cikin nutsuwa da kamewa. Bayanta ya koma ya tsaya, abinda ya bashi damar ganin dukiyar fulaninta sosai,cikin hanzari ya lumshe idonsa numfashinsa na fara sauyawa,yana jin yadda jini ya harba da sauri cikin jijiyoyin jikinsa "Ya Allah,ya assalam" ya furta,a hankali ya dafe batan kujerar da take kai da gwiwoyin hannunsa wanann ya kawo mugun kusanci a tsakaninsu,sabida gaba daya fuskarsa sauka tayi jikin dogon wuyanta dake sanye da wani chain me kyau wanda ya zama ado ga wuyan nata. Tsigar jikinta ta zuba sanda ya zura yatsantsa guda daya yana qoqarin kamo chain din "You are the hottest women in this planet" ya fada with slow and cool voice cikin tsakiyar kunnenta. Yadda ta zabura da jin kalamansa dake son kassara duk wata laaka ta jikinta tayi nufin zamewa tabar gurin,haka yayi wani tsallae guda daya ya haura ta saman kujerar dai gashi a kusa da ita cinyoyinsu na gogar juna. Sau daya tak ta kalli idonsa ta janye dubanta daga kansa, daga shigowarsa kadai zuwa tsaiwarsa a bayanta ya birkice gaba daya. Tattausan tafin hannunsa ya wuyanta daga gasan habarta.va kamo bakinta sosai vana masa wani irin narkakken kallo,kamar idanun mutumin da yasha wani abun maye ya bugu,ko kuma matsanancin bacci ke shirin rinjayarsa ya qara kusancin dake tsakaninsu sosai har sai da suka fara musayar numfashi a tsakaninsu,duk iskar data fita daga hancinta kai tsaye yake zuqeta,hakanan kowanne numfashi nasa hancinta yake sauka. "You look so sexy" ya fada yana fincikota cikin jikinsa saboda kwadayin jin dumin jikinta daya saukar masa. Da kyau ya rigeta,ya sanya harshensa a kunnenta cikin nutsuwa, abinda ya sanya ta qanqameshi ba tare da tayi niyyar aikata hakan ba. Jin abinda tayin ya sanyashi sakin murmushi ya kuma zare harshen nasa, saidai cikin kunnen nata ya saka rada mata "Let me see if you taste as good as you look" kaman giftawar walqiya ya dagata cak,bai direta ko ina ba sai dakinsa,saboda yanason yayi Linking past memory dinsu yayi renewing dinsa da wannan sabon,yana matuqar debe masa kewa da sakashi cikin wani yanayi da shi kansa baisan ana shiga irinsa da tunani kawai ba. Zuwa lokacin ta fara goqarin qwatar kanta tana kuma hawaye,qaramin murmushi ya saki,ya kama hannuwanta dake qoqarin tureshin ya riqesu sosai cikin nasa "Am sorry, bazan iya haqura ba,but i promise you,it will be sweetest thing da kika taba ji more than yadda kikaji rannan i promise" Daga wannan sai ya shiga lashe kowanne hawaye dake saman fuskarta. In a romantic way ya fara tattare rigarta, dame rigar tayi tana girgiza masa kai, saboda gaba daya ya kashe mata bakinta. Wani marayan murmushi ya sakar mata "Kinaso ki bani wahala SAHR?,bana gane komai fa zuwa yanzu" ya fada mata cikin mugun karyar da kai da sarewa,da kuma wani mugun duka da lahanin da shauginta da qaunarta me zafi suka yi masa. Zare idanunsa yayi daga nata,sabida bayason ta sanyashi ya karaya,yanason yaci gaba da tabbatar mata da cewa ita din tashi ce, don haka ya daidaici tsakiyar rigar ya tsargeta biyu kowanne sashe yayi gefe daban,take ya garasa haukacewa,saidai cikin ruhinsa ya gama yiwa kansa alqawarin itama yau saita dandana abinda yake dandana,sai ya sanyata ta sauka daga layi kafin komai ya shiga tsakaninsu. Cikin qasa da minti goma sha biyar ya sauketa tsaf daga kan layi,tun tana turjiya tare da qoqarin tureshi har jikinta ya fara saki yana amsar sagonnin da yake bata,kafin zuwa wani lokaci gaba daya ya samu yadda yakeso,ta sakar masa ragama gama daya,itama kuma ya aike da tunaninta can wata duniya me nisa qwarai. Sai da komai ya kammala sannan bacin rai da kunya suka addabeta,ta cusa kanta qasan pillow tana sakin wani siririn kuka,kukan takaici da baqincikin yadda ya yaudareta ta sake masa jiki har haka,harda tayashi wasu abubuwan,bata manta yadda ta riqe harshensa da kyau cikin bakinta,sanda yake gogarin janye bakin sai tasa hannuwanta ta rige kansa sosai yadda bazai subuce mata ba,shi kuma yaci gaba da biye mata. dai dai yayi saman gadon yana jin wani nishadi yana ratsashi tako ina,zuciyarsa fes tamkar farar takarda,kukanta a yau sai yake jinsa yana masa dadi cikin kunnuwansa,saboda dai dai suke da kukan shagwaba cikin qirjinsa. Idan ya tuna yadda tayi participating a wasu abubuwan sai yaji kamar ya dawo da mintunan baya ya sake moresu. Duk yadda yaso ya lallasheta amma taqi saurarensa,har yayi wanka ya dawo taba qududune tana kukan takaicin kanta da kanta "Na zubda ajina" take gayawa kanta da kanta. Yasan idanma yace ta tashi tayi wanka wani batu ne na daban,wannan yasanya bai tsaya ko bi ta kanta ba,ya nade hannun rigarsa sumarsa jige da damshin ruwa,ya tsugunna ya sunkuceta gaba daya. Comforter ta riqo a gigice tana kare jikinta tare da sakin wani hawayen "Ka saukeni Allah, Allah bazan yarda ba, Allah kuwa,bazan yarda ba, tunda ka karya yarjejeniya" murmushi ya sakar yasa tsinin hancinsa saman nata ya gogasu guri guda idanunsa a lumshe "Keep quiet babe,i also break my rules for you" ya fada softly,sai kawai ji tayi ya tsundumata cikin bathtub. Ko daya bai saurareta ba,sai data dinga masa magiya tana hawaye sannan yabar mata toilet din. Sanda ta fito kamar surukarsa haka ta koma, kaya ta diba ta koma toilet ta saka sannan ta dawo,har yanzu hawaye takeyi. Sofa bed ta koma ta cure guri daya,yana zaune daga gefan gadon yana addu'o'in bacci ta gasan idanunsa yake qare mata kallo. Tun yana jin motsinta a hankali har yaji shiru,hakan ne ya bashi alamar cewa bacci ya dauketa. A nutse ya miqe ya isa gareta, tsaye yayi a kanta,hannuwansa zube a qirjinsa yana qare mata kallo,wani sassanyan murmushi ne yake fita daga kan fuskarsa,yana jin zuciyarsa kamqr wanda aka cirota daga qirjinsa aka wanketa. Abu guda daya tal a yanzun zaice yana damunsa,shima kuma tunda ya tsananta addu'a yaketa samun nutsuwa karsashi da kuma kyakkyawan tunani akan hanyoyin da zai magance komai. A hankali ya durqusa saman kanta,ya sanya hannuwansa duka biyun ya tattarota ya dagata cak zuwa girjinsa. Sosai ta firgita, saidai suna hada ido tayi laqwas, idanunta suna hada wasu sabbin hawayen, saita maidasu ta rufe tana jin,tana jin tsananin kunyar hada idanu dashi a yau din. Hawayen suka biyo gasan rufaffun idanunta,tana jin ya gama da ita,har ya sata ta sauka a layi,da wanne idon zata iya ci gaba da kallon shi?. Lumshe nasa idon yayi ya bude yana duban fuskarta dake qirjinsa,har cikin zuciyarsa yakejin ba dadi akan fitar hawayenta "Kina bugatar second round ne?" Ya fada qasa qasa. Rasa me zatace tayi,wato yama gama rainata gaba daya? sai kawai ta fashe da kukan sosal tana cewa "Allah sai na rama,Allah" "That's wonderful. . I like it, kice nayi kwanciyata za'a shayar dani da... .." Bai garasa fadi ba kalaman suka katse saboda cizon data sakar masa a qirjinsa. Tana jin shi kadai ne abinda zata iyayi ta rama abinda yayi matan. "Wash Allah...... maji zata jimin ciwo" ya furta yana sakinmurmushi sosai,karon farko da yayi murmushi ne cakude da dariya,yana jin wani shauqi yana dibansa. Sauri yayi ya kaita saman gadon yabi bayanta ya sanyata ta garfin tsiya a jikinsa ya kuma nannadesu da duvet, ya hanata dukkan wani motso,tun tana kici kici har ta sallama masa. *_Washegari* Tun da safen taji cikinta yayi wayam kamar bata taba sanya masa abinci ba,sai data leqo taji bataji motsinsa ba,don tun sallar asuba da ya fita ta maida key ta rufe,ta bude ta lallaba ta shige kitchen din. A gurguje ta dafa tea,ta soya qwai tayi toasting bread guda uku. Daga gaban kitchen cabinet din ta tsaya tana ci a gurguje,so take ta gama ta koma daki kafin ya risketa. Tana tsaka da ci tattausan gamshinsa yayi mata sallama,bata waiwaya ba don ta saddaqar shine, ta cusa bread din a bakinta tayi tsaye kawai tana jin takunsa. A nutse ya kamo qugunta ya manna da jikinsa,ya dora kansa a kafadarta ya sanya hannunsa ya jiyo da fuskarta ya zamana suna facing juna. Miskilin murmushin nan nasa dake da wuyar gani ya saki "Halan marowaciya ce ke ko?" Ya furta yana lullumshe mata ido, kamar wanda ke jin bacci. Bai jira tace komai ba ya kai bakinsa a nutse saman nata bakin. Bread din ya gutsira a tausashe, numfashinsa ya gauraye da nata,ya janye idanun a nutse yana tauna bread din, sai ya kama hannunta dake riqe da cup na tea din yakai bakinsa ya kurba a hankali. Kai ya jinjina,komai ta dafa yana da wani irin taste na daban da baya jinsa a ko ina. Ko daya hadiye dake gutsire sauran na bakinta yayi,sannu sannu sai gashi ya cinye mata bread din tas da tea din,ya saketa a nutse yana murmushi "Thanks for this beautiful breakfast,i love you" yayi maganar yana tafiya da baya da baya idanunsa a kanta kamar bazai janye ba. Har yakai qofa sannan ya juya da hanzari ya qarasa ficewa yana jin shauqi na ratsashi. A gurguje ta juya itama tana wucewa daki, ko ina cikin kanta na maimaita amsa kuwwar muryarsa cikin taushin nan nata da kalmarsa ta qarshe ta "| LOVE YOU" "He loves me?" Ta tambayi kanta tana tsaiwa gaban madubi tana duban fuskarta. Ta yaya zai fada sonta indai har da gaske ne? bayan dab take da kammala aikinta ta koma inda tafi wayo?, qwaqwalwarta ta daure tsam, daidai lokacin da kira ya shigo wayarta. Da sauri ta dauka tana komawa gefen gado, maji ce,kamar tasan kuwa a yau take shawarar kiranta,ta tabbatar itace hanya mafi sauqi da zata bi tayi tafiyarta a sirrance cikin kwanciyar hankali. Cikin kunya da nauyi ta daga kiran. Kamilar muryar maji din ta ziyarci kunnenta da kyakkyawar sallama "Ibnaty.....kaif einty" "Barka da warhaka maji" sãahar din ta fada tana murmushi cikin kunya matuqa,kunyar da sai a yanzu takejinta ta gasken,irin kunyar dake wanzuwa tsakanin suruka da surukarta "Barka kadai d'iyata,munyi waya da nadeeya tace kina sashenki,ina fatan komai lafiya,kuma komai yana tafiya cikin kiyayewar ubangiji ba tare da matsala ba?" "Komai lafiya alhamdulillah" "Nima ina gab da dawowa,wata matsala ce takeson faruwa fil usbu'il maadi(cikin satin da ya wuce) wala kin in sha Allah sa'arji'u ilaikum fi hazash shahr(saidai in sha Allah zan dawo gareku cikin wannan watan)" "Allah ya amince maji munyi kewarki, nahnu mushtaquna ilaiki(munyi kewarki)" murmushi ta saki cike da jin dadi "Wa'ana aidan yabnaty (nima haka d'iyata)" "Maji" ta kirata a sanyaye "Na'am diyata,me yake faruwa?" Ta fada kai tsaye saboda yanayin kiran da taji tayi mata "Akwai maganar da nakeso mui,nayi wani danyan hukunci ba tare da neman shawararki ba" "Karkiji komai diyata,nayi imanin ba zaki taba cutar da kowa nawa ba,saboda addu'ata a kanki take,kuma Allah ya zabar mana ke,na tabbatar in sha Allah ke da duk abinda zakizo mana dashi alkhairi ne,gayamin kanki tsaye, menene?" *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 40 "Na shirya tafiya da fadeela don yi mata aiki ta rabu da lalurar da take fama da ita a sirrance ba tare da ko mahaifinta va sani ba bare mutanen da muke rayuwa tare dasu ba" "Allahu akhbar " maji ta maimaita har sau uku "Kamar tare dake muke wanann tunanin? wannan shine abinda na shirya aiwatarwa na farko bayan na dawo Nigeria,na baki goyon baya alf bil alf(dari bisa dari)" "Amma maji, banason kowa ya sani saboda ina tsoron kada a sanya abun yaqi yiwuwa" kamilin murmushi maji ta saki "Fauziyya hajiya qarama,ko ba ita kike tsoron kada ta sanya moha ya hana ba?,ina da labarin yadda tayi ruwa tayi tsaki ta hana duk wata maganar da za'a tayar akan a yiwa fadeela aiki,na bar zancen ne akan cewa ni daya zan iya aiwatar da aikin, koda ita din bataso,saboda nasan duk inda takai ga girman kaidinta,bata isa ta sanya moha ya hanani ba.….....har yanzu bakisan me fauziyya ta yiwa rayuwata ba,zauna da kyau diyata yau na gaya miki labarin da masu shekaru irin naki dake rayuwa tare dani basu sani ba" a sanyaye sãahar ta gyara zamanta saman gadon sosai, tun kafin taji komai daga bakin maji jikinta ya sanyaya,ba abinda take haskowa sai fuskar hajiya qarama a sannan. * TUNA BAYA 1988 * Mummunar faduwa gabanta yayi,wani irin hargitsatsen kallo daya watsa mata shi ya sanyata cikin rudani, batasan me tayi masa banda kulle qofa da tafiya da key din,kallon daya watsa mata yafi qarfin wannan laifin, kallo ne na zallar qasqanci da kuma tsana,tasan dai ranar yau lafiya galau suka rabu,ya fita cike da murna zai karbo upper dinsa aiki ya samu,suna ta murna dukkansu tare da saka ran fita daga tsanani zuwa sauqi, sai dukka gwiwarta tayi sanyi da irin nau'in kallon da yake jefa mata. Kafin ta qaraso ainihin tsakar gidan sai wulgawar fauziyya ta gani, wadda kanta ke daure da bandeji da yayi tsatstsafar jini gaba daya daga samansa,ta nufeshi a gigice ta cukuikuyeshi tana neman mafaka a bayansa,bakinta na wani irin rawa na zallar toro da firgici take cewa "Na shiga uku akh, gata nan ta dawo,don Allah ka boyeni,kada ka bari ta qaraso,wallahi zata qarasa illatani kamar yadda taci alwashi" tayi maganar tana wani irin haki da tawar jiki, kamar wadda tayi gudun kwana da wuni. Baki kawai ta saki galala tana kallon fauziyya,qwaqwalwarta gaba daya ta rikice,me take nufi ne? saita maida dubanta ga bandejin kanta tana mamakin me ya sameta daga fitarta "Bata isa tayi miki komai ba,a yau qarshen al 'amarinta yazo, muguntarta a kanki kuma ta qare!" Muryarsa mai zurfi dake fita da amon fushi ta fusgi hankalinta, saita maida dubanta kansu gaba daya, kwanyarta na sake rikicewa da salon maganganunsu da ba ganewa takeyi ba. Ci gaba tayi da kallonsa, saidai ya zaro biron dake. gaban aljihunsa ya kuma dauko takarda a daya aljihun nasa,ya bude kan biron cikin fusata. Cikin mamaki me yawa taga fauziyya ta kama biron ta riqe gam "Me zakayi yaaya, ka rufamin asiri don Allah, kada kace zaka saketa saboda ni" ta fada hawaye na wanke mata fuska. "Ki saki fauziyya,duk mutumin da bayason jininka kaima baya qaunarka,ban ga amfanin zama da ita ba, baya ga tarin dimbin gori da maganganun data fada a kanmu" kuka sosai fauziyya keyi,ta kuma riqe abun rubutun taqi sakar masa tana bashi haquri, abinda yayi masifar daure tunanin SHIFA, me yasa fauziyyan dake burin afkuwar haka ita ke bada haqurin kada a saketa?. "Kinci darajarta,ki dubi abun kunya wanda kike quntatawa shine yayi silar kubutar dake daga afkuwar wani mummunan abu a kanki" mamaki ya sake kasheta,kanta ya daure tamau, tama kasa cewa komai baki sake take kallonsa har ya miqe ya nufi hanyar soron gidan,har yanzu zallar bacin ran dake saman fuskarsa bata gushe ba. Har yakai bakin qofar sai kuma ya dawo,ya tsaya gaban fauziyya dake zube tana kuka "Tashi ki wuce ciki". Bai barta ba har sai daya rakata cikin dakinta,ya dan jima ma a ciki kafin ya fito,zuwa sannan shifa ta ja jikinta da qyar ta wuce zuwa nata dakin clkin mawuyacin hali,tare da hasashen me yake ta faruwa da ita ne a rayuwarta haka? tun ranar da fauziyya ta sanya qafarta a gidan da nufin zama dasu,na wata shidda kawai ta samu kwanciyar hanakali bayan zuwan nata,daga bayan wannan watanni shidan bata sake samun sauqi ko salama ba. Duk wani farinciki nata ta warwareshi tasss ba tare da tasan meye dalilin da yasa taketa aikata hakan ba. A iya saninta,mahaifiyarsu mahmud macace mai kirkin gaske da kowa ke yabonta bayan rasuwarta, zamanta da fauziyya na watanni shidan nan,zama ne na kyautata mata da kula da ita,saboda tana mata kallon mahmud, mahmud kuwa ba zata manta da soyayyarsa a gareta ba, duk da cewa ba kowa cikin danginta ke son aurensu da shi ba, kasancewarsa shi din dan Nigeria ne, ita kuma 'yar Algeria ce, duk da shi dimma fari ne tas kalar yarensu da idan ba fada kayi ba za'a dauka Algerian ne shi dinma, kasancewar ya fita daga tsatson SHUWA-ARAB wanda asalinsu dama larabawan ne. Wani irin zama tayi cikin dakin cikin qunci da kukan zuci,da Muhammad da nadeeya kowa kuka yake, amma kusan hanakalinta yayi nisa a tunani,taji alamun kuke sukeyi,amma saboda tsanar tunani da damuwa bata farga da kukan da sukeyi ba,har sai da taga fadowar fauziyya dakin kamar wadda aka jeho. Kafin tayi kowanne irin tunani ta dauke nadeeya dake tsaye daga bayanta tana kiran sunanta ta hau jijjigata. Sallamar mahmud da shigowarsa cikin dakin shi ya ankarar da maji dalilin wannan shigowar ta fauziyya ta ba zata,iya saninta ko daya bata iya tayata wahalar yaran,zafi ko sanyi koda azumi akeyi ita zata yi korai dinta fauziyyan na daga kwance, saidai ta fito ta debi abincinta ta koma daki, idan ta gama sabgoginta kuma ta wanke jikinta tayi ficewarta unguwa,ba zata dawo ba sal ta daidaicin lokacin dawowar dan uwanta. Hannu yasa ya karbi nadeeyan, fauziyyan da ta sake tara wani qwallan ta dubi yaran "Ku tayani bawa maji dinku haquri, kada tayi fushi da ni,ni din marainiya ce,bani da kowa sai yayana sai ita da nake saka ran ta zamemin makwafin uwa" ta qarasa fada tana share qwallar munafurci. Gaba daya jinin jikin maji so yayi ya tsaya da harbawa,tabi fauziyya dake ci gaba da sharar qwalla da kallo "Ni kadai na isa na tsaya miki, jeki abinki" mahmud ya fada yana miqa mata leda daya da ya shigo da ita ta takeaway. Har qasa ta durqusa ta saka hannu biyu ta karba tayi masa godiya tana fita. Wani kallo ya juyo ya watsawa maji, ba komai idanunsa face zallar bacin rai da har yanzu bai gushe ba "Yau na gani da ido na,ansha gayamin yadda yake wulaqantar da yaran nan,hatta a wajen aiki ba wata Kulawar kirki suke samu ba,saboda baqin hali tun daga waje nake jiyo kukansu amma kin gaza rarrashinsu,to daga rana irin ta yau na soke batun aikinki, ki zauna a gida ki kulamin da yarana da 'yar uwata" yayi maganar yana kamo toufeeq,ya zaunar dashi gefansa nadeeya na saman cinyarsa,ya bude musu daya takeaway din ya fara basu. Har yanzu jin komai take kamar a mafarki,sai a lokacin ta samu qwarin gwiwar waiwayawa gareshi "Allah S W T cewa yayi,yaku wadanda kukayi imani,idan fasiqi yazo muku da labari kuyi bincike a kansa kada ku afkawa wasu mutane cikin rashin sani da jahilci saiku wayi gari kuna masu nadama akan abinda kuka aikata. Wannan kenan kayi tunani akai,sannan meye hadin matsalar nan da maganar fitata aiki mahmud?" A harzuqe yake kallonta "Waye jahilin kenan? ‚ni ko 'yaruwata?,ki gayamin?. Ta tabbata kin rainanin d gaske, rainin da ake cewa kinyimin ban sake tabbatarwa ba sai a yanzun,illar mace ta dinga taimaka kenan,koda bakai ka buqata ba wataran sai irin wannan ta gifta a tsakaninku,Allah yasa ba ahaka kika aureni ba da na shiga uku wallahi wallahi, aiki kin daina yinsa,sannan duk wani abu da kikasan kin tallafamin da shi ki zauna ki rubuta daga yau zuwa gobe,tsinke kada ki dagamin qafa,zan maida miki abinki" qas tayi da kanta,hawayen da tun dazu basu zuba ba yanzu suke zuba,maganar da ya gaya mata yanzu tafi zancan barinta aiki ciwo,duk wani fadi tashin rufa musu asiri da takeyi bayan karayar arziqinsa,dai dai da rana daya bata taba jin ta qosa ko ya dameta ba, amma yau da wadan nan kalaman zai saka mata?,komai da tayi musu tayi masa ne saboda tana ganin ya cancanci fiye da haka,namiji ne shi me bala'in kulawa da gida da matarsa,sanda yake dashi babu abinda baiyi mata ba,a lokacin duniya tana kwance, fauziyya bata shigo rayuwarsu ba,sai lokacin ta tuna da kalaman haiia mahaifiyarsu,a duk sanda sukaje borno ba zata dawo ba ba tare da hajjan tayi gorafin fauziyya ba "Fauziyya, fauziyya,Allah ya shiryamin dai kawai" ba yawan zama take dasu ba,shi yasa a lokacin ba zatace • ga wani hali nata ba,hakanan ba zatace ga abinda ta taba yi mata maras dadi ba,ashe ita din kara da kiyashi ce daukan mara sani. Ranar har ta kwanta bata sanyawa cikinta komai ba sai bacin rai da taketa kurba da dogon tunanin ta inda zata kamo bakin zaren. Bayan sallar isha'i tana jinsa shida yara a dakin fauziyyan sunata hirarsu abinsu,kamar ma bata a cikin gidan. Sanda yaran sukayi bacci ya kawo mata su ya shimfide mata su ya juya abinsa ya fice. Kasa haquri tayi,bayan awa daya ta shirya ta miqe ta bishi dakinsa. Tunda ya amsa sallamarta bai sake daga kai ya dubeta ba,gabansa ta tsugunna cikin sanyi da mutuwar jiki "Ya kamata mu warware sabanin da yake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa,bai kamata mu fara yin abinda bamu saba dashi ba" har ta gama maganarta baice ci kanki ba,hasalima shirin bacci ya tashi ya fara yi daya kammala ya haye gadonsa ya kwanta yana fadin "Idan kin gama ki rufemin qofata" yaja bargo ya lullube har saman kansa. A ranar shifa tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi, meye da meye wai fauziyya ta gaya masa haka me zafi? wannan iri fushin koda mahaifiyarsa ta tsinewa albarka ai iyaka kenan. Washegari saboda bata samu bacci da wuri ba ta makara bata tashi da wuri ba,tana tsaka da baccinta ta dinga jiyo qamshi cikin hancinta,sai ta farka tana salati ganin ta makara,ta shiga toilet tayi brush ta fito tana qoqarin kama ayyukanta na gida,don ko ciwo takeyi babu mataimaki,haka zata rarrafa tayi ayyukan nata, Muhammad na taimaka mata da dauko wannan ajjiye,duk da shekarunsa ba wani kaiwa sukayi ba. Mamaki ne ya kusa kasheta,don fauziyya ta gyare gidan fes an kintsashi,hatta da yaran tayi musu wanka,hakanan ta kammala breakfast tana ta shiryawa a cooler da take zubawa mahmud abinci, yara nata tsalle hannunsu daya chips daya soyayyan qwai,shi kansa qwai din da chips din batasan ina aka samoshi ba,saboda tasan duk kayan abincin data siya musu wancan watan sun qare. Jiki a sanyaye ta qarasa shiga kitchen din,suka hada ido da fauziyyan tana rufe cooler din,sai ta sakar mata murmushi "Barka da tashi matar yaaya,nasan tun jiya akwai tambayoyi fal kanki ko?,to yanzun kina da minti talatin zuwa arba'in da zakiyi kowacce tambaya taki zan baki amsarta,saboda yaayan ya fita yomin cefane, zan iya saurarenki kafin ya dawo" kaman majin zata ce wani abun sai ta dauke kanta daga dubanta, dariya ta saki tana cewa "Bari to na taimakeki na rage miki wasu amsoshin tambayoyin…..nasan kin shiga kogin tunanin meye dalili na na hana yaaya ya sakeki ko? ‚nayi hakanne saboda banason tafiyarki yanzu,nafison saikin gasu yadda ya kamata, idanunki kuma sun gane miki girman matsayina a wajensa da kuma qarfin izzata,ta yadda zaki rayu kina bada labari a duk inda kika zauna" *HUGUMA* * _TABARMAR KASHI *®️ Book 02 Page 39 Fargaba ce ta cika zuciyarta lokaci guda cike da nadamar sanya rigar jikinta,tare da zama da tayi cikin dakin a haka. Wata silk nightgown ce a jikin nata wadda take bayyana shatin komai dake jikin nata,hatta da pant dinta kuwa hakan siffar albarkatun qirjinta da ya bayyana sosai, wanda yake tsaye qyam a cike. Danna wayarta ta soma yi tana amsa sallamar,ita kanta batasan inda take shiga cikin wayar tata ba saboda a mugun rude take. Da qyar ya fusgi numfashinsa yana runtse ido "She's killing me"ya furta a sarari amma kamar wanda baya so a jishi. Gaba daya jikinsa ya amsa,ya qarasa a sanyaye ya zube wayoyinsa da key dinsa saman bedside drawer. A nutse ya miqe yana nade hannun pyjamas dinsa, idanunsa all over her body. Duk yadda yake zaton zai iya jurewa,zai kuma iya controlling kansa yaji ya gaza,bazai iya din ba,step din da yakeson ya fara bi na shaquwa da ita da kuma Koya mata bacci cikin jikinsa kafin komai yaci gaba da wanzuwa a tsakaninsu sai yaji yana rushewa daya bayan daya. Daga inda yake tsayen yana qare mata kallon qurilla, ya karanci yadda qirjinta dake jan hankalinsa matuga da gaske yadda yake dagawa, abinda ke alamta masa cewa bugun zuciyarta ne ya qaru,sai ya sauke hannunsa ya fara takawa gareta cikin nutsuwa da kamewa. Bayanta ya koma ya tsaya, abinda ya bashi damar ganin dukiyar fulaninta sosai,cikin hanzari ya lumshe idonsa numfashinsa na fara sauyawa,yana jin yadda jini ya harba da sauri cikin jijiyoyin jikinsa "Ya Allah,ya assalam" ya furta,a hankali ya dafe batan kujerar da take kai da gwiwoyin hannunsa wanann ya kawo mugun kusanci a tsakaninsu,sabida gaba daya fuskarsa sauka tayi jikin dogon wuyanta dake sanye da wani chain me kyau wanda ya zama ado ga wuyan nata. Tsigar jikinta ta zuba sanda ya zura yatsantsa guda daya yana qoqarin kamo chain din "You are the hottest women in this planet" ya fada with slow and cool voice cikin tsakiyar kunnenta. Yadda ta zabura da jin kalamansa dake son kassara duk wata laaka ta jikinta tayi nufin zamewa tabar gurin,haka yayi wani tsallae guda daya ya haura ta saman kujerar dai gashi a kusa da ita cinyoyinsu na gogar juna. Sau daya tak ta kalli idonsa ta janye dubanta daga kansa, daga shigowarsa kadai zuwa tsaiwarsa a bayanta ya birkice gaba daya. Tattausan tafin hannunsa ya wuyanta daga gasan habarta.va kamo bakinta sosai vana masa wani irin narkakken kallo,kamar idanun mutumin da yasha wani abun maye ya bugu,ko kuma matsanancin bacci ke shirin rinjayarsa ya qara kusancin dake tsakaninsu sosai har sai da suka fara musayar numfashi a tsakaninsu,duk iskar data fita daga hancinta kai tsaye yake zuqeta,hakanan kowanne numfashi nasa hancinta yake sauka. "You look so sexy" ya fada yana fincikota cikin jikinsa saboda kwadayin jin dumin jikinta daya saukar masa. Da kyau ya rigeta,ya sanya harshensa a kunnenta cikin nutsuwa, abinda ya sanya ta qanqameshi ba tare da tayi niyyar aikata hakan ba. Jin abinda tayin ya sanyashi sakin murmushi ya kuma zare harshen nasa, saidai cikin kunnen nata ya saka rada mata "Let me see if you taste as good as you look" kaman giftawar walqiya ya dagata cak,bai direta ko ina ba sai dakinsa,saboda yanason yayi Linking past memory dinsu yayi renewing dinsa da wannan sabon,yana matuqar debe masa kewa da sakashi cikin wani yanayi da shi kansa baisan ana shiga irinsa da tunani kawai ba. Zuwa lokacin ta fara goqarin qwatar kanta tana kuma hawaye,qaramin murmushi ya saki,ya kama hannuwanta dake qoqarin tureshin ya riqesu sosai cikin nasa "Am sorry, bazan iya haqura ba,but i promise you,it will be sweetest thing da kika taba ji more than yadda kikaji rannan i promise" Daga wannan sai ya shiga lashe kowanne hawaye dake saman fuskarta. In a romantic way ya fara tattare rigarta, dame rigar tayi tana girgiza masa kai, saboda gaba daya ya kashe mata bakinta. Wani marayan murmushi ya sakar mata "Kinaso ki bani wahala SAHR?,bana gane komai fa zuwa yanzu" ya fada mata cikin mugun karyar da kai da sarewa,da kuma wani mugun duka da lahanin da shauginta da qaunarta me zafi suka yi masa. Zare idanunsa yayi daga nata,sabida bayason ta sanyashi ya karaya,yanason yaci gaba da tabbatar mata da cewa ita din tashi ce, don haka ya daidaici tsakiyar rigar ya tsargeta biyu kowanne sashe yayi gefe daban,take ya garasa haukacewa,saidai cikin ruhinsa ya gama yiwa kansa alqawarin itama yau saita dandana abinda yake dandana,sai ya sanyata ta sauka daga layi kafin komai ya shiga tsakaninsu. Cikin qasa da minti goma sha biyar ya sauketa tsaf daga kan layi,tun tana turjiya tare da qoqarin tureshi har jikinta ya fara saki yana amsar sagonnin da yake bata,kafin zuwa wani lokaci gaba daya ya samu yadda yakeso,ta sakar masa ragama gama daya,itama kuma ya aike da tunaninta can wata duniya me nisa qwarai. Sai da komai ya kammala sannan bacin rai da kunya suka addabeta,ta cusa kanta qasan pillow tana sakin wani siririn kuka,kukan takaici da baqincikin yadda ya yaudareta ta sake masa jiki har haka,harda tayashi wasu abubuwan,bata manta yadda ta riqe harshensa da kyau cikin bakinta,sanda yake gogarin janye bakin sai tasa hannuwanta ta rige kansa sosai yadda bazai subuce mata ba,shi kuma yaci gaba da biye mata. dai dai yayi saman gadon yana jin wani nishadi yana ratsashi tako ina,zuciyarsa fes tamkar farar takarda,kukanta a yau sai yake jinsa yana masa dadi cikin kunnuwansa,saboda dai dai suke da kukan shagwaba cikin qirjinsa. Idan ya tuna yadda tayi participating a wasu abubuwan sai yaji kamar ya dawo da mintunan baya ya sake moresu. Duk yadda yaso ya lallasheta amma taqi saurarensa,har yayi wanka ya dawo taba qududune tana kukan takaicin kanta da kanta "Na zubda ajina" take gayawa kanta da kanta. Yasan idanma yace ta tashi tayi wanka wani batu ne na daban,wannan yasanya bai tsaya ko bi ta kanta ba,ya nade hannun rigarsa sumarsa jige da damshin ruwa,ya tsugunna ya sunkuceta gaba daya. Comforter ta riqo a gigice tana kare jikinta tare da sakin wani hawayen "Ka saukeni Allah, Allah bazan yarda ba, Allah kuwa,bazan yarda ba, tunda ka karya yarjejeniya" murmushi ya sakar yasa tsinin hancinsa saman nata ya gogasu guri guda idanunsa a lumshe "Keep quiet babe,i also break my rules for you" ya fada softly,sai kawai ji tayi ya tsundumata cikin bathtub. Ko daya bai saurareta ba,sai data dinga masa magiya tana hawaye sannan yabar mata toilet din. Sanda ta fito kamar surukarsa haka ta koma, kaya ta diba ta koma toilet ta saka sannan ta dawo,har yanzu hawaye takeyi. Sofa bed ta koma ta cure guri daya,yana zaune daga gefan gadon yana addu'o'in bacci ta gasan idanunsa yake qare mata kallo. Tun yana jin motsinta a hankali har yaji shiru,hakan ne ya bashi alamar cewa bacci ya dauketa. A nutse ya miqe ya isa gareta, tsaye yayi a kanta,hannuwansa zube a qirjinsa yana qare mata kallo,wani sassanyan murmushi ne yake fita daga kan fuskarsa,yana jin zuciyarsa kamqr wanda aka cirota daga qirjinsa aka wanketa. Abu guda daya tal a yanzun zaice yana damunsa,shima kuma tunda ya tsananta addu'a yaketa samun nutsuwa karsashi da kuma kyakkyawan tunani akan hanyoyin da zai magance komai. A hankali ya durqusa saman kanta,ya sanya hannuwansa duka biyun ya tattarota ya dagata cak zuwa girjinsa. Sosai ta firgita, saidai suna hada ido tayi laqwas, idanunta suna hada wasu sabbin hawayen, saita maidasu ta rufe tana jin,tana jin tsananin kunyar hada idanu dashi a yau din. Hawayen suka biyo gasan rufaffun idanunta,tana jin ya gama da ita,har ya sata ta sauka a layi,da wanne idon zata iya ci gaba da kallon shi?. Lumshe nasa idon yayi ya bude yana duban fuskarta dake qirjinsa,har cikin zuciyarsa yakejin ba dadi akan fitar hawayenta "Kina bugatar second round ne?" Ya fada qasa qasa. Rasa me zatace tayi,wato yama gama rainata gaba daya? sai kawai ta fashe da kukan sosal tana cewa "Allah sai na rama,Allah" "That's wonderful. . I like it, kice nayi kwanciyata za'a shayar dani da... .." Bai garasa fadi ba kalaman suka katse saboda cizon data sakar masa a qirjinsa. Tana jin shi kadai ne abinda zata iyayi ta rama abinda yayi matan. "Wash Allah...... maji zata jimin ciwo" ya furta yana sakinmurmushi sosai,karon farko da yayi murmushi ne cakude da dariya,yana jin wani shauqi yana dibansa. Sauri yayi ya kaita saman gadon yabi bayanta ya sanyata ta garfin tsiya a jikinsa ya kuma nannadesu da duvet, ya hanata dukkan wani motso,tun tana kici kici har ta sallama masa. *_Washegari* Tun da safen taji cikinta yayi wayam kamar bata taba sanya masa abinci ba,sai data leqo taji bataji motsinsa ba,don tun sallar asuba da ya fita ta maida key ta rufe,ta bude ta lallaba ta shige kitchen din. A gurguje ta dafa tea,ta soya qwai tayi toasting bread guda uku. Daga gaban kitchen cabinet din ta tsaya tana ci a gurguje,so take ta gama ta koma daki kafin ya risketa. Tana tsaka da ci tattausan gamshinsa yayi mata sallama,bata waiwaya ba don ta saddaqar shine, ta cusa bread din a bakinta tayi tsaye kawai tana jin takunsa. A nutse ya kamo qugunta ya manna da jikinsa,ya dora kansa a kafadarta ya sanya hannunsa ya jiyo da fuskarta ya zamana suna facing juna. Miskilin murmushin nan nasa dake da wuyar gani ya saki "Halan marowaciya ce ke ko?" Ya furta yana lullumshe mata ido, kamar wanda ke jin bacci. Bai jira tace komai ba ya kai bakinsa a nutse saman nata bakin. Bread din ya gutsira a tausashe, numfashinsa ya gauraye da nata,ya janye idanun a nutse yana tauna bread din, sai ya kama hannunta dake riqe da cup na tea din yakai bakinsa ya kurba a hankali. Kai ya jinjina,komai ta dafa yana da wani irin taste na daban da baya jinsa a ko ina. Ko daya hadiye dake gutsire sauran na bakinta yayi,sannu sannu sai gashi ya cinye mata bread din tas da tea din,ya saketa a nutse yana murmushi "Thanks for this beautiful breakfast,i love you" yayi maganar yana tafiya da baya da baya idanunsa a kanta kamar bazai janye ba. Har yakai qofa sannan ya juya da hanzari ya qarasa ficewa yana jin shauqi na ratsashi. A gurguje ta juya itama tana wucewa daki, ko ina cikin kanta na maimaita amsa kuwwar muryarsa cikin taushin nan nata da kalmarsa ta qarshe ta "| LOVE YOU" "He loves me?" Ta tambayi kanta tana tsaiwa gaban madubi tana duban fuskarta. Ta yaya zai fada sonta indai har da gaske ne? bayan dab take da kammala aikinta ta koma inda tafi wayo?, qwaqwalwarta ta daure tsam, daidai lokacin da kira ya shigo wayarta. Da sauri ta dauka tana komawa gefen gado, maji ce,kamar tasan kuwa a yau take shawarar kiranta,ta tabbatar itace hanya mafi sauqi da zata bi tayi tafiyarta a sirrance cikin kwanciyar hankali. Cikin kunya da nauyi ta daga kiran. Kamilar muryar maji din ta ziyarci kunnenta da kyakkyawar sallama "Ibnaty.....kaif einty" "Barka da warhaka maji" sãahar din ta fada tana murmushi cikin kunya matuqa,kunyar da sai a yanzu takejinta ta gasken,irin kunyar dake wanzuwa tsakanin suruka da surukarta "Barka kadai d'iyata,munyi waya da nadeeya tace kina sashenki,ina fatan komai lafiya,kuma komai yana tafiya cikin kiyayewar ubangiji ba tare da matsala ba?" "Komai lafiya alhamdulillah" "Nima ina gab da dawowa,wata matsala ce takeson faruwa fil usbu'il maadi(cikin satin da ya wuce) wala kin in sha Allah sa'arji'u ilaikum fi hazash shahr(saidai in sha Allah zan dawo gareku cikin wannan watan)" "Allah ya amince maji munyi kewarki, nahnu mushtaquna ilaiki(munyi kewarki)" murmushi ta saki cike da jin dadi "Wa'ana aidan yabnaty (nima haka d'iyata)" "Maji" ta kirata a sanyaye "Na'am diyata,me yake faruwa?" Ta fada kai tsaye saboda yanayin kiran da taji tayi mata "Akwai maganar da nakeso mui,nayi wani danyan hukunci ba tare da neman shawararki ba" "Karkiji komai diyata,nayi imanin ba zaki taba cutar da kowa nawa ba,saboda addu'ata a kanki take,kuma Allah ya zabar mana ke,na tabbatar in sha Allah ke da duk abinda zakizo mana dashi alkhairi ne,gayamin kanki tsaye, menene?" *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 40 "Na shirya tafiya da fadeela don yi mata aiki ta rabu da lalurar da take fama da ita a sirrance ba tare da ko mahaifinta va sani ba bare mutanen da muke rayuwa tare dasu ba" "Allahu akhbar " maji ta maimaita har sau uku "Kamar tare dake muke wanann tunanin? wannan shine abinda na shirya aiwatarwa na farko bayan na dawo Nigeria,na baki goyon baya alf bil alf(dari bisa dari)" "Amma maji, banason kowa ya sani saboda ina tsoron kada a sanya abun yaqi yiwuwa" kamilin murmushi maji ta saki "Fauziyya hajiya qarama,ko ba ita kike tsoron kada ta sanya moha ya hana ba?,ina da labarin yadda tayi ruwa tayi tsaki ta hana duk wata maganar da za'a tayar akan a yiwa fadeela aiki,na bar zancen ne akan cewa ni daya zan iya aiwatar da aikin, koda ita din bataso,saboda nasan duk inda takai ga girman kaidinta,bata isa ta sanya moha ya hanani ba.….....har yanzu bakisan me fauziyya ta yiwa rayuwata ba,zauna da kyau diyata yau na gaya miki labarin da masu shekaru irin naki dake rayuwa tare dani basu sani ba" a sanyaye sãahar ta gyara zamanta saman gadon sosai, tun kafin taji komai daga bakin maji jikinta ya sanyaya,ba abinda take haskowa sai fuskar hajiya qarama a sannan. * TUNA BAYA 1988 * Mummunar faduwa gabanta yayi,wani irin hargitsatsen kallo daya watsa mata shi ya sanyata cikin rudani, batasan me tayi masa banda kulle qofa da tafiya da key din,kallon daya watsa mata yafi qarfin wannan laifin, kallo ne na zallar qasqanci da kuma tsana,tasan dai ranar yau lafiya galau suka rabu,ya fita cike da murna zai karbo upper dinsa aiki ya samu,suna ta murna dukkansu tare da saka ran fita daga tsanani zuwa sauqi, sai dukka gwiwarta tayi sanyi da irin nau'in kallon da yake jefa mata. Kafin ta qaraso ainihin tsakar gidan sai wulgawar fauziyya ta gani, wadda kanta ke daure da bandeji da yayi tsatstsafar jini gaba daya daga samansa,ta nufeshi a gigice ta cukuikuyeshi tana neman mafaka a bayansa,bakinta na wani irin rawa na zallar toro da firgici take cewa "Na shiga uku akh, gata nan ta dawo,don Allah ka boyeni,kada ka bari ta qaraso,wallahi zata qarasa illatani kamar yadda taci alwashi" tayi maganar tana wani irin haki da tawar jiki, kamar wadda tayi gudun kwana da wuni. Baki kawai ta saki galala tana kallon fauziyya,qwaqwalwarta gaba daya ta rikice,me take nufi ne? saita maida dubanta ga bandejin kanta tana mamakin me ya sameta daga fitarta "Bata isa tayi miki komai ba,a yau qarshen al 'amarinta yazo, muguntarta a kanki kuma ta qare!" Muryarsa mai zurfi dake fita da amon fushi ta fusgi hankalinta, saita maida dubanta kansu gaba daya, kwanyarta na sake rikicewa da salon maganganunsu da ba ganewa takeyi ba. Ci gaba tayi da kallonsa, saidai ya zaro biron dake. gaban aljihunsa ya kuma dauko takarda a daya aljihun nasa,ya bude kan biron cikin fusata. Cikin mamaki me yawa taga fauziyya ta kama biron ta riqe gam "Me zakayi yaaya, ka rufamin asiri don Allah, kada kace zaka saketa saboda ni" ta fada hawaye na wanke mata fuska. "Ki saki fauziyya,duk mutumin da bayason jininka kaima baya qaunarka,ban ga amfanin zama da ita ba, baya ga tarin dimbin gori da maganganun data fada a kanmu" kuka sosai fauziyya keyi,ta kuma riqe abun rubutun taqi sakar masa tana bashi haquri, abinda yayi masifar daure tunanin SHIFA, me yasa fauziyyan dake burin afkuwar haka ita ke bada haqurin kada a saketa?. "Kinci darajarta,ki dubi abun kunya wanda kike quntatawa shine yayi silar kubutar dake daga afkuwar wani mummunan abu a kanki" mamaki ya sake kasheta,kanta ya daure tamau, tama kasa cewa komai baki sake take kallonsa har ya miqe ya nufi hanyar soron gidan,har yanzu zallar bacin ran dake saman fuskarsa bata gushe ba. Har yakai bakin qofar sai kuma ya dawo,ya tsaya gaban fauziyya dake zube tana kuka "Tashi ki wuce ciki". Bai barta ba har sai daya rakata cikin dakinta,ya dan jima ma a ciki kafin ya fito,zuwa sannan shifa ta ja jikinta da qyar ta wuce zuwa nata dakin clkin mawuyacin hali,tare da hasashen me yake ta faruwa da ita ne a rayuwarta haka? tun ranar da fauziyya ta sanya qafarta a gidan da nufin zama dasu,na wata shidda kawai ta samu kwanciyar hanakali bayan zuwan nata,daga bayan wannan watanni shidan bata sake samun sauqi ko salama ba. Duk wani farinciki nata ta warwareshi tasss ba tare da tasan meye dalilin da yasa taketa aikata hakan ba. A iya saninta,mahaifiyarsu mahmud macace mai kirkin gaske da kowa ke yabonta bayan rasuwarta, zamanta da fauziyya na watanni shidan nan,zama ne na kyautata mata da kula da ita,saboda tana mata kallon mahmud, mahmud kuwa ba zata manta da soyayyarsa a gareta ba, duk da cewa ba kowa cikin danginta ke son aurensu da shi ba, kasancewarsa shi din dan Nigeria ne, ita kuma 'yar Algeria ce, duk da shi dimma fari ne tas kalar yarensu da idan ba fada kayi ba za'a dauka Algerian ne shi dinma, kasancewar ya fita daga tsatson SHUWA-ARAB wanda asalinsu dama larabawan ne. Wani irin zama tayi cikin dakin cikin qunci da kukan zuci,da Muhammad da nadeeya kowa kuka yake, amma kusan hanakalinta yayi nisa a tunani,taji alamun kuke sukeyi,amma saboda tsanar tunani da damuwa bata farga da kukan da sukeyi ba,har sai da taga fadowar fauziyya dakin kamar wadda aka jeho. Kafin tayi kowanne irin tunani ta dauke nadeeya dake tsaye daga bayanta tana kiran sunanta ta hau jijjigata. Sallamar mahmud da shigowarsa cikin dakin shi ya ankarar da maji dalilin wannan shigowar ta fauziyya ta ba zata,iya saninta ko daya bata iya tayata wahalar yaran,zafi ko sanyi koda azumi akeyi ita zata yi korai dinta fauziyyan na daga kwance, saidai ta fito ta debi abincinta ta koma daki, idan ta gama sabgoginta kuma ta wanke jikinta tayi ficewarta unguwa,ba zata dawo ba sal ta daidaicin lokacin dawowar dan uwanta. Hannu yasa ya karbi nadeeyan, fauziyyan da ta sake tara wani qwallan ta dubi yaran "Ku tayani bawa maji dinku haquri, kada tayi fushi da ni,ni din marainiya ce,bani da kowa sai yayana sai ita da nake saka ran ta zamemin makwafin uwa" ta qarasa fada tana share qwallar munafurci. Gaba daya jinin jikin maji so yayi ya tsaya da harbawa,tabi fauziyya dake ci gaba da sharar qwalla da kallo "Ni kadai na isa na tsaya miki, jeki abinki" mahmud ya fada yana miqa mata leda daya da ya shigo da ita ta takeaway. Har qasa ta durqusa ta saka hannu biyu ta karba tayi masa godiya tana fita. Wani kallo ya juyo ya watsawa maji, ba komai idanunsa face zallar bacin rai da har yanzu bai gushe ba "Yau na gani da ido na,ansha gayamin yadda yake wulaqantar da yaran nan,hatta a wajen aiki ba wata Kulawar kirki suke samu ba,saboda baqin hali tun daga waje nake jiyo kukansu amma kin gaza rarrashinsu,to daga rana irin ta yau na soke batun aikinki, ki zauna a gida ki kulamin da yarana da 'yar uwata" yayi maganar yana kamo toufeeq,ya zaunar dashi gefansa nadeeya na saman cinyarsa,ya bude musu daya takeaway din ya fara basu. Har yanzu jin komai take kamar a mafarki,sai a lokacin ta samu qwarin gwiwar waiwayawa gareshi "Allah S W T cewa yayi,yaku wadanda kukayi imani,idan fasiqi yazo muku da labari kuyi bincike a kansa kada ku afkawa wasu mutane cikin rashin sani da jahilci saiku wayi gari kuna masu nadama akan abinda kuka aikata. Wannan kenan kayi tunani akai,sannan meye hadin matsalar nan da maganar fitata aiki mahmud?" A harzuqe yake kallonta "Waye jahilin kenan? ‚ni ko 'yaruwata?,ki gayamin?. Ta tabbata kin rainanin d gaske, rainin da ake cewa kinyimin ban sake tabbatarwa ba sai a yanzun,illar mace ta dinga taimaka kenan,koda bakai ka buqata ba wataran sai irin wannan ta gifta a tsakaninku,Allah yasa ba ahaka kika aureni ba da na shiga uku wallahi wallahi, aiki kin daina yinsa,sannan duk wani abu da kikasan kin tallafamin da shi ki zauna ki rubuta daga yau zuwa gobe,tsinke kada ki dagamin qafa,zan maida miki abinki" qas tayi da kanta,hawayen da tun dazu basu zuba ba yanzu suke zuba,maganar da ya gaya mata yanzu tafi zancan barinta aiki ciwo,duk wani fadi tashin rufa musu asiri da takeyi bayan karayar arziqinsa,dai dai da rana daya bata taba jin ta qosa ko ya dameta ba, amma yau da wadan nan kalaman zai saka mata?,komai da tayi musu tayi masa ne saboda tana ganin ya cancanci fiye da haka,namiji ne shi me bala'in kulawa da gida da matarsa,sanda yake dashi babu abinda baiyi mata ba,a lokacin duniya tana kwance, fauziyya bata shigo rayuwarsu ba,sai lokacin ta tuna da kalaman haiia mahaifiyarsu,a duk sanda sukaje borno ba zata dawo ba ba tare da hajjan tayi gorafin fauziyya ba "Fauziyya, fauziyya,Allah ya shiryamin dai kawai" ba yawan zama take dasu ba,shi yasa a lokacin ba zatace • ga wani hali nata ba,hakanan ba zatace ga abinda ta taba yi mata maras dadi ba,ashe ita din kara da kiyashi ce daukan mara sani. Ranar har ta kwanta bata sanyawa cikinta komai ba sai bacin rai da taketa kurba da dogon tunanin ta inda zata kamo bakin zaren. Bayan sallar isha'i tana jinsa shida yara a dakin fauziyyan sunata hirarsu abinsu,kamar ma bata a cikin gidan. Sanda yaran sukayi bacci ya kawo mata su ya shimfide mata su ya juya abinsa ya fice. Kasa haquri tayi,bayan awa daya ta shirya ta miqe ta bishi dakinsa. Tunda ya amsa sallamarta bai sake daga kai ya dubeta ba,gabansa ta tsugunna cikin sanyi da mutuwar jiki "Ya kamata mu warware sabanin da yake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa,bai kamata mu fara yin abinda bamu saba dashi ba" har ta gama maganarta baice ci kanki ba,hasalima shirin bacci ya tashi ya fara yi daya kammala ya haye gadonsa ya kwanta yana fadin "Idan kin gama ki rufemin qofata" yaja bargo ya lullube har saman kansa. A ranar shifa tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi, meye da meye wai fauziyya ta gaya masa haka me zafi? wannan iri fushin koda mahaifiyarsa ta tsinewa albarka ai iyaka kenan. Washegari saboda bata samu bacci da wuri ba ta makara bata tashi da wuri ba,tana tsaka da baccinta ta dinga jiyo qamshi cikin hancinta,sai ta farka tana salati ganin ta makara,ta shiga toilet tayi brush ta fito tana qoqarin kama ayyukanta na gida,don ko ciwo takeyi babu mataimaki,haka zata rarrafa tayi ayyukan nata, Muhammad na taimaka mata da dauko wannan ajjiye,duk da shekarunsa ba wani kaiwa sukayi ba. Mamaki ne ya kusa kasheta,don fauziyya ta gyare gidan fes an kintsashi,hatta da yaran tayi musu wanka,hakanan ta kammala breakfast tana ta shiryawa a cooler da take zubawa mahmud abinci, yara nata tsalle hannunsu daya chips daya soyayyan qwai,shi kansa qwai din da chips din batasan ina aka samoshi ba,saboda tasan duk kayan abincin data siya musu wancan watan sun qare. Jiki a sanyaye ta qarasa shiga kitchen din,suka hada ido da fauziyyan tana rufe cooler din,sai ta sakar mata murmushi "Barka da tashi matar yaaya,nasan tun jiya akwai tambayoyi fal kanki ko?,to yanzun kina da minti talatin zuwa arba'in da zakiyi kowacce tambaya taki zan baki amsarta,saboda yaayan ya fita yomin cefane, zan iya saurarenki kafin ya dawo" kaman majin zata ce wani abun sai ta dauke kanta daga dubanta, dariya ta saki tana cewa "Bari to na taimakeki na rage miki wasu amsoshin tambayoyin…..nasan kin shiga kogin tunanin meye dalili na na hana yaaya ya sakeki ko? ‚nayi hakanne saboda banason tafiyarki yanzu,nafison saikin gasu yadda ya kamata, idanunki kuma sun gane miki girman matsayina a wajensa da kuma qarfin izzata,ta yadda zaki rayu kina bada labari a duk inda kika zauna" *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 41 Sosai zuciyar maji tayi wani irin nauyi,girman kaidai da dabi'ar fauziyya maras kyau tana ratsata,saidai kuma ta tuna da wata magana guda daya na cewa MURMUSHINKA GUDA DAYA TAK NA IYA SANYA FADUWAR GABA GA MAQIYINKA don haka fa waiwayo tana dubanta da murmushi saman fuskarta "Kin riga da kin makara,saboda bana tunanin lokacin da za'a rubuta littafin qaddarata kina gurin,na tabbatar da cewa kedin baki da matsayi a wajen Allah da kike da qarfin ikon canza qaddarata,na rigaki tsayawa a gaban Allah,na kuma rigaki ambatonsa" dariya fauziyya ta saki "To sannu sufiya". Kasa ci gaba da tsaiwa maji tayi a kitchen din,ta juya ta fice a hankali, zuciyarta cike da mamakin wanne abu ta aikatawa fauziyya haka data cancanci irin wannan sakamakon?. Ranar hatta da yaran basu wuni gurinta ba,sun wuni gurin fauziyya ne tana nan nan da su, sakamakon a ranar mahmud yana gida,saidai yadan fita ya dawo. Fauziyya ita tayi girkin rana da dare, kamar yadda tayi girkin dare,a lokacin idan ka shigo gidan zakayi tsammanin itace matar gidan idan ba kasan cewa matar gidan shifa bace. Tana daga daki tana sauraren dabdalarsu, yadda suka wuni suka kai kawo haka ta wuni kwance a daki. Sai bayan magariba lokacin da mahmud din yake zaune a parlor suna kallo da yara fauziyya ta shirya komai saman tray ta shigo dashi falon "Yaaya,don Allah kayi magana da maji,tayi haquri ta tashi taci abinci, yau duka bataci komai ba" dubanta yayi yana jin tausayin fauziyyan yana kama zuciyarsa tare da kallon kyawun halayenta "Ke kamar baki da zuciya?,kamar baki damu da abinda ta aikata miki ba?,har yanxu fa bandage ne a kanki fa na abinda ta aikata miki" cike da kissa da kisisina tayi gas da kanta "Bazan manta kyatatawarta a kaina ba,shi yasa bazan iya fushi da ita ba" Numfashi yaja sannan yace "Ni dai bazanje ba,idan kuma ke zaki iya bismillah". Hawayen da suka wanke mata fuska ta share,duk abinda suke tattaunawa a tsakaninsu tana jinsu. Zuciyarta ta gama amanna da cewa abinda fauziyya ta shirya aiwatarwa a kanta me girma ne, abu guda ne zai zame mata garkuwa tsakaninta da ita shine addu'a. Bata ko marmarin gain fuskarta,don haka salin alin kafin ma ta kai ga shigo mata daki ta miqe ta murza key ta koma ta kwanta. Tana jinta sanda take knocking da magyar ta bude, zallar kukan dake cin zuciyarta ya hanata koda qwaqwaran motsi. Fauziyyan da koda wasa bata tana kama mata aiki ba koda ciwo zai kayar da ita, fauziyyan da sautin INA KWANA da sunan sun kwana gida daya bai taba hadata da ita ba,fauziyya da bawai ta girka ba,wanda ita ta girka dinma qoqari take ta juye ta cinye, amma wai yau saboda zallar kissa ita ke biyota daki da abinci?. "Ki gyaleta,ta hadiyi baqar zuciyarta ta mutu ita kadai" shine abinda mahmud ya fada yana sake qufula, tare da garin yarda da dukkan maganganun da fauziyya ta gaya masa. Har dare ya raba tana kwance tana kuka,sanda agogo ya nuna mata qarfe uku na dare ta yiwa kanta fada,ta sauka daga saman gadon ta bude gofarta a hankali ta fito bandakin dake tsakanin dakunanta guda biyu dake manne da parlor. Ta kammala alwalar tana shirin fitowa mahmud ya shigo. Cikin sanyin jiki da karyewar zuciya take kallonsa, amma sai ya dauke kansa gefe ya rabata ya shige bandakin yana turo mata qofa. Da qyar ta qarasa dakinta, ta zube saman abun sallar tana bude sabon shafin kuka,abin ya fara wuce tunaninta,ko a lokacin da Mahmud din ke ganiyar karayar arziqinsa wani abu makamancin wannan bai taba hadasu ba,ko da yaushe cikin gogarin kwantar masa da hankali take tare kuma da yin amfani da dukkan abinda take dashi saboda aci gaba da tafiyar da hidimar gidan yadda aka saba. Sallar data kwana tana yi ita ta sanya sassauci cikin zuciyarta,a washegarin kuma ta tashi da wata irin dakiya tawakkali tare da qarfin zuciya,ta sameshi a tsakar gida yana bawa fauziyyan kudin cefane a madadinta. Ko a fuska bata nuna masa komai ba,ta tsugunna cikin girmamawa ta gaidashi yadda ta saba,yana fiffisgewa ya amsa mata,sai itama fauziyya ta rusuna tana gaidata. Kallo daya tak tayi mata ta dauke kai, don abun na fauziyya yanzu ya daina bata mamaki, abu daya fa sani, tabbas akwai mummunan qudurin data sanya a ranta. Mai hali inji hausawa sukace baya fasawa,yana fita ta baje kolin rashin mutuncinta,ta cika gidan da waqe waqe tana kuma bin kowacce waqa sau da qafa cikin daga sauti. Yaran kuwa gaba daya ta tattarowa maji din su ita tabi lafiyar katifa abinta. Bata waiwayesu sai data ga la'asar tayi,lokacin ta fito ya dora girkin dare,ta kuma fara kiran sunan yaran tana hilatarsu, har suka kai ga fitowa,ta tattarasu tana jansu da wasa tana kuma aikin abincin dare. Cikin kwanakin gaba daya gidanta ya koma kamar ba nata ba,bata dats cewa sai abinda fauziyya ta fada,baya aiwatar da komai sai abinda tace masa. Fadin irin tsananin damuwar da maji ta shiga a lokacin batà baki ne,a sannan tana ji har cikin ranta, inama ace fauziyya ba ganwar miji bace kishiya ce,ba shakka inda kishiya ce koda abun zaiyi mata ciwo bai kai kamar haka ba. Tun asali rayuwarta da Mahmud rayuwa ce ta soyayya da qaunar juna da kowa ya shaida da hakan,ko yaya ka zauna dasu zaka fahimci hakan,wannan ya Sanya suke bawa mutane da yawa sha'awa, haihuwar Muhammad da ta nadeeya ba abinda ta sauya game da yadda suke bawa junansu kulawa,koda kuwa bayan karayar arziqin Mahmud jarma din wanna kyakkyawar dangantakar bata canza ba. Asalin maji ta fito daga babban family a qasar Algeria,family ne na masu da shi,a sannan tana da kadarori, haka ta dinga dagasu daya bayan daya tana saidawa tana kula da Mahmud gidansa da yaranta,ko sau daya bata bari ya shiga damuwa ba game da abinda zasuci ko su sha,ko kuma karatun Muhammad ba. Har zuwa sanda riqon fauziyya ya dawo hannunsu. Batasan me ake ciki ba,tashin farko kawai ta yiwa rayuwarsu katsalandan,ganin kusan duk wani decision shifa ke yankewa,a hannunta taga yayanta yana karbar kudin duk wata hidima tasa,ba shi ba,hatta ita idan tana da bugatar abu a hannunsa zaice ta yiwa shifa magana ta karba a waienta.wannan vasa sannu a hankali ta dauki dukkan karantsana na duniya ta dorawa shifa,tana ganin ta mallake yayanta ne kawai sai abinda tace, tare da tunanin duk wata hidima da akeyi cikin gidan da kudin yayanta ne, kawai don bashi da katabus ne babu yadda zaiyi shi yasa ake juyashi haka. Duk wata wahala tare da fadi tashin aikin mahmud tare da shifa akayi, ta qarar da kudi masu dimbin yawa kafin tabbatuwar samun aikinsa a wani babban company. Gabanin ya samu aikin kullum maganarsa itace "Allah ya bani abinda zan kyautata miki nima, Allah ya bani damar mayar miki da halaccin da kika yimin a yanzun da bani da mahaifiya kece makwafinta a gurina,in sha Allah sai kinfi kowa jin dadi na shifa,bazan manta wannan halaccin naki ba" sau tari yana maganar ne a gaban fauziyya,idan yana irin wannan maganar tashi take ta basu guri, saidai ga dukkan me hankali a lokacin idan ya kalleta zai fahimci yadda zuciyarta ke suya a gasan qirjinta. Shifa kam takanyi murmushi ne kawai "Nisful hayaat,ban baka wani abu nawa wai don ka maidamin koda kwatankwacinsa ba bare ninkinsa,da kai da kaya duka mallakar wuya ne" kai yake girgizawa "Na sani,amma kada ki manta,komai naki ya qare,fili biyu ne kawai ya rage miki da gida guda daya" "'Kaci halak malak fa"tace dashi tana murmushi. Dukka wadannan algawura da alwashi sun tashi a banza daga lokacin da fauziyya ta yiwa zuciyarta saqa da mugun zare "Mu biyu kacal nahaifiyarmu ta haifa,bazan taba bari wata mace da ta sameshi daga sama ta fini cin moriyarsa ba" fauziyya ta fada sanda take tsaye a gaban madubi tana gayawa kanta da kanta. Dukka wadannan alqawura da burika a sannu suka bi ruwa suka kuma shafe daga tunani da kwanyar mahmud. Lokacin da ya kamata ace rayuwa ta koma musu dai dai maji da kusan ita taci wahalar komai sai ta koma 'yar kallo daga gefe,wasu abubuwan saidai taji daga fauziyya cikin waqe da habaici. A yanzu ta zama tamkar uwarsa,da ita yake shawara,kuma duk abinda tace ya zauna kenan. Kamfanin da suka bashi aiki sun hada masa da kyautar gida da mota kamar yadda ya shaidawa maji zasu bashin kafin tabbatuwar al'amarin,saidai koda suka bayar din a bakin fauziyya ta fara ji,ranar suna hira cikin falonta tana daga daki, ta fito zata wankewa nadeeya jikinta fauziyyan tace "Maji, kinji abin arziqi ko?, kamfani sun bawa yaaya gida da mota,zamu tashi daga nan in sha Allahu,ki tayashi murna" wani abune ya tsaya nata a wuya,al'amurinsu ya zama abun tsoro, saboda tako ina babu lamari na hankali a ciki,wai ita matarsa mafi kusanci da shi,a yau ta zama 'yar kallo,labarin da za'a ji a bakinsa yau ita takeji a bakin wani "Allah ya sanya alkhairi" kawai tace dasu tana ficewa abinta. Har taje ta dawo suna zaune a gurin, tana gyarawa nadeeyar jikinta sai gashi ya shigo. Sau daya tak ta kalleshi ta kauda kanta,saboda zuwa yanzu ta sallamashi,abu daya ne yake bata nutsuwar ruhi addu'ar da takeyi,ta rame sosai a lokacin saboda tsananin damuwar da take ciki da abubuwan da take ga suna faruwa,gidanta a yanzun bata jin nata ne sam. Akwai alamun jikinsa ya sanyaya kadan sai ya tako ciki "Wai ke me yake damunki? ‚gaba daya kin canza hali?" Ya fada yana kallonta,qasan ransa yana jin damuwa ne tarin yawa,amma kuma wani sashe na zuciyarsa najin ba komai bane muddin fauziyya tana cikin farinciki da walwala "Me yake damunki nace?,kin sake sabbin baqaqen halaye shifa" abun yayi mata ciwo sosai,wato itace ma ta sake sabbin halaye baqaqe "Ba komai" ta bashi ams tana daga nadeeya don saka mata riga "Ai shikenan,sai kije kiyita yi tunda haka kika zaba" ya. bata amsa yanason fita a dakin amma kuma sai ya kasa fitar,ya samu guri ya zauna,har ta gama shirya yarinyar ta kwantar da ita,ta gyarawa toufeeq shima tasa kwanciyar,saboda tun lokacin da abun ya soma faruwa ya raba daki da ita,itama bata sake nemansa ba,tunda taje sau daya yayi mata korar kare "Don Allah idan ka gama ka fita zan rufe qofata" ta fada da sassanyan muryarta "Korata ma kike shifa?" Yadda ya tambayeta a yau din da tausasawa sai ya sanya hawaye sauka daga idanunta,daga nan kuma ta fashe masa da kuka sosai harda shashsheda. Kasa rarrashinta yayi yadda suka saba a baya,yana zaune ya zuba mata ido yana jin zuciyarsa tana gonewa,a cikin ruhinsa yana jin shifa bata cancanci haka ba,amma kuma bazai taba iya daina abinda yakeyi ba,shifa tayi masa abinda uwa mahaifiya cs kawai zata yi hakan wa d'anta. Sai data ci ta cinye don kanta sannan ya qaraso gareta. Miji da mata sai Allah, a nan ya samu hadin kanta,abinda shi kansa ya jima bai nemeta dashi-ba. Bayan komai ya kammala cikin hikima da kwantar da kai ta soma masa magana akan matsalar da suke fuskanta su dukansu *HUGUMA* * TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 42 "Nifa bakiyimin komai ba kibar ma maganar don Allah, banason bacin ran fauziyya gaskiya,a kan ranta ya baci komai ma zan iya aikatawa,yar uwata ce bani da kamarta,farincikinta shine nawa, zama lafiya da ita shine zama lafiya da ni" shuru tayi tana juya maganar a ranta,tabbas akwai qamshin gaskiya akan abinda zuciyarta keta raya mata. Tun faruwar wannan mu' amalar tsakaninta dashi sai aka dan samu sassauci kadan,ya daina fushin da ya dauka gadan gadan da ita,yaci gaba da bata kufin cefane shima, amma kuma har yanzu abubuwa da yawa bata canza zani ba, fauziyya taci gaba da juya akalar gidan tamkar yadda mahaifiya ke juya akalar gidan danta. Hatta da abinci a yanzun suna cin duk abinda fauziyya ta zabi a girka ne. A haka aka yiwa mahmud albashin farko,sun kuma hada masa da wani kudi da suke bawa sabon ma'aikacinsu,don haka a sannan ya shirya tashinsu daga gidan, zuwa babban gidan da Kamfani ya bashi. Batasan hawa ba batasan sauka ba,sai siyayya da taga suna ta fita ita dashi. Ko sau daya bata nuna tasan abinda yake gudana ba,idan ma fauziyyan tayi ne saboda ta quntata mata ko ta bata haushi, saidai qasan ranta bacin rai ne danqar irin wanda fauziyya ke burin ganin ta cusa mata,ko a fuska a lokacin wani irin ramewa majin tayi,saboda dukka wani kwanciyar hankali da • nutsuwar gidan miji ta rasata, dukkan hankalin mahmud ya karkata ga buqatunta da faranta mata,kai idan kaga yadda abun yake zaka dauka kishiya ce fauziyya a wajenta,kishiyar ma irin wadda tayi dukkan me yiwuwa wajen raba tsakanin miji da abokiyar zamanta. Da wani dare mahmud ya aika toufeeq ya kirayi shifa din, a lokacin tana zaune saman abun sallah,don yanzu babu abinda yake bata nutsuwar ruhi da sanyin zuciya sai sallah da azkar. Ta iso ta riskesu a falo sunata sabgoginsu,fauziyyan ta wani murje a lokacin saboda tarin supplement da take dirkawa kanta na qarin qiba da kuma qara haske,wanda har sun wuce qa'ida,hips da boobs dukka sun fito sosai. Guri ta samu ta zauna a nutse tace "Gani" dubanta mahmud yayi,a idanunsa yaga ramewa da kuma canzawar da tayi, qasan zuciyarsa yana jin wani iri babu dadi, saidai baki ya gaza furta komai, hakanan wani abu yana tasowa yana danne dan qaramin tausayin da yakejin yana masa tasiri. "Nidai bansan me yake damunki ba, gaba daya kin tsangwami kanki?,lokacin da ya kamata ki tsaya mu fuskanci rayuwa, Allah amshi addu'ar da kiketa yi mana" wani kallo tayi masa sai ta kauda kanta,batason tace komai saboda bata son fauziyya ko kadan taga alamun karaya a tattare da ita,ta tabbatar abinda taketa son gani kenan,saboda yadda ta matsa qaimi kawai ya isa bayar da amsa ga maji "Nan da kwanaki uku zamu koma sabon gida,a baya na miki alqawarin sabbin kayan furniture da komai da komai,to yanzu yanayi ya sanya ba zasu samu ba,saboda nauyi da ya gara yimin yawa,an siya bawai ba'a siya ba, amma kayan furniture za'a sakawa fauziyya tunda itace garama, kuma ba mai zama bace, idan ta samu miji aurar da ita zanyi,kayan kitchen kuma na ajjiye mata su kada auren ya taso bani da komai a lokacin, idan Allah ya hore miki nan gaba sai a canza miki wasu,zan saka azo a kwashe wadan nan ayi musu gyara" qas tayi da kanta,har cikin zuciyarta takejin wani irin bacin rai,bawai na furniture din da yace za'a yiwa kwaskwarima ba,a'ah…...na yadda kullum kwanan duniya yake qara qasqantar da martabarta a idanun fauziyya yake kuma sake wulagantata. Ta tabbatar idanun fauziyya a kanta suke taga action dinta,don haka ta daga fuskarta da murmushi "Banda abinka ai basai ka tsaya yimin bayani ba, Allah ya hore ya bada yadda za'a yi‚ba komai" har ransa yaji dadi duk da cikin jikinsa yakejin bai kyauta ba, sai ya jawo wata leda "Gashi ganwarki tace ki fara dauka" "A'ah ta dauka ba wani abu;idan ta gama zaba moha ya kawomin" ta fada tana miqewa "Laaa maji ai ba wani abun bane,komai iri daya aka siyo, bambancin kala ne kawai" fauziyya ta fadi,wadda bata son maiin ta wuce ba tare data sake ganin wannan ba. Sabbin atamfofi ya siya musu masu tsada da zasu dinka na tarewa a sabon gida,waiwayawa maji tayi ta kalleta "Bani da zabin kala fauziyya,ko kin manta likkafani da kala qwaya daya yazo?, kuma shine tufafinki kuma tufafina na qarshe?" Turus tayi tana bin maji da kallo,tasan cewa magana ce ta gaya mata a fakaice,sai bata sake cewa komai ba har ta wuce zuwa dakinta. Saman abun sallarta ta koma ta zauna tana nazarin abun zuciyarta na soyewa,ta gaji da zubda hawayenta,zuwa yanzu zuciyarta ta fara soyewa,sai taci gaba da ambaton sunan Allah sannu a hankali har ta samu sassauci. Cikin wannan yanayin suka koma sabon gidan,wanda duk yaga dakin fauziyyan zai dauka shine dakin maji,ya zuba mata komai sabo,hakanan kayan yara ma suna gurinta da komai nasu "'Itace uwarsu ai ita zata kula dasu" abinda Mahmud ya fada kenan. Maji ta jishi kawai, amma ta barwa ranta koda zata sallamawa fauziyya komai banda yaranta da ita daya ta raini cikinsu ta kuma haife abinta. Tsayayyar macace da ita kanta fauziyyan tasan cewa nasararta dukka akan yayanta take,amma majin ta shallake hankalinta,duk yadda taso a maida mata maji kamar mahmud don taci duniyarta da tsinke ta gaza samun hakan. Hakanan yaran, kusan tunda suka koma gidan majin ta sake janye yaranta jikinta da kyau,ta kuma sakasu cikin dukkan wasu addu'o'i na tsari na sha da shafawa. Kwatsam Allah ya fiddawa fauziyya miji,a ranar har kukan farinciki maji tayi cikin daki, saboda tana ganin Allah ya kawo mata qarshen baqinciki da damuwarta. Da farko fauziyya taso taqi auren YA'AQOUB AJI, saboda yana da mata,sannan arziqinsa baikai yadda ta tsarawa mijin da takeson aura b,amma daga bisani yaci galaba a kanta bayan itama yaci galabar fidda matarsa daga gidan tun kafin takai ga shiga gidan. Mahaukatan kudi mahmud ya kashe wa auren fauziyya,duk abinda ta nuna tace tana so shi zai saya mata,a lokacin hatta hidimar yara data gida data makarantarsu sai data tabu,ya tsaida wasu abubuwan da yawa saboda ya cika muradin fauziyya yayi mata aure kece raini. Sam maji bata damu ba,saboda tasan aski ya riga yazo gaban goshi,akayi biki aka tattarata aka migata gidanta. A washegari sai da maji tayi azumin godiya ga Allah,a ranar gidanta ya fara zamar mata gidanta,hatta da iskar gidan sai da ta jita daban da wadda ta saba shaqa. Cikin lokaci kadan abubuwa suka fara komawa saiti,saidai hausawa sukance ba'a taba bari a kwashe duka,haka yake,don duk da da tayi nasarar daidaita al'amura masu tarin yawa,amma har yanzu fauziyya na baki da zuciyar mahmud,a qalla a rana sai yayi zancanta ya kusa sau goma,kira kuwa sai da maji ta gaji tayi masa magana "Kai yayanta ne kuma namiji, bai kamata ace kana vawan kiranta haka ba saboda tsira da mutuncinka, ina laifi a rana sau daya?" Shine aka samu sassauci ta fannin kira, amma banda haka babu abinda ya canza zani. * BAYAN SHEKARA BIYU_* Ana murna bago ya tafi ashe bago yana bayan gari,shekarar fauziyya biyu da aurenta da diyarta daya HASEENA MEENAL arziqin Mahmud ya fara dawowa yadda ya kamata. A take shaidan yayi mata kururuwa,taji sam zaman gidan YA'AQOUB bai dace da ita ba, hakan kamar ta tauyi rayuwarta ne,ta kuma barwa wata dan uwanta tana cin arziqin da daga ita har mahaifiyarta basu cishi ba,duk da babu abinda Mahmud ya rageta. dashi,komai ya samu tana ciki kuma taba da kaso a ciki. Dare daya ta shiga ta fita da yawan gidan malamanta ta tilastawa ya'aqoub ya rubuta mata takardar saki uku a jare,don bata tunanin har abada zata dawo,don yanzu ba wannan ravuwar bane a gabanta. Manya manyan zawaran dake tashe a media ake damawa dasu ta fannin kasuwanci su suke rudarta, rayuwar 'yanci da business,fita qasashen qetare a duk sanda suka so,gidan kansu da manyan motocin hawa da sutturu na alfarma vanzu sune babban burinta, sai kuma diyarta meenal wadda Allah ya jarabta da mugun sonta,irin soyayyar da bata taba yiwa wata halitta irinta ba. Tanason ta tara mata dukiyar da ba zata taba sanin meye talauci ba har garshen tata rayuwar. Ranar data isa gidan Mahmud da takardar shaidar saki a ranar baiwar Allah shifa na cikin farinciki,karon farko tun bayan karayar arziqinsa ya sake siyan mota,a lokacin yace ta dinga hawa tana hidimar gida,kai yara makaranta da daukosu,da sauran abinda ba'a rasa ba,idan ta kama kuma shima zai karba ya hau ya fita sabgoginsa,kafin ya samu damar siya mata tata. Sallamar fauziyya kadai a gidan janye da meenal da faggon kaya ya sanya maji cikin matsanancin faduwar gaba,tana fadin cewa sakinta yayi maji ta samu ta daddafa kuiera ta zauna a kai cikin zucivarta tana ian "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" yadda takeji cikin ranta da jikinta a sannan tamkar ita aka saka ba fauziyya ba. Zaman dai bai sauya zani ba,saima canza salo da fauziyyan tayi, cikin salon wata hikima da iya taku take tatsar kudi daga hannun Mahmud, adadin kudin da ko ita maji wadda ita tasha wahalar kusan komai kawo yanzu bata samesu ba daga jikinsa. Tunda majin ta qyalla idanu ta fuskanci mugun shiru fauziyya ta yi, wanda ya ninka na baya,saboda ayanzun ta samu makiran qawaye gwanaye iya bin malaman tsubbu, sai ta hana kanta sakat da addu'a ba dare ba rana,wanann ya sakawa majin qarfin zuciya da ruhi,duk wani kalar iskanci da fauziyya tayi mata awancan zaman wanna karon ko daya bata dauka ba,wanann ya kawo gagarumin sabani tsakaninta da mahmud, saboda muddin kanason kaga tashin hankalinsa ka taba fauziyya da 'yar lelenta meenal. Yarinyar Allah ya zuba mata rashin ji na tsiya,zuwansu ba dadewa amma ta fashe duk wani kayan ado da alatu na falon gidan. Lokaci galilan kuma ta fiddo dabi' ar tara mata qawaye a gidan,sabbin qawaye irinta,wadanda suka bawa duniya amana da dukkan qauna,suka kuma riqeta da kyau,wasu 'yammata ne wasu kuma zawarawa ne kamarta,cikinsu kuma akwai MANSURA wadda tafi kowa zagewa tare da rawar kai. Da farko falonta ake zuwa a baje,fauziyya ta shiga kitchen cikin taqamarta da jin izza harda yin gayyata ta bare duk abinda takeso tayi musu abincin wadata da alfarma,su bata ko ina a kuma fice abata guri a barta da aiki. Idanunta maji ta rufe, cikin tsayayyar nan tata da dakewa randa suka cika sati guda suna mata tayi musu tasss daga fauziyyan har qawayen,kai fauziyya ta jinjina "Zakiyi nadama" kamar yadda ta furta kuwa daren ranar majin bata samu cikakken bacci ba,saboda mugun tashin hankalin data haddasa tsakaninta da mahmud,ya gaggaya mata maganganu masu zafi da gori wanda tunda sukayi aure bai taba gaya mata irinsu ba. Ta kwana tana kuka tana kuma gayawa Allah,da safe kuma tayi qoqarin ta tashi kamar komai bai faru ba, abu daya ta sani, ko zasu dawwama suna rikici da Mahmud, ba zata. dauki wasu bagin halayen cin fuska na fauziyya ba,ba ita kadai bama,ace har gawayenta suna da power din shiga mata kitchen suyi yadda sukeso?, bazai yiwu ba, inda ita daya ce zata iya kau da kai, saboda kau da kai da haquri ta sani su kadai ne suka kawota warhaka gidan. Ba'a jima da gama wannan ba tana zaune da wani yammaci tana gyarawa su toufeeq farce fauziyya ta shigo,tanata baza qamshi hade da taunar chewing gum, tunda taji hayaniyar tarkacen qawayenta na banza marasa da'a ta hada kan yaranta cikin falonta suka zauna a nan "Key zaki bani" a nutse ta daga kai ta kalleta "Key na me fa?" "Na motar yaya na,zan fita unguwa,wani ma yayi rawa bare dan makadi, a bani na mori arziqin dan uwana ko kuma rai ya baci" bacin rai ne ya tasowa maji,yadda take mata magana a tsaitsaye saman kanta,sai ya maida dubanta ga aikin da takeyi "Bazan bayar ba,rai kuma ya dade bai baci ba,idan kuma kina da qarfin qwata saiki danne ni ki karba" "Abu me sauqi, kamar qofar dakin naki baqona ne" ta furta tana takawa zuwa hanyar bedroom dinta. Tsam maji ta mige ta kuma daka mata tsawa "Ke fauziyya!, dakata,kikayi kuskuren shigamin daki wallahi saikin gane sakarya ce ke,ina da kaidi da kuma tuggun da yafi naki ninkin baninkin,saidai kawai banbanci na dake ni din ba jahila bace,nasan sakamakon dake iya biyo bayan aiwatar da sharri tuggu da kuma makirci" tsaiwa tai tana duban idanun maji,ta rasa meye a tattare da matar da har yanzu ta kasa juyuwa a gareta kamar yadda take juya yayanta? ita kadai ce yanzu matsalarta *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI * Book 02 Page 43 "Zaki bayar ko sai nasa an karbarmin?" Murmushin takaici maii ta sauke "Har abada ba zaki taba cin galaba a kaina ba fauziyya,yadda baki taba karbar abu a hannuna gaba gadi ba saidai kisa a karbarmiki, har abada a haka zaki qare, ni maji bazan taba sallamamiki komai nawa hannu da hannu ba,saidai kisa na gaba dake din ya karbar miki,zoki wuce ki fitamin a daki" maji ta fada cikin zafinta,abubuwan da fauziyya ke mata tana kau da kai tana tarasu cikin haquri irin nata yau suna taso mata. Ganin ta tsaya zata bata mata lokaci sai kawai tasa hannu ta fincikota baya ta watsata waje ta maida gofar falonta ta rufe. A sanyaye ta koma gasan carfet ta zauna,gabanta na tsananta faduwa,batayi dana sanin abinda ta yiwa fauziyya ba,amma yau tabbas ba shakka tasan abinda zai biyo baya a gidan bame dadi bane, wannan ya sanya ta tattara ta gama yanke musu farcen da wuri,ta hadasu sukayi sallar magariba duk da nadeeya dama shi kansa toufeeq din basukai wannan munzalin ba amma ta soma horas da su,saboda haka kawai cikin jikinta takejin ba zatayi dogon zama dasu ba,ta basu abincin dare sukaci ta kaisu dakinsu ta kunna musu cartoon a tv din dake dakinsu tace idan sun gama kalla suyi bacci,sannan ta dawo ta zauna a falo. Ko minti talatin ba'a cika ba taji shigowarsa gidan,ta runtse idanunta saboda yadda gabanta ke duka tana kiran sunayen Allah tare da jan addu'o'in "Allahummakhfinihim bima shi' ita,inna kafainakal mustahzi'een,ya rabbi innalqaumas tad'afuni, wa khadu yaqtulunany fala tushmit biyal'a'ada'a wala taj'alni ma'al gaumizzalimin" a hankali ta dinga maimaitasu qasan ranta idanunta a runtse har zuwa sanda taji ya bankado gofar. Tana bude idanunta ya fada cikin nasa,a hankali yaji wani abu ya dakeshi, kaifin bala'i da masifar da yakeji suna tafasa cikin ransa sai yaji suna raguwa. Ci gaba tayi da kafeshi da idanu,yayin da fauziyya da idanunta sukayi luhu luhu na kuka wadda ke tsaye a bayansa tace "Muje yaya" ganin ya tsaya bai shiga ba bai fita ba. "Sannu da zuwa" maji ta furta a sanyaye, baice mata komai ba sai hannu da ya miqa mata "Bani key din motata" idanu suka hada da fauziyya,saita saki murmushi,batace komai ba ta miqe tsam,ta shiga dakinta ta fito dashi ta miqa masa. Juyawa yayi ya miqawa fauziyya "Ki riqe a hannunki ki dinga hawa,duk lokacin da ni nake da buqata na dinga amsa daga hannun naki,jeki" sanyaya gwiwar fauziyya din tayi, ba haka taso ba,so tayi yayi mata irin cin mutuncin da ya saba yi mata a gabanta,ya wulaqantata ya fifita darajarta akan tata. Juya key din tayi a hannunta sannan ta juya ta fice shi kuma yazo zai wuce cikin dakin nasa ba tare da ya sake bi takan maji ba. Kasa motsawa tayi tana zaune a gurin har ya gama abinda zaiyi ya fito,ya buqaci abinci ta zuba masa,yayi kiran shalelen tasa tazo suci abinci yadda suka saba tace ai ta fita dana mota. Maji na zaune tana nazarin rayuwa,me gobensu zata haifar ita da mahmud da irin wannan makauniyar rayuwar dake wakana a tsakaninsu. A daren bayan sun gama shirin kwanciya ta sameshi cikin kwantar da kai take tambayarsa abinda vake damunsa tare da shawarar yayi gogari ya daidata gidansa "'Ni ba abinda yake damuna, hankalina yana tashi idan fauziyya bata cikin walwala, raina yan baci idan nata ran ya baci saboda ba abinda nake tunawa sai amanarta da mahaifiyata ta barmin" yadda yake maganar kadai ya sake tabbatarwa da maji lallai abub yayi girma ya wuce duk inda ake zato,daga wannan lokacin ta sanya idanu kan fauziyya fiye da baya,babu jimawa kuma ta fahimci irin aikin asirin da takeyi akan yayan nata kuma miji ga maji din. Randa ta karanci hakan ta samu fauziyyan na zuba wasu abubuwa cikin abincin Mahmud din maji tayi ram da hannunta tana kallonta "Kin ganowa kanki ranar barinki gidan nan sakarmin hannuna" ta fada kanta tsaye bacin rai ya hana maji magana, wacce iriyar baqar masifa ce haka?,duka duka shekarunsu dava da fauziyya har yanzu babu wanda ya rufa shekara arba'in, gaba daya ba zasu wuce talatin da bivar ba amma ta zama wata bagar masifa?. "Kinyi asara wallahi,sannan bana danasanin barina gidan nan saboda nayi imani duk sanda hakan ta faru cikin qaddarata yake,ke baki isa ki zanamin gaddarata ba". Tun daga wannan ranar fauziyyan ta dauki damara,saboda ta sani maji din nada wani irin kariva da take hana asiri cimmata nan da nan, kuma tasan hakan baya rasa nasaba da yawan addu'a da azumin nafila da bata rabo dashi. * MAMAYA * Tun daga wancan lokacin da ta kama fauziyyan take kaf kaf da abincinsu su duka cikin gidan, don tayi imani ba abinda fauziyyan ba zata iya aikatawa ba. Ranar da ta zama baqar rana a gareta, ranar data shiga tarihin rayuwarta,ranar da ba zata taba mancewa da ita ba,ranar kuma data zama mafarin zanen dukkan qaddarorin da suka wanzu a rayuwarta dana iyalinta. A wani yammaci liqis wanda kadan ya rage magariba ta kunno kai,ta gama abincin dare cikin galabaita saboda yadda qamshin girkin yake damunta yana hautsina mata kayan ciki, yanayi ne dakan faru da ita a duk lokacin da take da qaramin ciki,ko a yanxun tana tsammanin cikinne saidai haka kawai ta kasa gwadawa bare ta tabbatar, saboda yanayin da take ciki wanda zaiyi wuya ta samu nutsuwa ta kwana uku cikin gidan fauziyya bata sakata a masifa ba,abinda yake dakushe kaifin abun wanda a yanzu sukanyi sati daya har zuwa biyu lafiya lafiya shine addu'ar data tashi tsaye tana yi, ba dare ba rana. Tana kammala abincin ta fita a kitchen din tana fatan samun wata iskar da babu qamshin abincin a ciki kota samu ta dawo dai dai,ta kama hannun nadeeya ta saka toufeeq a gaba suka wuce, zuciyarta na tuna mata da kalaman da fauziyya ta gaya mata kwanaki uku da suka wuce,wadanda suka sanya maji din dauketa da mari, abinda bata taba yi mata ba kenan. "Badai yara ba? sai na rabaki dasu rabuwa ta har abada,saina tabbatar miki da cewa ni fauziyya ni kika haifawa su". Ta jira abinda zai biyo baya akan marin da tayi mata amma har yanzu bataga alaman Mahmud ma yasan da abun ba,hakan bawai ya bata kwanciyar hankali bane, a'ah, ta sani tabbas akwai abinda zai biyo baya. "Abba ya dawo maji,muna masa sannu da zuwa bai amsa ba" toufeeq ya fadi mata,saita kalleshi da mamaki,don bataji shigowarta ba bai kuma nemeta ba,qilan yau an birkitashi ne kamar yadda ake masa duk sanda akaga dama. Batabi takan zancan toufeeq ba,sai ta zauna tana jira ta koma dai dai sannan ta iskeshi. Motsin da ta danji a kitchen ya sanyata yunqurawa babu shiri saboda tunawa da tayi ta baro abincinsu ta cewa da toufeeq "Ina zuwa ku zauna". Tun kafin ta garasa ta hangi fauziyya a ciki gabanta ya fadi ta kirayi sunan Allah tana qarasawa da gaggawa. Shigarta yayi dai dai da ware wani abu baqi cikin kwalba da fauziyya tayi tana shirin antayawa a cooler din abincin Mahmud. Caraf tayi da hannun fauziyya tana kallonta "Me kike shirin aikatawa maqiyar Allah da manzansa" maimakon ta amsa mata yadda suka saba sai kawai taga ta saki kwalbar,maji tadan ja baya tana duban kwalbar data fadi qasa ta fashe,wani irin wari wari yana fita daga ciki, shi ba warin fiya fiya ba shi ba na maganin bera ba, kafin ta gama wannan nazarin fauziyyan ta zame hannunta ta kama hannun majin ta rige tsam kamar me shirin hanata tabawa,sai kuma taji ta kwazara ihu tana kiran sunansa "Yaaya!, innalillahi wa inna ilaihi raji'un yaaya kazo ka gani* tunanin maji ne ya juye, ta kasa fahimtar abinda fauziyyan ke shirin alkatawa. Cikin qasa da second talatin ya iso qofar kitchen din, hannunsa riqe da wasu takardu,wani irin lafiyayyen fushi na kwance kan fuskarsa "Yaaya,kaga abinda na kamata tana shirin zuba maka,yaaya dama kasheka takeson yi,bata qaunarka" fauziyya dake wani irin rawar jiki ta fada hawaye na wanke mata fuska. Wani tashin hankali ne va bayvana baro baro saman fuskarsa ya zubawa maji ido, majin da lokaci guda tunaninta ya juye, tsananin kidima da rudewa da jin yadda fauziyya ta juyar da abin kanta lokaci guda ya gigitata "Shifa?,kece shifa da kanki?, bazan musa zancan fauziyya ba,saboda gashi na gani da idanuna" sai ya watsa mata takardun hannunsa saman fuskarta "Sati uku cur na fuskanci ana dauke takardun kadarorina,sama da qasa na dinga nemansu daya bayan daya ina rasawa,sai gasu guda shidan cif a dakinki, ashe kin shirya kasheni ne ki mallaki abinda na tara ko?" Wani irin kukan baginciki ne ya balle mata "Wallahi wallahi bani na daukar maka ba bansan dasu ba" ta fada tana jin ranta yana daci,sharrin kisa da sata duka lokaci guda?. "Idan bake bace nine kenan nakaisu dakin naki?,bayanke ki gayamin wanda yake shiga dakina" "Babu" ta amsa masa kai tsaye,saboda tasan babu din shine amsar "Gwara da baki wahalar da shari'a ba,kije na sawwaqe miki na gaji da yadda gidana yaqi zama lafiya sanadiyyarki,na sakeki saki daya" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, allahumma aiirni fi musibati, wa'akhlifni khairan minha" ta furta da madaukakin sauti dake gauraye da sautin kuka, idanunta suna sauka akan fuskokin nadeeya da toufeeq wadanda suke tsaye daga bakin qofa suna kallonta, daga shi har nadeeya din idanunsu cike yake da hawaye,sai taga uban yaja hannuwansu ya fice dasu ya barsu daga ita sai fauziyya. Dariya sosai ta fara qyaqyatawa wanda hakan ya tabbatar mata itace ta sauyawa takardun guri daga dakin Mahmud din zuwa nata dakin "Idan asiri baici ba,ai ita kissa bata da magani" ta furta kai tsaye "Fauziyya" maji dake hawaye ta kirayi sunanta "Alfarmar sayyadina rasulillahi S A W,yadda kika birkitamin rayuwar aure na,kika hanamin jin dadin gidan mijina,ina rogar ubangijin sammai da gassai ya hana miki jin dadin aure har gaban abada" daga haka batà qara ba ta wuce dakinta. A daren taso tabar gidan,saidai kuma abubuwa biyu suka hanata,na farko tunanin yadda zata hada kudin ticket din da zai maidata Algeria,sauqinta daya babban yayanta yayi mata visa ba dadewa ta shekara biyar, kuma shekara biyu kacal taci a ciki,abu na biyu kuma tana tsaka da hada kayanta jini ya balle mata, koda ta isa bandaki sai ta iske bari ne tayi,barin dan tayin cikin da jini ne zalla,ko ubansa baisan dashi ba, dole ta haqura ta kwana tana bigin kanta da jinin barin da take zubarwa,cikin taimako da dafawar Allah zuwa asubah ya tsagaita. Kafin gari ya waye ta gama shirya komai nata dana yaran,a daki suka iskota ta kamasu ta shiryasu tsaf tana shirvasun toufeeg yace "Jiya abba baiyi bacci ba maji,kije ki bashi magani" "Zaiyi toufeeq" abinda ta iya ce masa kenan. Ga kaya ga murdawar mara ga yara haka ta ratso falon gidan zata fice a gidan "Ina zakijemin da yara?" Ta tsinci muryar mahmud JARMA yana fadi. Kafin ta waiwayo ya iso gabanta,yasa hannu ya zame hannun toufeeq da nadeeya "Ba dasu kika zo ba ina ke ina tafiyar mana da zuri'a?" Fauziyya dake tsaye a gefe ta fada, ranta fes duniya yau sabuwa a gareta. Gaban fauziyya ya isa da yaran "Na mallaka miki su halak malak" "Na gode yaaya,na tabbatar ko ranar qiyama ummee zatayi alfahari da kulawar da ka bani" tayi maganar tana goge hawayen munafurci. Cikin dakiya da zallar jarumta maji ta tako gaban yaran, ta dora hannuwanta duka biyun saman kawunansu ta furta "U'izukuma bi kalimatillahit tammat min kulli shaidanin hammah wamin kulli ainin lammah" ta maimaita sau uku sannan tace "Ya ubangijin sama da gasa,ina neman alfarma daga gareka cikin karamci da adalcinka tare da isar ga bugatar wanda aka zalunta,wannan addu'ar da nayi musu koda ta zama ta qarshe, koda nisan dake tsakanin uwa da ‘ya'vanta ya wanzu a tsakaninmu kasa addu'ar tayita bibivarsu har garshen rayuwarsu,na damqa amanarsu a hannunka ya mijibancin al'amarin bayinsa" daga haka ta miqe,ta kuma kalli idanun fauziyya "Zan sake miki addu'a a Karo na biyu kafin na wuce, yadda kika shiga tsakanina da farincikina,ina roqon Allah ya gimtse naki farincikin a sanda baki taba zata ko kawowa ba, addu'ar da nayi miki rannan,da wadda nayi miki yanzu kadai sun wadatar, ba zan sake kai qararki gaban Allah ba,sai kuma jiran sakamako". Bata tabajin furucin da ya shiga jikinta yayi mugun kassarata ba irin wannan,amma sam batason majin taga kamar ta karaya,wadan nan addu'o'i biyu suka kasa barin ranta,suka kuma sanyata qudurar anivar kassara duk wani abun da zai zamewa maji farinciki a rayuwarta daga nan har zuwa garshen numfashi,wannan ne kuma ya sanya FADEELA a target na hajiya garama tun ba'a san da wanzuwar mahaifiyarta a duniya ba bare ita kanta. *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 44 Karon farko ta isa gidan aminiyar dake gaunarta dason qawancensu,ta shiga baqinciki da tashin hankali itama tayita roqon maji ta zauna dasu tace a'ah, tabar nigeria kenan har abada daga lokaci irin wannan, alfarma daya take nema tayi mata magana a landline phone dinsu da yayanta ya siya mata ticket na komawa "Allah ya sawwage ace har saikin nemi yanuwanki" a aljihunta ta siya mata ticket din, kwana biyu kacal maji ta qara ta koma Algeria,wanda tunda tabar nigeria bata gara waiwayarta ba sai a wannan lokacin. Kawa ga maji ita taci gaba da bibiyar al 'amarin su toufeeq kafin fauziyya ta ganota ta hanata shigowa gidan da ganinsu gaba daya. Cikin ikon Allah ta shiga neman mai aiki saboda a lokacin ta soma bungasa kasuwancinta da tafiye tafiye,ta kuma qulla aure tsakanin yayanta da daya daga cikin qawayenta,auren da sukayi yarjejeniya tsakaninta da qawarta ta. tata. Ruqayya qawar maji ita tayi wuf ta aika da baaba ramatu,saboda yadda da amintar da tayi da ita,ta kuma tabbatar zata bawa yaran dukkan wata kulawa tare da kula da lamarinsu. A hankali baaba ramatu ta fuskanci yadda fauziyya ta kawar da hankalin yaran gaba daya daga ganin kima da jin maganar kowa,duk abinda ta shimfida ya zauna daram. Da farko maji na kiransu,idan aka kwana bivu bata kira ba zasu nemi babansu ya kira musu ita suyi magana sannu sannu sai gashi gaba daya daga yaran har babansun sun soma mantawa da wata mai suna MAJI sam cikin gidan,duk wata kewa da qulafucinta da sukeyi ta sanya anzareshi tsaf daga ransu,sai abinda tace sai abinda takeso. Tun ba'a ie ko ina ba ta raba auren maryam qawarta da dr jarma,ta sake kutun kutun ta aura masa murja itama bayan wasu shekaru ta raba auren da salon kissa da kuma asiri. Cikin shakarun sai data aura masa mata hudu tana sanyawa yana sakinsu, mace ta garshe da ta aura masa mansura. Mansura itace babbar aminiya cikin gawaventa, kuma ta kashe aurenta ne don kawai tazo fauziyya ta aura mata Dr jarma,ta fito daga gidan baban labiba ta baro yara hudu labiba auta ta biyar,can qasan zuciyar mansura itama danqare fal da buri da nata qudurin na mallakar Dr jarma da uban dukiyar da ya fara tarawa a dare daya. Mafarin rashin gaunar da toufeeq yake yiwa mansura din ya samo asali ne da zuwansa gidan wata rana,a lokacin duka duka shekararsa sha biyar ya samu tana yiwa Dr jarma barbaden magani, wanda kusan maganin nata ne data fauziyya,yawanci mansura ita ke sabuntawa fauziyya aikinta,saboda komai yana tafiya mata dai dai,rayuwa tana mata yadda takeso,bata bugatar Dr jarma ya koma Mahmud dinsa, ta tabbatar inda har yanzu maji na cikin rayuwarsa babu lallai takai matsayin da take kai yanzu a rayuwarta. Komai yana iskar maji ta hanyar ruqayya,co sau daya bata taba sassautawa wajen yiwa yaranta addu'a ba,tasha hana idanunta bacci saboda sallah,ta sha hana cikinta abinci saboda azumi, duka tana yine saboda nemawa yaranta kariya,a kullum idan ta kwanta babu abinda ke mata yawo a kunne sai kukan nadeeya dana toufeeq, wani irin kuka me karyar da zuciyar me imani suna kiran sunanta,kukansu na qarshe da taji bata kuma sake ji ba saidai tayi hasashe. Shekararta biyar da rabuwa da DR JARMA sannan tayi wani auren,saidai auren duka duka shekara biyar mijin ya rasu, bata kuma sake sha'awar sake wani auren ba,ko wancan matsantawa ce ta yayanta guda daya daya rage, shekara biyu kadai da yin auren kuma ya rasu. Sau biyar hajiya qarama na yin aure bayan aurenta na fari da ya'aqoub, amma auren baya wani lasting sal ta fahimci ba don komai suke aurenta ba sai don abinda ta tara,saita sallami mutum tunda yawanci auren dauki sandarka ne. Allah ya jarabceta da sha'awar auren amma haka ta tattara ta haqura saboda tsoron kada abinda ta Jima tana yaqi akan tarashi ya salwanta. A karo na shidda ne taga DR GIREMA(mahaifin säahar), a lokacin suna abota sosai da Dr jarma kafin rayuwa ta cilla kowa wani sashe na daban. Ta mutu sosai akan dan mutanen borno shuwa arab na asali dake da kyau na burgewa,irin kyan da take ganin yayi dai dai da nata kyan. Ta soma shiga da fita akan a jawo mata hankalinsa,cikin ikon Allah duk inda take tunanin nasara babu ita,a hankali ta fahimci matarsa tsayayya ce,ta tsayawa kanta da mijinta da addu'o'in tsari,sannan gwanace kuma qwararriyar mace wadda ta amsa sunanta wajen iya kula da miji tare da dasa soyayyarta me zafi a zuciyarsa,don duk inda ka zauna dashi zama ya danyi tsaho sai yayi maka zancan AMINATOUnsa. Tayi barnar kudi akan dr girema kamar ba gobe amma kusan a banza za'a ce,don babu wani ci gaba ko nasara data samu,tana ji tana gani haka ta haqura da shi, don ta fahimci kallon ganwa kawai yakeyi mata, daga gaisuwa kuma babu abinda yake qara shiga tsakaninsu. Abinda maji ta mallaka daga gadon iyayenta da tumunin takabarta data samu shi ya shiga kasuwanci dashi babu kama hannun yaro. Family dinsu babban family ne kuma sananne da suke da mutane masu tarin muqamai kala daban daban,wannan yasa bata wani sha wahala ba kasuwancinta ya samu karbuwa daga gurin matan manyan qasar ta Algeria, a hankali kuma sai ya fadada zuwa qasashen qetare maqwabta,harma da Nigeria din kanta, amma bata taba yarda ta saka qafarta Nigeria ba saidai aike, duk da cewa Zuciyarta da gangar jikinta ko da yaushe tana kan yaranta,tana kuma bibiye da dukkan wata nasara ko faduwa tasu. Taso zuwa auren toufeeq na farko amma hajiya qarama ta aike mata da saqon basa gayyatarta. A sanda sagon ya isketa tana asibiti bata da lafiya,saita saki murmushi kawai tana girgiza kai. Ta sani tabbas addu'a babu abinda ya kaita kaif,ta jima ta fahimtar wata muguwar shakkarta da tsoronta ya shigi hajiya qarama,gamuwarsu kuma shine abu na qarshe da bataso. Ciwonta shi ya hanata zuwa bawai barazanar banza da wofi ta hajiy qarama ba,ta barwa ranta akwai lokaci na gaba,akwai kuma dama ta gaba,don tana ji a jikinta dama lokaci yayi da zata tabbatarwa da fauziyya yaranta data bar mata,ta bar mata su raino ne kawai,ta gama yanzun kuma zata karbi ajiyarta. Sanda taji matar toufeeq ta haihu sai taji kowacce soyayya tata ta tattara akan FADEELA, tun tana jaririyarta har kawo shekarun da take kai a yanzu,sai taji tamkar itace ta yiwa nadeeya qanwa. Wata iriyar soyayya ce da bata boyuwa sam sam,wannan ya sanya hajiya qarama karkade makaman yaqinta data binne,ta kuma tabbatarwa kanta lokaci yayi da zata dawwamar da hajiya qarama cikin toro firgici da kuma zulumi _wannan kenan_* _sauran warwarar lamuran suna nan a gaba kadan zakuji komai filla filla_* "sauran duka abinda fauziyya ta aikatawa rayuwata data su moha wanda idanu basa iya gani ita daya ta sani,sai kuma ubangijin sama da qasa,wanda idan yaso bayyana komai zai bayyana shi ba tare da wani jinkiri ba,wannan itace fauziyya,wanann itace hajiya qarama, kina tunanin akwai yanayin da zaizo wanda zai sanya na manta wacece ita?,na baki goyon baya dari bisa dari ki fita da fadeela,ba'asan abinda Allah ya hukunta ba,zama ba shine mafita ba tunda har akwai chance na yiwuwar warkewarta" gaba daya jikin säahar ya gama yin sanyi,duk gwiwarta ta mutu,cikin ranta tsoron Allah yana sake kamata,ashe ire irensu adam da momee suna da yawa a duniya? ‚ashe har yanzu mutane basa ji a jikinsu bisa yarda da imanin akwai ranar sakamako?,a yanzun bata ko shakka ko kokwanto,hajiya qarama zata iya aikata komai ma,sannan qarfinta ya karkata dari bisa dari akan sanya hannunta da ta'azzarar ciwon fadeela,ta sake imanin akwai wata boyayyar manufa tata data sanya take matsa qaimi akan duk wanda yace zaiyi maganar a yiwa fadeela aiki,ita ta cusa toro da fargabar surgery na fadeela a zuciyar mahaifinta,hakan na nufin shi dinma yana kan wani TARKO nata ne kenan ba tare da ya sani ba?. A karon farko wani tausayinsa ya sauka ya lullube zuciyarta, idanunta da suketa zub da qwalla suka saka tara sabon hawaye tana jin radadinsu dikin idanunta,da gasken gaske maji taga rayuwa,ta hadiyi abinda ba kowacce maca ce zata iya hadiyarsa ba "Ki ajjiyemin account number dinki, zan saka miki duk iya adadin abinda zaku kashe da wanda zaku buqata,wacceqasa ce?" "Germany ne maji,bonn, amma don Allah mai, inason nayi wannan aikin da kudina ne, ko da duk abinda nake dashi zai qare, ina kwadayin ladan" kai ta gyada "Bansan wanne lokaci zaya daukeni kafin na samu visa din can ba,tunda ban taba shiga ba,amma zanyi iyakar bakin goqari na,ina matuqar alfahari da wanzuwarki cikin ahalina khadijatu,banzan kuma da kalar bakin da zan miki godiya ba". Hirarsu da maji a ranar ta maqale mata a wuya,ta yini tana juya abinda suka tattauna da ita. Yau gaba daya sai ta kasa fita a sashen,saidai duk wani motsi idan akayi cikin gidan yana kan kunnenta,sai ta dinga jin taron data baiwa fadeela a baya ma kamar yayi kadan, kamar hajiya qarama zata iya yin wani motsi don ta cutar da fadeela,don haka a idanunta da kunnuwanta motarsu ta shigo gidan,cikin motar toufeeq jarma wanda a yanzun ya zamana vadda suke fita tare tare suke dawowa. Labulen ta sauke tana sakin ajiyar zuciya sanda ta tabbatar sune tanason taje ta tari fadeelan amman kuma tasan suna tare ne da toufeeq. Har yanzu wani matsanancin kunya ce take lullubeta idan ta tuna abubuwan da suka faru a dazun,wuni tayi abin yana dawo mata tana mamakin kanta na vadda ya sanyata ta saki layi haka lokaci daya, sai ta juya a nutse ta koma kitchen din,ranar farko da zata girka wani cikakken abinci a ciki. Yadda jilkinta vake a sanyaye yau tasan ba lallai ta gama abinci da wuri don haka tun bata dora ba ta fara yiwa fadeela pancakes da smoothie ta ajiye mata,sai fura data dama daban Incase ko batason smoothie din. Tana aikin yayyanka vegetables amma hankalinta yana cikin gidan. Tana jin lokacin da suka bude gofar suka shigo,fadeela ta rada mata kira da kyau. Tanason ta amsa amma idan ta tuna da toufeeq na gurin sai ta kasa. Har zuwa sanda fadeela ta kalleshi "Abby,ko anty N na wajen baaba ramatu?" Kafada ya maqale yana murmushi tare da dan tabe baki "Muje na rakaki ki gani" ya fadi can qasan ransa yana jin zumudin ganinta. Sallamar yarinyar cikin kitchen din ya sanyata sakin abinda takeyi tana amsawa ba tare data juyo ba "Anty,yau bakiyi welcoming dina ba" fadeelan ta fada tana togewa daga bakin qofar gami da qin qarasowa ciki. Qaramin murmushi ya saki yana jin farinciki na saukar masa a zuciyar ,kamar fadeela tasan muradinsa a yanzun na kallon qwayar idanun säahar din,wanda ya tabbatar ko zai narke a banza ba zata bari ya gani ba. Gyara tsaiwarsa yayi sosai yana sake zube idanunsa a kanta,tana sanye da high tummy skirt na yadin chiffon wanda aka yiwa qananun tattara ainun,hakan ya santa qugunta fita das a jikina,ya kuma fitar da shape dinta. Rigar jikinta ta plain chiffon din ce wadda ta dace da skirt din jikinta, gashinta na nannade a boye cikin dankwalin kayan. Idanunsa ya lumshe yana fitar da iska tun daga hunhunsa,hancinsa na dawo masa da sassanyan qamshin gashinta wanda yake jinsa kamar yanzun yake nutsa kansa cikin sumar sa. Tana takowa idanunsa nakan lips dinta,baya gajiya dasu sam, akwai sirri me yawa da wani irin softness samansu "'Faddee rigima" ta furta a hankali, abinda ya bawa lips din nata damar motsawa da juyawa a hankali, wannan ya sanyashi sake fidda wata iska me nauyi ta hancinsa. Duqawa tayi tana karbar lunch bag da school bag din fadeelan "Sannu da zuwa" ta fadi ba tare data dubi sashen da yake ba. Banza yayi da ita kamar baiji ba "Sannu da zuwa" ta sake fada still da yanayin dazu,sai a sannan ya saki hannayensa yana dan waiwayawa,kamar me neman da wanda take magana "Da wa kike?" Yayi mata tambayar da ta sanyata daga kanta zuwa gareshi cikin mamaki, don dai ita bataga kowa a kitchen din ba saishi da ita sai kuma fadeela "My angel, karba kayanki ki qarasa dasu daki,oya" ya fadi yana duban fadeelan. Bata musa ba ta miga hannu ta karba komai nata da sãahar din ta cire, ta kuma fella da gudu ta fice ta barsu a tsaye. Da kallo säahar tab fadeela duk data qule, gabanta na faduwa kadan kadan,tana tsoron kada ya zamana wata muguntar ya sake hada mata,har yanzu bata warke daga mikin jiya ba. Bata gama tunanin ba kuwa tattausan gamshinsa ya ya soma ratsata qofofin hancinsa,ta daga idanunta ta kalleshi, karon farko da yaga karaya da tsoro a cikinsu. Taku ta fara yi da baya yana biye da ita,cikin zafin nama ya sanya hannu ya rigo qugunta ya tsaidasu cak shi da ita tsakiyar kitchen din yana jifanta da wani shu'umin kallo da narkakkun idanunsa *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI* Book 02Page 45 "Na dawo daga office a gajiye, ina jin yunwa,inaso nayi wanka,amma duk baki lura ba, sai kawai ki bini da wata sannu da zuwanki me kama da bada umarni umarni?" Ya qarashe maganar yana lashe lips dinsa,hankalinsa na fusga akan nata lips din zuwa qirjinta da yaketa son rudar masa da tunani, rigar jikinta din doguwace sakakkiya,amma duk da haka akwai wata tattara a qirjinta data sake yiwa halittunta mazauni da kyau. Sake fincikota yayi sosai zuwa cikin jikinsa yana ci gaba da ifanta da wani narkakken kallo cikin qwayar idonsa "You know what?" Ya fada yana hadiye yawu,ba tare da ya jira amsarta ba ya bata amsa yana sake jawota cikin jikinsa da kyau "I swear i straight up forget my name for a second duk sanda na kalli wadannan qwayar idanun" ya qarasa fada yana sanya yatsarsa tare da yi mata yawo dasu softly saman idanun nata, abinda ya tilasta mata lumshesu, tana jin tsigar jikinta na neman fara tashi "Hold me so close for some minutes your breath already become my oxygen" ya fada yana kama hannuwanta ya kuma sanyata ta zagaye bayansa da su,sannan ya kama fuskarta a tausashe ya rige suna musayar numfashi me dumi dake fita daga hancin kowannensu. Qafafunta ne suka fara rawa, ta fara gogarin zamewa,bai hanata ba ya barta ta janye,saidai bai barta ta matsa duka daga jikinsa ba ya rige hannunta "Wannan shine kalan gaisuwar da nakeso bayan na dawo a office,zan shiga nayi wanka, kafin na fito please i want something to eat....am starving" tuntuni ta juya masa baya,a haka ta gyada masa kai tana addu'ar ya fita a kitchen din, tana tunanin zai fitanne tunda ya gama abinda ya kawoshi saita tsinci muryarsa cikin karyar da murva a shagwabe "Please,my lips are so lonely one kiss please" har cikin bargonta taji tasirin muryar tasa. Qarasa rudata yayi,har spoon din hannunta na faduwa qasa,ya tsugunna ya dauka yana miga mata "Matsiyaciya" ya fadi yana sakin wani tattausan murmushi hadi da soma takawa a nutse yana fita a kitchen din. Bayan ta tabbatar ya fita din sai data samu guri ta zauna saboda ta daidaita bugun zuciyarta,idonta ta lumshe tana mamakin yadda yake yawan sanyata faduwar gaba da rudewa, abinda a baya Sam ba dabi'arta bane?. Komai ta zubawa fadeelan har furar ma tace tanaso, sanann ta dawo ta shirya masa nasa saman wani kyakkyawan tray bisa tsari,sai taji kaman ta aikata fadeelan takai masa,amma kuma tunda ya fuskanci ya zama dan garari me neman dalili galilan ya moreta son ranshi,sai ta haqura ta zura hijabinta ta dauki tray din ta wuce dakin nasa tabar fadeela na kallo a parlor. A nutse ta bude bedroom din ta shiga gamshin da yake fitarwa da sanyi suka buso mata,first night dinta da tayi da ranar Allah shi ya fara dawo mata fes a kai,ta dauke kai daga kan bed din ta soma takawa da gaggawa,tanason ajiye masa ta fice kafin yakai ga fitowa daga toilet din da take jiyo qarar ruwa. Har ta kusa isa qofar fita ya bude qofar bandakin ya fito "Wait mana" ya furta yana dubanta, kamar ta zura da gudu haka taja ta tsaya sannan ta waiwayo da nufin ta samu gurin zama. Kadan ya rage bata fadi ba saboda tsabar rudewa,murdadden jikin nan nasa dake dauke da curarrun muscle ya bayyana muraran, gargasar dake lullube da jikinsa da damatsensa da suke fadin yadda mamallakinsu ke yawan daga qarfe, ba komai a jikinsa sai wani gajeran towel da ko cinyarsa bai gama rufewa ba don tabbas idan yace zaya zauna ne to kana iya hangen jikinsa sosai. "Come and serve me masallaci zaki shiga ne haka na ganki da hijabi?" Ya fada cikin gatse, don ba haka yaso ganinta ba,yaso ya morewa kallonta ne sosai. Bata tankasa ba ta dawo gaban tray din "Stop madam,ki cire wanann hijab din kada kiyimin gazanta" magana ce fal bakinta takeson maida masa, amma kuma tana tsoron kada allura ya tono garma,abisa dole ta hadiye ta zare hijabin yadda ya bugata ta fara saving nasa pancake "Furar is enough" ya fada yana duba wayarsa da ya samu da tarin miscalls Gida biyu hankalinsa ya rabu,rabi yana kan wayarsa rabi kuma tana ta fusgar hankalin nasa,so samu ace yanzun tana jikinsa yana shan duminta bai taba tunanin akwai ranar da wata mace zata dinga wasa da hankalinsa haka ba. A nutse ta mige ta isa gareshi, dai dai sanda ya daga kiran dava shigo wayar tasa, miqa masa cup din tayi,ya miga hannu da zummar karba, kawai sai ya hade hannuwansu guri daya ya kuma jawota a tausashe yayi mata masauki saman cinvarsa tare da manneta da qirjinsa ya riqeta tsam. Ko motsi hanata yayi,cikin tattausar muryarsa din nan da yau tayi kusanci sosai da kunnenta taii ya ambaci sunan maji yana kuma gaidata. A galla ya kusa minti talatin suna magana da majin,ita kuma tana zaune zaman cinyarsa,wata muguwar kunya na dawainiya da ita,duk sanda ta motsa zai zake maidata jikinsa va manneta gam, har ya kammala wayar sukayi sallama,ya aje wayar gefansa sannan ya tattara hankalinsa a kanta. Tallafo hannayensu dake riqe da cup din yayi ya matso dashi saitin bakinsa,sannan ya kamo daya hannun nata ya aza saman cokalin dake cikin furar, murvarsa gasa gasa cakude da alamun damuwa yace "Oya...feed me please" ya furta kamar wanda ke tsoron wani ya jishi. Shi ya taimakawa hannun nata ta hanyar rigeshi, yana tayashi debowa tare kaiwa bakinsa. Wani irin shiru ya ratsa tsakaninsu,ba wanda ke cewa komai a tsakaninsu,sai jikkunansu dake hade,dumin fatar cinyarsa da towel din bai gama rufewa ba tana ratsa saahar tare da haifar mata da wani irin vanayi a cikin jikinta. Shima baice komai ba har suka gama,sai ya sanya daya hannun ya sake dafe tafukan hannayenta yana kallon cikin idanunta tare da sauke wata ajiyar zuciya me nauyin gaske "Na gode, Allah yayi miki albarka" har ciki tsakiyar ranta tali dadin addu'ar, batasan cewa shi ya fita jin dadin samun wannan kulawar ba, duk da sai daya tilastata kusan ya samar da ita "Ameen" ta furta can gasan ranta amma kuma labbanta sun motsa "Amma....kin saka an dakeni kuma an hanani kuka?" Ya fada yana langabe kai cikin wata shagwababbiyar murya data sanyata daga kai ba shiri, idanunsu kuwa suka hade guri daya,sai ya dage mata gira abinda ya sanyata saurin mai da kanta qasa "Yes maji tace zakuyi tafiya tana neman alfarmata na barki ki tafi, batason kuma doguwar tambaya ita tasan inda zakin keda angel" ya qarasa fadi cikin yanayi na nazari. "'Nima ina sake neman alfarma tare da rogon kauda duk wata tambaya daga ranka shakka ko kokwanto, khairan in sha Allah" har cikin bargonsa sautinta ya ratsashi, karon farko data masa magana da irin wannan salon, hashi kuma kusancin dake tsakaninsu ya bashi damar jin tone dinta tarrr "Oh my god,repeat please,sake fadi" fuska ta tsuke,ta kuma shammaceshi ta mige da zafin nama,saidai ya rigata ta hanyar cafko hannunta "Waye yace ki tashi?, haka kawai kin ciremin towel,oya mayarmin da abuna" sulalewa kawai tayi a wajen ta tsugunna tana curewa guri guda,ko kallonsa a haka ba zata iya sake yi ba bare ta gyara masa munafukin towel din daya dauro. Magiya ta hau masa "Tashi kije" ya fada yana danne dariyar dake qasan ransa,da gaske yarinyar ta horu yadda ya kamata,inda dane da tuni yasha tsiwa da musu sau babu adadi. Koda ta fita waiwayawa tayi ta ballawa dakin harara tana jan awafa sannan tayi gaba _niko nace a banza,ihu bayan hari kenan,idan yarinya ta isa tayi a gabansa mana 😂😂 "HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02Page 46 _assalamu alaikum,barkanmu da dare,jiya an samu typing error,zakuga na sana matsiyaciya a maimakon matsoraciya,ina fatan kun fahimci kuskuren dake gurin,na gode_ Tun daga ranar data fuskanci ina ya sanya gaba take rufe dakinta da wuri su kwanta ita da fadeela,idan yazo ya gani saidai ya koma ranshi babu dadiyaso ya sake wasata da kyau ya kuma more kafin lokacin tafiyar kamar yadda maji ta gaya masa. Amma a kwanaki itace take shirya musu breakfast tayi musu abincin da zasuci idan sun dawo,ta kuma hada lafiyayyen dinner. Sai a lokacin ya vadda da zancan hausawa da sukance a rashin uwa akanyi uwar daki, tabbas a rashin samun girkinta yake yaba abincin Jacob, bai taba tunanin akwai wani da yakai Jacob iya girki ba sai gashi ya samu wadda ta fishi nesa ba kusa ba. Hankali kwance säahar keyin shirin tafiyarta,shiru da meenal da hajiyan sukayi da al' amuransu jikin säahar ya bata tabbas ba a banza ba,saidai ita kanta cikin satin baccinta ragagge ne, don addu'ar neman nasara tuquru takeyl. Qarfe biyu na dare yana zaune cikin dakin nasa yana sarrafa CCTV camera din dake cikin dakin nata,duk da ta haramta kwanansu tare amma hakan bai haramta masa ganinta ba ta hanyar CCTV camera din, abinda ya zame masa kamar ibada,a kullum idan ya dawo daga aíki ya kammala komai sai ya zauna yayi bitar wuninta na ranar a cikin dakin,saidai daukar kadan yake samu,duk da cewa yawanci zazzafar dauka ce dake yawan dagula lissafinsa,don a nan ne yake samun damar ganinta sosai, abubuwan da bata iya barinsa ya kalla yadda ya kamata a nan yake samun dama. Kwanakin data dauka tana sallar daren duka yana sane da su,ko a yanzun da tafiyarsu ta kama jibi ne yana bibiye da komai,amma har yanzu baici karo da inda tayi maganar tafiyar ko wani abu daya danganceshi ba. Ajiyar zuciya ya sauke,ya tabbatar gobe zai tafka mata tsiya ne,bazai iya bari tayi tafiya me nisa haka ba ba tare da sunyi kyakkyawar gaisuwa ba,sai ya maida daukar ya rufe ya koma duba history na jiya da daukan da camera din ta yiwa sashen hajiya qarama. Bude video din yayi yana sake nazari,hajiya mansura ce ita da hajiya qaraman,kowacce fuskarsa cikin bacin rai,kuma magana suke da juna cikin fushi, saidai har yanzu ya kasa tantance me suke gayawa junansu saboda sunyi nisa da ma'ajiyar camera din tsaron. Ya jima yana duban fuskokinsu su biyun,yadda suke a haka a hakan ake nuna masa su cikin mafarkinsa,ya dade sosai yana sake bibiyar wasu motsinta na baya dake ajjiye sannan ya kashe yana sauke ajiyar zuciya "Akwai gagarumin abu a qasa" ya furta a hankali, gaba daya zuciyarsa da gangar jikinsa suna bashi akwai babban al' amarin dake tunkaroshi, saidar ya rasa meya wannan?. *********Washegari tun bayan sallar isha'i da sukaci abincin dare ya kafa ya tsare a falon, wanda kusan wannan ba al'adarsa bace yafi zama a balcony dinsa study room ko cikin dakinsa,kasancewar shi din mutum ne maras son hayaniya ko a shiga al' amarinsa. Fadeela na lafe a jikinsa tana ta masa hira,yayin da nashi idanun kekan säahar duk wani shiga da fita da taketa yi tana sake kammala musu kayansu na tafiyar da zasuyi a gobe saman idanunsa ne. Tun a yanzun ya dinga jin wata kewa tana ratsashi. Bai tashi a gurin ba har fadeela tayi bacci a jikinsa,sai ya gyara mata kwanciya yana canza tasha zuwa News channel. Sai data tabbatar komai ya kammala,ta canza kayan bacci fadeela kawai zata dauka su kwanta sai ta zura hilabinta ta sanya slippers dinta ta fito falon don dauke fadeelan su kwanta. Takunta ya sanyashi waiwayawa,kallo daya tak yayi mata ya dauke dubansa daga kanta zuciyarsa tana harbawa,cikin baby hijab din jikinta fuskarta tavi wani mugun kyau,tattausar rigar baccinta me gajeran hannu ta fidda qirarta ta coca-cola shape, duk da idanunsa baya kanta amma idanun zuciyarsa yana tattare da ita,ya kuma qididdige takunta har ta iso gareshi,ta kuma duqa zata dauki fadeelan "¡dan kin kwantar da ita ki kawomin coffee daki" "Tom" tace da shi ba tare data kawo komai cikin ranta ba, don zuwa lokacin ta fannin abinci bata ayashi ta data ta bashi. Ba abinda take tunawa a duk sanda ya bugaci abinci sai yadda yayi missing mahaifiyarsa a shekarun da yake da buqatar kulawarta,hajiya qarama ta shiga tsakaninsu,ta tarwatsa soyayyar da Allah ya ginata,sannan ita din bata zauna ta basu irin kulawar da uwa ke bawa danta ba. Kasancewar sai ta tsaya ta dafa ya dan ja lokaci wannan ya bashi damar gama nasa shirin baccin. Yana zaune saman gado rabin gafafunsa lullube da duvet ta shigo dakin da sallama. Bata lura ds kallon da yake binta da shi ba,saboda ta qagu ta gama dashi taje ta kwanta ta samu isashen baccin da zata farka tsakiyar dare tayi addu'a ta musamman saboda samun dacewa da nasara. "Migo min" ya fada a nutse yana lumshe ido, sassanyan qamshinta yana hautsina tunaninsa tare da qara masa kwadayinta. Hannunsa cikin nata kamar yadd ya saba mata duk sanda zata bashi wani abun sha ya riqeta tsam. Duk zafin coffee din haka ya dinga kurbarsa da zafi zafi saboda wata wuta ce ke ruruwa cikin ruhinsa da zuciya,dama kowanne sashe na gangar jikinsa. Kurba hudu kacal ya gama dashi,ya zare cup din da daya hannun yayi wurgi dashi cikin zafinsa, saboda ji da yakeyi cikin jikinsa yakai maqura. Gaba dayanta ya fincikota jikinsa,ta samu kyakkyawan masauki tsakanin girjinsa da tsakiyar qafafunsa,yayi mata wata zazzafar runguma yana laluben bakinta da nasa bakin dake dauke da dumin coffee. Kyarma jikinta ya fara yi ganin yadda gaba daya yake a gigice yadan dakata kadan yana duban idanuntà da jirkitattun idanunsa tamkar wanda yasha abun maye "Baki d imani wallahi, kin sani sarai yadda na jigata a kwanakin nan, amma kin dauke kanki kamar baki sani ba,har yanzu baki sona ne?, ko irin dan kadan din nan ki soni mana don Allah" ya furta kamar zai shide saboda yadda qamshinta da dumin jikinta ke sake birkitashi,ga abubuwan dake tone masa ido yau din suma cikin yancinsu suke, don rigar baccin ne kawai a jikinta "farewell mee..." Kasa garasawa yayi saboda muryarsa gaba daya ta sarqe, sai ya lalubi bakinta ya fara aike mata da wani zazzafan kiss kamar zai cinye bakin, saidal kuma cikin taushi da laushi. Duk yadda take zaton jikinta zaiqi karbar abun sai zancan yasha banban,a duk wani saqo da ya aiketa masa sai ta samu jikinta ya karbeshi da kyau har fiye da yadda ya kamata. Yaqi ta dinga yi da zuciyarta saidai itama zuciyar tako ina lugiguita yakeyi cikin salo da qwarewa,duk da haka saboda qi fadi bata fasa yunqurin tureshi ba. Cak ya dakata da abinda yakeyi, sanann a zafafe ya kama hannuwanta yayi musu kyakkyawan rigo yana kallon tsakiyar qwayar idanunta fuskarsa a dinke tsaf. Bai shirya ba wata qaramar dariya ta kufce masa yana sake ci gaba da kallon idanunta da suka sauya launi, tabbacio ko ta ina itama sagon yana isar mata "Malama you are just pretending fa,amma tun daga zuciya gangar jiki dama ko ina na jikin sun nuna suna karban saqo,so stop please,let's enjoy our selves" kunya ce ta sanvata tattarashi ta tureshi da sauran garfin da ya rage mata, baiyi musu ba ya fada gefe,sai yayi rigingine idanunsa a lumshe yana sakin boyayyen murmushi "Okay,baki buqata ko?‚am sorry you can go" ya fada yana jan duvet ya lulluba har kansa. Minti daya biyu sannan yaji ta motsa tana shirin sauka,ya birkitota da sauri ya aza mata nauyinsa yana dariya "Ki daina pretending din nan,ki fada kanki tsaye, kina bugatar mijinki simple and easy" bai bata damar yin magana ba ya hade bakinsu guri guda. Bata sake turje masa ba,saidai cikin ranta ta cika da mamakin yadda komai yake kai mata inda bata zata ba. Da wannan damar shima yayi amfani ya kwance mata lissafinta tasss fiye da wancan ranar, shima dai daga baya kukan kunya ta saki,ya biye mata yana bata haquri dariya kuma na cinsa,yayi mata kyakkyawan masauki a faffadan qirjinsa ta boye fuskarta da kyau tana kula "Kiyi haquri,tsautsayi ne ko? ‚kuma baya wuce ranarsa" ta fahimci gatse yake mata,saita tattarashi ta ture tana sauka a gadon ta nufi qofa bayan ta lalubi rigarta da ayar. Baiko motsa ba saima gyara kwanciyarsa da yayi yana dariya qasa qasa,ya fuskanci idan ba sauketa yaci gaba da yi daga kan layi ba ba zai taba sauke mata zafin kanta a nan kusa ba "Idan aka shiga turaka ba'a fita sai da asuba koma da safe" dole ta dakata, kamar zata saki kuka ta dawo da baya ta zauna bakin sofa bed. Kusan minti sha biyar tana zaune,har ya miqe ya shiga toilet yayi wanka ya fito. Gajeran wando ya sanya wani cotton fari qal,ya shammaceta ya isa gabanta. Hannu ya sanya ya lakuce dogon hancinta "Indai kikaci gaba da wannan abun bayan kun dawo daga tafiya tabbas aure zan gara" daga haka bai jira komai ba ya sunkuceta ya wuce gado da ita. Tas ya tube rigar data sanya ya kuma matseta cikin jikinsa yana lullubesu da duvet tare da sakin wata sassanyar ajiyar zuciya. A duk sanda ya samu wani mu' amala tsakaninsa da ita yanajin duniyarsa kamar ta banbanta datà kowanne dan adam,wata mahaukaciyar soyayyarta da kullum yake goqarin ya saisaita kansa da ita kada ya wuce gona da iri qara ninkuwa takeyi cikin ransa. Yayi imanin batasan me yakeji tattare da ita bane,da duka ta sauke abinda takeji din akansa. Can qasan maqoshi tsakiyar kunnuwanta ya furta a hankali "| always sleep better with you by my side,gobe da sauran kwanakin bansan ta yadda zanyi bacci me dadi har haka ba,to be honest,at this point in my life, i just need one women to love me hard, and never leave me alone" ya furta da alama har cikin zuciyarsa abinda ke ciki din kenan. Kashe mata jiki kawai yayi gaba daya,saita lumshe ido kawai ba tare data sake motsawa ko tace komai ba. Da asuba ma bai ayaleta ba,kiran sallar farko taji ya sake cewa "I want to water the plants" bata sake tunani na biyu ba ya sake wurgata wata duniyar,yayi alqawarin sai ya bar mata abun tunawa tun daga tafiyarta har dawowarta,muddin baiyi hakan ba ya tabbata looser,bai kuma amsa sunansa na Muhammad toufeeq ba,yaci alwashin goge mata haddarta fes da duk wani daagiya tata da qi fadinta. ****Qarfe tara na safiyar ranar suna a filin sauka da tashin jiragen sama na mallam aminu kano. Yana rige da hannun fadeela,fuskarsa da safiyar yau din ke cike da annuri cikin shigar farin yadi na maza me taushi wanda yake da shara shara har kana iya hangen fara qal din vest din jikinsa,ginannen jikinsa dake a tsaye qyam ya zauna cikin dinkin ya kuma dace dashi. Sassanyan kyansa me cakude da kwarini ne shimfide akan fuskarsa,zubin halitta da kyansa kuma yana ci gaba da fusgar hankalin duk wata diya mace. Sãahar na tsaye a gefe cikin doguwar riga sakakkiya sosai wadda ta yiwa rolling da mayafin da ya sauka har mazaunanta ya rufesu sosai,shiga ta biyar kenan da tayi a safiyar kafin ya danne zuciyarsa ya haqura aka taho a hakan. Haka kawai yau din ta samun kanta da satar kallonsa,kyakkyawan murmushin sa da wani irin aji cikin maganarsa da aikinsa. Karo na barkatai idanunta ya sauka akan fuskar 'yammatan dake facing dinsu,ta sake samu idanunsu a kansa dukka su biyun. Janye dubanta tayi daga kansu tana jin wani abu yana tsaye mata a wuya. Sake maida kallonta tayi kansa a sace,sai takejin babu dadi cikin ranta, tunda suka fito cikakkiyar magana bata hadasu ba,yayi ma kamae baya ta tata, dukka attention dinsa na kan fadeela. Zaman gaba daya taji baiyi mata ba,kallon da matan dake gurin suke masa taji ya fara hawa kanta,duk da wani sashe na zuciyarta nason qaryata hakan, amma tabbas tasan she's not comfortable. Ajiyar zuciya ta sauke sanda lokaci da zasu wuce zuwa ciki yayi. Sai a sannan ya waiwayo suka hada ido,sai ta janye idanun nata gefe tana tura baki gaba wanda ita kanta batasan tayi ba,a qasan ranta tana cewa "Dan rainin hankali sai yanzu yasan ina wajen" shi da fadeelan suka qaraso gurin,ya miga hannu a tausashe ya rigo nata hannun yayi kissing sannan ya dage hannun sama alamun yanason miqar da ita. Kamar ba zata tashin ba, amma idanun mutum biyun nan da sukafi kowa baci a gurin ta fahimci yana kansu,sai ta samu confidence sosai na miqewar, tana kuma miqewar ta fada jikinsa tayi hugging nasa tightly. Zafafa biyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI * Book 02Page 47 To dama shi din me neman kuka ne aja jefeshi da kashin awaki inji hausawa lea, maida hannuwansa yayi ya rufeta ruf "Na baki amanar kanki da kanki, kiji tsoron Allah ki kulamin da kanki,Allah ya sani na barku kuyi tafiya ne a bisa harshen maji, saboda duk duniya babu alfarmar da zata roga na kasa yi mata, ki kularmin da amanar kanki da kanki,i love you and am gonna miss you" wadan nan sune kalaman da suka yiwa säahar abokan zama har cikin jirgi. Yana tsaye bai matsa a gurin ba har jirginsu ya tashi,ya kuma nausa dasu qasar Germany ba tare da Muhammad toufeeq jarma yasan abinda zasuje yi can ba. _tofa, Allah ya kiyaye tsautsayi da asara,muje zuwa dai,munata gangarewa_ 😃 *_GERMANY_* HOMBURG Zweibrücken Airport_ K'arfe biyu agogon qasar Germany jirginsu ya sauka a Zweibrücken airport dake homburg, bisa jagoranci da kulawar asibitin wanda sajjad ya hadasu da dukkan wanda ya dace da zai musu jagora akan komai kafin isowarsa da ya shirya yi ba tare da ya gayawa sãahar din ba suka sauka a leaonardo hotel dake kusa da Saarland university hospital main campus, inda anan ne suka suka shirya ganin prof Dr med Klaus fassbender wanda shine shugaban department na neurology and epileptology na jami'ar gaba daya. Miss Sophia da mr Stephan sai da suka tabbatar da komai yayi settling, hatta da layin wata na kira suka bata sannan suka ce su huta, sai zuwa gobe ne appointment dinsu da Dr Klaus. Ta window din dakin hotel dinsu akwai kyakkyawan view na garin Saarland,ta fidda kayansu tana ajjiyewa a inda ya kamata, ita kuwa fadee na daga can tana kallon garin tana zuba mata surutu har ta gama,gamawarta nata yayi dai dai da isowar ma'aikatan restaurant na hotel din da lunch dinsu. Karba tayi tayi godiya ta rufe qofar tare da kiran fadeela tazo taci. Kusan duk wani motsi na fadeelan na kan idanunta,zuciyarta nata karyewa,sai a yanzun takejin kamar tayi wauta data taho gari ya gari ita daya da yarinyar mutane, zuciyarta a raunane tana duban yarinyar,Allah shine masanin gaibu, zata tashi ko kuma komai zai sake rikicewa ne?,ko kuma ita zata zamo sila na garuwar ciwon nata?. Da sauri ta kawar da wannn tunanin ta hanyar kiran sunan Allah, ta sauko ta jawo abincin suka fara ci tare. Ko da suka kammala layin ta saka a wayarta,afifa ce mutum ta farko data fara kira sannan maama dinta,sai kuma mahaifinta Dr girema "Baki kiramin abby na ba" fadeela ta fada tana karyar da kai. Dan murmushi ta saki tana juya wayar a hanunta,fadeela nason sakata yin abinda batayi niyya ba, amma tausayin yarinyar takeji, kowanne motsi na yarinyar tausayi yake bata,ta kuma kawota qasar da babu kowa nata sai ita,itace uwa da ubanta,to amma bata da tabbacin tana da number nasa a wayarta,don haka ta fara kiran nadeeya. Kiran nadeeya din shi ya dauke hankali fadeelan daga kiran abby din,suka dinga hira kafin daga bisani sãahar ta karba wayar "Nadeeya ki turawa fadee number abby" dariya nadeeyan ta saki a boye "Fadee ko ummin faddee, aunty N kada dai ace har kin fara missing yaa moha?" "Kinga sister nadeeya,kin fara rainani ko?" "Tuba nake aunty N,waye ni da raina matar babban yaaya,so kike yayi tamaula da ni?, already na miki saving number din nasa a wayarki saboda rana me kama da wannan" sai kiran ya yanke. Wayar kawai ta sauke tana kalla,sai kuma murmushi ya subuce mata, yaushe har nadeeya din tayi saving number bata sani ba? ,sal ta fara binciken contact nata, amma ku suna me kama da nashi babu,daga qarshe tayi finding out suna guda daya da iya saninta dai ba ita tayi saving number din ba FOREVER. A bisa dole ta saki dariyar da batayi niyya ba,ko yaushe ya zama forever din oho?. Tana shirin editing ta canza suna taji fadeela na kiranta tazo ta kunna mata tv,dole ta ajjiye wayar ta fita gurinta. Washegari miss Sophia da mr Stephan ne suka sake dawowa, already ta shirya saboda tasan da zuwan nasu. Tun daga yadda suka samu asibitin ta tabbatar afifa ta zaba musu gurin da yafi dacewa. Sun gana da Dr Klaus ya kuma yiwa säahar dukkan tambayoyin da suka dace,ya shirya komai ya kuma bada gwaje gwajen da za'a fara yi mata kafin a fara zancan surgery. Cikin kwanaki hudun duka basu wani zauna ba,ta bada hankalinta dari bisa dari akan aikin fadeelan da zirga zirgar asibitin, don ma wasu abubuwan da yawa basu zasuyi ba daga asibitin ne. Kwana take saman abun sallah tana addu'a,sunyi waya da maji tun randa suka iso da daddare, kuma daga ita har afifa suna samun update na yanayin da ake ciki, dukansu kuma neman visa ta shigowa Germany sukeyi kafin ranar aikin,saidai dukansu basu gaya mata ba. Cikin kwana biyar kacal komai ya kammala, Dr Klaus kuma ya tabbatar mata part na brain din fadeelan dake bada matsalan seizure din nata za'a iya removing nasa,so ta cancanci surgery, amma kafin nan zasu bata treatment na sati biyu, zasu rigeta a asibitin. Kukan farinciki ne ya qwace mata, bakinta ya kasa gajiya da addu'a da fatan samun nasara a gareta da fadeelan baki daya. A ranar suka bata daki da komai da komai, su zasu dauki nauyin kula da ita,basa buqatar majinyaci,akwai qararrun ma'aikatansu da zasu bata duk wata kulawa data dace. Tayita roqon alfarma su barta gurinta amma suka bata haquri kan haka tsarinsu yake,dole a ranar ita kadai ta koma hotel, saidai sam bacci yaqi zuwar mata,kewar fadeelan takeyi sosai,sai tayi alwala ta hau abun sallah kawai ta tsaya gaban ubangiji. ******Bai taba kawowa zata dauki wadan nan kwanakin ba tare data nemeshi ba,cikin kwanakin gaba daya karsashi da komai nasa ya ragu,yana jin kamar yayi missing wani part na jikinsa, komai yana yinsa ne kawai cikin qarfin hali da juriya,bai taba kawowa cewa ta kama zuciya da rayuwarsa har haka ba sai a wannan lokacin "Wanann wanne irin abu ne?" Ya tambayi kansa da kansa a wani dare da bacci ya qauracewa idanunsa. A nutse ya miqe ya sauka daga saman gadon nasa,yana sanye da wasu silk pyjama bagaqe da suka fitar da zallar kyansa cikin hasken dakin da bashi da yawa,yana bugatar wani abu da zai debe masa kewarta,yana jinsa kamar mara lafiya, kowanne sashe na jikinsa yana bugatarta. Slippers dinsa ya zura,ya miqa hannu zai dauki wayarsa dake kan bedside drawer sai wanilabu yaja hankalinsa. A nutse ya miqa hannu cikin wani glass bowl dan garami ya dauko wani abu. Dan kunnenta ne,dan kunnen da ya fadi a wancan ranar cikin elevator,a wancan lokacin da yake matuqar jin zafi da haushinta, zafin da ya tabbatar yana jinsa ne a sannan saboda yadda zuciyarsa ta kasa jin qinta a ransa kamar vadda yakejin na sauran mata,yana tsoron faruwar wani abu tunda har zuciyarsa ta kasa jin wannan emotion din a kanta sai wani feeling na daban. Wannan abun dai da yake gudun faruwarsa sai gashi a yanzu ya tsinci kansa dumu dumu a cikinsa, dumu dumu din da ko gefenta bai taba isa ba sai a wannan lokaci, mummunan kamu na soyayya me wahalar cirewa a rai, soyayyar da ya fuskanci tamkar tanason jefashi zuwa ga son maso wani. Yana shaugi da burin ganin martani me zafi daga kan fuskarta,duk da ya sanya zuciyarta tayi laushi yadda ya kamata, amma mizanin soyayyarsa a zuciyarta yana hasashen kamar bai kai ba,yana tsoro da fargabar sake, afkawa wani ramin da baisan iyakacin zarfinsa ba a kanta. A kullum ya tuna kulawa da tattalin da ya bawa ameesha da sakamakon da ya samu daga baya sai gwiwarsa ta karye akan lamarin soyayya. Kissing na earring din yayi, sannan yasa hannu ya jawo drawer din ya zura,baikai ga rufewa ba dairy dinta daya dauko yaja hankalinsa. Qasan ransa ya gayawa kansa ya samu abun debe kewa,sai ya fiddoshi yana budewa,ya sake bude page din farko ya maimaita rubutub rannan, sai ya zare slipper din da ya sanya ya maida jikinsa kan gadon ya zauna sosai vana sake bude next page. Kai tsaye a kuma tsanake ya fara bin rubutun dake shinfide cikin tsari da kuma qwarewa, tun daga farkon haduwarta da ADAM,a nan ya dinga gaza jure wasu abubuwan ya dinga jin wani abu me kama da zallar kishi yana tabashi saidai zuwa sanda zai kammala karanta labarin zuciyarsa da ma gangar jikinsa sunyi tubus _Thats me,hurt in private, heal in silence,we fall, we learn we rise_ _My dear heart,one day you will heal to such an extent that you will smile as if it was never broken in sha Allah_ “In sha Allah" din shima ya maimaita a bayyane yana rufe bangon qarshe na littafin,fararen zagayayyu idanun nan nasa sun canza launi, kwanyarsa ta cika da abubuwa masu tarin yawa,ya mots lips dinsa a hankali "We are all hurting and healing in silence, tabbas we go through one similar condition, i have made many errors in my life,but loving you is definitely the thing i have done right!" Ya furtawa kansa da kansa yana lumshe nasa idanun,tashi madubin rayuwar na haska masa,cikin jiki da zuciyarsa wani irin gamammen aminci da kanta yana gauraye jinin jikinsa, da gaske! Allah yaso wanke musu kowanne bacin rai da suka shiga,shi yasa ya jarrabesu a mabanbantan gurare da kuma mabanbantan mutane. Hikimarsa!, Ya hadasu zaman tare na har abada a sannan shine zasu Fi fahimtar muhimmancin funansu "Exactly!" Ya fada yana bude idanun nasa. He really missed her,yana jin kamar zai zauce da son ganinta, me yasa tun tuni bai karanta diary din ba? ‚sai yanzu da tayi nesa dashi. Saman gadon ya zauna sosai yana duba number dinta, saidai duka kiran da zaiyi matan a kashe layin,ya sani dama ba samunta zaiyi ba,kawai idanunsa sun rufe ne da son jin muryarta. "A ina zai samu number dinta?" Itace tambayar dake masa yawo akai. Har zai kira nadeeya ya tambayeta sai kuma ya fasa gudun raini. Maji ya tuna, don haka ya maida akalar kiran nasa gareta, KARON FARKO da wani qulli ya warware daga tsakiyar kansa ba tare da ya sani ba. A dai dai lokacin kuma hajiya qarama tayi wata mummunar firgita cikin baccinta,ta kuma miqe ta zauna sosai saman gadonta a gigice tana dube dube. Fadeela ta gani cikin asibiti, asibitin ya cika da yan uwa da abokan arzigi wai ana tayata murna ta warke daga ciwonta,yarinyar tana ganinta ta karbi wuga daga hannun säahar dake yanka mata fruit tayo kanta da gudu, tana tsaka da gudun ta farka a mafarkin. Jikinta sharkaf da gumi ta sauka daga gadon,ko ina na jikinta rawa yakeyi tanason ta fassarawa kanta da kanta mafarkin. Kai tsaye ta isa drawer din data killace magungunan da take sauyawa fadeelan dasu,ta fiddosu gaba daya ta fito falonta dasu. Zaman dirshan tayi saman carfet ta zazzagesu,ta kuma hau irgasu daya bayan daya tsaf har ta gama "Turqashi" ta fada a bayyane tana goge gumin fuskarta. Yau kwana d'ai d'ai har kwana sittin bata samu damar bawa fadeela maganin ba "Ko warkewar ne ma a gaske ai sai tayi, tunda na zauna yarinya qarama tana son firgitani da kawomin tsaiko akan aiki na" ta fada a fili kamar wadda ke magana da wani. Tattara magungunan tayi ta maida cikin leda tana rayawa a ranta yanzun nan komai duhun dare sai ta isa dakin fadeela ta aiwatar da shirinta. Daxu daxu ta dawo daga Cotonou order din wasu atamfofi,bata da masaniyar ma fadeelan basa gidan yadda ta saba ba,sai kawai ta sauka a sashenta tana huce gajiya. Mayafi ta yafa,ta kuma taka a hankali ta fita a sashen nata. Farfajiyar gidan tsit take,babu kowa sai hasken fitilu da kuma kukan qananun qwarika dake cikin tsirran dake baibaye da gidan. Babu tsoro ko fargaba ta sanya spare key ta bude qofar falon ta kuma saka kai cikin takatsantsan. Bata tsava a ko ina ba sai dakin fadeelan, ta tura ta shiga ta sauke ajiyar zuciya ganin babu kowa,ranta ya bata yau a sassan toufeeq din zasu kwana kenan, don tana lissafe da duk sanda basu kwana a nan din ba suna sashensa "Bagar matsiyaciya,kin kusa fita daga rayuwata, kin kusa barin gidan nan,gidan nan gidan meenal ne, toufeeq da abinda ya mallaka dama wanda ubansa ya mallaka duka na meenal ne da abinda zata haifa" ta sake fadi a fili cikin sumbatun da batasan tana yi ba. Zafafa biyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02Page 48 Loko da saqo na dakin ta dinga bincikawa tana neman robar maganin fadeelan,sai data gaji sannan ta samu nasarar ganota. Saman gadon fadeelan ta zazzage maganin duka,ta lissafa wasu ta kwashe,ta debo iya wannan adadin ta zuba ta cakuda su da kyau sannan ta maidata kamar yadda take ta ajjiye, ranta fes, zuciyarta na mata dadi. Har abada ba zata taba bari maji ta huta completely ba,babu wata hanya mafi sauqi da zata ci gaba da razana rayuwarta irin wannan hanya,kafin zuwan lokacin da. zata maidata marainiyar da bayan rasa uwa da uba,yaya da jikokinma suyi ma rayuwarta sallama su barta ta rayu cikin maraicinta na haqiqa,ledarta ta dauke ta juya tana fita a dakin cikin nutsuwar da sai a yanzu ta sameta. * Shuka a idon makwarwa_☺️☺️ Kira daya maji ta dauka,sai a sannan kuma yaji wani nauyi yana kamashi sanda amintacciyar muryarta Re furta sallama a gareshi, idanunta na tara ruwan hawaye,yau itace Muhammad da kansa ya daga waya ya kirata bisa radin kansa?,wacce irin farar rana ce yau a gareta?. "Muhammad" ta kirayi full name dinsa cikin karyewar murya,duk wani qunci da take ciki a dan kwanakin saboda abinda mahaifinsa ke shirin aiwatarwa a kanta sai taji yana kwaranyewa "Kiyi haquri maji,qila na tasheki a barci ko?" "Bacci Muhammad?, ina daku a wani muhalli da ban aminta da amincinsa ba ina ni ina bacci?,shekara ashirin da wani abu rabona da bacci a irin wannan lokacin, kada ka kashe Muhammad, gayamin dalilin kiran" sosai yaji zuciyarsa tayi wani mugun karyewa,duk yadda yaso ya rige hawayen da suka taso masa abun yaqi yiwuwa,UWA wata halitta ce da kaf duniya babu inda zaka samu rahamar da tayi dai dai da wadda ke cikin zuciyarta akan d'anta,shin sau nawa ya hana idanunsa bacci kamar haka ya yiwa maji din addu'a koda na sati guda ne? ya sani duk salla ya sanya goshinsa a qasa sai ya musu addu'ar "Rabbirhamhuma kama rabbayani saghira" saidai yasan ko kaso daya cikin dari na wadda ita ke musu baiyi ba "Ki yafemin majl,am sorry for all the....." Sargewa muryarsa tayi,sai kuma maji din ta tari numfashinsa "Muhammad kai da 'yaruwarka baku taba yimin laifi ba,kuma ba zaku taba yimin ba,idanma kunyi na yafe muku har wanda zaizo a gaba" furucin da ya sake kashe masa jikinsa kenan,ya cikata da godiya sai kuma ya kasa cewa komai "Baka neman matarka Muhammad?" Ta tambayeshi kai tsaye,saboda tasan basuyi waya ba, hakanan ta tambayi nadeeya ko ya karbi number a wajenta tace a'ah "Ya zanyi maji? ji nake kaman ni kadai ne a gidan" Yayi subutar bakin fada,bai kuma farga ba sai da murmushi me sauti ya qwace mata "Zan tura maka number dinta,ka kira matarka, Muhammad ka riqe matarka fiye da rigon da zaka yiwa duk wani abu me muhimmanci cikin rayuwarka" kai yake jinjinawa "Ka tayani addu'a,wani al'amari ne ke son sake waiwayowa cikin rayuwata ya kuma tunkareni, Allah yayimin zabi mafi alkhairi koda zuciya ta bataso" maji ta fadi a sanyaye. Hankalinsa yaji ya tashi a lokacin farko da ya fara jin haka "Me yake faruwa maji?" Murmushi tayi "Ba wani abu bane, karka daga hankalinka, addu'a kawai na bugata daga gareka" "Amma dai kina lafiya ko? ‚ba wani abu dake damunki?" Idonta ta rufe hawayen da take tattali suka sauka,lallai babu wani abu tabbatacce sai ikon Allah,yau itace toufeeg din da aka nesanta tsakaninsu ta kowacce fuska ke tattalin farincikinta da tambayarta lafiyarta? "Lafiya galau nake Muhammad ta kowacce fuska,ka kira matarka, Allah yayi maka albarka" daga haka ta yanke kiran saboda kukan da taji yanason kubce mata. Bata daga cikin mutane marasa yafiya,to amma kuwa anya zata iya yafewa fauziyya?. Ba jimawa number wayar ta shigo wayarsa "Germany?" Ya fada a hankali bayan ya gama qarewa number kallo ya kuma fahimci code din wanne country ne maqale a jikin phone number din. "Me sukeyi a Germany? ‚basa tare kenan da maji" ya gayawa kansa sanda wayar ta soma shiga tana ringing. Idanunta da sukayi nauyi saboda kuka da bacci ta daga,a kasalance takai hannunta ta jawo wayartata,batare data duba ba ta daga,saboda jikinta ya bata afifa ceko maama,tafi zaton afifan ma don haka tace "Bestie" cikin wani irin sanyi sanyin da ya sanyashi jin saukar muryarta cikin kowanne sashe na jikinsa,ya lumshe idonsa sannan ya sakar mata sallama cikin taushi. Tashin farko ta nemi baccin da yake idanunta ta rasa, saita maida jikinta ta jingina da jikin gadon dake kusa da ita tana amsa sallamar zuciyarta na wani irin harbawa "Matata nake nema,tana kusa?" Ya fada a nutse. Rasa amsar bashi tayi don haka tace "Bata nan" garamin murmushi ya saki "Matar toufeeq fa?" Salon yadda yayi maganar ya sake daburtata tare da kashe mata jiki gaba daya "'Idan sago ne ka bayar sai a bata" jikinsa ya amsa gaba daya,sai ya gyara zamansa tsakiyar gadon sosai yana sakin mata murmushin da sautinsa ya sauka har kanta,ya kuma tayar mata da kowacce tsiga ta jikinta "Sago ne me nauyi,wanda babu kunne da zai iya dauka,hakanan babu harshen da zai iya isar dashi,saboda kebataccen sirri ne da ya shafi mijin da kuma jarumar matarsa.....Please tell her, her taste,scent and feel of her skin next to mine.....its all i want every single night,but ta barni cikin kewa da matsanancin so, ki gaya mata am falling and falling and falling for her entirety,ki sake gaya mata i want to feel her skin and i want breath her in i want her in the worst way,| want kisses every corner of her body to express all love which ¡ have in my heart,a million feelings all for one person" gam ta rintse idanunta, tana jin wani abu me nauyi yana saka saman zuciyarta,wani irin yanayi da bata taba tsintar kanta a cikinsa ba,wani irin saqo da ya isa kowanne sashe na gangar jikinta dama zuciyarta,wasu kalamai masu matugar nauyi da zafi da bata taba sauraren kamarsu wajen zaqi da qawata zukata ba. Duk da kasnacewar adam a baya gwani wajen iya tsara kalamai, amma a yanzun sai takejin wadan nan kalaman da kuma kalaman adam,tamkar an dauko ginin gargajiya na ainihi an sakashi tsakiyar fadar white house ta amurka "SAHR" ta tsinci kalmomin sunanta a bakinsa da wani irin amo me narkar da zuciya kamar yadda ya saba kiranta "Am too late to be your first. But right now am preparing my self to be your last" kasa jurewa daukan nauyin kalamansa tayi,tsarin yadda yake furta kalaman kadai sun banbanta da muryarsa da yake magana da ita ko da yaushe,wani irin shauqi da soyayya me tsananin tasiri ta sanya ya rasa kowanne kuzari a jikinsa,yana jiran yaji koda kalma daya daga bakinta, amma maimakon hakan sai katse kiran yaju tayi. Zare wayar yayi a kunnensa yana dan sakin qaramin murmushi, kafin ta katse wayar ya iya tsinkayar yadda taja numfashi da sauri cikin sheshsheqa. Wayar ya sulale ya ajjiye a gefansa,ya miqe yana sake jin wani irin shauqi tare da tsananin tausayinta yana fusgarsa. Diary din ya rungume a qirjinsa yana jin tamkar ita ya runguma,ya zura slippers dinsa ya sauka a gadon a hankali ya fice daga dakin. A nutse ya murda qofar dakin nata, idanunsa da hancinsa suna sake tabbatarwa lallai nan din muhallinta ne, ko ina a tsaftace a kuma gyare da sassanyan qamshinta me wani irin sanyin da bai taba jin irinsa ba. Kai tsaye ya wuce gadonta,ya haye abinda tare da jan duvet dinta ya kawoshi saman fuskarsa,yakuma dauki pillow dinta guda daya ya rungumeshi saman fuskarsa yana sansanar sassanyan qamshin hair mist dinta. Har cikin kwanyarsa ya zuqi qamshin da kyau sannan ya saki pillow din ya dawo qirjinsa. Sake bude dairy din yayi duk da ya gama karanceshi, idanunsa suka sauka saman page na goma layi na farko "FAKE MEDICATION" ya karanta zuciyarsa na harbawa,yanayin fuskarsa ya canza ya rufe littafin a hankali tunaninsa yana komawa baya "Ko shine dalilin da yasa taqi yarda da kulawar kowa akan fadeela? ko wannan ne dalilin da yasa ta dauki nauyin siya mata magani tare da bata maganin da kanta ba tare data bugaci kowa ya kusanceta ba?. Meye ya sanyata wannan tunanin? ,wannan matakan tsaron masu garfi haka "Hasbiyallahu la'ilaha huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim" ya fada yana nutsa yatsunsa cikin sumar kansa me santsi da laushi, sunan hajiya qarama kawai ke yawo cikin kwanyarsa,wani irin gumi ya yanko masa, ya sauko a hankali daga saman gadon, cikin jikinsa kawai yaji yana bugatar bibiyar footprint na CCTV cameran da bai samu bibiya ba a yau. Saman qawataccen madaidaicin study table dinsa ya zauna,ya fara bibiyar motsin komai na dukka guraren da ya sakawa CCTV camera din. Cikin mintunan da suke na qarshe,wadanda suka nuna masa awanni biyu da suka shude kenan yana gab da kammala kalla ya koma parlor din hajiya qaraman, inda yayi ajiyar CCTV camera din ba tare da saninta ba. Fitowarta daga dakinta afujajan yaja hankalinsa,yayi zooming na video din take komai ya bayyana,sak irin robar da me aikinta ta yar,tablet din da a ido suke kama da irin na fadeela,gama irgasu da ficewarta,sai yayi hanzari ya koma sashen CCTV din dake sashen su nadeeya din. Yaga wucewarta falo ya duba ta dakin sãahar ba alamar motsinta,gabansa yana faduwa tare da ambatar "'La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" ya shiga bangaren dakin fadeela,cikin tsananin tashin hankali jikinsa nason rikicewa,saboda tuni zuciyarsa ta gama hasaso masa komai. Ko ina na jikinsa ya dauki kyarma,ya saka tafin hannunsa guda daya yana lullube fuskarsa sanda hajiya garaman ta gama musayar qwayoyin tare da bin aikin nata da wadan nan kalaman. Gumi ne ya jiqashi sharkaf bakinsa yana rawa kamar wanda iskar qanqara ke kadawa "Hajiya why?,why hajiya why!" Ya fada da mugun qarfi yana dukan table din har sai daya amsa kamar zai balle gida biyu "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" yayita maimaitawa,hawaye suna sauka daga idanunsa zuwa fuskarsa. Duk da yana iya tuna wasu abubuwa kadan kadan da suka faru zamanin quruciyarsa, amma bai taba tunanin hajiyan zata iya aikatawa fadeela irin wannan mummunar ta'asar ba "Me tayi miki?! me tayi miki?!, ni zaki yiwa haka!, ni zaki illata ba ita ba,she's innocent, batasan me duniyar ke ciki ba har yanzu!" Ya furta da qarfi kamar mahaukaci,ya kasa controlling kansa gaba daya,wani irin tashin hankali da matsanancin fushi yakeji sosai yana cin zuciyarsa "Ya Allah, ya hayyu ya qayyumu,la takilni ila nafsy darfata ainin,aslih li sha'any kullahu ya Allah, astagfirullah wa'atubu ilaihi" harshensa ya samu ya kama wadan nan addu'o'in, yayita maimaita su babu adadi. A hankali nutsuwa ta fara saukar masa,saidai kuma hade take da wani irin mugun ciwon kai mara misali,bai shiryawa kwanciya ba sam amma tilas sai da gangar jikinsa takai ga gadonsa, idanunsa a runtse yana kiran sunan Allah kowanne sakan,yanason tuna wanne zunubi fadeelan ta aikata mata?, meye takeson cimmawa?, tabbas säahar ta hango abubuwa masu tarin yawa,abubuwan da yaci ace ya zauna sun tattauna komai zafin kanta da dojewarta, amma zuwa yanzun anzo gurin da bazai iya jurewa dawowarta ba. Sosai ta dinga bitar kalamansa cikin kwanyarta. Juyi kawai takeyi cikin duvet tana jinta so lonely,gadon yayi mata wani irin fadi,ba fadeela,wata zuciyar tace BABU KUMA ABBYNTA ko?. Kamar zata qaryata amma sai ta kasa qaryatawar, saidai kuma tana mamakin ta saba da shine da har zataji kewarsa? bata da amsa face maida idanunta da tayi ta lumshe kawai. Zafafa biyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02Page 49 Washegari har qarfe sha biyu na rana bai fito ba,yana kwance yana jinyar jiki da zuciyarsa gaba daya. He's ready to meet them ko ina ma suka tafi ba tare daya gayawa maji ba,don bayason ta hanashi ko ta rogesa don yasan bazai iya ba,wannan ya sakashi ba shiri ya nemi Dr anwar,ya iskeshi cikin yanayin matsanancin zazzafan zazzabi,wanda dole ya sanya aka daura masa drip a parlor dinsa. Ranar sukayi da Jacob zai dawo, amma baikai ga isowa ba, sannan Dr anwar yace lallai yaci wani abu,dole ta sanya ya turama nadeeya gajeran tex,sai gata ta iso parlor din a gigice "Yaa moha,dama baka da lafiya?,jiya ba lafiya ka kwanta ba? me ya sameka?" "Relax, relax" ya fada cikin coolness da jigatacciyar muryarsa da abubuwa da yawa suka tarar mata, idanunsa akan fuskar nadeeya wani irin tausayinsu yana ratsashi,waye yasan yawan adadin cutarwar da ta yi musu ne ma?. Ita dinma kallon toufeeq din takeyi,tana mamakin wanne irin ciwo ne haka farat daya da ya sanya fuskarsa ta faada?. "Ki samo min tea da wani abu lite zanci kafin ruwan ya aare" "Okay yaaya" ta fadi tana juyawa da hanzari ta fita a sashen,ya rakata da ido har ya gama fita sannan ya maida idanun nasa ya kulle. Shawaginta na biyu kenan cikin gidan, saidai sam sam bataga wulgawarta ba,hakanan bataga motsin fadeela ba koda wasa,duk kuwa da cewa yau din weekend ne,baka rasa zirga zirgar yarinyar a farfajiyar gidan wunin ranar gaba daya,musamman idan basu fita ba, sannan shi kansa toufeeq an shaida mata yana cikin gidan,amma tun daga wayewar gari zuwa yanzun ace bai nemeta ba?,duk da ta dade da lura abubuwa nata canzawa, tun daga ranar da yarinyar ta amsa sunan matarsa kawo yau,to amma kuma lokaci ta bawa kowa,jira take ta gama yiwa kowa shirinsa na daban. Ko ubansa jarma da yayi tafiya ba tare da ya shaida mata inda yaje ba,da kuma adadin kwanakin da zaiyi kamar yadda ya saba shaida mata, tana sane da wannan, kuma ba zata taba bari hakan taci gaba da faruwa ba Nadeeya na fitowa sukayi clashing da hajiya garama "Ke,ke lafiya?" Hajiyan ta kira nadeeya da sauri,dan datakawa tayi "Ba komai yaa toufeeq ne bashi da lafiya zan sama masa wani abu yaci kafin a gama qara masa ruwa" gaban hajiyan ya fadi, saboda a yanzun bata shirya wani abu ya samu toufeeq ba sam, shine hope dinta, shine kuma matakala sannan kuma tsananta na dukka plans dinta "Me ya sameshi?" Ta tambayeta cikin damuwa, dan goge zufar goshinta tayi da tafin hannunta "Ban sani ba mommy, kinsan sanin ainihin ciwon yaa moha ba abu bane me saugi tun asali" "Na sani, jeki kawo masan" ta fadi tana wuce nadeeya zuwa sashen toufeeq din. Sallamarta kadai yaji ya maida idanunsa ya rufe, ko da wasa baison gain fuskarta, domin har zuwa lokacin bai gama yanke matsaya akanta ba ganinta da idanunsa a wannan yanayin da yake ciki na iya tunzurashi, kuma. komal yana iva faruwa "Muhammad" ta kirashi a hankali amma sai yayi banza da ita duk kuwa da hannuwansa suna motsawa kadan kadan. Sake kiran sunan nasa tayl a karo na biyu amma ya bawa banza ajiyarta,saukar muryarta cikin kunnensa dai dai yake da saukar tafasashen ruwan dalma. "Ko ya samu bacci? na dawo anjima" ta fadi qasa qasa sai ta juva tana fita daga falon. Tun bata gama fita ba ya bude idanun nasa, yanajin kamar ya jawota yayi mata mugun dukan da sai ta gaya masa laifin da fadeela tayi mata a rayuwa,amma dole yayi aiki da hankalinsa a dukka hukuncin da zai yanke, saboda ya riga ya sani girman matsayinta wajen mahaifinsa, after all hausawa sukace idan baka iya kama barawo ba shi sai ya kamaka, saidai daga rana irin ta yau, koda fadeela tana gasar, to ba shakka ya haramta mata ganinta kwata kwata. A gurguje nadeeya ta hada masa duk abinda zai bugata, tana fitowa falo zata wuce meenal ta shigo, ba wani sabo bane me yawa a tsakaninsu ba duk da cewa shekarunsu tazarar kadance ga kuma dangantakar dake tsakaninsu amma ko yaushe kamar bagin juna suke. Ita nadeeya mutum ce me faran faran da son jama'a ko kadan bata dauki duniyarta da fadi ba bata kuma dauki kanta ta aje can da nisa ba yayin da meenal take akasin haka tana da matugar fadin rai da jin kanta cewa ita din wata ce ta daban, gwanar girman kai da fadin rai, kamar zata wuce sai kuma tace "Sister nadeeya baqo mukayi ne?" Sai da tayi gaba sannan ta amsa mata "Yaa toufeeq zan kaiwa, bayajin dadi ne" ajiye komai tayi ta biyo bayanta da sauri, kwanaki kusan bakwai kenan tanason ganinsa amma kuma tana hagura saboda zazzafan warning din da ya aje mata kan shiga sashensa haka siddan ba tare da dalili me qarfi ba,a yau din kuwa ta samu dalili me qarfin. Idanunsa da har yau basu gama dawowa dai dai ba va zubawa meenal,wani kwarjini nasa tare da zazzafan gaunarsa na sake hudata "'Tsaya a nan" ya fada cikin tsawa, maganar tasa data sanyata jan burki ta tsaya din tana dubansa gabanta yana faduwa "Daga yau sai yau, daga kuma rana irin ta yau, koda wasa, koda ganganci idan na sake gain gafarki a sassan nan sai na ballaki balluwar da bazaki moru ba kin gama tashi a aiki kenan har abada, bacemin a gun idiot!" Ga fada da tsawa me garfi wadda hatta nadeeya sai da hantar cikinta ya kada. Har takai qofa ta jiyo muryarsa yana cewa "Ki hada dukka kayanki ki koma bangaren babarki, daga yau kar na sake ganinki a wannan sashen" kamar zata kifa haka ya garasa ficewa tana sakin kuka me sauti, bata ko damu da ma'aikatan gidan dake binta da kallo ba,har ta isa sashen hajiya qaraman ta sameta a parlor ta fadi a jikinta. A rude ta dagota tana tambayarta "Ke lafiya? me ya sameki haka?" Cikin sheshsheqar kuka ta gaya mata "Banason qarya da sakarci, yanzun nan na shiga dubashi na sameshi yana bacci,sannan bugu da gari ma babu ta yadda za'a yi toufeeq ya gaya miki haka" masifa da fada sosai ta rufe hajiya garama dashi "Haka kike gani ko? zan miki qarya ne?, komai nace yayi sai kinyi shakka, bayan a gaban idanunki yakeyin wasu abubuwan?, ina dukka tutiyarki da alfaharinki? ina abubuwan da kike alfahari da su? duk ni a wajena a banza suke tunda toufeeq kawai kin kasa mallakamin shi to wallahi wallahi nan da watanni biyu masu zuwa indai baki mallakamin muradin zuciya ta, kema ba zakiga abinda ranki yakeso ba" tsananin bacin rai ya sanya hajiya garama ware hannunta ta mari haseena, karo na farko da hakan ta faru tsayin rayuwarta "Baki da hankali ni kike gayawa haka?" Dafe da kuncinta take duban hajiyan "Ni kika mara momy?" Yadda tayi tambayar a tsaye tamkar hajiyarce diya ta mari mahaifiyarta haseena. kallon da take binta da shi ya sanyaya jikinta,sai a sannan ta tuna, mahaifinta sai da yayi mata bayani kafin va barta ta taho "Ba'a bata mata rai,saboda tana da wani hali me kama da cutar tsananin fushi" da sauri ta kamo hannunta ta rige tana fadin "Kiyi haquri, nayi miki alqawarin mallakar toufeeq a wata guda kacal, qasa da abinda kika buqata" "Ashe zan take faranti kenan kowa ya rasa" muryar hajiya Muneera ta baqunci kunnensu, abinda ya sanya suka maida hankalinsu bakin qofa. Kaifin idanunsu bai hanata ci gaba da qarasowa falon ba, itama su take kalla "Ashe da gaske ke din 'yar kunama ce fauziyya?,ni zaki yaudara kiyi wasa da tunani na? ki lasawa diyata zuma a baki yanzun kuma ki maye mata gurbinta da madaci?, tunda haka abun ya zama nafsi nafsi, kowa divan cikinsa ya sani to ki kwana da sanin muddin labiba bata samu toufeea ba haseena ma ta rasashi har abada" tana sauke furucin haseena na sauke mata lafiyayyen mari a fuska. Tsananin mamakin dava zarta zafin marin da shi hajiya Muneera ke kallon haseena baki bude "Shashasha. ke har kin isa ki hanani samun muradin raina? ba mutum ba, ko mutuwa banajin tayi wannan isar" "Kinyimin dai dai,ai da kin barta ma baki maretan ba" sai hajiya qarama ta matso gaban hajiya Muneera din tana mata wani kallo "Bazance karki taka faranti ba,ki taka,amma ki takashi kina da sanin cewa idan zai bare zai bare ne harda aurenki da YAYA NA, zakiga mummunan sakamakon da baki taba tunanin aukuwarsa ba,karki manta inada qarfin sawa a auro a kuma saki a duk sanda naso hakan" Sai a sannan ta sauke hannuwanta daga kuncinta inda haseena ta mareta "Bavan kuma va bare da aure na alagarki da yayanki shine abu na garshe da zai garasa zirarewa daga farantin,wannan marin da 'yarki tayimin ki rubuta ki ajiye,sai ya zame muku nadama da ba zaku iya kauce mata ba, fauziyya kada ki manta,ni dake kar tasan kar ne‚wanda ya fasa a tsakanina dake baya ya raina Allah" "Da kyau!" Hajiya garama ta fada sai haiiya mansuran ta tsugunna ta dauki jakarta data fadi a gurin,ta kuma juya tana fita daga sashen cikin matsanancin baqinciki vau ace yarinya kamar haseena da aka haifa a gabanta?,yarinyar da ko autarta ya girmeta ita zata daga hannu ta sauke a fuskarta?. Gaba daya hankalinsa bai kwanta ba har sai daya tabbatar ya sanya a nema masa visan Germany. Duka duka so yayi ace ya samu cikin sati guda kacal,amma aka shaida masa bazaiyiwu ba,short stay ma zata iya daukan sati biyu kafin ta samu "It's too long ya rabbi* ya furta qasa qasa yana karanta bayaman da aka turo masan. Hakanan don babu yadda zaiyi yayi accepting a hakan ya sanyama ranshi salama da dangana, amma ji yakeyi ranar kamar ba zata zo ba, kamar ba zasu hadu ba. A ranar bayan Dr anwar ya cire masa garin ruwan yayi booking na daki a bristol palace, suit din da ya saba kamawa ya kama na tsahon sati biyun, sabodia baya jin zai iya ci gaba da zama gida daya tare da hajiya garaman. Ya riga ya saita camera din da wayarsa, koda yana can zai iya ganin dukkan abinda yaso. Nadeeya batasan abinda yake faruwa ba kawai taji toufeeg din yace ta shirya kayanta kaman na 2weeks zasu bar gidan su sha iska, hakanan ya tura baba ramatu gurin abokiyar zaman mahaiffyar sajjad, gidan ya rage daga hajiya garama sai masu aiki. *******Cikin nasara fadeela ta kammala kwanakin da suka diba mata kafin aikin, duka gwaje gwaje sun kammala,hakama shirin aikin nata,aka sanya mata rana da kuma lokaci. Zuwan ba zata sajjad da afifa sukayi mata ana ya gobe za'a yi aikin,batasan cewa tana da rauni ba sai da taga bestie dinta,ashe dai tana bugatar wani a kusa,ta rige hannun afifa da kvau hawave nason sauko mata "C'mon bestie meye haka? u are strong woman,kinyi abinda ba kowa ne zai iya ba, kici gaba da addu'a,it will be successful surgery in sha Allah". A ranar babu wani wadataccen bacci da tayi,kamar ko yaushe ta kwana tana sallah tare da addu'a me tarin yawa. ***K'arfe takwas na safe afifa ta shigo musu da lafiyayyen breakfast da sajjad yayi musu order. A tsaye gaban madubi ta samu säahar cikin black laffaya me adon silver a jiki. Agogon hannunta silver color take daurawa, komai nata cikin sanyi take yinsa,saidai tayi wani irin mugun sassanyan kyau,kayan sun haskata sosai tare da gara mata wani irin kwarjini, Wayarta ta jawo ta sake duba sagon toufeeq na daren jiya,wasu irin sagonni yake aike mata masu taushi da narkar da zuciya cikin kwanakin saboda koda ya kirata bata dagawa,haka kawai takeii a ranta kamar tayi masa wani babban laifi da bazai gogu ba,ta dinga jin kamar ta shaida masa abinda sukeyi a Germany. Idanun afifa a kanta har ta garaso, dai dai sanda fa ajjiye wayar ta maida dubanta kan afifa "Afifa, am afraid" a nutse ta tako ta dafa kafadarta tana murmushi "Karki saare bestie,khairan in sha Allah" sai ta miqa hannu ta dauko cup na tea data hada mata da plate dindake dauke da tarkacen chips dasu ketchup "Kici wani abu kafin mu fita" kai ta girgiza "'Bazan iya ba bestie, tunda nazo garin nan sau daya nake iya cin abinci" ido ta fiddo "Saboda me?" Kafada ta dage "Ban sani ba afifa, kawai inajin cushewar ciki ne,sannannayi loosing apatite gaba dayaa, bakina bashi da taste" "Kuma a hakan sai a duka yawon shaqatawa kikazo fatarki tayi wani mugun fresh da haske kamar wadda ke wanka da madara" wani marayan murmushi tasaki tana kaiwa afifan duka "Ke har yanzu baki girma ba wai?,ga baby kina shirin ajemana,mutumin da bai iya cin abinci yaushe zai samu irinwannan nutsuwar da kike fada?" "Eh kika sani ko babies din namu tare sukeson isowa" afifa ta fada tana murmushin tsokana. Dan tsuke fuska tayi tana harararta Zafafa biyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 "HUGUMA* •_ TABARMAR KASHI_ Book 02 Page 50 "An gaya miki kowana ayu ne irinki?, besides mani ba auren zama nayi ba wannan shine last aikina da zanyi na gama zama a wajen" dariya sosai afifa ta saki harda kama ciki, sanann kuma daga bisani ta samu guri ta zauna. Dariyar ta qular da sãahar "Waye kikema dariya haka?" "Astagfirullah,da wanda ya tsargu nake" ta fadi tana fuskewa. Bata taba gain wauta zalla irinta sãahar din ba,da gasken gaske autar ce ta gaske, duk yawan buda sagonnin toufeeq da yadda fuskarta kan saki a duk sanda ta gama karanta sagon afifan na karance da shi daga jiya zuwa yau din,amma duka wanna ta tattara ta ture, itakam zataso taga ya wanna drama zata kaya. _muma zamu so mu gani ni da jama'ar zafafa_😃 Sai säahar din bata sake cewa komai ba don vau din bata jin kowanne wasa da afifan zata yi mata zaiyi tasiri, amma hakanan maganar baby din data fada saita tsaya mata a rai. Ta yaya zata samu wani baby?, bayan ko kafin ta taho tayi period, kuma zuwa next week take sanya ran zuwan next period dinta,sannan ko a yanzun tana jin cramps a mararta, amma idan ya tabbata fa baby dinne? ta yiwa kanta da kanta tambayar,sai kawai ta samu kanta da subucewar murmushi a fuskarta wanda ita kanta batasan dalilinsa ba. Kurba uku kacal ta yiwa tea din taji ya cika mata ciki fal, qamshin madarar dana Lipton din ciki yana son hautsina mata ciki,sai ta ajjiye tana duban afifa dake cin abincinta tuquru kan jiki kan qarfi. Kaman zatace wani abu sai kuma ta janye idanunta, tuni afifan ta ganta, murmushi ta saki "Bestie wannan dan naki acici ne Allah" Sai da dukkansu suka jira afifan na kusan minti ashirin ta gama lodin abincinta sannan suka fita farfajiyar hotel din,inda taxi din da zata garasa dasu asibitin su ukun take jiransu. Ko a hanya ma shuru ne nata,tayi nisa a duniyar tunanin me ranar ta vau zata haifar musu? farinciki ko akasin haka?, abinda ke qara sanyaya mata gwiwa daya ne,dukkan sakamakon da zai biyo baya ITACE SILA ALKHAIRI KO AKASINSA. Da gudu fadeela ta sauko daga saman gadon ta rungumeta tana kiran sunanta "I missed you anty N" sosai sãahar ta rigeta hawaye nason zuba a idanunta amma tana danneshi, ta tsugunna a hankali ta rungume fadeelan cikin jikinta hawayen na zartowa. Har an aske area din da za'a yi mata surgery din. Tsanar hajiya garama ta sake cika a zuciyarta sanda fadeelan ke fadin "Abby bazaizo na ganshi ba?" Banda gudun sharrinta, ta yaya za'a yiwa fadeela aiki irin wannan toufeeq baya gurin? baima sani ba?. "'Zaizo in sha Allah my fadee, kada ki damu" "Yaushe anty?" Ta sake tambayarta tana rungume a jikinta "Yau in sha Allah" taji afifa ta fada tana riqe hannun fadeelan a tausashe. Ajiyar zuciya säahar din ta saki, har a ranta taji dadin yadda afifan ta kubutar da ita, don batason viwa fadeelan qarya. Migewa tayi ta aza fadeela din saman cinyarta tana jin labaran da take bata na nurses din dake kula da ita,da sauran abubuwan da ke wakana a asibitin duk sanda ta tafi gida. Awarsu guda nurses biyu suka shigo dakin nasu,cike da kulawa da sanin darajar mara lafiya suka shaida musu zasu shirya fadeela za'a shiga da ita theater room din. Dukkansu dai jikinsu yayi sanyi, banda ita abinka da yaro da kuma quruciya, tana ta yiwa säahar hira ita kuma tana qoqarin boye hawayenta. Har suka kammala shiryata hannunta yana cikin na sãahar, ba ita ta sake mata hannu ba har sai data isa gofar theater room din. A hankali ta zame hannunta cikin nata, amma idanunta cikin na fadeelan. Duk yadda taso dakewa ta kasa, muryarta na rawa tace "Allah yasa ayi lafiya a gama lafiya fadee na,in sha Allah,in sha Allah from this day kin rabu da wannan lalurar rabuwa ta har abada. Murmushi kawai fadeela tayi mata,idanunta gyar bisa fuskar säahar din har suka maida gofofin suka rufe suka daina ganin juna. Afifa ce ta matso tana dora hannunta akan kafadar saahar din "Wannan damuwa ta isa hakanan-karkije ki yiwa kanki illa fa, damuwa a irin situation dinki bata kamaceki ba,an viwa mutane bila'adadin surgery din nan,kuma alhamdulillah they're healthy and safe,suna rayuwarsu vanzu kaman kowa,ya riga ya zama tarihi ma,samu guri ki zauna" sai taja hannunta suka zauna saman kujerun dake shirye a gurin. Sannu a hankali sakanni suka juye zuwa mintuna, mintuna suka juye zuwa awanni, awa ba daya ba har biyu shiru,zuwa lokacin sai ta dinga jin kamar hankalinta nason barin jikinta, da gyar ta iya daurewa aka cinye awanni uku cur. Tuni duk wani fata nata ya yanke, confidence dinta ya soma zagwanyewa tsoro da firgici, ta waiwaya ta dubi afifa data dawo daga cin abinci, abincin da babu yadda batayi da sãahar din tazo suci ba amma tace ba zata iya motsawa ko nan da can ba "Bestie lafiya kuwa? 3hours fa" dan murmushi ta sakar mata na kwantar da hankali "Ba komai in sha Allah, suna aikinsu ne" kasa zama tayi,sai ta mige ta koma dakinsu ta daura alwala,sannan ta dawo gurinta,ta bude qur'anin cikin wayarta ta fara karantawa gasan ranta ko hakan zai taimaka mata ta samu nutsuwa komai qangantarta. Sannu sannu sai gashi an sake shafe wata awa dayan har da rabi, adadin awanni hudu da rabi kenan,zuwa lokacin karatun kawai takeyi, amma gefen lafayarta gaba daya ya jiqe da hawaye, idanunta kuma sun tasa sunyi jajur, kamar yadda fuskarta ta hada jaa musamamn wajen hancinta zuwa habarta, abinka da farar fata. Duk iya hilatar da afifa zatayi tayi matan amma kuma bata samu nasara ba dole ta zuba mata ido ta shiga tayata da addu'ar itama cikin zuciyarta. Sajjad ne ya shigo gurin, ya tsaya daga baya ya yiwa afifa alamar tazo da hannu,dukka tana kallonsu,amma hankalinta baya kansu, har zuwa sanda afifan taie sukavi magana qasa qasa sannan ta sake dawowa wajenta,shi kuma ya juya ya fice a hankali. ›Wasu mintuna arba'in dinne suka zo suka wuce duka akan idanunta dake a rarrabe tsakanin qur'aninta da gofar theater room din. A hankali gofar ta bude, abinda ya kusa tsayar da bugun numfashinta saboda wata qaqgarfar faduwar gaba. Ko ina a jikinta rawa yakeyi sanda likitan ya bayyana a gofar dakin. Zumbur ta mige har wayar hannunta na subucewa ta fadi a gasa, dukkan idanunta a kansa tanason zuwa ta riskeshi taji daga bakinsa amma tsananin tsoron abinda zataji daga gareshi ya hanata aikata hakan. Lokaci daya kuma gabanta ya sake faduwa fiye da na dazu sakamakon tsintar muryar da bata taba zaton ji ba. Da wani irin sauri ta juya tana kallon qofar farko ta shigowa gurin. Sajjad ne gefansa kuma toufeeq, nadeeya na biye dasu. Sanye yake cikin wasu lafiyayyun suit da aka saqa da asalin zare me daraja na vicuna giviut fabric. Kalar suit din data dace da kwantacciyar fatarsa da hutu da kulawa suka ratsata. Idanunta ta sauke kan fuskarsa,abinda ta hanga wani irin shimfidadden bacin rai tare da cushewar fuska,ainihin kamanninsa na cikakken miskili kuma fusataccen MT JARMA take gani muraran, hakanan cikin sassarfa yake takowa fiye da sajjad da nadeeya. Kamar ya sani ko yaji a jikinsa tana kallonsa. Nasa idanun va zube a kanta sanda idanunsu suka sarqe cikin na juna sai taji gafafunta sun fara rawa, bugun zuciyarta ya garu ainun, mararta ta daure tamau yana sake kusantota tana jin kamar ana juyata daga hagu zuwa dama, daga gaba zuwa baya. Sai ta fara gani dishi dishi lokacin da mararta tayi wani mugun murdawa dai dai lokacin kuma da likitan ke magana da harshen jamusanci "Wo sind Fadeelas Verwandte? Folgen Sie mir ins Büro, es gibt etwas sehr Wichtiges, das ich Ihnen sagen mochte (ina 'yan uwan fadeela?,akwai bayani me matuqar muhimmanci da zanyi muku". Idanunta ta dauke daga kansa tana mayarwa kan likitan dake nufar office dinsa da sauri sauri. Ganinta yana sake zama dishi dishi toufeed na kusantota idanunsa a kanta,lokaci guda kuma taji wani abu me dumi yana ratsa jikinta sannan ya zarto zuwa qafafunta ta cikin lafayar jikinta,sannan ya taba takalminta ya kuma fara sauka a farin marbles din dake shinfide a gurin. Idanunta takai kai,wani irin abu ya daki kwanyarta,jini ne, irin jinin da ta taba gani kenan sau biyu a rayuwarta,zamanin rayuwarta a gidan adam,zamanin da take mararin haihuwa da samun iri, yau ga na uku na fita daga jikinta wanda shi kuma wanna bata da tabbacin jinin meye?. Ruf idanunta suka gama fullubewa, tayi baya gaba daya zata zube a wajen,saidai tsananin zafin naman da toufeeq yayi ya hana hakan faruwa. Cikin zallar tashin hankali ya tarota ta fada a jikinsa. Tuni afifa ta taso kanta, itama nadeeya ta garaso da sassarfa, shi da su kowa na kiran sunanta da garfi hankali tashe, toufeeq din yana jijiga kafadunta,saidai ko alamar motsi batayi ba. Hankalinsa a matugar tashe yake duban jinin dake zuba daga jikinta,sai ya dauketa cak kawai ya wuce office din likitan da gaggawa. Suna shiga likitan dake rataye lab coat dinsa ya waiwayo,zuwa lokacin tuni ya shimfideta saman gadon dake dakin,cikin rudani ya juye harshen jamusancin shima yana cewa "'Der Arzt hat ihr schnell das Leben gerettet, ich weiß nicht, was mit ihr passiert ist (Dr ka ceto rayuwarta da hanzari bansan me ya sameta ba)" da gaggawa ya danna wani abu sai ga nurses har biyu sun shigo, ya kalli toufeeq "Sir, geben Sie uns einen Arbeitsplatz?(sir ko zaka bamu guri muyi aiki?)" Kai toufeeq ya girgiza,yana tsaye qyam a gabanta hannunsa cikin nata,yana jin wani tashin hankali na ratsashi "Ich kann nicht rausgehen und ihr vor meinen Augen irgendetwas antun(bazan iya fita ba,kuyi mata komai a gabana)". Yadda suka karanceshin sunsan ba zaya fita din ba,abu daya yayi dole ya sake mata hannu don ya basu damar gabatar da aikinsu,ya koma baya kadan hannunsa zube a aljihun suit dinsa, idanunsa da suka sauya launi saboda tsananin tashin hankali qur a kanta tamkar an gaya masa yana janye idanun zai rasata. Cikin lokaci gangani suka farfado xa ita daga suman da tayi sukayi goqarin tsaida jinin. Bai tsaya ba amma ya ragu,ganin hakan ya sanya likitan ya kunna na'urar scanning ya fahimci ne yakeson yi,sai ya matso gabansa "Fass es nicht an, lass die Frau es ihrer Tochter antun, ich kann es nicht ertragen, das zu sehen(kada ka tabata,ka bari mace 'yaruwarta tayi mata,bazan jure ganin haka ba)" likitan nada fahimta sosai da kuma saugin kai ya saki murmushi kawai ya matsa baya yana-sakarwa daya nurse din na'urar,har yanzu murmushi yakeyi sannan yace "Du liebst sie anscheinend sehr, deshalb bist du so eifersuchtig auf sie(kana son ta da yawa da alama, shi yasa kake wannan kishin)" Kansa ya jijiga da qarfi don ya tabbatar masa da girman hakan cikin zuciyarsa "extreme Liebe(matsanancin so)" ya amsa masa a taqaice. Idanun likitan nakan allon computer din sanda take scanning din yana kuma yiwa toufeeq din bayani "Kaine mahaifin fadeela?" Kai ya sake jinjina masa,sal ya waiwayo a nutse ya kalleshi, sannan ya saki murmushi, haka kawai yaji toufeeq yayi masa,ya miga masa hannu yana murmushin "'Ina tayaka murna,munyi aiki successful irin wanda bamu taba yin kamarsa ba,munyi nasarar cire sashen dake sakata jijiga in sha Allah daga yau zata rayu kamar kowanne mutum, amma zaku kula sosai da qa'idoji da kuma zuwa dubata har ta kammala warkewa duk da dai mun fahimci kamar any amfani da wasu magunguna a kanta da sukaso fadada ciwon ya taba wani sashen daban na qwaqwalwarta,wanda inda hakan ta faru ba zata taba warkewa ba, saidai taci gaba da rayuwa akan magani har qarshen rayuwarta,to sai kukayi dabarar tsaida maganin, abinda yayi nasarar hana afkuwar hakan,kuka kuma yi dabarar kawota akan lokaci akayi mata aikin,Glückwunsch(congratulations)". Wani irin abu me sanyi ne ya sauka saman zuciyarsa tamkar ana sanya sassanyan ruwa ana wanke masa zuciyarsa. Cikin sanyin da mutuwar jiki ya migawa likitan hannu shima "danke Doktor(na gode dr)". Maida dubansa yayi ga saahar dake numfashi a hankali saboda allurar baccin da yayi mata bayan farfadowarta "Wanne irin nau'in so zai gwadawa rayuwarta ne?" Ya tambayi kansa da kansa,shi kansa baisan iya adadin sonda yake mata ba,ga wasu dalilai da suka qara rura wutar qaunarta me tsanani a ransa,shi kam bai sani ba baisanta yadda zai sarrafa wannan soyayya da qaunar da yakej) cikin qirjinsa ba. "Setzen Sie sich, Herr (zauna yallabai)" likitan ya fada yana dubansa, koda suka bashi seat din gaban gadontaya maidashi hannunsa cikin nata vana sake kula da dukwani motsinta "'Zamu bata daki itama,zuwa nan da awa sha biyu zamu tattara bavananta zamu sanar maka" likitan va fadi yana sake nazarin scanning din. Zafafabiyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 "HUGUMA • TABARMAR KASHI* Book 02 Page 51 Lokacin da aka fito da ita tana bacci. Afifa so tayi ta rude, toufeeq din ya riga yasan situation din da afifan ke ciki, don haka ya yiwa sajjad din alama na ya jata yabar gurin da ita. *********Sannu a hankali ta dinga bude idanunta da taji sun dan mata nauyi ga kuma hasken da ya cikasu. Yana zaune a gabanta hannunsa cikin nata,ko motsi baya yi da idanunsa bare hannun nasa dake dame da nata. A nutse ya miga hannunsa zuwa saman goshinta don tabbatar da farkawarta. Dumin hannunsa dake saman goshin nata ya sakata dauke idanunta daga kan maji dake zaune gefe daya saman kujera ta dawo dashi kansa. Sarqewa idanunsun sukayi cikin na juna,ta dan zuba masa ido tanason tabbatar da shi dinne?, har yanzu akwai fushin nan saman fuskarsa ko kuma yayi qaura?. Hawaye ne suka fara tsatstsafowa idanunta,idonsa ya lumshe sannan ya bude yana girgiza mata kai alamar a'ah dai dai lokacin maji ta dawo da dubanta kansu,ta matso a nutse tana fadin "Ta farka ne?" "Eh" ya amsawa maii din. Qogarin zame hannunta daga nashi takeyi saboda gain maji a wajen, amma saidai bashi da niyyar motsawa daga wajen ma bare ya bari ta zame hannun nata. "Sannu d'iyata" maji ta fada cikin kulawa. Kai ta gyada mata sannan ta motsa bakinta a hankali "Yauwa" ta amsa mata,dai dai lokacin likitan ya shigo, bayansa afifa ne ita da sajjad. Dukkansu kayan data gani a jikinsu a daxun yanzu basu bane ba,da alama ta dauki wasu awanni kenan tana bacci ba tare da tasan abinda yake faruwa ba. Sannu suka yiwa likitan, afifa ta matso tayi mata sannu sannan suka juya dukka suna fita saboda bawa likitan damar dubata, banda toufeeq da ya gara matse hannunsa cikin nata. Wannan karon cikin harshen turanci likitan yake masa bayani "'Ina mai baka haguri, ta samu bari na ciki dan sati hudu" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Allahumma ajirni fi musibati, wa'akhlifni khairan minha" ya furta yana runtse idanunsa. Har cikin saman kansa ya dinga jin wani abu, sai ya kasa ci gaba da tsaiwar,ya koma a hankali ya zauna saman kujerar yana ci gaba da rige hannunta,kana ya sauke idanunsa a kanta. Tunda likitan ya fadi maganar taji kamar an sauke mata dutse mai nauyi a girjinta "Anya tana rabon ganin qwanta a duniya?" Tambayar data yiwa kanta kenan,tana jin numfashinta kamar yana mata wahalar shaqa. "Akwai abinda yadan raunata qarfin mahaifarta,don haka tana da dan rauni,wanda cikakken motsi ko zirga zirga me yawa,ko kuma razana suna iya kawo mata miscarriage" idanunsa ya mayar kan likitan,yana jin zuciyarsa na quna "Yanzu sai yaushe zata iya sake conceiving?" Maganar ta sanya likitan dagowa ya dubeshi tare da sakin qaramin murmushi "Kada ka damu yallabai, indai za'a kula da ita yadda ya kamata, maida wani babyn bazai zama abu me wahala ba" Magunguna ya rubuta cikin file din sannan ya ajiye yana qara masa was bayanai sannan ya juya ya fita. Ya barshi cikin wani irin yanayi,ya dinga ji kamar laifinsa ne, kamar shi yayi sakacin da cikin ya fita,amma bai sani ba ba shakka inda yasan akwai ajiyarsa tattare da ita ko sama da gasa zasu hade bazai bari tayi tafiyar ba. Shi daya yasan yadda Allah ya jarabceshi da son tara zuri'a,musamman a yanzun a yadda yake,Allah yayi masa dukkan wata ni'ima da sutura ta rayuwa. Idanunsa ya dauke daga kan likitan a nutse ya maida saman fuskarta dake a runtse wani abu me masifar garfi yana sake fusgarsa a kanta. Duk da idamunta a kulle suke, duk da a gadon asibiti take amma hakan bai hana bayyanar kyan siffarta ba. Sosai ya zubawa gefan idonta ido yana son tantance hawaye takeyi?,ya gani kuwa dai dai?. Yatsansa ya sanya ya dangwali hawayen,ya tabbatar sune, abinda ya sanyashi tashi cak daga kujerar da yake zaune a kai ya koma gefan gadon saitin kanta. Cikin taushi ya daga kanta ya dora saman cinvarsa, sannan ya sanya tattausan tafin hannunsa ya fara dauke mata hawayen. Saukar hannun nasa saman fuskarta ya sanya ta dakata da kukan saboda yadda ta jita kwance saman jikinsa. Sai da ya gama tas sanann ya sunkuya da kansa saman fuskarta,sai ya zamana kamar yayi mata rumfa. Cikin muryarsa me taushi da kuma wani irin deepness yace "Kema kina bugatar sa ko?" Yayi mata tambayar da sai da taji kamar zata nutse a gurin. Sake sassauta muryarsa yayi "me yasa ya tafi a irin wannan lokaci? ya tafi ya barmu da kewa me yawa ni da mommy dinsa,we missed him a lot, but karki damu,kiyi goqari ki warke da wuri, nay algawarin zanyi replacing wani very soon in sha Allah" kasa jurewa tayi duk da idanunta suna a bude ne, saita mirgina kanta daya sashen tana sake lumshe idanunta. Tsaye tayi daga bakin qofar ICU din, inda aka kwantar da fadeela,wadda a qalla zata iya kaiwa gobe ko jibi tana bacci saboda allurar baccin da sukayi mata,suka saka mata na'urar ventilator saboda ta taimaka mata wajen yin bacci da kyau. Duk lokacin data kalli fadeelan sai taji zuciyarta ta tsinke sosai, tsoron Allah yana sake kamata,tare da tabbatar da cewa lallai dan adam ba'a bakin komai yakeba. Haka kawai cikin jikinta takejin zargin hajiya qarama me garfi akan ciwon fadeela,har yanzu kunnuwanta suna iya jiye mata fadan da take a dazu cikin wayar jarma bayan ya kirata don ya gaya mata ta aikawa mansura a kira company din nan suyi gyaran sashensa irin wanda sukeyi duk shekara, daga nan ya shaida mata suna Germany tare da sãahar da fadeela harma da toufeeq da nadeeva an yiwa fadeela aiki. Saura qiris ta zame ta fadi saman marbles na kitchen din da take tsaye a ciki a sannan, don sai data dafa me aikinta sannan ta samu guri ta zauna zuciyarta na wani irin rawa kamar zata tsinke daga qirjinta "Yaaya? yanzu har rashin muhimmanci na yakai kowa da kowa ya tafi gurin aikin ciwon fadeela amma banda ni? bayan nice nafi cancanta da naje?" "Nima daga qasar da naje na samu visa na wuto, bansan me yake faruwa ba" "Amma yaaya ina cikin gidan nan, har yaushe aka yanke. shawarar yin hakan ba tare da na sani ba?" "Wannan kuma ki jira danki yazo sai yayi miki bayani, don hukuncin surukarki ne,ita ta tsara hakan, ban sani ba ko da saninsa ne koma meve dai anvi aikin successfully inji likita, farfadowarta kadai muke jira" "Turgashi!" Ta fadi cikin matsanancin tashin hankali "Ita har waye yaaya da zatayi kutse a rayuwarmu? har ta isa tayi hukunci cikin rayuwar 'yarmu?, to wallahi ka shaida mata ta kuka da kanta, muddin daya daga cikin matsalolin da akan iya gamuwa da su sanadin surgery din nan ya samu fadeela to la shakka sai nayi shari'a da ita,sai na daureta wallahi, akwai visa ta ta garmany dana taba yi, batayi expire ba,ina nan tafe nan da kwanaki uku in sha Allah" ya zuwa yanzu haka kawai Dr mahmud yakeji ya fara qosawa da damuwa da matsalolin fauziyya "Sai kin iso. kawai vace da ita vaja jan garamin tsaki. Hayaniyar da tayi masa cikin waya yaji tana bata ransa, ya waiwava va dubi maji dake zaune a gefansa cikin mota. Ko a fuska bata nuna taji komai ba, duk kuwa da yasan bata yadda za'a yi tace bata ji din ba saboda handsfree ya saka,amma yadda ta nuna din sai ya garyata maka hakan. Ajiyar zuciya kawai ya saki,shi kadai yasan irin rudanin da yake ciki, tunda me afkuwa ta afku suka baro. Algeria ko sau daya bai gara ganin murmushinta ba. Sallamar Dr mahmud jarma din ta sanyata motsawa kadan,ta kuma amsa ba tare data juyo ba. Gefanta ya garaso ya aza hannunsa daura da nata,sai kawai ta cire nata hannun ta fara takawa tana barin gurin. Kamar ya kirata sai kuma ya fasa, gudun kada ayi abun kunya gaban surukai,ya maida kansa ga fadeelan vana ci gaba da yi mata addu'a,don shi kansa yayi matuqar damuwa, kasancewarta tilon jika a gurinsa. ******* Kusan minti guda cif yayi yana kallonta daga nesa zuciyarsa tana narkewa. Kwata kwata bata zauna ta samu cikakken hutun da likita ya bugata ba daga gareta, tunda har taji zata iya migewa taqi zama,sai zirga zirga da takeyi tsakanin ICU din zuwa dakin da aka bata, tsahon kwanakin ukun duka ta tashi hankalinta,ta dorawa kanta laifin komai da komai har da rashin farkawar fadeela akan lokaci. A hankali taji an rungumeta ta baya, sannan cikin taushi ya sanya hannunsa va hannuwansa saman ruwan cikinta ya sake jawota cikin jikinsa sosai. Kansa ya dora saman kafadarsa,cin taushi ya soma mata magana a kunne me kama da rada "Damuwarki tana ciremin kowanne karsashi daga raina" hannunsa ya sanya ya juyo da ita suna fuskantar juna,ya miga yatsansa yana dauke ruwan hawayen dake layi saman kuncinta "Karki sake kuka we'll figure this out together, she will be fine in sha Allah,don't blame your self" qas tayi da fuskarta wasu sabbin hawayen na saukowa,sai kawai ya bude girinsa ya sanyata a ciki,ya kuma rungumeta tsam yana shafa bayanta a hankali idanunsa kan fuskar fadeela da ta dan kumbura kamanninta suka dan jirkita kadan. "Toufeeg" yaji an kira sunansa daga bayansa. Dukkansukoda basu waiwaya ba sunsan me muryar. Motsawa säahar tayi kadan da nufin janye jikinta "Don't move" ya furta can gasan magoshinsa, idanunsa a lumshe yana ci gaba da shafa bayanta. Bata sake motsawar ba kamar yadda ya buqata,hakanan bai juya ba shi dinma, har zuwa sanda ta iso gabansu Hajiya qarama ce, cikin shigar nan tata da ko yaushe take nuna tsananin alfaharin da take dashi,izza da kuma nuna isa Toufeeq.…...au lallabata kakeyi ma?,na tsammaci zanzo na samu kana hukuntata da mafi tsananin hukunci? yarinyar da take shirin yi maka sanadin rasa tilon 'yarta saboda shegen shishshigi da rawar gafarta? ko an gaya mata mu bamusan hanyar germany din bane da zata kwaso gafafunta ta kawo mana yarinya uwa duniya? gashi har yanzu bata farka ba? waye ya sani ma ko cinikin qodarta kota qwaqwalwar tata tayi mana" "Stop" ya furta cikin gautsi da bacin rai,yana jin kamar ya juya ya wanke mata fuska da mari,saidai a yanayin da ake ciki yanzu bayason yace mata komai,lokaci kawai yake jira. Sai a sannan ya bude idonsa kan fuskar sãahar wadda ta daga kanta daga qirjinsa tana duban awayar idanunsa cikin damuwa da razanin kalaman hajiya qaramar. Hannunsa ya dora saman kanta kamar qaramar varinya "Banason wannan tsoron, banason wannan firgitar,tun yanzu nakeson ki ajiyeta, da irin wannan abun naki kikayi mana asarar baby". Wata nutsuwa taji tana saukar mata da kalamansa dake nuna ko daya zancan annamimiyar matar baiyi tasiri a ransa ba. "Asarar wanne babyn bayan fadeela?" Tayi masa tambayar adan rude. Kai tsaye ya waiwaya,karon farko tunda ta iso ya dubi qwayar idonta kai tsaye "She had miscarriage, cikina dake jikinta ya bare" mummunar faduwar gabanta yayi wanda sai data jishi har tsakiyar kanta,me yake shirin faruwa tana toshe wata barakar wata barakar tana kunno kai? yanzu har tayi saken da wata macen da ba meenal dinta ba zata dauki cikin toufeeq?. Kafin ta sake cewa wani abu ya dauke idonsa daga gurinta "Ko zaki matsa daga nan gurin, saboda basa bugatar hayaniya da tarin tarkacen mutane" dubansa tayi a mamakance a karo na biyu, Ita toufeeq yake kira da tarin tarkace?, koda yake tayi masa uzuri yana cikin dimuwar rashin farkawar fadeela,to amma kuma idanunta suna nuna mata canzawar mu'amala tsakaninsa da yariyar, yaushe hakan ta kasance? indai hakanne kenan aikinta ya sake linkuwa?,kenan wani dogon zangon zata ci muddin hakan ya tabbata kafin cikar muradinta?. Shuru ne va ratsa gurin bayan ta juya ta bar gurin cikin wasi wasi. Ci gaba yayi da boyeta a qirjinsa, saboda weakness din da yake hanga tattare da ita bayason ganinsa, she's strong enough,tayi abinda dukka dangin fadeela suka gaza yi mata,bai kamata ta karaya haka ba. "Subhanal malikil guddus" taji ya furta yana sakinta daga jikinsa. Daga kanta tayi da sauri ta kalleshi,sai kuma ta maida dubanta ga inda yake kalla. "HUGUMA* _TABARMAR KASHI* Book 02 Page 52 Fadeela ce ke motsawa tana bude idanunta, likitocin da basa rabo da gurin suka isa gareta,sai dukka hankalinsu shi da ita ya koma kai. Suna ganin sanda suka yi wasu dube dube jikin na'urorin dake tare da ita,suka zare mata na'urar ventilator din dake tare da ita,sannan suka kamata suka zaunar da ita sosai suna jinginata da pillow, daya daga cikinsu yana magana da ita tare da yi mata tambayoyi. Batasan ta rungumeshi ba sai data ji yana goge mata hawaye, abinda bata taba yi ba ta rigeshi cikin jikinta tsam tana hawaye,cikin haka aka buda gofar aka fito. Likitanne, sai hankalinsu ya tattara a kansa "Ta farfado, kuma muna saka ran lafiya lau take, amma yanzun zamuyi mata gwaji don tabbatar da dawowar memory dinta da kuma bangaren dake da alhakin magana na brain dinta vana nan lafiva nan da awa uku kacal zamu fiddota daga nan icu zuwa ward na gaba (inda zaku iya ci gaba da ganinta" sake rugungume toufeeq din tayi da kyau tana rasa inda zata ajjiye kayan farincikin da takeji,har cikin qashinsa yakejin rungumar tata,ya maida kansa ga likitan "Mun gode likita,muna fata jin labari me dadi game da hakan" yayi maganar yana miga masa hannu "'Da yardar ubangiji" shima ya maida masa cikin murmushi, soyayyar da yake hanga a idanunsu su biyun kullum ya kallesu burgeshi sukeyi, baiyi zaton samun irin wannan soyayyar daga gurin baqar fata ba. "A cikani don Allah na samu damar zuwa na shaidawa su maji" da hanzari taja da baya tana sakinsa a kunyace tare dauke kanta gefe guda kamar ba it bace yanzu tabar iikinsa ba,dariya ta kubce masa,sai ya girgiza kai kawai yana soma yin gaba,yanzun ya fara dawowa hayyacinsa,zai dora daga inda ya tsaya,saboda har yanzu baiji kalmar i love you daga bakinta ba. Tunda suka tsaye a gurin sun magana hankalinsa yake kanta,kamar yadda hankalin hajiya qarama yake kansu su dukka. Ta fahimci bayan wucewar kowanne second hamsin zuwa sittin sai yayan nata ya waiwaya ya kalleta, saidai ko sau daya ita maji din bataga ta juya ta dubeshi ba,tamkar ma basarwa takeyi batasan da zamansa ba. Isowarsu ya sanya maji migewa kunnuwanta suna sauraren albishir din da yake tafe dashi. Gaba daya kowa dake gurin rudewa yayi, yana sake kiran sunan Allah tare da qara tsarkake girma da buwayarsa. A hankali ta zame ta koma da baya ta zauna bugun zuciyarta na bugawa da matsanancin garfi,can gasan ranta taji tana fata da addu'ar samuwar tabuwar memory din yarinyar ko kuma sashen maganar na qwaqwalwarta ya tabu,roqo me tsanani cikin ranta, saboda ita daya ce hanya qwal dsya tilo mafi saugi da zata zare sãahar daga rayuwar kowannensu cikin ruwan sanyi, ta kuma maye gurbinta da haseenarta. Kowanne mode na hajiyan da ya sauya yana bibive dashi yana kuma karance da ita,ba kuma wai shi daya ba,daga maji har sãahar suna ankare da hakan, gefe daya afifa itama tana monitoring komai, tana sake samun limani da yaginin matar da gaske akwai wata guba a tattare da ita,walwalarta ta banbanta da walwalar duk mutumin dake gurin. Cikin gasa da awannin da suka fadi komai ya kammala, suka samu tabbacin komai nata ya davo normal, abinda ya rage mata kawai shine kwana bakwai da zatavi a asibitin ana sake kula da ita. Cikin mintuna galilan suka dawo da ita general ward dake qarqashin neurology department. Sãahar ce mutum ta farko da fadeelan ta fara runguma sannan abby dinta. Maji taja da baya tana dan harararta "Au, haka zamuyi dake? lallai sai kin nuna kishina kikeyi ko?" Ta furta cikin wasa,wasan da yasa fadeelan dariya ""Sorry grandma,dukka nayi kewarku fa, kwana na nawa ban ganku ba?" Ta furta tana son lissafa kwanakin, to amma ita Ranta batasan kwana nawa bane. Duka kowa sai data ambaci sunansa, fuskarta cikin murmushi don ita din tun asali nadeeya tayo wajen fara'a ba oga toufeeq ba Duk wani kai kawo säahar ita ta dinga yi,wajen bawa fadeelan abinci da sauransu. Tsakanin toufeeq dr mahmud da maji bansan waye yafi yabawa tare da jin qaunar säahar din cikin ransa ba, taqi yarda kowa ya karba hidimar fadeelan. Tana tsaka da bata abinci kadan kadan tace "Ina mommy garama?" Tambayar da aka rasa me amsa mata tsakanin toufeeq da ita sahar da aka yiwa tambayar. Idanu sãahar ta maida kan toufeeg,don shi yafi cancanta ya amsa tambayar, ita kadai taga lokacin da yake magana da security kan kada su bari ta shigo dakin. Ido daya ya kashe mata tare da vi mata nuni da taci gaba da aikinta,saita maida kanta ga fadeelan dai dai lokacin da yace "Zaki ganta angel, bata kusa" daga haka bata sake tambayar ba. **Rubuce rubuce likitan ya sakeyi gefe daya yana sake musu bayani tare da tabbatar musu da komai lafiya yake "Kuna iya tafiya gida, likitocinmu zasuci gaba da lura da ita har wayewar gari kamar yadda aka saba" ya fada yana ajjiye musu file din sannan ya fice. Sassanyan boyayyar ajiyar zuciya toufeed ya saki, dama yana da buqatar hakan,a kwanakin gaba daya ta hautsine ta hautsinashi,ko dumin jikinta bata bari yaji. Kai tsave kawai sai va ciro wayarsa ya fara yi musu booking daki na hotel, don yanaji a jikinsa hotel din da yake ciki vanzunma yayi masa kadan. Daki daya tal ya kama musu me hade da komai da komai,sai kuma ya sake laluba wani hotel din ya sake kama dakuna uku. Daya na Dr jarma,daya na maji dasu nadeeya,daya kuma na sajjad. Kadaici yake buqata, bayason su hada hotel da kowa nasu,shi yasa yayi hakan. Sai daya kammala komai sannan hankalinsa ya kwanta dai dai da isowar taxi guda uku. Da daya da daya suka yiwa fadeela sallama suka fice, saura shi da sãahar din suka rage. Maimakon yaga tayi hanyar waje kamar kowa,sai yaga ta samu gu ta zauna "'Let's go" ya fada idanunsa a narke a kanta, dan daga kai tayi ta dubeshi "Ni ba zasu hanani kwana ba,nayi magana da wata nurse" idonsa ya dauke daga kanta,ba tare da yace mata komai ba ya isa gabanta, yasa hannu ya zare wayar dake hannunta ya jawo jakarta ya jefa a ciki qasa qasa yana cewa "Na fuskanci har yanzu yarinyar nan baki da wayo, sai na fara miki magana da manyan baqi a gaban kowa" baice da ita komai ba ya qarasa yayi kissing hannun fadeela yayi ficewarsa. Komai nata yana cikin jakar, kuma ya hada ya fice dashi, babu yadda ta iya dole ta matsa gaban fadeelan tayl sallama da ita,tare da yi mata alqawarin dawowa gobe da wuri. Dukka taxi's din su maji sun bar gurin da alama sun tafi, saishi ta samu a tsaye yana danna waya rige da jakarta yana jiran isowarta. Qofar yabar mata a bude ya zagaya daya sashen ya shiga. A nutse ta shiga itama ta rufe, driver din taxi din ya tayar da motar suma suka fice daga asibitin a hankali. Tun basuyi nisa ba lalubi hannunta ya matse cikin nasa ta daga idonta a hankali ta zube cikin nasa. Kafeta yayi da kakkaifan kallonsa har ta kasa janye nata idanun, cikin taushi da laushin murya yace "'Baki ganewa a duk sanda mijinki yayi missing dinki ne? duka kin hautsina ni kamar ance fadeela zata wuce ta barki?, finally fadeela ta warke ina bugatan kulawarki" ya fadi da idanunsa da suka rusuna kamar wanda yakejin bacci "Please please, ko kwatan kulawan da fadeela ta samu nima adan sanmin" da car ta zare idonta daga cikin nasa tana jin bugun zuciyarta na qaruwa, kamar wanda va zubawa sassan jikinta wani guba ko dafi da suka kassara gabobinta. Tana jin wani yanayi sosai a likinta matuga da gaske, irin vanavin da bata taba in kamarsa ba, amma cike take da tsoro da kuma firgicin sake afkawarta wani rami, kada sai ta saki zuciyarta tayi nisan kiwo kuma ya zamana ta barota a inda daukota zaivi mata mugun wahala. Daga shi har ita ba wanda va sake cewa wani abu, har zuwa sanda suka isa hotel din. Shine va bude dakin sannan va matsa vana bata hanyar shigowa. A nutse take kallon dakin,wani irin daki dake da wani tsari me kyau burgewa da kuma sanyaya zukata. A nutse ya maida gofar ya rufe yana takowa tsakiyar dakin idanunsa har vanzu vana kanta, sai kuma ya kauda kai vana wucewa gaban wardrobe na dakin ya bude ya zube kayansu a ciki. Kayan jikinsa ya fara zarewa saboda wanka da yake bugatar yayi,ya gaji sosai kuma dare na sakeyi yanaso yayi bacci yadda ya kamata saboda gajiyar da ya dibawa jikinsa ta kwana da kwanaki.. Idanunta ta kawar gefe, don ba kadan ba qirar jikinsa take mata kwariini. Qaramin murmushi ya saki yana karantarta,har yau bata taba tsaida idanunta a jikinsa ta gare masa kallo ba,yana lura da duk wani motsinta tun ba yau ba. Ya gama fidda kayan daga shi sai pant,ya fara takowa a hankali,bai tsaya ba har ya cimmata, ya tsaya dab da ita yana dan taka yatsunta da nasa yatsar ta vadda zatasan da isowarsa. Sarai ta jishi, amma bugawar da zuciyarta keyi ya hanata motsawa "A bani towel" va furta vana kallonta. Cikin rawar jiki ta waiwaya tana duban gefanta ko zataga towel din, suna ninke a kusa da ita,hannu ta miga ta dauko ta miga masa ta baya ba tare data waiwayo ba. Hannunsa ya miga ya riqe towel din hadi da jawota gaba daya sai gata a tsaye a gabansa,dukka qugunta ya kama ya rigeta tsam yana matsowa da ita jikinsa ya mannata da qugunsa. Wani irin shock mai qarfi ya fusgeta ya kuma ratsa kowanne sashe na jikinta ya tayar mata da tsigar jiki, dumin fatarsa yana ratsata qwarai "'Look into my eyes" yafadi qasa qasa shima yana jin wani yanayi na sauka a nasa jikin sanadiyyar haduwar jikkunansu guri guda. Na second daya tak ta iya daga kai ta kalleshi sai taji ba zata iya jurewa ba. Ya sani dama saboda abinda ya sakar mata ta cikin idon zaiyi wahala ta iya jura,sai ya saki qaramin murmushi na gefan baki yana kallon lips dinta. A duniya labbanta na daya daga cikin abinda ke tafiya da tunaninsa yake kuma jin marmari, iya kallonsu kadai suna haifar masa da tarin bugatuwa zuwa gareta "You are one person with the power to give me a thousand feelings...can i order a large tight hug until I feel okay please?" Ya fadi yanason kallon tsakiyar qwayar idanunta da har yanxu taqi yarda ta kalleshi dasu, saboda wani irin feeling da yake saukar mata "Please" ya fada a narke, nan ma bata amsa ba,kasa jurewa tayl a karo na biyu,yanzun kuma taji duk duniya idanun nasa takeson kallo,tanason ta tabbatar da salon muryar da kuma wannan shagwabewar ita MT JARMA yake yiwa. Sosai vaja numfashi sanda idanunta suka shiga nasa,ya kama kanta da hannunsa dukka biyun ya riqe, numfashinsa na kai kawo da sauri cikin zafin nama ya matso da fuskarta dai dai tasa "You just stole my words" ya garashe fada yana hade bakinsu guri guda. Wani irin kiss me zafi yake sauke mata ko ta ina, tuni ya sanya jikinta itama ya dauki rawa, lokaci kadan ya fara juye mata tsantsar kewarta da yayi da kuma yadda zuciyarsa ta azabtu da soyayyarta, tun tana iya dauka har ta fahimci abun nasa nisa yakeyi, kamar yana shirin ficewa daga hayyacinsa. Kasa tsaiwa sukayi dukkansu suka zube saman lallausan carfet din dake iya area din da suke a tsaye. Sai tayi qarfin halin tureshi, muryarta na fita da qyar saboda gudun da zuciyarta keyi “Am in...am in.... miscarriage bi.." Bai bari ta garasa ba ya zame jikinsa va tsani ya tuna wai tayi miscarriage, shikenan ya rasa babynsa? bai kuma san ranar maida wani ba, sai kawai ya zura jallabiyyar daya fidda ya nufi gofar fita zuwa parlor yana hada hanya. Ta jima zaune a gurin tana maida numfashi kafin ta iya migewa ta shige toilet don cire pad din jikinta ta sauya wata. Cikin mamaki take sake kallon pad din, tayi tsammanin zata sameta da jini a jiki, tun ranar da akace tayi miscarriage din bata sake ganin jini ba,sai dan sports data gani zuwa jiya,yau kam babu komai ma a jiki, yau kwanaki hudun yadda ta saka pad din haka take cireta,sai ta jefata dustbin tayi tsarki ta kuma daura alwala tana yankema ranta zuwa asubahin yau idan bataga komai ba zatayi wanka taci gaba da ibadarta. Saman sofa din dake dakin ta koma ta cure guri daya, tana jin mararta na daurewa sosai, idanunta a lumshe har zuwa sanda ya sake turo gofar ya shigo. Ta lumsassun idanunta take satar kallonsa har ya wuce bandakin, sai daya rufe qofar sannan ta sake maida idanun nata. Zurfi qwarai zuciyarta tayi akan nazarinsa da nazarin halaye da dabi'unsa, bata tana tsammanin samunsa da wannan fuskar ba, MT JARMA, mutum mara uzuri mara dagin gafa, mutum me tsananin zafi,wanda bai maida korar ma'aikata a bakin komai ba, bata taba zaton samun wanna side din daga gareshi ba. Duk wasu qarin dabi' u da take tsammanin samu daga gareshi sai taga akasin hakan. Zafin kai izza tagama da kuma tarin qasaitarsa takan rasa ina sukayi a duk sanda suke kebe,wani mutum daban take gani a mafi yawancin lokuta,bawai MUHAMMAD TAUFEEQ JARMA ba. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI- Book 02 Page 53 Mintuna kusan talatin ya sake fitowa,saita sake bude idonta kadan tana ci gaba da satar kallonsa. Daure yake da towel yanzun a qugunsa, duk wata siffa da gira da Allah yayi masa ta bayyana,idan tace tsahon rayuwarta bata taba ganin namiji me qira koda kusan tasa ba batayi garya ba,inda za'a dauko adam a tsayar dashi a gabansa,tabbas zai tashi kamar siffar jikin mace ne da kuma wani ingarman namijin. Zame towel din da yayi ya sanyata maida idanunta ta kulle da garfi harda juya kanta wani sashen. Murmushi me sauti ya saki yana sane yayi hakan, tun daga shigowarsa har yanzun da ya fito daga wankan ya fahimci tana satar kallonsa "Idan kin gama qaremin kallon ki tashi kiyi wanka,ki fidda wadan nan kayan ko zakiji dadin bacci" ya fadi yana sanya short necker sannan ya fara feshe jikinsa da tattausan turarensa mai kwantar da zuciya. Har ya gama bata motsa ba. Bai sake ce mata komai ba,sai ya taka cikin kamewarsa ya isa gareta sai kawai ji tayi an dagata cak "Na daina magana biyu daga yau, komai zan vishi ne a aikace". Bai saurari magiyarta kan ya sauketa ba "It's too late" yace da ita yana isa toilet din, sai kawai ya tsumbulata gaba daya cikin bathtub. Qanqame jikinta tayi guri daya "Pleaaaaaaaassssseee" ta fada murvarta na rawa. Murmushi ya saka yana fasa shiga cikin kwamin kwankan da yayi niyya,yaja da baya yana nufar qofa sai-kuma ya tsaya cak yana kallon dustbin din data jefa pad, har zaice wani abu sai kuma ya fasa ya sanya kai ya fita. A reception na hotel din sajjad ya karba musu keys na dakunan sannan suka haura zuwa floor na biyu. Migawa Dr jarma key din nasa dakin yayi cikin girmamawa sannan yayi gaba yana cewa nadeeya "'Muje ga naki key din" afifa da nadeeya suka bi bayansa. "Shifa" Dr jarma ya kira maji wadda sai yanzu ta iskesu ganin tana marawa su sajjad baya. Tsaiwa tayi cak sannan ta waiwayo tana duban idanunsa. Nauyinta kadan ya kama Dr jarma "Ga namu dakin, naga kina shirin bin yara" "Eh tare dasu zan kwana" ta amsa masa kai tsaye. Kai ya girgiza "Kada kiyi haka don Allah shifa,tsahon shekaru talatin ba wani abu,yau dai ki yarda mu hada makwanci, koda kwanan zaune zamuyi ni dake,aqalla ko hira mayi,ko bitar bayan rabuwa mayi" "Dakai da wa?" "Da shifa dina" ya amsa mata kai tsaye yana kallonta. Ta fuskanci lagonta yakeson karyawa,sai kawai ta dauke kai tayi gaba ba tare da tace masa komai ba. Caraf ya kama luggage dinta ya riqe,nan ma bata ce mas komai ba ta sakar masa tayi gaba abinta Zare ido nadeeya ta hauyi da gain maji ta shigo dakinta,daga ita sai afifa ne kadai sukasan yanzun maji tana amsa sunan matar Dr mahmud jarma a karo na biyu "Maji ai munyi sallama ko?" Harara ta watsa mata, dole ta tsuke bakinta ta bata qofa ta shigo. Tana kintsa dakin tana satar kallon majin, amma bata da bakin magana dole ta qunshe abinta a ciki, saidai gasan ranta tausavin abban nata sai ya kamata. Kusan minti biyar yayi a tsaye a gurin rige da luggage din shifa data bar masa,jiki a matuqar sanyaye yaja luggage din ya bude dakinsa ya shige da ita. Yana shirin zama kira ya shigo wayarsa,koda ya duba sai yaga fauziyya ce,ya daga kiran yana zama saman stool "Fauziyya ya akayi?" "Wai yaaya ina kuka shiga?" "'Meye ya faru?" Wani abu me daci ta hadiye "Yaaya,wanne irin mutane ne marasa mutunci cikin asibitin da fadeela ke jinya? kodai yarinyar ta shirya wulagantani ne kawai?" "Wai meye fauziyya ya faru?" Ya fada cikin qagauta da jin gorafinta. "Yanzu yaaya kamar ni?..…... ni fauziyya za'a hana shiga ganin fadeela? bayan na gaya musu matsayina a gurinsu? wai ba'a basu izini ba? wallahi yaya muddin kana sona kana kuma gaunata saika binciko wanda yasa a hanani shiga ganin jikata" ta fada da murya mai rawa dake nuna hawaye takeyi "Yanzu kina ina?" "(na Mercure hotel" "Ki saki wannan dakin ki samu taxi,zan turo miki address din hotel din da muke" "Tom" ta fada cikin zafin da ita kadai tasan yadda takeji a zuciyarta. Wayar ta ajiye tana furzar da iska,ta fara fahimtar fissafinta na neman wagajewa ne,a yanzun kuma tana buqatar nutsuwa qwarai tare da takatsantsan wajen fidda sabon takunta "Bansan wanne kaidi ne zaiyi dai dai da abinda kika aikatamin ba säahar, maji…...maji....bazan taba bari kici gaba da rayuwa kusa da yayana ba bare gaddarar sake zamowa matarsa a karo na biyu ya afka min ba". Abindata furta kenan tana kallon fuskarta ta cikin madubi, zuciyarta kamar zata fito ta bakinta saboda zallar bacin rai. Da kansa ya fito bayan isowarta hotel din,ya sauka qasa ya shigo da ita. Suna shigowa veranda din nadeeya na fitowa a dakinsu "'Mommy ina kika shiga ne tun dazun?" Harara ta ballawa nadeeya din,saboda a yanzun dan sauran tausayin nadeeyan da takeji wanda shine silar da yasa take daga mata qafa bata sakata cikin budget yanzun ya fara ja baya "Sai yanzu kikasan da ni,saboda kinga uwarki ko?" Yar Daria kawai ta saki,dr jarma da yanzu bayason jin zancan maji daga bakin fauziyya yace "Nadeeya,maza ki cewa ummanki ta fito muyi sharing dakina,ke sai ku kwana da mummynku" "Toh abba" Nadeeya da hakan ya yiwa dadi ta juya zuwa dakin nasu. Wani razanannen kallo hajiva garama ta sakarwa dr jarma "Yaava? va zaka hada dakin kwana da matar da ba halalinka ba? ka manta ba aure a tsakaninku shekaru kusan talatin?" A nutse ya kalli fauziyya din,karon farko sai mamaki ya mamayi zuciyarsa saboda tsananin tashin hankalin da ya gani saman fuskar fauziyya "Kinsan dai ni musulmi ne kuma babu ta vadda zan aikata abinda yake Haram, ko 'ya'yana yanzun ba zasu barni ba, bare na jima da mallakar hankalin kaina" "Kanaso kacemin ka maida aurenka da SHIFA?" Hajiya qarama ta jefa masa tambayar cikin matsanancin tsoron amsar da zata fito daga bakinsa. Kai ya jinjina mata, kafin yakai ga bude baki yayi mata bayani har ta fashe da kuka me sauti sannan ta juya cikin sassarfa tana nufar stairs da sassarfa. "Fauziyya,meye haka?" Ya fada yana bin bayanta da sauri. Gabanta yasha yana kallonta, mamaki yana sake kamashi tare da irin kukan da takeyi,kuka ne irin wanda yake fita kai tsaye daga cikin zuciya kuma bilhaqqi "Wanne irin kuka kikeyi haka fauziyya?, na dauka zakiyi farinciki ki kuma taya 'ya'yanki murna akan daidaito da muka samu da mahaifiyarsu bayan shekaru masu yawa bama tare?" Yayi mata tambayar idanunsa cike da ayar tambaya. Cikin rai da zuciyarta gangar jikinta ta bata muddin batayi da gaske ba zata fallasawa kanta asiri "Ba wannan bane damuwata ba yadda yaaya a watannin nan kai da toufeeg baku daukeni a bakin komai ba, tamkar ma kuna shirin fara juyamin baya, kunata al 'amuranku ba tare da shawarata ko sanina ba, saboda kaga qasa ta lullube idanunsu ummee?, wayyo ni Allah fauziyya,sai da girma yazomin sannan zan fara ganin ainihin abinda maraici yake nufi?,said..... " Bata garasa fadin abinda tayi niyya ba qirjinta taji ya riqe kamar ana sukarta,kadan kadan ta fara jin jiri da wani irin ciwo da wani sashe na kanta ya riqe dashi,sai numfashinta ya fara mata wahalar jaa,abinda yaja hankalin Dr jarma kenan,.ya fahimci akwai matsala va matsa kusa da ita vana rigeta tare da tambayarta lafiya?. Tuni ta fara wani irin haki,Allah ya taimakeshi a sannan daya daga cikin ma'aikatan hotel din yazo wucewa. Shi va taimaka masa suka rigeta bayan yay kira zuwa clinic na hotel din, aka dace akwai likita,kai tsaye suka nufi dakin nadeeya da ita. Sanda suka tura gofar suka shiga nadeeya na tsaye tana yiwa maji nacin taje abbanta yana kiranta "Nadeeya,wai yaushe na zama kakarki ne? ki fita a idona fa?" Kafin nadeevan ta sake cewa komai suka shigo da hajiya qaraman a rirriqe,sai maji ta mige tsam tana dubansu har suka kwantar da ita saman gadon, ma'aikacin hotel din ya juya ya fita don ya garaso da likitan. Zafafabiyar *HUGUMA* * TABARMAR KASHI * Book 02Page 54 _Assalamu alaikum warahmatullah_ _Zan danyi wani qarin haske game da hukuncin jinin b'ari_ _Duk cikin da akayi b'arinsa gasa da kwana tamanin da daya,ya zamana a b'arin gudan jini ne ko jini ba wasu alamu na halittar dan adam ana daukan jinin da ya biyo baya ne a mazaunin jinin cuta,zakiyi sallah da dukkan ibadunki,me gida kuma yana iya zuwa miki_ _Cikin da yayi sama da kwana 81 sannan akayi barinsa,ko kuma cikin barin anga was alamun halitta kamar hannu ko qafa ko yatsa da sauranu,to hukuncinsa hukuncin jinin haihuwa ne_ _Jiya na sha'afa cikin rubuta na,cikin sãahar yana qasa da wadan nan kwanakin,duka duka bazai wuce kwana talatin ba,so kunga kenan sallah da sauran ibadu zataci gaba dayi,sannan me gida na iya zuwar mata,saidai ya danganta,wani yana da tsantsamin da bazai iya aikata wannan ba,wannan zabinsa ne,yana iya jira har ya dauke,ina fatan an fahimceni_ *Wallahu A'alam* Duk yadda taso ta boye hawayenta,ko don kada ta bawa maji damar ganin rauninta amma ta kasa,tana jin zucivarta kamar zata fita daga qirjinta,duk wahalar da tayi?,duk shekarun data kwashe tana tanadi?,duk shekarun data diba tana qullawa tana kwancewa yanzu ya tashi a banza?, tayi wahalar banza kenan tunda har gashi maji ta dawo cikin rayuwar dan uwanta? lallai matar nan,da wadanne irin manya manyan bokaye take aiki da suka tsaya mata haka tsahon shekarun?, taketa wahala bata samu nasara dari bisa dari ba? ‚guntuwar nasarar kuma da take ganin ta sameta yanzun lokaci guda ta shammaceta ta sanya hannu ta tankwabeta?. "ita kuma me ya sameta haka?" Maji ta fadi tana duban Mahmud kai tsaye, shima ita ya kalla "Ban sani ba shifa,muna cikin magana da ita naga tana shirin faduwa" idanunu maji ta mayar kan hajiya qaraman,ta santa ba qaramin sani ba,kalar kuka da hawayen da fauziyya ke zubarwa a yanzu tabbas bana banza bane. Miqewa tsam maji tayi tana maida dan madaidaicin hijab dinta "Hala ka gaya mata wani abune daya tayar mata da hankali ko kuma yayi mata zuwan ba zata?" Tayi maganar da sigar tambaya saidai kuma bata kalli dr jarma ba tana laluben jakarta, don a yanzu ji takeyi ya kamata ta fita zuwa dakin jarma din ko don idanun fauziyya su sake gane mata abinda take tantama a kansa,don tayi imanin labarin gizo baya wuce qoqi "Wannan family matter ne, Allah yasa kaffara ce" ta fadi tana ratsa tsakaninsu ta fice a dakin. Hajiya qarama na kallon sanda Dr jarma yabi maji da kallo,ya kuma sauke ajivar zuciya lokacin da ya tabbatar dakinsa ta nufa,wani sashe na hanakalinsa yaji ya kwanta dari bisa dari. A nutse likitan ya cire abun awon bugun zuciya dake wuyansa,ya kuma fara tattara abun gwajin B.P dinsa yana rufewa "Jininta ne yayi mugun hawa lokaci guda,kuma dole ta kiyaye abinda zai sanyata bacin rai,idan ba haka ba komai zai iya faruwa da ita,zata iya samun matsala a zuciyarta,kuma zata iya haduwa da paralyse". Bayanan na likitan ba qaramin girgiza mata zuciya sukayi ba, abinda ya sanya hawayenta yaqi tsayawa kenan,ta sake saka Dr jarma a gaba da kuka "'Indai farinciki na kakeso yaaya da kuma lafiyata dole sai idan ka rabu da maji, har yanzu shifa bata qaunata" duban nadeeya data zubawa hajiya qarama ido dr jarma yayi "Jeki tava mamanki zama nadeeya,ina zuwa" tsam ta miqe tana jin wani daci cikin zuciyarta,karo na farko fuskar hajiya qarama na komawa baqiqqirin a idanunta,ta dauka ita din me lallashin abbansu ne akan ya maida musu majinsu suyi rayuwa tare da ita kamar kowanne d'a da mahaifansa,sai gashi abun mamaki a gaban idanunta mommy qarama din ke cewa a saki mahaifiyarta?,me maji tayi mata?, ita da duka duka ko awa hudu basuyi da haduwa ba a yau din. A nutse ya maida dubansa ga fauziyya dake ci gaba da aikin kuka kamar wata qanqanuwar yarinya,zuciyarta ja sake cika da mamakin yadda a yau yaya Mahmud din yayi funfurus da kukanta,abinda a baya baya taba iya jurewa kukanta koda na minti daya ne "Fauziyya,yanzu ke bakijin kunya a gaban yarinya ki dinga fadin a saki uwarta?" Tambayar ta sake gigita tunanin hajiya garama,ta yungura zata tashi don ta kalli yayan nata da kyau, amma yadda kanta ya sara ya hanata aikata hakan,sai daga kanta tayi tana daga kwance ta kalleshi "Yaaya, matsayina baikai ka saki shifa ba saboda ji?" Kai ya girgiza "Komai ana yinsa ne saboda dalili, banga dalilin da zai saka na saki shifa ba, abinda nayi mata a shekarun baya ma kadai ba tare da qwaqwqwarar hujja ba har yanzu ina nadamarsa" "Ba zaka iya sakinta ba yaaya?" "Fauziyya ki kwanta kisha magani,ki daina maganar sakin maji a gabana banaso,karon farko da zan nema abu nima daga gurinki kenan" ta qarasa maganar yana danna wayarsa yayi kiran nadeeya. Idanun nadeeya saman fuskar maji data hade yatsun hannunta guri guda,har yanzu tana jiran amsar tambayar data yiwa majin. "Maji,don Allah ki gayamin,me kika yiwa hajiya qarama haka a rayuwarki?" Maji ta daga kanta a nutse tana duban nadeeya "Idan nace miki ban sani ba zaki yarda dani?" Kai nadeeya ta gyada "Na yarda maji, saboda tunda kike damu baki taba yi mana qarya ba,koda qaryar wasa kuwa maji" nadeeya ta furta cikin gamsuwa tare da yarda da kowanne furuci da yake fita daga bakin maji din. _K'alubale a gareku iyaye,babu abinda yake matuqar ruguza rayuwa,ya sauke maka dukkan wani kwarjini da kima taka irin K'ARYA, duk wata matsala da muke fama da ita a yanzun ta fara ne daga gidajen aure,matsalar shugabanni na gari, matsi da wahalar rayuwa, daya daga cikin jigon matsalar itace K'ARYA,muna wani kuskure na yiwa yara qaryar "idan naje guri kaza zan siyo maka mota,ungo (bayan babu abinda zaki bashi)yiwa wata ko wani garya idan kuna hira bayan ke kanki kinsan qaryar ne,ko yiwa mahaifinsu qarya don ki kubuta daga wani laifi da kika aikata masa,wallahi irin wadan nan qananun abubuwan da muke rainawa su yara sukafi dauka tare da qoqarin kwatantawa,kafin kace meye wanann sai a wayi gari yaro ya zama shahararren maqaryaci, tun yana qarami yana ganin ba komai bace, zuwa sanda zai girma sai ya zama gagara badau a fagen qarya,qarya masifa ce,qarya masifa ce,tana iya sanyawa a tsani mutum,kamar yadda gaskiya ke siyawa mutum soyayyar jama'a,iyaye mu kula,mu raini 'ya'yanmu a cikakkun masu gaskiya da fadinta da aiki da ita,mu nuna musu ita kadaice hanya mafi dorewa da sanya rayuwa tayi dadi nan duniya da ranar gobe, Allah ya bamu dacewa,ya bamu ikon tarbiyyantar da su bisa tafarkin addinin musulunci_. K'arar wayarta ta katse tunanin da kowannensu ya shiga,ta daga wayar Dr jarma din sannan ta ajjiye tana fadin "Gani nan zuwa abba" saita waiwaya ga maji "Abba na kirana,sai da safe maji" murmushi tayi "Ki kwanta kiyi baccinki, bance kuma ki tanka mata da maganar ba,kici gaba da addu'a da tsare kanki" abinda maji ta gaya mata kenan,wanda har ta isa dakinsu tana juya maganganun a ranta. Nadeeya din na fita ta shirya kanta tayi kwanciyarta saman sofa bed tare da qudundunewa a duvet,lokacin da ya shigo kwarjini tayi masa,ya kasa cewa komai da ita,ya sani ya mata laifi a rayuwarta me girman gaske, da ya tashi dawowa da ita kuma zucivarsa ta kasa daurewa ya tsaya lallabata,ya biyo ta ganin kakanta suka tilastata suka maida aurensu,ya sani dole ya lallabata ya gama wanke laifinsa fes sannan su dora daga inda suka tsaya,don cikin zuciyarsa yana jin kamar yanzu ya fara son shifa din. Yana zaune daga saman gadon, qafafunsa a miqe yayin da ya jingina bayansa da fuskar gadon. Duvet ya jawo ya rufe qafafun nasa zuwa qugunsa, idanunsa nakan wayarsa da yake rage saqonni na mutane, sannan fiye da rabin hankalinsa yana kanta sanda take gaban madubi tana shafe skin dinta da mai tare da gyara jikinta da turarukanta tausasa. Dagowar qarshe da yayi ya kasa dauke idanuwansa daga kanta,sai ya sauke wayar daga cinyarsa ya miga mata hannuwansa yana daga zaunen, murya can qasa yace da ita "Come closer" wani abu ne ya saukar mata a take, irin abun nan da ba'a rasa kowacce diya mace dashi,jan aji tare da jan rai, iya kallonsa a gareta ya saukar mata da wata kasala da yanayi a jikinta,wani abu me qarfi yana buda zuciyarta ta qarfin gaske,sai ta fara takowa cikin jan aji da yanga fiye da yadda ainihin tafiyarta ta halitta take,wanda ita kanta batasan hakan na faruwa da ita a daidai lokacin ba. Kasa jura yayi,ji yayi kamar ba zata iso ba,sai kawai va vaye duvet din ya sauko gaba daya daga kan gadon ya tako ya risketa a hanya. Hannayensa ya sanya ya zagaye bayanta dasu tare da matsowa da ita dab dashi a zafafe, fuskokinsu sukayi kusa da juna sosai, ta yadda kowa na iya ganin fuskar dan uwansa fes. Kallon kallo suka fara yi a junansu tamkar yau suka fara ganin fuskokin juna. Daga kan kyakkyawan girarta zuwa dogon hancinta me dan tudu da ya zauna sosai akan tsararriyar fuskar dake da shinfidadden kyau,ya zarto a hankali zuwa zaman lips dinta dake hasken lip gloss data dan shafa masa. Tsigar jikinsa yaji ta tashi,ya miqa yatsantsa saman lips din nata a hankali yana kewayeshi da su "You're super hot!" Ya furta a hankali kamar me rada "Kinsan kiss guda daya yana burning around 6colories a jikin dan adam?, do you want to workout with me?" Yayi tambayar yana dage mata dukka girarsa guda biyun?. Wani siririn murmushi ne ya kubce mata ba tare data sani ba,murmushin da ya qara mata kyau, kyan daya sake ingizashi,ba tare da ya jira ta bashi damar da yaso samu tun farko ba ya hade bakinsu guri guda,ya dora lallausan lebansa saman nata ya fara yadda yaso dashi. Wani irin abu ya shiga aikawa jikinta,kowacce gaba tata ta amsa,ta kasa kowanne motsi tana jin yadda yake sarrafa bakinta zuwa lips dinta cikin qwarewa kamar ya samu sweet,tsahon wasu mintuna kafin ya janye a hankali yana maida numfashi. Kasa hada ido tayi dashi tana jin nauyinsa yana saukar mata, hannuwansa yasa ya kamo fuskar tata a tausashe da sautin da koda kana cikin dakin babu lallai ka iya jin me yake fadi "Kinsan meye?" Kai ta girgiza masa a hankali "A da banason abu me zagi sam sam,but when i tasted your lips,sai na zama addicted to sweet, because your lips are the yummiest thing in the world" kunya ce ta kamata matuga da gaske, kalamansa suna da wani irin girma da ko yaushe ya furta su sai ta jita kamar a wata duniya ta daban take, kalamai ne da ba gama gari ba qwaqwalwarta da zuciyarta basu tana amsar kalamai masu tsada da girma irinsu ba tsahon rayuwarta, ta rasa inda zata boye kanta sai kawai ta cusa fuskarta tsakiyar qirjinsa tana boyeta. Murmushi ya saki yana dora hannunsa saman tattausar sumarta "Good!, duk sanda na nema gurin fakewa nima i will bury my face in your boo..... .." Saurin miqewa tayi daga jikinsa,tasan yanzun sai sake mata zancan da zai kusa sanyata narkewa a wajen. Ko taku guda bai bari ta qara ba ya dagata cak ya nufi gadon da ita yana cewa "Muie na karanta miki wani abu" adan tsorace tace "Am still bleeding" bai kulata ba sai daya direta saman gadon,fuskarsa dauke da sirrintaccen murmushin nan da ita daya take samunsa yace da ita softly "So?,all i want is to feel you close to me,tell you my story and at the end watch you fall asleep in my arms,ba wani can gurin zan je ba" ya furta yana zare rigar jikinsa,sai kuma yayi mata rumfa da qirjinsa. Kunya ta sanyata mirginawa,sai yasa hannunsa ya birkitota bayan ya kashe hasken dakin daga nan inda yake ta hanyar switch din dake kusa dasu. Bayanta ya koma ya kwanta tare jawota cikin jikinsa "Sanyi sanyi nakeji kadan kadan,let's cuddle so i can steal your body heat" kafin tayi wani motsi sai ta jishi yana cusa kanta ta cikin oversized shirt din data saka,kafin tayi wani yunquri tuni ya shige cikin rigar,ya zagaya hannunsa ta saman plate tummy dinta ya sake janyota sosai kamar me shirin tsaga jikin nata su narke su zama abu daya. Sanda dumin jikkunansu suka gauraya waje daya sai wata ajiyar zuciya ta subucewa kowannensu lokaci guda "I know the real KHADIJA SÄAHAR,but har yanzu bakisan waye MUHAMMAD TAUFEEQ na gaske ba,i will tell you duk da baki buqata ba,zan gaya miki ne to clear all the doubt and negative think" kunya taji da abinda ya fada,ya akayi yasan tana masa wani bahagon kallo?. Bai fira ta bawa kanta amsa ba ya fara magana da nutsatsiyar muryarsa. "Kinsan waye mahaifina, qanwata da mamana,na taso hannun mommy qarama fauziyya tun ban gama mallakar hankalin kaina ba har na zama mutum, a lokacin na dan fuskanci rigonmu a hannunta akwai qalubale da matsaloli, amma duka mun shanye na kuma kula da nadeeya fiye da yadda nake bawa kaina kulawa har muka kawo yanzu. Na girma wani mutum na daban bawai ina yabon kaina ba,dukiyar mahaifina bata a cikin lissafina,komai ina lissafin yadda zan mallaki nawa ne na kaina,sai kuma na fuskanci wani abu. Fauziyya bata qaunar na mori komai daga mahaifina,ko yaushe tana cewa da ni da shi 'ka tashi ka nemi naka na kanka' sannan tana cewa da dr 'ka barshi ya nemi na kansa yasan zafin nema', a haka na gina rayuwata, kusan komai nafi sha'awar na yiwa kaina". Duk yadda naso boye kaina daga mutane su fahimci ni din waye hakan bai yiwu ba, daukan kamanni da mukeyi da abban da kuma ganina cikin was lamuran nasa ya sanya yake wahala na shiga guri ba'a san wayeni ba. Cikin hakan abban ya bada gagarumin taimako ga wata organization ta marayu da iyayen marayu, a nan gurin ne naga AMEESHA. Tana cikin layin wadanda zasu karbi taimako da suke cikin matsanancin hali na rashin muhalli da abinci,acikin masu karbar tallafin duka ta fisu quruciya da qananun shekaru,abinda ya fara jan hankalina kenan a kanta. Komai ina qoqarin yinsa akan tsari, don haka a sannan ban tunkareta ba kai tsaye,sai da aka tashi taron nabi address da komai nasu na isa gidansu. Na tsaya na tabbatar da halin da suke ciki din kafin na gabatar da kaina a wajenta. Murmushi naga tayi bayan na gama mata bayani "Na ganka a wajen taro, ba kaine d'an Dr mahmud jarma ba?" A zahiri banzo da nufin gaya mata waye ni ba,to amma kuma bazan iyayi mata qarya ba,don haka na amsa mata da "eh nine" Zafafabiyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 *HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 55 Tom Bai taba dauka fada mata hakan zai zama babbar matsala a tsakaninsu ba,ya sanya tausayinta da na mahaifiyarta shine gaba da komai, tausayinta ya sanya masa soyayyarsa a ransa, musamman da ya fuskanci mahaifiyarta dake kwance tana fama da jinya mutuniyar kirki ce qwarai. Irin mutanen nan da sam rayuwa bata damesu ba,basu da wani buri me zurfi a cikinta. Kusan tafi kowa farinciki da wanzuwar taoufeeq cikin rayuwar d'iyarta, bawai saboda dukiya ko kuma wani abu daya mallaka ba, a'ah tsantsar nutsuwa hankali da hangen nesa da ta hanga muraran tattare dashi,dukiyar mahaifinsa ko wadatarsu bata sanya masa girman kai ko jin cewa shi din wani bane,tayi imani ameesha din zatayi aure hannun da za'a datajtata, za'a mutuntata,inda koda bata raye ba zatayi kukan maraici ba. To ita rayuwa a duk yadda kaga Allah ya ajiye bawa,tofa yafi cancanta da wannan matsayinne, saboda shine Allamul ghuyub wato (masanin gaibu). AMEESHA na daya daga cikin matan da zuciyarsu ke cike da dimbin burika na rayuwa saboda kyawun fuskar da Allah ya azurtasu dashi. To amma me? yanayin talauci da matsi na rayuwa da kuma yanayin environment da suke ciki dukkan alamu sun nuna babu inda wadannan burika nata zasu shura,saidai duk da hakan akwai was baqin halaye da idan kayi tsinkaye zaka iya fahimta a tattare da ita. Yadda ameesha din bata da saurayi duk da kyau da take dashi da kuma yadda matasan unguwar ke sonta ya gara kafa ameesha a zuciyar toufeeq,a nasa tunanin tsananin kamun kai ne da kuma darajta kai,abinda bai sani ba shine,ita din ta raina ajin dukkan mazan da suke zuwa mata da kalmar soyayya,tana ganin tafi qarfin ajinsu,ko a ranar da taje karban tallafin sai da mahaifiyarta tayi da ayar sannan taje din, da kuma tsananin rabon haduwarsu da toufeeq. Shigowar toufeeq cikin rayuwarta sai ya sanya ta fara jin kanta yana budewa,idanunta suka fara budewa,ta fara shanshanowa tare da hango cikar wadan nan burikan da talauci ya yiwa dukan mutuwa suka kwanta magashiyyan,sai ta fara farfado dasu, musamman da ya kasance toufeeq din me sakakken hannu ne, mutum ne me tarin kyauta. Cikin lokaci qalilan tafi qarfin sutura da cima,ta samu tsadajjiyar wayar hannu wadda tayi sanadin haduwarta da 'yammata irinta da suka dauki rayuwar duniya da fadi,'ya'yan da sai da taimakon Allah da huwacewarsa ake samun abicin da za'a ci cikin gidajen iyayensu,amma idan sukayi wanka suka riqe wayoyinsu zakayi tsananin 'ya'yan wani commissioner dinne. lya wayar hannunsu kawai tafi jarin ubansu kauri. To bare kuma ameesh da a sannan abinci a gidansu baya yankewa, toufeeq ya fahimci yanayin rayuwar da suke ciki, ya kuma dauki nauyin komai hatta da jiyyar mahaifiyarta. Mutuniyar kirki ko yaushe addu'a take Allah vasa ameesha ta kasance tasa ce ta har abada,ko yaushe fada takewa ameesha ta riqeshi hannu bibbiyu. To koda umma batace mata ta riqeshin ba itama ba zata soma sakinsa ba,ina taga ta sakin toufeeq din?, mutumin da ya fara matso mata da burikanta kusa kusa da ita ya kuma fara cika mata su?. Ai bata ma gama sanin waye toufeeg din a zahirance ba sai bayan haduwarta da hadaddun qawayen data maye gurbin rayuwarta dasu,ta sake sanin waye mahaifin toufeeq, a nan suka hure mata kunne akan ta qara yawan buqatunta tana sake samun abubuwan rayuwa masu tarin yawana jikinsa,su saka sanya ta fara raina hidimar da yake mata,saboda suna gaya mata "A arzigin ubansa,wannan hidimar da yakeyi miki tayi matuqar yin kadan" yana mata kwarjini sosai,tana kuma kunyar ta tambaya kanta tsaye,sai ta fara shigo da qarairayi tana karbar kudade a hannunsa. Bai taba hanata ba,duk da sannu a hankali ya fara fahimtar wasu kudaden da take karba setup ne kawai,yana yi matan, saboda kawai a lokacin bugatunta basa hawa kansa,kuma basufi qarfin samunsa ba. Sanda ya gabatar da zancan aurensa ga Dr jarma hankalin hajiya garama yayi mugun tashi,ko kusa ko alama bata taba tsammanin zaiyi zancan aure a lokacin ba, babban abinda ya Sanya take sake ingiza Dr jarma akan yabar toufeeq ya nema na kansa kada ya sangarce ya shagala da dukiyar sa ba,ba komai bane sai don taja lokaci zuwa sanda HASEENA zata sake tasawa,ta zama mutum, kuma a nata lissafin sanda haseena zata gama nata karatun zuwa lokacin ya zama wani me fada aji,yayi irin kudin da take buqata daga mijin diyarta, tunda toufeeg din yana da wani irin nasibi da albarkar hannu. Kiransa tayi tayi masa fada sosai bayan ta gama binciken wace ameesha?,diyar wacece?. Fadan da tayi masa ta bullo masa ta bayan gida ne "A matsayin da mahaifinka yake dashi, da baiwar da Allah yayi maka,ai abun kunya ne ace kaje ka nemo aure a wannan gidan" "Arzigin kaykkyawar nasaba shine arziqi bana dukiya ba,so ni banga abun damuwa ba mommy, please cool down" ya fada da I don't care manner dinsa. Duk hanyar da zatabi don ta ruguza abun bai yiwu ba saboda rabo da Allah ya tsaga a tsakani,tana ji tana gani akayi auren, saidai kuma ta barwa ranta lallai saita ruguza abun ko ba dade ko ba jima, don ba zata bari ma haseena ta zauna da kowacce mace da sunan kishiya ba. Tun lokacin shagalin bikin ameeshan ta fidda tsarukan biki na kere sa'a da kuma kashe kudade,yayi wasu wasu kuma yace bashi da kudi bazai iya ba. Maganar data sosa ran ameesha, zugar tawagar qawaye kuma suka sake azata akai suna fadin "Anya zaki qulla abun arziqi da mutumin nan?, ki dubi dukiya irin ta mahaifinsa amma ya dinga ambatar babu?, ina babu taga gurbin zama a family dinsu ma gaba daya?. Washegarin ranar da Ameesha ta tare bayan sunyi first night dinsu,tana langabe a jikinsa saboda hannu da tasha a hannunsa tace dashi "Mota nakeso a matsayin tukuicina na first night" gyara zamansa yayi "A yanzun bani da kudin siyan wata sabuwar motar, motocina guda biyu,duk sanda kk fara fita kidauki guda daya aro kafin na samu sukunin siya miki". Tashi tayi ta zauna sosai tana kallonsa "Nikam mamaki yake kamani idan kana cewa BABU.kasan me wannan kalmar ke nufi? duk tarin dukiyar da Allah ya mallaka muku kai da mahaifinka?" Murmushi yayi ya girgiza kai, zuciyarsa na girgiza sosai da yadda ta iya buda baki kanta tsaye ta fadi abinda ya fahimci ya jima a zuiciyarta,yau ta amayar dashi da alama ta gaji da boyonsa "Bana lissafi da abinda ba gumina bane ya tarashi ba,sanann ban isa nayi rabon gadon mutumin dake rayuwa lafiya lau cikin iyalinsa ba,duk abinda naga ya kamaci nayi miki zanyi miki gwargwadon wadatata ba wadatar mahaifina ba,nayi miki alqawarin ko sau daya ba zakiyi kukan rashin ci sha ko suttura ko kuma kudin da zaki biya bugatunki ba tare da almubazzaranci ba". Hakan da ya fadi baiyi mata sam,tun a satin ta fara fushi dashi akan ya gaza siya mata mota,bata kuma sake bari ya tabata ba,har sai bayan wata guda da ya kawo mata motar har farfajiyar gidan. Ba kunya ba tsoron Allah ta ware,ta dinga murna tana waya da qawayenta tana labarta musu zuwan motar,ranar kyautatawa sabuwa tare da wani sakin jiki na musamman, tun a sannan jikinsa ya fara sanyi, tunani kala daban daban ya shiga kai kawo a ransa. Watansu uku kacal ta soma ciwo wanda aka tabbatar musu da shigar ciki na watanni biyu, abinda bai taba kawowa ba,don kuka ameesha ta dinga yi,da yabi ba'asi babu kunya tace dashi "Nifa ban shirya haihuwa yanzu ba,haba.....kamar wata akuya,aure wata uku kawai? ,bana tunani cikin friends dina da akayi aurenmu tare akwai wadda ke da ciki, sai kuma ni?duka duka ma sau nawa mukayi tarayya?, uku ne fa kawai" Kansa kawai ya kawar ransa yana baci zuciyarsa na masa suya Sosai,dazun kafin su fito ya raba rigima tsakaninta da hajiya qarama,ci mata mutunci tayi sosai abinda ya hanashi daukan mataki rashin lafiyarta,gashi yanzun ta sake dasa masa wani bacin ran "Me kikeso yanzu kice?" Ita kanta kafin ta furta sai dataji shakka,saboda tasan halinsa sarai,idan ransa ya baci ko va baude bashi da dadin sha' ani,ciki ciki tace "Kawai, kawai aje a zubar dashi, a sakamin implants,kamar nan da next two years sai a cire kafin na samu ciki na haihu aqalla munyi 4 to 3yrs" wani wawan birki yaja tsakiyar titi,saura kadan ya daki motar dake gabansu "Ni inaso, kuma ina gaunarsa ko da dan qadangare zaki haifa,sannan ina miki rantsuwa da ubangijin da ya busamin numfashi, duk ranar da kika sake yimin magana makamanciyar wannan sai kin gane ni toufeeq asalin tataccen mara mutunci ne" daga haka bai qara ba ya tashi motar ya figeta da mugun gudu,har tana yin gaba kamar zata daki gaban motar. Har suka isa gida bai sake kallon koda koda gefen da take ba,duk da kikan da taketa yi har da sheshsheqa. Suna isa gidan ya fita a motar abinsa ya barta. Cikin watanni uku kacal tayi masa abubuwa masu tarin yawa,abu daya zuwa biyu yasa yake shanye komai,darajar so da zuciyarsa ke mata zalla mara algus kuma fisabilillahi, sai kuma mahaifiyarta da a kullum yaje gaidata ko yayi mata aike take bashi tausayi,bakinta baya gajiya da gode masa da sanya masa albarka tare da bashi amanar ameesha,don a koda yaushe takance bata dauke tsammani da mutuwar ta ba. Yadda ya watsar da ita itama data gama kukan baqinciki kan yadda cikin zai kawo mata cikas akan sabuwar rayuwar morewa da more arziqin mazajen da suka aura da cikin zai kawo mata, taga baibi ta kanta ba kwana daya biyu har zata nema sulhu sai ta fasa,zugar qawaye da tarin shawarwari batakai marasa kan gado sukayi mata caaa a saman kai,sai itama ta watsar dashi taci gaba da rayuwarta. Shawara daya ce tasu da bata zauna mata a kai ba,na tayi amfani da qwayar zubda ciki ta cire cikin kawai. Ita kanta tasan aikata hakan babban ganganci ne da kuma kuskure me tarin yawa a gareta,tunda tafi kowa sanin waye toufeeg din. Zafafabiyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥 "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI_* Book 02Page 56 Koda suka iso gidanma cikin motar yayi tafiyarsa ya barta bai kuma sake bi takan al 'amuranta ba,ya ajiyeta gefe saboda yadda tayi mugun bata masa rai saidai bai fasa sauke duk wani nauyi da haqgin ta ba, da kuma sauran bugatu da yasan mace me juna biyu zata iya buqata. Fushi itama ta dauka sosai dashi, hukuncin data yanke na farko na qaurace masa a shimfida, abinda ta manta dama duka duka ina abun yake? sau nawa ta bayar da kai?. Randa hakan ta fara faruwa migewa yayi ya zauna sosai ya kuma kunna fitilar dakin, idanunsa a kanta sanda take tattare kanta gefe guda cikin fushi "Me kike nufi?" "Kai tsaye bazan iya bane, tunda nima ba wai ina samun abinda duk zuciya takeso daga gareka bane" "Okay" kawai vace da ita. Tun daga ranar shima ya ajiyeta a side ya shiga sabgar gabansa. Tun tana daukar abun da saugi tana kumbure kumburenta har ta fahimci duk inda ta dosa shi ya wuce nan, tilas ta fara neman hanyoyin shiri. Shirin nasu babu jimawa sai kuma Allah ya saukar masa da wani ibtila'i a cikin kasuwancinsa. Asara ya dinga samu daya bayan daya,kafin kace meye wannan?, komai nasa ya tafi sai abinda ba'a rasa ba. To duk sanda vanayi irin wannan ya faru dole a samu sauyin rayuwa abubuwan da aka saba yi a baya dole a sassauta wasu ma sugi samuwa don dai a samu a tsira da abinda yayi saura,a kumayi qogari da tanadin mai da rayuwa kan bigirenta na asali. Sam ameesha tace batasan zancan ba, kawai dai yayi niyyar wulaganta ta ne da tozartata, kamar yadda mata da yawa ba kasafai suke iya fuskantar irin wannan yanayi ba idan ubangiji ya jarabci mazaje da shigarsa ba (akwai mugayen mazaje asalan,wadanda ba'a san samunsu ba saidai rashinsu, mazajen da basusan su yalwatawa iyali ba,suna da arziqi amma matansu saidai suji labari ko su gani a iya jikinsu su kadai, irin wadan nan koda ibtila'i irin wannan ya fada musu,ba kasafai ake zargin mace da kau da kai da rashin nuna tausayi a kansu ba,muddin namiji tsayayye ne wanda yake hidimtawa iyali da wahalta musu kaman toufeeq a labarin nan, to butulci na garshe da zaki masa shine ki nuna baki damu da shigarsa matsala ba,sanann baki zama matar rufin asiri ba, Allah yasa mu dace).. A wanann lokacin da yake fafutukar gain yayi maintaining rayuwarsa tare da goqarin cike gibi da guraben da da wanann babbar gaddarar ta fada masa,daga gefe kuma ameesha na zuba nata lalatar kala kala. Ko sau daya bai taba yunqurin kaita qara ba,saboda tausayin mahaifiyarta da ko yaushe adduarta Allah ya qaddara dogon zama a tsakaninsu, mutu ka raba. Cikinta yana da wata hudu kacal ta matsanta masa sai ya saketa, tace sam ba zata iya zama dashi ba,ta gaji da zama cikin talauci bayan mahaifinsa shahararren mai kudi ne, muguntar kai ko kuma girman kaine yake damunsa?, Da bazai shiga dukiyar mahaifinsa ya amfana da ita ba?,itama ta samu damar cika duka burikanta da muradan rayuwarta?. Maganganun data fada a lokacin masu tsauri ne sosai da suka sosa masa zuciya. Daga daren har wayewar garin bata barshi ya runtsa ba, haka ya dauki takarda ya rubuta mata saki guda daya. Har zai fita ya dawo ya yanka mata zazzafan warning "Koda wasa wani abu ya samu cikina,na rantse da ubangijin sammai da qassai sai nayi miki daurin da koda dukka qasarnan gatanki ne basu isa su karbeki ba". Al'amarin ba qaramin farantawa haiiya garama yayi ba "Ai duk mutumin daka ganshi a waje nan ne yafi dacewa da shi shi yasa Allah ya barshi a nan, ai duk inda talaka yake matsiyaci ne(ita ta manta tushenta),ni dama tunda naga idonta Muhammad nasan ba son Allah da ma'aiki takeyi maka ba,dukiyarka take so". Baice mata komai ba,saboda shi kadai yasan yanayin da yake ciki. Yayi tsammanin so guda daya ne tak!, ya dauka so na gaskiya shine so,wanda babu wani abu da yake iya canzashi, bai taba dauka akwai randa ameesha zata iya neman saki daga hannunsa ba saboda kawai raguwar abun duniya daga hannunsa, bayan bai gaza mata ta fannin ci sha suttura ko lafiyarta ba har a lokacin kuma. Duniya ta yiwa •/ hajiya garama dadi, dama wani mugun tsana ta yiwa ameeshan,ko kusa ko alama bata gaunarta,don ko sau daya babu jituwa a tsakaninsu. Sosai hankalin mamarta ya tashi, tayi kuka tayi fadan amma ameesha tayi kunnen uwae shegu,a sannan tayi wani irin kyau ta sake zama mace me aji ta kuma sake sanin cewa ita din matar manya ce duk ta silar auren toufeeq,ta samu sutturu masu aji, ta kuma sake smaun wayewar da take hangen doguwar shimfidaddiyar rayuwa data dara ta gidan toufeeq.yanzu abu daya ne zai zame mata cikas cikin da take dauke dashi,a galla akwai wasu watanni masu yawa a gabanta kafin ta haife ta kuma yaye,ita a yanzun koda haihuwarsa ta samu tayi, komai da zai biyo baya me sauqi ne. Warning din da toufeeg ya karta mata shine abu guda daya da zai hanata juye cikin. Ta sani su din ba qananun mutane bane don dai kawai toufeeq din yana daukan kansa ba'a kowa ba, danginta kuma basa da garfin karawa dashi,so haquri ya zame mata dole kenan. A zahiri tana son toufeeg sosai amma rayuwar data tsarawa kanta ta fuskanci ta sha banban datasa rayuwar da ya tsara,dole to ta ajiye nasa tsarin don cikar nata tsari da burin. Allah me musanyawa bawan da ya dogara dashi daga mummuna zuwa abu mafi kyau cikin rayuwarsa. Wata guda kacal da rabuwarsa da ameesha wani Erin 1 gofofin alkhairi suka dinga bude masa ta kowacce fuska.wasu alkhairan shi kansa bai taba tsammanin samunsu ba a irin wannan lokacin. Lokaci qalilan ya maida ninkin abinda ya rasa harda ma ninkin abinda ya rasa din a baya. Cikin wata hudu kacal duk wanda ya kalleshi yasan ya samu sauyi na rayuwa fiye da rayuwarsa ta baya,ya warware sosai yaci gaba da harkokinsa,sabbin hanyoyin neman kudi suka bude masa fiye da zato. Har a lokacin yana lissafe da watannin cikinsa dake jikin ameesha,kowanne wata yana aika mata da komai da yasan zata bugata, dai dai da ruwan sha na roba haka yake ajiye mata, komai na watanni biyu yake ajewa ninkin abinda zata bugata kenan, hakan baya hanashi sake aika mata da wani bayan kowanne wata. Mamanta naso gwarai ta ganshi amma bata samu wannan damar ba, saboda bata da wayar hannu,sannan kuma shi kansa toufeeq din bai sake taka gidan ba tun daga ranar, amma kuma hakan bai hanashi yiwa mama din aike ba kamar yadda yakeyi mata a baya. Tafiyar da yayi china wadda dawowarsa yayi dai dai da shigar cikin ameesha watan haihuwa, ya iso da siyayyar kayan baby me azabar yawa, har hajiya garama ta kasa jurewa "Kai kam kamar wanda za'a haifawa taron arfa?, yariyar da basusan mutunci da darajarka ba toufeeq kae yiwa* wadan nan hidindimun?, kamar wanda ya rasa mafadi?" Dan qaramin murmushi kawai ya saki,a sannan kome hajiya qaraman ta fadi baya bata ransa ko yaga cewa hakan ba dai dai bane, saidai idan abinda tace din yaji baiyi masa ba ko bai gamsu ba ya canza da abinda zuciyarsa ta kwanta da shi "Mahaifiyar ta nagartacciyar macace,wadda nake da imanin da halinta tayo tare zamu tsufa ni da ita din, saidai mutuwa ta raba, haihuwa kuma ta fari ce hajiya, ko china din gaba daya ake da bugatar na siya masa indai arzigina ya kai zan siya din" "To mara kunya,tashi ka bani waje" ta waske da fadin hakan ta bishi da kallo sanda yake barin wajen ranta a mugun quntace. Lokacin da siyayyar kayan fitar suna nata da kayan baby ta iski ameesha ta gama saddaqarwa toufeeq din ya fara komawa CLASSY TOUFEEQ JARMA din da takeson gani, ta kasa zaune ta kasa tsaye a ranar sai data samu dukkan information da take nema akan TOUFEEQ din "Turgashi, seema kina gain ban tafka wauta ba muddin na yarda na haihu a gida?bayan har yanzu da sonsa nake kwana da sonshi nake tashi?" Tace da gawarta da sukeJ zaune cikin dakinta dake eikin gidansu,wanda ta qawata fiye da kowanne guri na gidan. Tayi furucin ne a sanda take tsaye saman kan qawar tata da tirtsetsen cikinta da take lissafe da randa zata saukeshi ta huta "Ba garamar wauta ba,wannan arzigin dake yafi dacewa,ke yafi cancantar ki cishi" "Yanzu meye mafita?, ta yaya zan jawo hanakalinsa?" "Ke kike da hanya kuwa" seema ta fada tana mata nuni da cikinta. Murmushi ta saki tana shafa cikin nata hadi da gyada kai,sai ta koma ta zauna ta jawo wayarta ta fara kiran number wayar toufeeq din. Har ta garashi ringing dinta ta katse bai daga ba,a qalla ta kirashi ya kusa sau goma amma abiyi picking ba,wannan ya soma daga mata hankali,seema tace "Yasan ke kike kiransa karanto min numbers din na kira miki shi a wayata ko za'a dace ya daga" Harara ta watsawa seemar tana jin kamar ta mareta,ita zata bawa kura ajiyar nama?. "An gaya miki yana daga baqin numbers ne? ai saidai ki dige kina kiransa amma bazai dauka ba,bari ki gani" ameesha ta fada tana gyara zama tare da tura masa gajeran text. Ba dadewa saiga kiransa, murmushi ameesha tayi ta migawa seema wayar "Ki daga kice masa yazo yanzun kamar labour nakeyi yazo mu wuce asibiti" lokacin yana tare da wasu baqi,jin zancan yasa ya barsu ya tsallako ya taho. Yayi mamaki da ya ganta tana fitowa lafiya sumul, Ransa kuma va baci da jin abinda vasa ta kirashi da wannan sigar data daga hankalinsa. Har ta gama bayaninta da koke koke baice mata ta tafas ba,sai data gama sannan ya juya ya bude motarsa zai shige kafin ya waiwayo "Karki sake maimaita yimin irin wannan shashancin, don ni din ba mara aikin yi bane ba zaman banza nake ba da zaman jiran kiran wayarki" sai ya tashi motarsa yabar gurin. Hankalinta yayi gololuwar tashi qwarai, saboda yadda take ganin so kulawa da qauna daga idanun TOUFEEO din bata taba tsammanin zai juyawa buqatarta baya ba,musamman da ya zamanto a yanzun tana dauke da abu mafi soyuwa a wajensa a jikinta ba. A ranar da gyar ta iya bacci. Kwana biyu kacal da faruwar hakan Allah ya yiwa mahaifiyarta rasuwa,wanda shine ya zama silar sassautowar zuciyarsa,ya kuma sauka daga dokin nagin da ya hau,ranar sadakar bakwai ya dauketa ya maidata gidansa da kansa. Ashe wasa farin girki!! Zafafabiyar 🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥 "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 57 Zuciyarsa ta sake jin amanna data koma din, saboda gananun maganganu da yaji sun fara yawo akan shi dinma kada Allah yasa ba irin halin mahaifinsa na auri saki yake dashi ba. Sanda ta koma din duniya ta samu,don haka ta kwantar da kai sosai, duk wani biyayya kulawa da tattali tana bakin qoqarinta, duk da cikinta yayi nauyi amma bata fasa duk wani abu da tasan yana so din ba. Wani lokaci tausayinta kan lullubeshi qwarai,ya sanya hannu suyi duk wasu ayyuka tare, tayi wani mugun laushi, ta sauya kwata kwata daga ameesha din da ya sani. Tun yana mamaki yana d'ari d'ari har ya saki jikinsa, ya kuma barwa ransa rasuwar mahaifiyarta ne ya kawo hakan, tunda ya san ciwon mahaifiya,shi da ba rasuwa ma tayi ba. Biyayyarta da canzawarta ya sanya shima yake tuquru wajen kyautata mata, ya sakar mata komai da take da bugata. Wannan ya sanya ta sake ninka biyayyarta,kyautatawa da kulawa da nuna zallar soyayya me zurfi data sake sanyashi sakankacewa da ita,ya kuma sakar mata zuciyarsa,ita kuma hakan ya bude mata gofofi da dama na abubuwa masu yawa. Cikin wata na goma ta sauka ta haifi fadeela, yarinyar da tazo da wani irin farinjini da tarin alkhairai masu yawa ga mahaifinta harma da mahaifiyar tata. Suna na kece raini ameesha tayi kanta ya fashe sosai, toufeea ya fasa mata kai ya sanya taji ta kere sa'a cikin mata. Hankali kwance ta fara rainon fadeela saboda masu aiki biyu da toufeeq ya dauko mata saboda yarinyar. Wani irin raino takeyi mata kamar ba diyarta ba,a lokacin ya siya mata mota irin wadda takeso saboda dadin zama,a sannan ko watanni biyu fadeela batayi ba ameesha tana iya fita ta barta hannun masu aiki ba zata dawo ba sai yamma awa daya ko biyu kafin toufeeq ya dawo,zata shirya ta shiga sabgoginta cikin gidan sannan ta dauki yarinyar, tun bata gama mallakar hankalin kanta ba ta saba da rashin uwa a kusa. Kusan baba ramatu ce ta zame mata kamar kaka kuma uwa,ta jima tana wanann dabi'ar kafin toufeeq ya ankara. Ya nuna mata bacin ransa qwarai, amma saita kwantar da kai ta bashi haguri tare d algawari ba zata sake ba,don a sanann ko zaginta zaiyi bata tada kai bare ta nuna masa ta damu, bata gaunar duk wani abu da zai hadasu, saboda kudade sosai take karba daga hannunsa, bai kuma taba cewa a'ah ko don me ba?,shi a ganinsa muddin zaka samu kulawa daga wajen mace da biyayya meye ba zaka iya kashe mata ba?,meye ba zaka iyayi mata ba?. Abu daya ne har a sannan ya gaza canzata akai shine bugatar aure, baisan abinda ke faruwa ba da ita sam,amma ya aza hakan akan yanayin halittar ne wanda yasha banban da rasa neeesa ba kusa ba. Damuwar kawai shi tun asali ba meson auren mata biyu bane, hakan ya samo asali da yadda yaga mahaifinsa na yawan aurar mata yana kuma saki tun bayan rabuwarsa da mahaifiyarsu. Kyautatawar bogi da biyayyarsa ya sanya yakejin haquri da mace idan tana da wani nagasu ba aibu bane, dama duk dan adam tara yake bai cika goma ba,duk kuwa da yana shan dan karen wahala amma yana goqari tare da neman sani akan hanyoyin da zai magance matsalar a tsakaninsu a samu daidaito. •_SHEKARA UKU_* Shekara uku da haihuwar fadeelan,a wata rana cikin ranakun sa'a a wajen toufeeq ya samu fiye da yadda yake samu daga gurin ameesha. Sunyi sallama dashi sallama me kyau,cike da aminci da qauna, zaiyi tafiya zuwa Canada. Har bakin mota ta rakoshi tana koke koken zatayi kewarsa, vana dauke da fadeela akafadarsa,yayi murmushi yayi kissing goshin yarinyar yana jin qaunar yarinyar har gasan zuciyarsa sannan ya miga mata ita hadi da kamo hannunta va rige cikin nasa a tausashe "nayi alqawarin ina gama abinda naje yi zan dawo gida immediately, zan iso tare da dream car dinki" wani dan garamin ihu tare da tsalle ta saki ta kuma rungumeshi, yayi mata suprise, bata taba zaton zai siya mata motar ba,ta dai fada ne kawai "Thank you, thank you so much" "You deserved it" ya fada a tausashe yana kissing goshinta itama. Ita ta bude masa motar ya shiga sannan ta rufe masa sukayi gaba tana gurin a tsaye. Sanda ya isa airport sai ya samu anyi cancelling tashin wannan jirgin, sunata bawa mutane irinsa haquri wadanda basu duba sagon da suka tura musu ta email ba akan hakan tun yau din da sassafe, ransa ya baci da wannan al'amarin da sai a qasata Nigeria kawai yake faruwa.haka suka juyo suka bar airport din. Har zai koma gida sai kawai ya fasa ya wuce sabgoginsa,a can din magriba ta kusa cimmasa,sai ga kiran hajiya qarama "Ya akayi number dinka na Nigeria ya shiga? kai da yanzu warhaka ya kamata ace kana canada?" Dan garamin tsaki ya ja yana mata bayani "To Allah yasa hakane yafi alkhairi, yauwa idan zai yuwu don Allah ka dawo yanzun, ina bugatar takardun nan da na baka ajiya,nan da awa daya alhaji kutama zaizo ya karba, ana bugatarsu urgently" ta fada da alamun gaggawa a muryarta "Alright, na gama abinda nakeyi nima,gani nan" "Yauwa,sai ka garaso, koda zaka rigani isa ka jirani please,don ina asibiti yanzu duba hajiya barratu" •"Ba damuwa" yace da ita sannan ya aje wayar. A hanya ya tsaya ya ya duba musu kayayyaki a wani shopping mall na ciye ciye da yasan ameesha da fadeela sunfi so, kowa ya siya masa nasa. Yana tafe yana imagining murnar da zasuyi da bai samu flight ba,yanason yaga kulawa qwarai da soyayyya daga fuskar matarsa,shi yasa ma yaso mata suprise bai gaya mata bai samu flight din ba. Suna gab da karya kwanar shiga gidan haka kawai gabansa yaji ya fara faduwa. Ya lumshe ido yana kiran sunan Allah, me yake faruwa haka dashi?, Ya tambayi kana. A haka suka garasa cikin gidan shi da jibril ne ya dauki ledojin ya buda motar ya wuce kai tsaye sashensa. Harabar gidan ba kowa kasancewar magariba ta kawo kai. Qofar a rufe take, sai ya sanya key dinsa ya bude ya tura ya shiga ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Parlor din babu kowa shuru kakeji,ya danji mamaki ya kamashi,sai yaci gaba da kutsawa zuwa hanyar da zata sadashi da stairs yana kyautata zaton sun haura sama ne ita da fadeela din. Wani mahaukacin bugawa zuciyarsa tayi yaji qwaqwalwarsa na neman tsayawa cak daga aiki. Fadeela ce kwance saman saman sassanyan marbles din dake shinfide a gurin, qafafunta na saman stairs na garshe, kanga kuma daya langabe na a qasa,sassalkar sumarsa ta baje sosai a gasa,yayin da kakkauran jini ya soma bata gurin. Wani irin mummunar rawa jikinsa ya fara yi yanajin kamar numfashinsa zai bar iikinsa sanda va dagata yaga jikinta ya saki gaba daya kamar babu ruhi a tattare da ita. Bakinsa rawa yakeyi yanason kiran sunanta amma ya kasa yanason ya kira ameesha nan ma komai yaqi fitowa daga bakinsa,sai kawai ya saketa ya haura saman da mugun gudu da zummar nemo ameeshan yaji me ya samu diyarsa, saboda komai ya kwance daga kansa tunanin fara zuwa asibiti ma ya fita a kansa,so yake yaji meye ya sameta. A hankali va janye hannunsa daga marigin gofar dakin sakamakon sautin darivar ameesha da yaji cakude da sautin muryar wani namijin "Ya isa haka please mana, kai wai baka gajiya ne?" "Ta yaya zan gaji? bayan har yanzu kawai dandanamin zuma kike a baki, kinqi barina na shiga ainihin inda abin yake?, kina rudani kawai da jikinki, kina barina akan hanya navita fama" "Au, hakanma baiyi maka ba?,an gaya maka taba jikina din ma abune mai saugi? to ko mijin aurena sai randa nayi ra'ayi naji jima ina cikin yanayi matuqa nake sallama masa, kaima ka godewa Allah daka samu wannan damar,gaka yau har cikin dakin mijina,zaka kwana kana murzata" Dariya ya saki "In sha Allahu vau sai na cimma gaci" dan tsaki taja "To watagila idan naii abun yayimin yadda nakeso" "Kina son muyita wahala ne na baki shawara ki kashe auren nan kawai kizo muyi aure ki huta da debar masa dukiya da kadan da kadan, kizo inda zan bude miki bakin lalitata kivita diba har sai kin gaji" dan shuru tayi sannan tace "Ba zaka gane ba, kayi suna a rayuwa ma wani abune,yau ace ni matar dan MT JARMA ne ma wani babban alfarma ne, tabbas kana da kudi irin kudin da nakeso, amma matsalar sunanka baiyi fice kamar nasu ba,sannan kuma inason guy din sosai,yana da kyau ya iya soyayya garshe ne" "Bansan baki da wayo ba sai yau, don ya fini kyau ni mummuna ne a kansa ai ba wani abu bane, kuma da kike maganar so soyayya, da soyayyarsa da dukiya wanne kika fi so?" Ya tambaya seriously "KUDI malam sune fa gare magana" gyalgyalewa yayi da dariya "Yauwa,aini na sani, shi kansa da bashi da komai ba zakiii sonsa ba na san halinki fa....ki bani kanki a yau kawai na miki algawarin million goma yanzun nan zakiji alert idan kin yarda" "Amazing!" Ta fada da matuqar farinciki da zumudi fal muryarta "Na yard…" Kamar an hankadashi da baya haka yaji, bai iya tsaiwa yaji ragowar kalmar daga bakinta ba yaji kamar na daka tsawar sunan "FADEELA!" tsakiyar kwanyarsa. Da wani mugun gudu da sassarfa ya dinga hada matakala bibbiyu uku uku yana sauka,yana isa yasa hannu ya kwashi fadeelan ya fita da gudu. Jibril na hangoshi ya tabbatar babu lafiya, bai bari ya iso ba ya wangle masa gofa,suna shiga ya figi motar da mugun gudu tare da searching na asibitin da zasuje a kansa ba tare da ya tambayi ogan L nasa ba,hankalinsa a mugun tashe sakamakon ganin hawaye saman fuskar mai gidan nasa,mutumin da ya sani sama da shekaru, bai taba ganin karaya ko girgiza saman fuskarsa ba komai girman tashin hankali, lallai abinda ya sameshi ba qarami bane, duk da kowa yasan tsananin qaunar da yakewa fadeela din wanda bata boyuwa. Har sukaje asibitin aka karbeta tare da qogarin dawo da ita cikin hayyacinta ameeshan batasan abinda akeyi ba. Sai da likitoci suka gama komai suka masa bayanin idan ta farka za'a yi mata X-ray saboda tabbatar da lafiyar qwaqwalwarta akan buguwar da tayi,yana dakin gaban gadon fadeela din a zaune sannan uwar ta iso a birkice tana kuka. "Me ya sameta?" Ta jefa masa tambayar da sai da yaji kamar ya Sanya wuga ya yanka maqogaronta banda zuciyar musulunci dake qirjinsa, da sunayen Allah daya dinga kira wadanda suka taimaka waien daidaita shi, banda haka ya tabbatar a yadda qirjinsa yayi nauyi shima iwar haka ba shakka yana kwance saman gado ana jinyarsa "Fita!!" Ya fada a tsawace muryarsa na wani irin sargewa da matsanancin bacin rai,fitar saurin muryarta ba abinda yake tuna masa sai gazantacciyar hirarsu da kwartonta "Kayi haquri don Allah, ba laifi ko sakacina bane,na gama mata wanka na shiryata kenan,na hau sama nayi wanka nima kafin na shirya na fito na sauko naga babu ita,sai jini wajen stairs, masu aiki suke gayamin ka fita da ita" ta fada cikin gunjin kuka,gabanta kuma yana faduwa da matsanancin toro da firgicin zaiyiwu yaga ANAS ko Kuma wani abu da yayi kama da haka Zaki fita daga nan ko sai na wulaqantaki?, maci amana me tozarta sunnar ma'aiki banason na sake ganin fuskarki daga yau a gaban ido na, muddin kika sake kika qara nunan fuskarki sai nasa bindiga na harbeki,ki tafi na sakeki saki daya" ya furta cikin matugar danne zuciyarsa ya furta saki dayan, amma zuciyarsa tafi amanna da ya qarasa guntule igiyar guda dayan da a yanzu tayi saura a tsakaninsu. Sosai ta gigice da jin sakin da ya rattabo matan,ta bude baki cikin rawar murya ta fara roqarsa yace "Ki yiwa kanki suttura ki fita tun ban tattaka ki a nan wajen ba,kije ki auri me kudin da ya fini,ki tara dukiyar da duk kikeson tarawar wannan damuwarki ne, abu daya zan gaya miki,daga yau ki cire a ranki a duniya kin taba haihuwar wata diya fadeela har abada" zata ci gaba da rogonsa yace "Duk kalma daya idan kika qafa furtamin a bakin aurenki take, get out from here idiot!!!" Dole taja qafafunta ta fice, yasa hannu ya lullube fuskarsa zuciyarsa na bashi yanxun haka akwai janaba a jikinta na wancan kwarton nata. Bincike akan fadeela ya kammala,ya kuma tabbatar data samu ciwo cikin qwaqwalwarta wanda shine sila na haduwarta da lalurar EPILEPSY. randa ciwon ya fara motsa mata yayi mugun birkicewar da bai taba yi ba,saboda shi dai bai tana ganin ciwon a gaban idanunsa ba daga wajen wani sai yau akan diyarsa mafi soyuwa a wajensa. Zafafa biyar "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 58 Tun daga ranar bai sake bari ameesha taga fadeela ba, kamar yadda ameeshan bata sake ganin fuskarsa ba sai a hoto ko a media. Duk wanda zai tilasta masa yabar ta ta dinga ganin diyarta ya musu rantsuwar da suka tabbatar babu janyewa,duk da bai fito ya furta ainihin abinda ya rabasu ba,dr jarma kawai ya shaidawa saboda gudun kada yace ya maidata dakinta, ko ya bata diyarta,shi kurna ya gayawa hajiya qarama. Hajiya qaraman murmushi ta saki "Ehe, ka gani ko? ni dama na jima ina ganinta tana shigowa da maza gidan, to amma idan kayi magana yanzu za'a ce ka takurawa surukarka shi yasa na bari, amma kullum ina addu'ar Ubangi ya nuna maka". "Ince ga yadda na rayu a wadan nan shekarun cikin ciwuka masu zafi guda biyu bata baki ne,ciwon fadeela da kuma mummunan ciwon da ameesha ta dasawa zuciyata,da gyar nima na qwaci kaina daga bugawar zuciya saboda mummunan hawan jini daya kamani wanda da gyar na qwaci kaina daga gareshi Allah ya kawomin waraka don ya dubi zuciyata akan ban zalunci kowa ba.tun daga sannan ta cire kowanne aminci a zuciyata daga kan diya mace, nayi mata uzuri duk da yadda bayyanar halinta na aureta mun zauna nayi haquri da ita mun rabu na tausaya mata na dawo da ita,na sanya qafa na ture duk wani aibunta saboda ganin kamar ta canza,ashe lumbu lumbu tayimin take cin dunduniyata,A DUNIYA AKWAI ABINDA YAFI CIN AMANAR WANDA KA AMINCEWA CIWO DA ZAFI!" ya furta wani irin dumi yana fita daga numfashinsa, alamu suna nuna cikin gololuwar bacin rai yake "Babu" yaji sãahar ta fada cikin rawar muryar daya tabbatar kuka takeyi. Hannunsa yakai ya shafi fuskarta,sai ya samu fuskartata jige sharkaf da hawaye,zuciyarsa ra motsa sosai. shi da itan dukkansu an bar musu wani tabo da har su mutu ba zasu daina tunashi ba,ba kuma lallai su fasa jin ciwo idan an taba musu gurin ba,sai ya zameta daga jikinsa cikin nutsuwa,ya sauka daga saman gadon ya kunna fitilar dakin, haske ya gauraye ko ina. Stool ya jawo gaban gadon,ya zauna sosai yana kallonta da idanunsa da suka canza launi zuwa kalar ruwan goro kamar an disa jini a cikinsu. "Tashi" ya furta a tausashe yana miga mata hannunsa. A hankali ta yaye duvet din sannan ta sanya tattausan hannunta saman nasa ya migar da ita ta zauna sosai,sai ya koma shima ya zauna sosai din, yayi folding hannayensa a qirjinsa yana dubanta kai tsaye "Kiyi haquri, na karanta miki diary ba tare da izininki ba" kai ta daga ta kalleshi sai suka hada do,wasu sabbin hawaye suka zarto mata tana jin tausayinsa yana sauka a girjinta,wasu similarities dake cikin labaran su suna dawo mata "Yayi fama da yawa,shi din bayan yaudara da cin amana harda nakasa ta barwa 'yar cikinta 'yar cikinsa?" "I hope you forgiven" kai ta gyada masa a hankali. "Thank you" ya furta yayi shuru na wasu 'yan daqiqu vanason hada abinda zaice da ita, saboda yanzun lokaci ne da zai nema dukkan wata yarda tata du gina kammalalliyar rayuwar da yake buri,iska ya furzar daga bakinsa,sannan ya sake mayar da dubansa a kanta "Duk da Allah yana iya jarabtar bawansa ta duk sigar da yaga dama, amma ina kyautata zaton an zaluncemu ne ni dake, shi vasa Allah ya hada tarenmu da qaddararmu waje daya,ya kuma hukunta ni dake mu zama miji da mata me yiwuwa dama can cikin littafin gaddararmu dani dake din mili da matar ne amma may be idan tun a karon farko ya gaddara mana zama miji da matar, akwai possibility din ba zamu san darajar juna da kimar juna ba, shi yasa ya fara jarabtarmu ta yadda idan zaman namu yazo zamu riqe juna rigo dan gaske ba tare da wasa ba" vakai garshen maganar yana sauke numfashi, idonsa akan kyakkyawar fuskarta "Hajiya qarama" ya furta sunan da shima ya sanyata dagowa "Sai yanzu na fahimci dalilinki nagin aminta da kowa ciki harda NI kina da experience ta wannan fannin wanda ni bani dashi ban taba experiencing haka a rayuwata ba. Mace ta biyu da tayimin cin amanar da har na koma ga mahaliccina ba zan taba mantawa da ita ba" ya fadi fuskarsa tana sake canza launi, alamun baqincikinsa ya sake ninkuwa fiye dana dazu "Da idona,da kaina na kamata tana canzawa fadeela magani,wanda daga qarshe bincike ya nuna magani ne dake da illa ga lafiya da qwaqwalwa, nan asibitin na bayar aka gwadamin ingancinsa" ta girgiza saidai abun ba wani shahararren mamaki ya bata ba,ta riga ta gama duka wadan nan tunanin akan hajiya qaraman, ashe ta lissafa daidai, girgizarta daya yadda mutum mafi kusanci da kai zai ci amanarka har haka? inaga wani bare can wanda baku hada alagar komai dashi ba?. ""'dlan kin shirya cewa na sakeki bayan fadeela ta warke na roqeki kada ki furta min hakan, saboda wallahi wallahi ko sama da qasa zasu hade I can't divorce you" ya fada a raunane. Qasa tayi da idanunta tana jin nauyinsa kadan,kamar ya karanto abinda ta tsara a ranta kenan kafin isowarta qasar. "'SAHR" ya kirayeta da suna da kuma lafazin dake ratsa kowacce jijiya ta jikinta. Fararen idanunta dake cike taf da hawaye ta daga ta kalli tsakiyar nasa idanun "I Am done with people who suck on my life and energy and just leave me in the end like i was stupid to trust and give my all to them,SAHR...i just need one human to love me hard and never leave me alone....zaki iya yimin wannan alfarmar? coz naga abubuwa da yawa tattare dake da suke bani tabbacin na samo gold din da nake nema,you gave me a million reasons to love you,zaki yimin nima alfarma?" Ya fada yana riqe yatsun hannunta hopefully. Iconta ta lumshe kana ta budesu, shin idan tace bata sonsa ma a yanzu bata yiva kanta gundumemiyar garya ba? ya riga ya wuce da dukka tunaninta da muddin tace zata iya rayuwa babu shi tayi qarya matuga da gaske yayi mata wani irin ba zata ya qwace komai data mallaka,ya dandana mata meye ainihin so na gaske meye ainihin hidimar miji wa matarsa bawai hidimar mata ga mijinta ba,ya koya mata yadda zata so kuma a sota, bawai ya koya mata yadda zata soshi bane zallar bashi da intention na maida mata wannan zallar soyayyar kamar yadda adam yay ba "Am ready to be your paradise" ta fadi da mafi dadin muryarta me taushi, sautin da ya ratsa masa kunne,ya kuma kashe kowanne fargaba bacin rai da damuwarsa dukka a lokaci guda,ya fidda wani kyakkyawan murmushi daga saman fuskarsa irin wanda bata taba gani ba "Kice i love you Muhammad toufeeg, that's all I want to hear daga wannan dan mitsitsin bakin me tsiwa" ya furta yana kallon lips dinta da suka fara motsa shi yana masifar sonsu,suna daya daga cikin abubuwan dake motsashi a kanta,shi kadai yasan taushi da zaginsu. Kunya ta kamata sai ta kisa fuskarta kan hannunsa dake rige da nata hannun "Pleaaaaaaaassssseee.…say it mana" ya fadi mata a mugun shagwabe har sai dataji kamar zata shide. "Say it mana" ya sake fada har yana zamowa daga saman stool din, sai gashi durqushe saman gwiwoyinsa a gabanta "Its what I want to hear SAHR karki haramta min,na rogeki ki fadi abinda kikeji a kaina tell me you love me.. only true love can heal all the wounds of the past" Kasa riqe kanta da zuciyarta tayi, idanunta a lumshe ta motsa bakinta "You are the missing link of my heart, you are the best thing that ever happened to me I LOVE YOU AND I CAN'T LIVE WITHOUT YOU" "Ya salam!, harda gari" Ya furta muryarsa na rawa,ya riqe hannunta da kyau yana dan jijigashi with so excitement "Can you say that again?, I want to relieve the feeling" idanunta ta bude tarrr wanna karon ta zube masa,sai kuma ta janye su a nutse tana jin nauyinsa. Da sauri ya kamo fuskartata ya dawo da ita saitinsa "Look at me once again with those bold beautiful eyes and say it please SAHR" juya qwayar idon tayi cikin nasa idon a rarrabe kamar me koyon magana ta sake maimaitawa din. Jikinsa duka ya gama amsawa, sai ya mige cak vana garasawa saman gadon vana fadin "How i wish i could listen to those words again and again,you deserved a kiss" bai sake bata second chance ba ya shiga aike mata da zazzafan sago,lips din nan dake tafiya dashi da kuma albarkatun jikinta bai daga musu gafa ko sau daya ba. A karon farko itama ta fara maida masa da martani, abinda ya taka muhimmiyar gudunmawa wajen haukatasu gaba daya shi da ita. Sanda taji tana gogarin kaiwa wani waje saita riqd hannunsa numfashinta yana rarrabewa,da rinannun idanunsa ya kafeta shima nasa numfashin yana tsere da kyau "You are halal for me jininki bai haramta min ke ba duk da ma dai fake jini ne,naga komai" ya fada yana matsar da hannunta gefe ya kuma ci gaba da abinda yakeyi,bakinta ya mutu murus ba abinda ya rage mata illa bada kai bori ya hau. "_HAJIYA QARAMA_* Wani mawuyacin dare ne a gareta wanda kaf tsahonsa bata samu bacci ba. Tana kallon nadeeya ta shirya ta kwanta abinta, tunda tayi mata sannu sau daya bata gara waiwayarta ba,duk da abun yadan bata mamaki saboda duk sanda take lalura tana tsaiwa a kanta fiye da abinda haseena zata yi mata, amma yau ta nuna halin ko in kula a kanta. Ba wannan bane damuwarta, damuwarta a yanzun shine kan yadda komai yake lalace mata, anya mutuwar bokanta bata da alaqa da lalacewar aikinta? tunda hatta da gawarta da akayi musu ayyukan tare a wancan lokacin,duk da ita tana zuwa sabunta aikin amma itama yanzun hakan ruwa yanata qarewa dan kada ne. Qafe hudu da rabi na asuba sago ya shigo wayarta,a mugun razane ta mige hannunta na rawa wayar na neman faduwa a hannun nata, maimaita kiran "Na shiga uku, innalillahi, na shiga uku" shine abinda ya tayar da nadeeya daga baccinta "Me ya faru?" Ta tambaya a rude saboda ganin yanayin da hajiya qaraman ta shiga. Bata iya amsa mata ba sai hawaye data fara yi,abinda nadeeyan bata taba gani ba, don haka ta mige ta bude qofar ta tafi taso Abbanta. Maji na zaune saman abun sallah har ya tashi ya bude mata gofar tayi masa bayani suka rankaya suka fice. "Lafiyarki fauziyya?" Dr jarma ya tambayeta "Yaava,plaza ta gaba daya wuta ta cinye ta" ta fada tana sakin kuka me ciwon zuciya. Guri ya samu ya zauna yana maimaita innalillahi wa inna ilaihi raji'un shima. Dukka shagunanta ne a ciki da ta zuba kaya iri daban daban ake saida mata,wadanda ta bada haya basufi kaso daya cikin hudu ba. Da ayar ya samu ya lallabata ta tsaida kukan "'Kada ki damu, za'a san abinda za'a yi in sha Allah" wannan magana tasa ta dadada mata qwarai, tasan zata rage asara sosal daga wajensa,shi yasa ma bata gaya masa babu kaya masu yawa a dukka shagunan ba,don an kammala ciniki da lissafin shekara ta maqare duk wata dukiya tata a account, tana shirin zana tayi kasafi tayo order na dukka kayayyakin shagon nata a sake sabon zubi da lissafi sai kuma ga wannan tafiyar ta Germany ta taso mata. Awa biyar tsakani, da safe likita yana dubata dr jarma na gefe suna magana da nadeeya kira ya shigo mata wayarta. Da daga wayar da fasa kukanta hadi da fusge hannunta duka cikin minti guda tana sake fasa kukan "Daya plaza din tawa data ragemin yaaya wadda tafi kowacce girma,itama ta gone tun daga sama har casanta yaaya‚na shiga uku,wanne irin ibtila'i ne haka?" Dr jarma yadan rufe idonsa kadan ya bude yana kiran sunan Allah, kansa yana sara masa da wani irin ciwo,gaba daya jiya bai samu isashen bacci ba wajen rarrashin maji data tubure masa kamar bata taba gainsa ba a rayuwa yanzun kuma ga matsalolin fauziyya daya na bin daya da wanne zaiji? "Kiyi haquri ki kwantar da hankalinki,kinga yanzun nan likita ke maganar jininki bai sauka ba duk da magungunan da suka baki,zaki iya samun matsala kowacce lokaci muddin kikaci gaba da wanann abun" "Ya kamata na koma gida yaaya na bincika meke faruwa, manyan plazas har biyu yau babu ko daya?" "Karkiyi sabo fauziyya,Allah yana iya jarabtar bawa a duk lokacin da yaga dama bawai sai da dalili ba". Tsam nadeeya da haka kawai takejin takaicin yadda take sharban kuka kamar yarinya qarama ta miqe tana fita qasan ranta tana jan qaramin tsaki. Zafafabiyar "HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 59 *****Tunda gari ya waye ta fara maganar tafiyarsu asibiti,yana cikin duvet yana wani almurin bacci da sãahar din tasan na neman magana ne kawai, don sau uku tana kamashi yana binta da kallo tana kai kawon nata shirin tafiyar. Koda ta kammala gabansa ta iso, idanunta a qasa a kuma shagwabe tana lanqwasa yatsun hannunta "Please na gama fa,kai nake jira" kallon qasan ido yakeyi mata zakayi zaton baccin yakeyi har yanzu, tayi masifar kyau,shigar da tayi ta karbeta,inda yana da hali wani abu shapeless zai samu ya lullubeta ta yadda babu me iya genta har balle yaga tudun qirjinta ko na mazaunanta "A bani coffee to" ya fada muryarsa can gasa "Okay" ta fadi da hanzari tana juyawa. Mini coffee maker ta kunna ta hada masa irin wanda yakeso har two cups, duk abinda takeyi din yana kallonta yana dariya qasan ransa, tare da tuno abinda ta jiyar dashi daren jiya wanda shi kam bai taba sanin akwai wannan abun ba. Gabansa ta iso ta tsaya da mini tray tana cewa "Ga coffee din" dan Jim yayi kamar bai jita ba,sai kuma ya miqe yana yaye duvet din,ya zauna sosai saman gadon ya miga mata hannu yana kallonta. Tray din duka ta miga masa, hannu yasa ya karba,da hanzari ya ajjiye shi saman bedside table dai dai sanda ta juya ya saka hannunsa ya kamota,fincikota yayi a tausashe sai gata gaba daya cikin jikinsa "Me yasa baki da wayo kullum,ni da nace ki bani hot coffee saiki bani cold coffee?" Ya fada yana riqe da fuskarta yana kallon cikin idanunta. Zare masa manyan fararen idanunta tayi tana cewa "Sai dava tafasa fa sosai,ka duba ka gani" It was not hotter than you,and ba wani hot coffee da ya fiki,i like hot shower,a regular shower but with me in it" "Don Allah,na yiwa fadeela alqawari zamu iso da wuri" Tsayawa yayi da abinda yake shirin yi, yana dubanta da jirkitattun idanunsa "'Me yasa zaki hukunci bayan kinsan idan baban fadeela yana guri rayuwarki da lokacinki duka nasa ne?" A yadda ta hangi fitina fal idanunsa tasan muddin bata lallabashi ba tsaf zai iya soke fitar ma "Sorry i make a mistake but bazan sake ba" ta fada tana hada hannuwanta guri daya tana dan boye murmushin. fuskarta saboda yadda ta fahimci tayi masifar yi masa yankan hanzari. Kansa yadan juyar gefe guda "Na fahimci idan akan fadeela ne zaki iya komai shine kikemin wannan 'var murvar don kawai a cuceni ko? yayi….. na yarda,but i need a kiss please" "Tashin hankali" ta fadi qasa qasa,tasan kiss a gurinsa kamar wani mabudi ne na bude shi "Eheen, baki shirya fita asibiti ba?" Ya tambayeta yana taba lips nashi da yatsansa. Yana gama fadi ta hade bakunansu ta fara masa yadda yakeso din, saidai daga garshe shi ya karba ragamar. Yadda ta zata din kuwa fara wuce gona da iri yayi, ta kama hannunsa ta riqe tsam don ba damar yin magana da baki, ya fahimci me takeson fada ya daga kansa yana dubanta "Am sorry for being too forward but your lips make me wonder what the rest of you would taste like da safen nan". Bai bata dama ba ya warware shirinta tsaf yayi yadda yadda ransa yakeso . Bayan ya kammala ya sauka ya sauka ya barta yana mata dariyar cewar da takeyi "Ka karya algawari " cikin kukan kissa da shagwaba "Eh ai dama indai nine ta wannan fannin na dade da zama rules breaker, but duk da haka am sorry my MOONBEAM" sai yayi kissing nata a tausashe ya wuce toilet. Har ya fito tana kwance, ya zaci zai samu ta shiga daya daya toilet din dake parlor ta shirya, qarasowa yayi gabanta fuskarta na rufe cikin pillow "Hello ko kina son gari ne?" Hararar wasa ta jefa masa sannan ta sake qunshe kanta,can qasa tace "Marata ce takemin ciwo* "Ya salam* ya fada vana tayar da ita. Da gasken take don sosai ta rigeshi tana cije lips "Let me help you kiyi wankan mu wuce asibitin sai kiga likita ko?". Duk yadda taso dojewa bai fita ya barta ba,sai da tayi wankan ta fito ta shirya duka a gabansa,ga kunya ga ciwo,shi kuwa ya murje idanunsa,saima wani mayen kallo da yake bin ko ina na jikinta dashi har ta gama shiryawa "Ko na sake warming maka coffee din,bakasha ba" kai ya girgiza yana murmushi "'Nooo,I got the better ai sukutun da guda daga wajenki” kunyarsa ta sakata kau da kai, bayajin kunyat baro zance baro baro, sai sun fita kuma waje kaga ya kame kamar ba shine me b'arin zancan nan ba. Sun samu an gama yiwa fadeela komai daya Kamata, tasha magani an gyara mata jikinta,sai zaman jiransu. Sanda suka shigo kamar zata koma cikinsu,sosai farinciki ya cikata,ga abby dinta ga aunty N,duk inda ta waiwaya sune. Basu wuce awa dava da isowa ba afifa da sajjad suka iso. Sanda suka shigo sahar na saman gadon daga gefan fadeela tana bata fruit yayin da ogan yake zaune saman kujera a gaban gadon hannunsa goye a qirji ya tsaresu da kallo. Migewa yayi ya bawa sajad hannu sukayi musabaha,afifa ta matsa kusa dasu bayan sun gaisa da toufeeq tana duba jikin fadeelan,shima sajjad din ya dubata,sai suka juya suka fice suna magana a tsakaninsu. Ba jimawa suka dawo,a lokacin ta gama batan tana zaune daga gefanta tana tayata karanta wasu abubuwa da likitan dake kula da sashen magana na qwaqwalwa ya bata. A tausashe yake jifanta da wani irin kallo har ya qaraso daf dasu. Afifa ta kula,sai taja jikinta baya tana boye dariya qasan ranta. "Moonbeam" ya furta gasa gasa yana dubanta. Kunya ta kamata jin ya maimaita sunan da ya sanya matan a gabansu afifa, ta daga idonta a hankali ta dubeshi, hakan yakeso sai ya marairaice mata "Ki barwa su sajjad din ita kizo muje kiga likitan" kai ta jinjina, ta sakarwa fadeela dan qaramin littafin tana zamowa daga saman gadon. Kafin ta qaraso ya sanya hannu ya saita mata takalmanta, kunya da nauyinsu. sajjad ta sake kamata,ta zira takalman a nutse tana dawurwura na abinda zatace da afifa "A dawo lafiya" kawai taji afifan tace sai bata ce komai ba tayi gaba kamar yadda toufeeq ya bugata. "Dan tsaya" yace da ita bayan sun fito, ta tsaya cak ya qaraso kusa da ita, sai ya lalubi hannunta ya saka a nasa "Yauwa to muna iya tafiya,naga alaman turawannan suma mayun mata ne" ya fadi yana wani tsare gida,abinda ya sanya qaramin murmushi ya kubce mata,sai taji dadi gasan ranta, karon farko kenan da taga haka daga wajen mijinta. Abinda adam bai taba damuwa yayi ba kenan, hasalima shi duk inda zasu shiga qoqari yakeyi aga kyanta,yana alfahari sosai da kyan da take dashi. Ko cikin office din yana tsaye daga bayan kujerarta kamar wani bodyguard ita kuma tana a zaune. Qwararriyar gynecologist ce da take a wani department daban a asibitin cikakkiyar musulma ce, abinda ya qara masa nutsuwa kenan,säahar tayi mata bayani dalla dalla da harshen turanci "Ina zargin wani abu" likitar mai yawan fara'a da kirki ta fada bayan ta gama yi mata tambayoyi tare da duba report nata. Scanning ta fara dayi mata cikin nutsuwa, kai kawai take gyadawa murmushi na fita a fuskarta,sai ta sanya hannu ta kirayi toufeeq tana tsaida na'urar kan wasu abubuwa guda biyu masu suffar wake ko gananun ayaba "Kalli babies dinka" ta fada tana masa nuni da allon computer din da hannu. Ido sosai ya zubawa abun da take nuna masan,zuciyarsa na dan bugawa cikin wani irin zumudi da rikicewar tunani "Ban fahimta ba likita" ya amsa mata shima, sai tayi murmushi tana sauke na'urar scanning din daga saman marar säahar "Yanzu zanyi maka bayani,sauko madam" wannan karon kasa tsaiwa vayi va samu kujerar dake facing din säahar din ya zauna vana bawa likitan dukka attention dinsa "Alamu sun nuna babies uku ne a mahaifarta,guda daya ne ye fita, yanzun haka akwai sauran guda biyu" daga shi har säahar din ji sukayi kamar jinin jikinsu ya daskare,ji yayi kaman kunnuwansa basu ji masa dai dai ba "Karkiyimin irin wannan wasan likita, saboda bazan iya jurewa ba kic wasa ne daga baya" ya fada yana jin duniyarsa na kewayawa dash cikin wani madaukakin farinciki "Ba wasa bane sir,shi yasa na kiraka na nuna maka su" kasa jurewa yayi saboda farincikin da yayi masa yawa,sai yaji kamar zuciyarsa ba zata iya dauka ba,don haka ya zamo saman gwiwoyinsa ya kamo hannun sãahar ya rige da kyau yana dorashi saman qirjinsa, idanunsa a lumshe yana ambatar sunayen Allah. Itama kasa rige kanta tayiyadda hannunta yakejin tsananin bugun zuciyarsa sai taji kamar a tafin hannunta zuciyar tasa take "Wannan babban sakamakon ba zata da ubangiji yayi mana,duk da mudin ba wasu bayi bane masu tsananin biyayya ba a gareshi, bansan meye zanyi da zai sake sanyawa ubangijr ya sake yarda dani ya kuma aminta dani ba ina da bugatar irin wannan falalar daga ubangiji na a duk kowacce shekara idan zai bani, Alhamdulillahil lazi lam yattakiz walada walam yakun lahu sharikun fil mulki walam yakun lahu waliyyum minazzulli wa kabbirhu takhbira" ya fada vana kifa hannun nasa a tafin hannunta idanunsa na ciccikowa da gwallar da bayaso ta zubo din,wannan hawayen yafison ya zubdasu a gaban ubangijinsa don nuna tsantsar godiya a gareshi. Sai da dr marhooma tayi gyaran murya sannan ya tuna tana a wajen,don yayi nisa wajen lallashin säahar da nata idanun suka kasa rige nasu ruwan hawayen "Akwai bayanin da ya dace nayi muku" ta fadi tana gyara zamanta "Amma likita,dama mata irina suna iya samun cikij 'yan uku?" Tambayar da säahar taketa juyawa a ranta kenan ta kuma kasa rigeta. Murmushi dr marhooma tayi "Kyautar Allah ce yana iya baiwa duk wanda yaso,musamman idan a danginki akwai history na haifan twins ko triple din, sannan yawanci matan da suka doshi shekara talatin ko suka gota sunfi yiwuwar samun haife haifen 'yan biyu ko uku ko hudu ma,duk da masu qasa da hakan ma suna samu musamman wadanda ya zama musu kamar gado, lokacin da mace te saki qwai wato ovulation idan aka dace da gwan namiji ya hadu da nata @wan, maimakon ta gyangyashe qwai guda daya sai ta gyangyashe biyu uku ko hudu ko sama da haka,wani kuma yana rabuwa ne yayin gangarawa cikin ainihin qwaryar mahaifa sai a samu irin hakan, hikimar Allah ce duka yanayin yadda yaso a sanda yaso" dukkansu sun gamsu tsoron tare da tabbatar da afkuwar ikonsa suka shigesu, yayi ajiyarsa a muhalli daya,ya kuma fidda wanda bashi da rabon taka duniya,ya tsare sauran wadanda yaso suci gaba da wanzuwa "Kamar yadda wancan likitan ya fada muku, tabbas mahaifarta tana da rauni, saboda haka zamuyi mata daurin mahaifa, sannan zamu bata bead rest wanda shi ko a gida zata iya yin abinta, saidai tana bugatar yallabai adan daga mata qafa don Allah daga yawan bugatu" ta gada tana sauke dubanta akan TOUFEEQ. Murmushi kawai ya saki yana debe dubansa ya maida kan sahar, suka hada idanu sai ya kashe mata ido daya, yayi qasa sosai da muryarsa cikin harshen hausa yadda dr marhooma ba zataji ba yace "Raguwa ce ke wallah, dama neman mafaka kike,to ai dai ba'a hanani shan dumin babies dina ba ko?" Ido ta lumshe tana sakar masa murmushi, sai yaja ajiyar zuciya "Wannan lumshe idon kawai na tsokanan magana ne saboda kinga bazan iya fanshewa ba?" Siriryar dariya ce ta kubce mata,sai tasa hannu kawai ta rufe bakinta tana kwantar da kanta gefe guda. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 60 "'Excuse me" Dr marhooma ta fada tana tashi hadi da fita daga office din. Da gyar ya zare idonsa daga kanta kamar zata bace masa idan yabar kallonta ya fidda wayarsa yana jin qirjinsa har yanzu cike da farinciki,ya rasa dawa zai fara wanna maganar, idan ya kira sajjad yasan tabbas! Tsiya zaita masa, infact ma zai addabeshi ne ya buwayeshi, qila har sai dr yayi musu tsakani ma. Maji dinsa ce ta fara fado masa a rai, fuskarsa na fidda murmushi ya soma neman layinta yana qiyasta irin farincikin da labari zai bawa zuciyarta. Tun da safe yake aikin lallashinta har sukayi breakfast sukayi shirin wucewa asibiti shi da ita,sai nan nan yakeyi da ita da al'amuranta yayin da ita kuma take basarwa a shekarun ita kadai tasan yadda ta rayu, cikin baqinciki da daci da qunar rai, inda Allah ya taqaita wahalarta ita din me yawan addu'a ce, bata wasa sam da addu' a,amma abune mai matugar ciwo ka bawa mutum rayuwarka ka zauna dashi fisabilillahi amma ya jefeka da miyagun kalmomi,yasa hannu ya tankwabe dukkan wata kyautatawa taka ya kuma yi maka kallon maciyin amana. Ko yanzun data gama saka komai cikin handbag dinta caraf yayi ya kama hannun jakar ya riqe, ta waiwaya ta kalleshi ya marairaice mata gaba daya,sai taga ya koma mata mahmud dinta zam a zamanin quruciya da samartaka "A saussautamin mana shifa ta,ko don idanun yaran nan‚banason su fahimci abinda yake faruwa" "Sakarmin jakata,meye ya rage dama wanda basu san ka viwa uwarsu ba" "Bakina bazai gaji da neman afuwa ba" ta fuskanci ba sakar mata jakar zaiyi ba,ita sai ta sakar masa tayo gaba ya biyota a baya. Dakin su nadeeya suka wuce don duba hajiya garama. Nadeeya na fesa turarenta itama ta gama shirinta sukayi sallama suka shigo. Tana zaune saman gado, idanu da kuma fuskarta dukka sun wani qoje,dare daya Allah ya saukar mata da wani irin rudani da razani daya sake firgita nutsuwarta ya kuma hana jininta saukowa kamar yadda likitan yakeso. Da sauri ta kauda kanta daga kallon maji, cikin ranta tana jin yadda ta muzanta, majin kuma na mata wani kwarjini da cika mata ido. Tayi kyau sosai cikin wata doguwar riga data dorawa madaidaicin hijabi, fuskarta da jikinta suna nuna nutsuwa kwanciyar hankali da kuma cikakkiyar kamalarta,abubuwan da ta tabbatar itadin ta rasa dukkansu. Cikakkiyar sallama majin tayi wadda ta sanyawa hajiya garama faduwar gaba, bata ma iya amsawa ba sai nadeeya ce ta amsa, ranta na mata wani irin dadi. Ashe dama haka tarayyar iyaye biyu yake? a duk sanda taga maji da Dr a tare, sai taji kamar an sabunta mata duniyarta,ita ta yiwa majin da Dr gurin zama,sanann ta koma gefe tana hada tarkacenta cikin jaka. Da dr suka fara gaisawa, gaba daya ta zama wani iri, ciwo kam ciwo yana mintsinin zuciyarta,iya kallon maji da Dr kawaj a mazaunin miji da mata a karo na biyu kadai ya usheta masifa da tashin hankali. "Sannu da jiki" maji tace da ita a taqaice tana maida hankalykan wayarta da kira ya shigo. Qasa qasa hajiya garama din ta amsa, hankalinta nakan maji amma idanunta akan Dr suke da yake tambayarta tasha magani da abinci. Murmushi ya subuce mata ganin toufeeq ne yake Kira "Assalamualaikum, Muhammad" maji ta fada tana murmushi. Kiran sunan kawai ya sanya hajiya qarama faduwar gaba,ya kuma gara sanyata maida hankalinta kan maji cike da mamakin toufeeq ne yake kira? ita ta mance ma lokaci na garshe rabon da yayi kiranta "Lafiya alhamdulillah....too.... Ma sha Allah,ma sha Allah,gamu nan a hanya muma zamu iso" saita katse wavar bakinta na furta "Alhamdulillah zahiran wa bad'inan" Sai ta sauke wayar daga kunnenta tana murmushi sannan kuma ta mige "Zan jiraka cikin taxi, marasa lafiyan sun garu" daga kai Dr jarma yayi ya kalleta "Waye kuma ba lafiya?" Murmushi ta kuma saki "Surukarka zasu yiwa daurin mahaifa, Allah dai yayi cikin me zama ne, ba duka bane suka fita" muraran farincikin Dr iarma ya kasa boyuwa "'Ma sha Allah,nima yanzu zan fito" yace da mail "'Allah ya kiyaye gaba fauziyya" maji ta fada tana ficewa abinta. Tsabar bagincikin da yake sussukar zuciyarta kasa cewa komai tavi. Ga mamakinta shima dr jarma din migewa yayi "Zamuje wuce asibitin, daga nan akwai inda nakeso muje ni da maji din, inaga nadeeya ke ki zauna da ita kada a barta ita kadai,idan akwai wani damuwa saiki kirani" dr jarma ya fada. "Don Allah abba zan biku, zaman hotel babu dadi wallahi" nadeeya ta fadi kamar zata saki kuka "Jeki nima bana bugatar zaman naki" hajiya garama ta fada a qufule zuciyarta kamar zata fado gasa, cikin kwana biyu kacal ta fahimci yarinyar gaba daya ta canza itama, kamar bata Santa ba,duk wata damuwa da kulawa da take bata koda tana zazzabine yanzu babu shi "'Ni nace ki zauna nadeeya,ya za'a bar mara lafiya shi kadal?" "Taje yaya, kaima ka tafi bare ita" ta fadi tana jin kamar zata saki kuka Tuni nadeeya tayi gaba abinta, don bata tsaya bama bare ta gane yadda suka qare da abban nata. Kasa zama guri daya hajiya qarama tayi, takai ta kawo ita kadai yau itace a wulaqance haka?,cikin dakin hotel bayan tana fama da ciwo? yau itace ba wanda yake daukan maganarta da muhimmanci bare ace za'a yi amfani da ita? anya batayi sake ba? zaman me ma takeyi ne wai a Germany? bayan matsaloli na shirin rufto mata su murqushe dukkanin nasararta?. Ba'a jima ba suka gama mata daurin mahaifar aka dawo da ita daki, saidai sun roqi alfarma an dawo da ita department din su fadeela kusa da dakin fadeelan saboda abubuwa sufi yi musu sauqi. Yana riqe da hannunta tsam kamar za'a qwace masa ita,maji da Dr suka turo gofar suka shigo dakin. Qoqarin yunqurawa takeyi ta tashi maji tace "Yi kwanciyar ki d'iyata" ta iso bakin gadon. Sai a sannan toufeeq ya zame hannun nasa daga nata,ya matsa baya yana yiwa Dr jarma barka da isowa, qasan ranshi yana mamakin yadda suketa zirga zirga shi da maji din, gefe guda kuma ko yaushe ya gansu tare sai yaji zuciyarsa ta zurafafa da addu'ar dawowarsu da dinkewarsu a mazaunin ma' aurata kamar kowanne iyaye. A kunvace ta gaida maji, majin ta hamsa mata, sannan gasa qasa take mata tambayoyin da suka gara saka säahar cikin jin nauyinta. Duban toufeeq maji tayi "Yaushe zasu sallameta?" "Zuwa anjima suka ce,zatayi bed rest ne kawai koda a gida ne" "Yavi kyau, zan wuce da ita gurina" maji ta fada tana ciro wayarta don ta sanya a sake samar musu wani dakin wannan din kamar wata dama ce a wajenta da wajen sãahar dinma gaba daya,zata sake waana Dr jarma da kyau,itama kuma sãahar din zata samu cikakken hutu,zasu kuma sake fahimtar juna tsakaninsu ta sake samun damar da zata shirya kyakkyawar alaqa tsakaninta da toufeeq din. Tunda yaji maji ta fadi haka ya kasa sukuni,yayita goqarin kallon qwayar idanun säahar din don yayi mata alama amma bata ko kalleshi ba. Cikin jikinta tasan za'a rina hakan indai toufeeq dinne da yake jin kansa kamar tuzurun da yayi aure kwanan nan, to amma ita kanta tana da bugatar hutun ko don su tsira da abinda take dauke dashi din karo na uku a rayuwarta shi kuma karo na biyu. Har akayi la'asar bai samu wanna damar ba, duka ya shiga damuwa walwalarsa ta ragu,sajjad na ankare dashi,yaji komai daga bakin afifa,ba abinda ya rage masa illa dariyar da yaketa boyewa,har suka idar da sallah,ya gama azkar dinsa, haqurinsa ha gaza,ya cire wayarsa ya tura mata gajeran tex "please ki gayawa maji fa, bazan iya ba,Allah bazan jure ba" Wayar na hannun afifa,sun gama waya kenan da maama data duba jikin fadeela da na sãahar din gaba daya, Murmushi afifa ta saki tana miga mata wayar. Sai data kalli fuskar afifa din sannan ta karba wayar ta karanta saqon,tana kaiwa qarshe ta daga kanta ta kalli afifan suka hada ido, saita watsa mata harara, dariya ce sosai ta qwacewa afifa "Meye zaki nade tabarmar kunya da hauka a kaina? munafukai,kun gama gulmar baku son juna Allah ya toni asirinku shine zaku wani dinga dojewa,ni kinga tafiyata gwara naje naji dumin hayatee daga nan na duba fadeela ko ta tashi" ta fadi tana rolling mayafinta doguwar rigarta a kanta. Fitar afifa ya maida dakin shuru, maji ta shiga wajen fadeela,Dr ya fita tun dazun, nadeeya kuma na saman abun sallah tana sallah. Gyara zaman wayar tayi a hannunta tana tunanin amsar da zata bashi, ita kanta tasan akwai rikici, har ta shiga gurin tura saqo aka tura gofar dakin aka shigo. Muhammad toufeeq ne, hannunsa daya cikin aljihun wandon lallausan yadinsa, idanunsa carrr a kanta,yayi wani sanyi da laushi da yasa zuciyar saahar cika da mamaki,kawai don maji tace zata wuce da ita shi ya hautsina shi haka? wanne irin so ne haka?. A nutse ya iso gaban gadon, kai tsaye ya yiwa kansa guri a gefan gadon shima kusa da ita, kafadunsu har suna gogar juna. Da sauri ta dubeshi tana masa nuni da nadeeya dake zaman tahiya zata sallame, sai ya daga mata gira murya can gasa "And so what?" Ya fadi gaba gadi abinsa, hannunta ya lalubo ya rige cikin nasa "Maji so take kawai ta horani yadda take hora Abba, dazu sailad vake gavamin va maida aurensu.lalurar fadeela yasa bamu sani ba" wani lafiyayyen murmushi dake qarawa fuskarta kyau ne ya kubce mata,bayan samun nasara a alkin fadeela wanzuwar cikin jikinta wannan shine labari na uku da yayi masifar sanya farinciki a zuciyarta. Kaman zaice wani abu sai ya waiwaya sashen da nadeeya ke zaune "Tashi ki bawa mutane guri munafuka" ya fadi vana dan fidda fararen idanunsa waje. Batasan ya akayi ya fahimci ta sallame sallarta ba, sosai taso jin gulma shi yasa tayi kaman zaman tahiya takeyi, tanason taga wanna salon boyayyar soyayyar tanason taga salon soyayyar yayanta Classy anty N da muskilin yayanta yaa moha, ta tabbatar wanna kalar soyayyar zata kasance ta musamman,sai gashi ya baro jirginta. Hakanan ta miqe tana ninke abun sallar tana satar kallonsu har ta fita a dakin. Dariya ce sosai ta kama nadeeyan,afifa dake fitowa daga dakin fadeela sukayi kacibus "Lafiya sister nadeeya?" "Anty afifa,wadancan mutanen,wai dama suna so suke kaiwa kasuwa?" Baki afifa ta tabe tana dariya "Ko ba bestie ba, gulmammu, kowa ciwon dake ransa kadai ya sanyashi jin babu wani da zai sake burgeshi, basusan ita zuciya ba'a ci mata alwashi ba" "Zo kiga don Allah" nadeeya ta fada tana yafito afifa. Hannuwanta afifa ya daga tana dariya "Wallahi bazan iya leqensu ba karna ganowa kaina abinda yafi qarfina" dariya suka sanya su duka suka wuce dakin fadeela tunda zaman dakin säahar din yafi garfinsu. Zafafabiyar "HUGUMA* • TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 61 Shuru ne ya ratsa dakin, nauyi kallon da yake mata ya yiwa idanu da gangar jikinta, saita zame idanunta zata sunkuyar da kanta qasa. "Mom twins" ya furta a hankali yana jin farinciki yana ratsashi. Qaramin murmushi ta saki a kunyace tana maida kanta gefe,sai yasa hannu ya juyo fuskar tata "Ki gayawa maji ba zaki ba.......am telling you akwai matsala, komai zai iya faruwa kika bita" fararen idanunta ta daga ta kalleshi tana dan bata fuska "Maji din? i can't* sosal ya sake zubawa fuskarta ido,sai tadan ja da baya kadan tana sake dubansa "What do you want from me?" Ta samu kanta da furtawa ta yadda labbanta kawar ya iya kalla ya fahimci me tace "I want to wakeup to you every morning and fall asleep to you every night ban shirya bin tsarin maji ba,please help me, tell her zaki iya warkewa koda muna tare" ya qarashe maganar yana sake matso da fuskokinsu kusa dana juna,har tana iya jin fitar numfashinsa sosai. Idanunta ta lumshe tana jan ajiyar zuciya "Bazan iya gaya mata ba" ta fada a shagwabe, har sai da tsigar jikinsa ta zuba "'Zan gaya mata ni, zance mata ni dake duka bama so" I "No please" "'Whay?" Ya tambayeta still idanunsa suna cikin nata suna wani irin narkewa da gaunarta "Inajin kunya" "Ni kuma bana ji" wani garamin kukan shagwaba da batasan daga ina yazo ba ta shiga sauke masa, take ta soma kunnashi,jikinsa duka ya amsa. Hannu yasa ya jawota ta fada jikinsa, sautin qaramin shagwabben kukan nata yana sauka a wuyansa yana ratsa tattausan gashin fuskarsa yana taba kunnensa kadan kadan "If you kiss my neck, am not responsible for what happens next" yayi maganar kamar yana rada mata a kunne. Da sauri ta janye fuskarta daga gareshi, amma sai yayi caraf ya rigota yana ritsata da narkakken kallonsa "| crave you emotionally and physically do you even realize how amazing you are to me?" Kasa bashi amsa tayi, saboda kalamansa suna mugun kashe mata jiki tare da dasa wata sassanyar soyayyarsa mai matugar garfi a jininta "Am sorry" ya sake cewa,yadda yayi maganar ya sakata daga kai ta kalleshi "Sorry for what?" "For loving you too much" dukka hannayenta ta bude ta zagaye bayansa dasu,ta kuma kwantar da kanta a girjinta, sosai take iya jin bugun zuciyarsa cikin kunnuwanta,da muryarta mai laushi da wani irin nutsuwa tace mishi "Kalamanka suna da zagi kamar zuma,All very sweet,i'll never get enough of you,i want to spend the rest of our lives together, baka qetare iyaka bai feel the same way and i can prove it to you in sha Allah" ta qarashe maganar tana cusa kanta a tsakiyar qirjinsa saboda nauvinsa da takeji. Kamar me jin bacci haka ya dinga lumshe ido saboda zagin da kalamanta sukayi masa "You're the only person who makes me smile constantly" ya furta yana qoqarin daga fuskar ta daga qirjinsa,a sannan yaji ba abinda yake buqata irin ya dandana lips din da suka furta masa wadan nan kalaman masu zaqi "Your lips on mine tell me better than your words" ta fahimci kiss yana daya daga cikin weakness dinsa,kuma babu abinda zai hana maji tafiya da ita,don haka ta bashi cikakken hadin kai tare da maida masa martani me kyau. Basusan me vake faruwa sai muryar maji da sukaji tana fadin "Subhanallahi" shi ya fara zare fuskarsa daga tata tare da rigeta da kyau don kada ta firgita. Basuga maji din ba sai gofar data maida ta rufe da sauri tare suka dauke idonsu daga kan qofar suka mayar fuskokin juna. Tuni kunya ta lullube sãahar,ta kebe baki zata masa complain, ya dora yatsansa saman lips dinsa da sukayi jaa "Shshshsh" vace da ita saita maida maganar da tayi niyyar yi din, abinda ya bashi daman gyara mata gashinta da ya hargitse. Yanayi yana kallon cute face dinta,ba magana a tsakaninsu sai bugun zukatansu kawai, kowa na tuna tarayyarsa tare da dan uwansa. Yana gyara mata yafen mayafinta nadeeya ta tura gofar ta shigo,ya juya ya watsa mata wani kallo saita koma ta lafe tana cewa "Maji ce ta aikoni,wai anty N ta fito" "Bacemin daga gun" ya fada adan zafafe, sai ta juya ta fice tana gunshe dariya. Tunda taga maji ta fito tana maimaita salati tasan tayi gamo ne. Ba jimawa wayarsa tayi qara,daya duba yaga maji ce dole ya daga "Okay to,in sha Allah" yace yana ajiye wayar,sai ya miqe yana zube hannayensa a aljihunsa yana dubanta,sai kuma ya miga mata hannun nasa, ba musu ta dora nata hannun saman nashi ya rige da kyau ya tasheta tsaye. Duk inda suka gifta sai idanu yakai kansu tsakanin turawan dake kai kawo cikin asibitin, sai daya kaita gurin fadeela sukayi sallama sannan suka wuce gurin ajiyar motoci na asibitin inda taxi ke jiransu. Da kansa ya bude mata back seat kusa da maji,ya mayar ya rufe ya matsa baya yana folding hannunsa a qirji. Duk duniva banda maji ba wanda zai yadda yayi masa hakan,yana tsaye yana kallonsu har motar ta tashi suka fice a asibitin, ya bita da kallo yana jin kamar wani sashe na iikinsa ne aka tafi dashi "Mr man" ya tsinci muryar sajjad daga bayansa, koda ya waiwayo sai ya dinke fuskarsa tsaf saboda yasan tabbas tsiya sajjad din zaiyi masa "Muje ka rakani wani guri" yace da saijad din,sai yayi gaba yana biye dashi shima dai dariyar yake boyewa. Kafin su isa already ma'aikatan hotel din sun gama shirya dakin. Sanda Dr jarma yaga maji na maida luggage dinta dakin sai ya kalleta "Kada ki fara shifa indai baso kike muyi abun kunya a gaban surukarki ba" kallon shakulaton bangaro ta watsa masa "Ai ba damuwa" "Haka kika ce?" Ya tambayeta,sai bata amsa masa ba kawai tayi gaba abinta. Tunda maji ta shigo dakin sam sãahar ta kasa sakewa,kunyar yadda ta gansu dazu ne keta dawainiya da ita.ko hada ido da ita ta kasa. Itama majin ta fahimci hakan ta kuma tabbatar idan tace tare zasu kwana zata kwana ne a takure,sai ta aika nadeeya toilet tace ta hada mata ruwan dumi ta shiga tayi wanka. Shigar nadeeya toilet din sai ya zamana saura su bivu.a tausashe maii din ta kira sunanta.ta amsa ba tare data lya daga kanta ta dubeta ba "Ki saki jikinki dani ba abun kunya kikayi ba,mijinki ne kuma lada zaki samu, saidai abu daya nakeso, ki kula da kyau saboda mu tsira da wadan nan bayin Allahn,nasan me yiwuwa ne moha bame haquri bane a take takensa dana gani, that's why na daukoki,kina cika kwanaki goman da likita ya fada zan maida masa ke, karki biye masa azo ayi aikin dana sani" kai ta gyada a mugun kunyace, dai dai sanda nadeeya din ta fito tace ta gama, ta miga mata babban towel ta zauna shirya musu abincin da aka kawo musu daga restaurant a hotel din. Tare da maji din sukaci abincin dare,Dr mahmud na dakin hajiya garama yana fama da koke kokenta da a yau yakejin kamar yayi mata dukan tsiya,yana mamakin yadda ya dinga dauke wadan nan abubuwan nata tsahon shekarun, bai kuma taba ji ya gajiya ba sai yanzu?. Maji tanata kaffa kaffa da sãahar din, sai data tabbatar taci abinci da kyau,ta kuma tambayeta bata bugatar komai sannan tayi musu sallama ta fito. A qofar dakin sukayi kacibus da dr jarma,sukabi juna da kallo,sai ta kauda kanta tana mamaki, da gaske zaije ya taho da ita din kenan?, tana jin sanda ya saki ajiyar zuciya tare da wani qaramin murmushi ya juya ya rufa mata baya. Sai da suka dan taba hira da nadeeya kan yadda fadeela ke sake warwarewa da farincikin da yarinyar ke nunawa duk sanda aka gaya mata ta daina irin faduwar nan da takeyi "Kinsan daxun me tace?" Kai säahar ta girgiza tana murmushi "Bansan waye nafiso tsakanin anty N da abby dina ba" murmushi ya kubcewa säahar, Allah ne kadai yasan me ya ajjiye tsakaninta da fadeela tun bata wani santa ba amma Allah ya jarabceta da tausayin yarinyar, kafin daga bisani a hankali ya koma gauna, gauna tamkar ta d'a da uwa Sai sha daya saura na dare sannan suka kwanta kowa saman gadonshi. Dakin ya dauki shuru,sai dim light da nadeeya ta sanya musu,a hankali sai kwanyarta ta tafi tunani, ta maida idanunta ta lumshe. Ba abinda ke mata kai kawo sai fuskar toufeeq a mabanbantan gurare, tun daga farkon haduwarsu har zuwa yau cikin Saarland university hospital. Doguwar ajiyar zuciya ta saki, tana gyara kwanciyarta da taji sam batayi mata dadi ba,saidai duk da gyara kwanciyar da tayi hakan bai sanya taji dadin makwancin nata ba "'Wai kewarsa nake?" Ta tambayi kanta cike da dimbin mamaki "'Yes you missed him" wani sashe na zuciyarta ya bata amsa. Idonta ta sake lumshewa tana hasaso taushi dumi da kuma sassanyan qamshin dake fita ko yaushe a jikinsa "Da gaske ni munafukar kaina da kaina ce" ta fadawa kanta da kanta qaramin murmushi yana subuce mata Ashe duk yadda taje avoiding nasa a baya duk sanda yayi nufin rungume ta,ashe da gaske da yace tana pretending pretending din takeyi "Ya Allah" ta fada gasan ranta tana runtse idonta. Sansa ta bude idanun nata ta danna wayarta don duba lokaci. Har sha biyu saura na dare, ta sake maida idonta ta kulle ranta yana jagulewa gaba daya,wani matsanancin kewarsa tana ratsata har zuciyarta na quntata sosai. A karo na biyu ta sake bude idanunta, hakan yayi dai dai da hasken da wayarta tayi,ta miga hannu ta jawo wayar tana dubawa. Sunan nan nasa ne da nadeeya tayi mata saving a wayarta ya bayyana. Tayi dan Jim,sai kuma taji ta cika da zumudin ganin abinda sagon ya qunsa,ta bude a nutse ta duba _how are you?_ yace a taqaice, ta sauka qasa a hankali ta maida masa amsa a taqaice itama,ranta yana mata babu dadi, saboda ta saka ran jin kalamansa masu dadi da sukafi haka dadi a zuciyarta,saita tarar da gajeran sago _am fine_ ta amsa tana maida idanunta ta lumshe, qasa da second biyar taji alamun shigowar wani sagon _are you sure?_ tabe baki tayi kaman zata saki kuka,saita maida masa still a taqaice _"yeah i said am fine"_. Wannan karon ko idanun bai bari ta rufe ba ya maido mata amsa _tell me the truth_ "Haka kawai zuciyarta tayi rauni, idanunta suka cika sosai da qwalla, kewarsa takeji ba dan kadan ba,a gaggauce ta maida masa itama _i miss you okay?‚i miss you so much, and it's killing me_ Qaramin murmushi ya saki vana sauke gafafunsa dake saman qaramin glass table din dake gabansa,tsam ya miqe tsaye yana zura wayarsa cikin aljihun ya wuce can cikin daki ya jawo luggage dinsa ya soma cire wasu kayan yana fidda na jikinsa. Minti daya biyu uku har minti goma tana jiran taj§ amsa daga gareshi amma shuru kakeji,ta rufe idanunta ta kuma bude har batasan iya adadi ba, qwallar da take •I rigewa sai gata tana saukowa,me yasa ta zura jiki haka ta fallasa masa sirrin zuciyarta?. Sanda ya cika mintuna talatin sai ta gaza daurewa,ta sake daukan wayar ta rubuta wani sagon a tagaice _hey,why are you not replying?_ tana turawa ta saki ajiyar zuciya tana dora wayar saitin fuskarta. Minti daya tak wayar ta qara haske _am sorry. Am here front of your room, come outside and see me_ miqewa tayi ta zauna ba tare data zata ba tana raba ido, saita maida idanunta bakin qofar tana tantama. Taba qofar kadan taji anyi, mamaki sosai ya cikata,ta zamo a hankali daga saman gadon ta zura slippers ta nufi qofar dakin,ta murza key din ta cireshi daga jikin qofar, kafin ta bude har ya murda handle din qofar ya turota,sai taja da baya tana dubansa ta hasken waje daya ratso dakin mamaki yana kasheta. Zafafa biyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 62 Murmushin nan nasa dake gara masa kyau ya kasheta dashi,sannan ya dora yatsansa saman lips dinsa "Kina mamaki ne?,zan iya binki ko ina kika tafi, no matter how far it is" ya qarasa fada yana ratsawa ta gefanta zai. wuce. Har yazo tsakiya ya tambayeta "Maji tana ciki ne?" Kai ta gyada masa tana boye darivarta gasa gasa, baice komai ba sai ya fidda wayarsa daga aljihunsa ya kunna torch ya haska daya gadon da garamin haske. Waiwayawa yayi ya jefeta da wani salon harara me dauke da wani nau'in kallo "Inda maji dince, zan roqi alfarma ne kawai wajen abba,nasan shi zai fahimceni" yayi maganar yana isa makunnin fitilar dakin ya kunna,yasan abu guda kenan dake tayar da nadeeya daga bacci komai nisan da tayi. Take kuwa haske ya gauraye dakin dai dai da sanda ta motsa tana mitstsika ido "'Anty N,tashi kik....." Magale mata maganar tayi ganin mutum a tsaye tsakiyar dakin, duk da ya bata baya amma ta fahimci toufeeq dinne, saboda yanayin tsaiwarsa daban take "Tattara kayanki ki koma dakin wancan matar garama ki kwanta" ya fadi ba tare da ya waiwayo ya dubeta ba. Salin alin ta sauko daga gadon bayan ta lalubi garamin hijabinta ta zura,ta saka slippers dinta tana rungume da duvet da wayoyinta tazo ta rabasu zata wuce "Saura naji kina bada labarin nazo" ya fada a dake yana wani shan gamshi "Ba'a bakina ba yaa moha" ta fada tana qara wuta. Tana jiyo sanda ya maida qofar ya kulle, murmushi kawai ta saki,gaba daya yaa moha din ya sauya, da alama dukkansu soyayyar data tashi kamasu batayi musu da saugi ba. Yana gama rufe gofar ya juya ya kashe wutan dakin sannan va sanya hannunsa ya dagata cak, bai sauketa ko ina ba sai tsakiyar gadon nata. Idanu ta fidda sanda taji yana qoqarin duvet "Amma... "Shshsh....a nan zan kwana" "Maji fa?" "'Itama tana gurin mijinta, infact ma bani da gurin kwana sai inda matata take........sleep please" ya fadi yana zuge zip na gaban rigarsa gaba daya har gasa ya ballesa,sannan ya sanya hannu ya zame sleeping dress din jikinta ta wuya ya saukar da ita har zuwa cinyoyinta,ya sanya qafarsa a tausashe ya qarasa zameta har zuwa gafafunta,sannan ya hade fatar jikinsu guri daya,suka samu good skin to skin contact. A tare suka saukar da ajiyar zuciya,wata irin nutsuwa taii ta saukar mata lokaci guda hadi da kasala da wata tsumammiyar gajiya da batasan da ita a jikinta ba "Good night moonbeam-may your rest be complètely peaceful" sai ya karanta addu'o'i ya shafe musu jikinsu shi da ita. _sai muce asuba ta gari MT jarma angon Sãahar_ ******Akan lokaci sukayi sallar asuba duk da nauyin baccin da suka samu,sukayi jam'i shi da ita ya jasu sallar da daddadar murvarsa data sake sanya mata nutsuwa. A gajarce sukayi addu'o'i duka ta dauka yana sauri ne ya wuce kada gari yayi haske maji ta iskoshi,saidai suna gamawa tana shirin maida kanta saman pillow ya isketa "Gari yafa waye" "I know" ya amsa mata a taqaice "Amma, kada maji ta sameka fa a nan?" "Haka nakeso"" sai ya jawota cikin jikinsa kawai ya hardeta tsakiyar qafafunsa,bai sake bata damar yin wata magana ba har bacci ya sake awon gaba dasu. Maji tana gama shafa addu'o'inta ta miqe,dr jarma da a yau soyayya tayi aikinta,yayi galaba akan mail tarihi ya kuma maimaita kansa bayan tsahon shakaru kusan talatin,ya daga kansa yana jin zuciyarsa fess ta shayar dashi wani tafki daya manta rabonsa da samun makamancinsa,duk da tanata kumbure kumbure tana kuma basarwa amma sam bai dameshi ba,ya sani magana ta riga ta qare a tsakaninsu,aikin da yayi saura ba me yawa bane yanzun a gabansa "Ina zaki fita da safe haka?" "Zan tavar dasu nadeeya kada su kwanta suyita bacci basu tashi sunyi sallah ba" murmushi kawai ya saka ya maida kansa saman pillow yana cewa "Da kin dawo kawai kinyi kwanciyarki, don nasan toufeeq bai taba makara sallar asuba ba na tabbatar sun tashi sunvi" a mamakance ta juyo tana kallon dr dake kwance "Toufeeq kuma?, toufeeq din da yake a daya hotel din, me ya kawoshi nan kuma?" "Matarsa kika dauko masa shi yasa ya biyoku,da da baki dauko masa matarsa ba kin ganshi ne?" Cikin hanzari ta zura slippers dinta tana salati gasa gasa toronta Allah toronta kada ya warware aikin likitan nan azo a zamu sabani. Caraf Dr jarma ya rigota "Dawo ki zauna, ba inda zakie kina zaton kin fishi son cikin nan?,na tabbata yasan abinda yakeyi, ba abinda zai sameshi, kwanta ki huta hakanan" ya gwada mata garfi ya maidota kan gadon,tilas ba yadda zatayi haka ta koma ta kwanta tana qwafa amma qasan ranta. "Qarfin hali" taji Dr ya fada. Tasan sarai da ita yake amma sai tayi kamar bata jishi ba. Duk ta rude saboda kunya da tunanin sa wanne ido zata kalli su maji? amma shi sai taga hankalinsa a kwance yake,hasalima ko a jikinsa,yayi zamansa saman stool daure da towel yana waya da jibril ya shiga wani • shago ya siyo masa kaya ya bayar a reception a kawo masa. Ya gama wayarsa yayi wankansa,ya dawo ya shirya hankali kwance a gabanta,sai nata idanun taja ta kulle har ya gama. Ji tayi yana bude qofar dakin,sai ta zabura ta zauna tana dubansa a marairaice, shima ita din yake kalla. Fasa budewa yayi ya dawo da baya a hankali yana cewa "Ki daina razana hakanan, ki rufamin asiri gurin maji, kinga dai banyi komai ba,dan kadan ma nace adanji tausayina a sanmin amma ba'a bani ba, kada zaburar nan ta haifar da wani abu kisa maji ta hukuntani". Narke masa sosai tayi tana sauke masa kukan shagwaba. Zubewa yayi a gabanta gaba daya ya tsugunna saman gafafunsa ya kamo zara zaran yatsunta yana kallon qwayar idanunta "This shagwaba.....bani da jarumtar shanyeta fa ba tare da na biya tukuicinta ba, ki taimaka ki sassauta min" sosai ya bata kunya, gashi ya tsareta da ido, ta dan kauda kanta gefe tana fadin "'Amma....ta yaya zan iya zuwa na gaida maji don Allah" "Zo na rakaki" ya furta yana game tafukan hannayensu guri guda. Yadda säahar ke sissingewa tana jin kunya da nauyin maji haka suka bar majin itama da kunya da nauyinsu. Wato namiji dai komai qanqanta ko girmansa duka halinnan dai guda daya ne. Ta gefan ido take kallon Dr jarma, ya wani sake yana hira da toufeeq din sosai, farinciki ne zallah saman fuskarsa da zai nunawa mutum me shekaru da zurfin hangen nesa lallai a yau din va cimma burinsa. Shan tea din kawai take amma kunya ta cikata tsakanin Dr jarma din da toufeeq dan dikinta da sahar surukarta batasan wanda tafi jin kunya ba. Jefi jefi take jan sahar da hira wadda itama kunyar ta hanata tabuka komai,a haka hajiya qarama ta tura gofar da dama ba rufeta akayi sosai ba ta shigo. Kamar zuciyarta zatayi tsalle ta fito haka taji,ga maji ga mahmud again ga kuma toufeeg, toufeeq din da sannu sannu take kallo yana komawa qarqashin iko da mulkin maji din ta ruwan sanyi,sai ta girgiza kai,wannan babbar asara ce da tabewa a gareta, ba zata taba yarda wannan abu da ya fara afkuwa yaci gaba da wanzuwa a haka ba. Tana wani shan qamshi ta shigo dakin, ta samu waje ta zauna Dr mahmud na tambayar ta fito “Eh, ai naga ba kasafai kuka fiyawa tunawa da kun aje mutum a dakin ba" dire cup din hannunta maji tayi ba tare data dubi sashenta. Ta shirya sauya taku don haka ta hadiye wani abu da ya tsaya mata a wuya tace "Barka da safiya matar yaaya" wani kallo maji ta ajewa hajiya garama, a hankali ta sakarwa hajiya qarama din murmushi, a kallo daya tak ta fahimci inda maganar ta dosa "Barkanki fauziyya* ta smisa mata a taqsics taria barys dubanta daga kanta. Duk yadda toufeed yasi controlling carisa gaidata don ya sake binneta ya pra isovar fariar da /5 gayawa duniya wace ita, da fiddata a rayanarsa fitsrea ta har abada da kuma sarin hukuncin da yay imani sal yali kowanne hukunci yi mata cio a rayura sai ya kasa. Tsar ya mique abinsa, yanata cocarin had ye bein fan dake taso masa a duk sadda ya kalli fuskar ha, ja garama, baya ga amneesha itace mutum ta biyu a durija da tayi masa abinda zai koma ga manaliccinsa da tabonsa. "Zuwa nayi na gaya maka inason na koma gida,zan yank. ticket zuw anjima in sha Allah" hajya carama ta fada tana hadiye wani abu me daci da ya tsaya mata a wuya,ciwo kan ciwo,duka kan duka,yadda toufeed yayi watsin ruwan tsarki da ita ta karanci hakan. Tayi laluben duniya ta gano wanne laifi ta aika masa data cancandl yayi mata wannian rashin arzigin a matsayinta na wra kuma uwar goyo a gareshi?. Abu daya zuciyarta keta nanata mata,sãahar ce kawai ta shiga tsakaninsu, ita ta avatar da kornai,shi yasa batajin zata sassauta miata. duk randa ta tashi miga hukuntata,sai ta san ya yarinyar tayi dana sanin saninta a rayuwa,sai ta saryata ta zama izina ga kowacce diya mace dare shirin sake shiga rayuwar toufeeq din,ciki harda uwar data haifesa _uhmm, kifi na ganinka me jar koma_ "Ki gara haquri duka saura kwanaki biyar mu wuce gaba daya har da ita fadeelan,zan saka a yau din a duba mana ticket da zai maidamu gida lokaci daya" sai data hadiye wani abu a gasan ranta sannan ta dauke dubanta ta mayar ga yayanta "Yaaya, vanzu lalacewata yakai toufeeq ya wuce ba tare da ya gaidani ba?, hakan ba 'yar manuniya bace ga matarsa tayimin duk wani diban albarka da taga dama?" Dan dubanta kadan maji tayi, sai ta mige a nutse ta fice tabar musu dakin. Cikin ranta takejin indai toufeeq din bai gaidata ba bai kyauta ba da gaske, koba komai ganwar uba uwa ce komai lalacewarta ita da Dr din duka ba wanda ya lura da hakan. Reception ta wuce tana fidda wayarta ta kirashi tace ya sameta a can. Ba jimawa ya taddata, ta nuna masa guri ya zauna "Moha ban zaci samun dabi'ar raina na gaba daga gareka ba,ko meye a tsakanina da fauziyya ba huruminku bane wannan wani abu ne dava shafemu,me yasa baka gaida fauziyya ba?" Qas yayi da kansa, ya rasa wacce amsa zaya bata, ya sani ba Dr ba,ko ita da yayi imanin tasan halinta ciki da waje sai ta girgiza idan taji abinda hajiya qaraman ta aikatawa jininta gudar jikarta, yanzun kuma bayason yacewa kowa komai,so yake su isa gida ya gabatar da komai da hujja "Bazan iya gaidata bane maji, kiyimin afuwa" ya furta a hankali vana daga idanunsa zuwa kan majin. Kafeshi tayi da kallo tana mamakin yadda tashi guda kamanninsa da launin idanunsa suka sauya, idan ma idanunta sun gane mata dai dai harda kwanciyar hawaye a qasansu. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI* Book 02 Page 63 "Me yasa Mohammed?" Ta jefa masa tambayar a mamakance tana karanto tsantsar duhun bacin ran dake qasan zuciyarsa, tana son karanto zuciyarsa kai tsaye, inn karatun da cikakkiyar uwar da tasan abinda takey, takewa yaron cikinta komai girmansa. Dauke dubansa yay ya maida gete ransa yana soyewa "Zakiji maji a gaba, kiyimin afwa" shuru dukkansu sukayi shi da ita,jilkinta ya bata tabbas akwar wani gagarumin abu da ya faru,duk da ba'a shaidar dan yau amma ita din tayi amanna da Muhammad din d'ari bisa d'ari "Shikenan,Allah ya rufa asiri" ta fada a sanyaye "Ameen" ya amsa. Har ya miqe tace "Ka dauki matarka ku wuce zan saki dakin dana Kama din tunda babu amfani, ruwanka ka taimaki likitocin Kan taimakon da sukayi muku don ku samu ganin diyoyinku, ruwanka kuma ka wargaza aikinsu" sai a sannan yaji kunya ta kamashi,yasa hannu ya shafi lallausar sumar kansa yana murmushi cike da jin kunya "Allah ya saka da alkhairi ya qara girma". Kai kawai ta girgiza bayan wucewarsa, har ranta tana jin wani farinciki yana saukar mata,nutsuwa tana gauraye rayuwarta,ta tuna da darensu na jiya ita da Dr jarma din, komai nashi dare zuciyarta ya koma sabo. Yadda a ajiyan ya dinga bayyana mata bazai taba samun wata mace da zata maye masa gurbinta ba Itama tayr imanin hakanne a tata zuciyar, kawai tana ja masa aji ne saboda ya sake sanin muhimmancinta, tabbas, dan adam abun toro ne, kuma sharrinsa abun neman tsar ne. _ya ubangiji dukkan wanda zai nufemu da sharri cutatarwa ko quntatawa ga rayuwa da farincikinmu,ya rabbus samawati ka shagaltar dashi da damuwoyinsa,kayi mana tsakani da shi tsayin nisan tazarar da bata da yaka don hasken fuskar annabi muhammad S A W. ******* Qwarya qwaryar honeymoon suka gudanar a Germany din tsakanin toufeeq da saahar. Wata irin narkakkiyar soyayya ce me matugar tsayawa a ral ke huda zuciyar kowannensu. Wani irin so me matuqar qarfi da tasirin karya kowanne qarfi kafiya zati da turjiya na zuciya. Karon farko saahar din ta koma masa tamkar wata raqumi da akala,gaba daya ya sauke mata tunaninta,ya goge haddar kanta tasss!!' ,ya tsiyayar mata da man kai babu wani abu da yayi saura cikin zuciya ruhi da gangar jilkinta sai MUHAMMAD TAUFEEQ din. Gwarzon namijin da cikin lokaci qalilan ya tabbatar mata da karin maganar nan ta hausawa da suke cewa MAZA SUNA SUKA TARA Kuma KOMAI LALACEWAR AL' UMMA AKWAI NA GARI. Yayi nasarar cisge kowanne mummunan tunani a ranta damuwa da bad memories dake damunta,ya maye gurbinsu da wata zazzatar qauna soyayya da zallar kulawa. Irin nau'in kulawar da ta sanya ta dinga hango tsananin wauta da sokonci da take kallon abinda adam ke mata a baya da sunan KULAWA,sam sam babu hadi tsakaninta da wanna kulawar ta ainihi da toufeeq yake nuna mata. Sassanyar soyayya me tafiya da imanin diya mace, duk kuwa da cewa bashi da damar shiga gonarsa yayi ban ruwa,amma a hakan daga ita har shi cikin wani irin aminci suke. Baisan lya adadin sau nawa bakinsa ya furta godiya ga ubangiji ba,wato inda Ubangly bai cire ameesha daga rayuwarsa ba haka zai tabbata cikin quncin kurkuku da sunan AURE?,haka zai dawwama cikin mayaudariyar soyayyarta wadda bata da ma'ana ko gardi ko kadan?,cikin kwanakin KHADIJATU SAAHAR ta zame masa ALJANNARSA TA DUNIYA kamar yadda taci alwashi. Komai nata a nutse yake da want inn tsari me tsayawa a zuciyar namiji,tana da want irin Kula da takatsantsan a komai nata da sanya farincikinsa a gaban nata. Sun hadu sun kulle sun dinke sun zama cikakken abu guda. _RAMIN KARYA kurarre ne_* karfe uku na rana jirginsu ya sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na mallam aminu kano dake garin kano. Jirgin da yayo dakon iyalin DR MAHMUD JARMA da kuma surukansa. Toufeeq da sahar,dr din da kansa • da sarautar mata maji, afifa da hayatee dinta sajjad, sal kuma sister nadeeya da shalelensu fadeela, daga gefe kuma hajya qarama ce dake ankare da takun kowa,cikin ranta da zuciyarta kuma tana jin duk wannan scenes din ya qare tun a Germany,dukkansu sun gama cin gaajiyar soyayyarsu, a yanzu lokaci ne da kowa zai girbe hukuncin data tanadar masa. Duk da haka babu abinda ta tsana irin idanunta su sauka akan maji da Dr, ko kuma säahar da toufeeq,basu ba hatta nadeeya ta sakawa ranta wannan karon ba zata sassauta mata ba,ita kanta afifa saita fita daga da'irar danginsu tunda ta silar saahar ta shiga family din. lauranin masoyan guda biyu,zaka rantse da Allah saboda hutunsu da jin dadinsu yasa aka shirya tafiya garmany, daga toufeeq din har saahar sunyi wani irin kyau sunyi fresh cikin sati biyun da suka qara akan kwanakin da suka shirya tahowar. Saahar ya hade mata da yanayin cikinta wanda ya samu cikakkiyar kulawa da tabbacin zamansa dai dai bisa mahaifarta, ya kuma sake zuba mata wani irin kyau kamar 'yar sarkin aljannu. Toufeeq kuwa zai iya cewa kafff! Tsahon rayuwarsa bai taba samun nutsuwa makamancin wannan a rayuwarsa ba,nutsuwa ta ainihi tun daga gangar jiki zuwa ruhi. Ko da soyayya bata burgeka kana kallonsu zasu baka sha'awa ta kowacce fuska,sai nan nan yakeyi da sahar din tamkar sarauniyar matan duniya, o yaya ta motsa sar ya tambayeta "Me kikeso ne moonbeam?" A sannan dumin jikinsa kadai take bugata,amma tana jin kunya da nauyin nuna masa,ta tsinci kanta a wani yanay na tsananin son kasancewa dashi. Sanda ta fahimci hakan hankalinta ya tashi,ba da wanda zata iya maganar dashi sai bestie dinta. Dariya afifa tayi sosai kamar zata kifa akan dan matashin cikinta,har sai da saahar da zuciyarta yanzu yanzu zakaga tazo kusa tace da ita "'Ki yarfani yadda kikaso,dama aini na kawo kaina ko?" Rigo hannunta afifa tayi tana qoqarin saita kanta "Ki yafemin Bestie, Allah bazan ya riqe dariyata bane, nasan wannan yanayin zar yiwa moha dadi qwaral,ashe akwai wanann lokacin zaizo?" "Ban sani ba,sakeni" "Zauna kiji" ta fada tana daidaita dariyarta,sannan ta zauna tana fuskantar saahar din. "Akwai yanayi irin wanann dake iya samun mace me ciki dama, saboda qaruwar hormones dake jikinta, amma karki damu,tunda kwanakin da zaki wake ki koma mu'amalarku yayi,ba wani matsala, kibar toufeed yaci karensa kawai babu babbaka,nayi imanin zai sake haukace miki ne kawai, saboda a yanzun jikinki na sakin sinadaran da suke sake maida mace cikakkiya qwarai,kada ki damu,zan fahimtar da hayatee,ya daukawa yaa toufeeq hutu a kowanne branches na Kamfaninsa dake kowacce qasa har sal ya gama biyan bashin dake kansa" dariya wannan karon bestie din nata ta bata, sal kawai ta dungure mata kai,amma qasan ranta kunyar aritan takeji,itama ta fahimci haka sai tace "No boundaries between us bestie, komal nawa ya shafeki, kamar yadda komai naki ya shafeni". "Tunanin me kikeyi moonbeam?" Ya tambayeta yana dan Jan hancinta,kanta yana kwance akafadarsa "'Ba komai" muryarsa ya sassauta yana yin qasa da muryarsa "Na gane komai fa, kuma zan biya duka basussuka,ina • tsoron qetare ryaka ne maji tace nayi wani abu da ba dai dai ba ta daukemin Kai,shi yasa nayi kawaici na qara wadan nan kwanakin akai, amma definitely am craving for you" sunne fuskarta kawai tayi ta rasa amsar bashi. Madubi hajya mansura ta dauka tana sake kallon fuskarta da kyau, kamar yadda labiba ta kasa zaune ta Kasa tsaye,duk bayan mintuna saita duba make-up din Tuskarta. Dukkaninsu ita da mahaitiyar tata sun shirya tarbar uba da dansa, bayan cikakken shiri da kuma tabbacin da suka samu daga bakin sabon boka na musamman da mansura ta canza saboda gain bayan hajiya qarama. A yau din kacokam ta sauka gidan toufeeq don tarbar mijinta, labiba kuma ta tarbi touteeq ta Kuma ci gaba da zama a gidan tana farautar zuciyarsa kamar yadda tayi imanin hajya qaraman na cusa haseena cikin lamuransa ta qarfi da yaji don samun shiga a wajensa. Taci alwashin wannan Karon babu gudu babu ja da baya, kanta tsaye zatayi fito na fito da hajiya qaraman,ta kuma gama shirya duk wata hujja akan hajiya garaman koda zata nemi kawo mata wargi ko ta Kawowa shirinta tarnaqi. Manya manyan hujjoji ne da ake tanada saboda rana irin wanann,manyan hujjojin da kake ajjiyewa saboda tarwatsa maqiyi kuma abokin adawa a duk sanda yakejin zai tsallake lyaka da kuma gonarka. Karo na uku hajiya mansura ta sake leqawa da Kanta farfajiyar gidan ta window din sashen Dr jarma wanda bazai iya tuna yaushe rabonsa da shi ba. Da kanta ta sanya akayi masa gyara na musamman saboda zamanta a nan dinne kadai zai iya bata damar aiwatar da burinsu hankali kwance. Duk da ta fara qaguwa da jiran isowarsu amma zuciyarta fes take saboda albishir din data samu daga mutumin da take Kira da malam. "Akwai nasara a goben guda d'aya,akwai faduwa da asara guda biyu" bayanan da yayi mata kenan, bayan ya sake bata tabbacin hajya qarama na daya daga cikin faduwa da asara guda daya cikin biyun da ya lissata "Nike da nasara!, tabbas nike da nasara!!" Abinda ta maimaitawa kanta kenan,saboda tako ina idan ta juya tunanita nasarar take hangowa kanta,cikakken shirt ta yiwa kanta da take da yaqinin babu faduwar!!, nasarar dal!... -tofa jama'a, maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta,maga wake da nasarar,wake da asarar da kuma faduwa_ Zafafabiyar "HUGUMA* *_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 64 Dukkansu suka mige sanda sukaj| qarar bude gate din gidan tare da qarara shigowar ayarin motocinsu su MT JARMA. Kallo sosal hajiya mansura ta mayar kan labiba "Wannan karon babu sauqi babu sassauci,babu kuma daga qata,fatatawa ce ta gaske,yaqin sunquru za'a yi tsakaninmu da duk wanda zai hana mana cikar burinmu,ni dake kowa yayi amtani da damarsa ya samawa zuciyarsa abinda takeso" kai labiba ta jinjina cike da gamsuwa "In sha Allah mama" tare suka fara takawa suna fita zuwa harabar ajjiye motoci na gidan, don zuwa yanzun sunsan duka motocin sun isa can. Lissatinsu ya basu dal dal, sanda suka isa din duka suna qoqarin fitowa daga motocin, banda toufeeq, da säahar dake zaune cikin tasu motar kamar basu shirya fitowar ba,ya tsareta da fararen idanunsa yana Kalionta bayan ya dauke kallonsa daga duk jama' ar dake farfajiyar gurin, kama daga ma'aikatan gidan da haseena dake riqe da hannun hajiya qarama dake qogarin fitowa da mota,har labiba da ke isowa gurin. "SAHR…...bana buqatar..... "Shshshsh" tace dashi tana dora yatsantsa kan labbansa fararen idanunta masu wani irin haske ta zubesu a cikin nasa "Kada kace komai,duk wadan nan tarkace nima bana bugatarsu,for now ya kamata su nisanci rayuwar mijina ko? idan ba haka ba zasuy nadaman cusa kansu ga rayuwarka,am new version of saahar, ba tsohon version din da suka sani bane" a hankali ya kama yatsanta dake kan labbansa ya tura bakinsa yadan tsotse kadan. Da sauri ta fuse hannun tsigar jikinta na tashi tana masa nuni da fadeela dake zaune gaban motar, kafadunsa duka biyun ya daga sannan ya rausayar da idanunsa ya maidasu waje shi da ita duka suna ci gaba da kallon wajen. Cikin takun kissa da jan hankali hajiya mansura ke takowa zuwa gurin har ta iso bakin motar dr jarma "'Barka isowa,marhaban da......." Qafewa kalaman bakinta sukayi suka tsaya mata a wuyanta,su basu fita ba su basu koma ba,wani irin abu ya tsarga mata wanda ya haifar da tsatstsafowar gumi daga kowacce kafa ta jikinta sakamakon ganin maji da tay na fitowa a motar mazauni daya da Dr din. Duk wata walwala tata ta janye kaff!. Bata taba zaman kishi da maji ba, amma tayi imani zaman kishi da matar bazai taba yi ma kowacce macce dadi ba,duk wadda kuma tayi gangancin aikata hakan tabbas zata iya kwasar kashinta a hannu. Da boka da malam cakude da tuggu da makirci amma tsahon shekarun da tayi da Dr din basuyi nasarar cire maji dari bisa dari daga zuciyarsa ba,ta wahala ta wannan fannin da tsantsar baqin kishi, wanda ta dinga ji inda tare suka rayu da maji babu abinda zai hana zuciyarta bugawa fes. Murmushi hajiya qarama ta saukewa fuskar hajya mansura,ta tabbatar a yau boom na farko da zai fara tayar mata da kan mansura batun maida auren mijinta ne da tsohuwar matarsa da tayr imanin mansura din bata sani ba,kuma tasan itace mutum ta farko da zata fara aje zarginta a kanta,to ko hakan ma yayi mata,wannan zai qara mata tsoronta cikin zuciyarta hadi da shakkarta,zai kuma sake dasa mata cewa ita din ta isa da yayanta kuma kome tace ya aikata zaiyi din,duk da lamuran sun fara sauyawa. Murmushin da ta gani a fuskar fauziyya shi ya sanyata hanzarin maida nata murmushin saman tata fuskar itama,ta sani murmushin fauziyya irin wannan ga abokin takun saqa ba alkhairi bane,sai ta sake matsawa tana yi masa maraba,fiye da rabin hankalinta nakan maji. Ko sau daya majin bata dubeta ba,saboda bata qaunar kishin dake ranta ya motsa a kanta,abu daya ta sani,ranta yana baci da yadda Mahmud din ya buge da auren mansura. Tasan mansura farin sani tunda tana daya daga cikin qawayen da fauziyya ke tara mata suna keta alfarmarta har cikin gidanta a wancan lokacin. Ta gefansu ta wuce abinta tana migawa nadeeya Jakar hannunta,sannan suka wuce zuwa sashensu. Idanun Dr yana kan maj,yayin da idanun mansura yake kan Dr,har zuwa sanda maji tayi nisa ya maido hankalinsa ga mansura. Fuska ta bata sosai baqinciki yana ciciyar zuciyarta,babu ta yadda zata yarda ta bari matar nan taci gaba da zama a qasar nan,idan ba haka ba kuwa tayi imanin tata ta kusa qarewa. Juyawa tayi abinta saboda bacin rai,sai yasa hannu ya kamota "Yaki mana,ya zaki tafi?" Ya fada a tausashe. Dole yabi a sannu, saboda yasan a yau din Allah ne kadai yasan kalan tashin hankalin da za'a yi a gidan idan taji maida aurensu, amma hakan ya zama dole ya shelanta kowa ya sani saboda fidda zargi da kuma sake shaidar zamantowarsu miji ga mata din ga family dinsa. "To me yayi saura kuma?" "Muje" kawai yace da ita. Gaba tayi tana qoqarin hadiye fushinta, tanason taci ribar yau din,ta kuma kwashe dukka nasarorin da malamin tsubbun ya gaya mata, tasan tushi kuma ko tashin hankali bazat sanya ta tsira da komal ba indar Mahmud ne. "Ki koma suna cikin motar, ki tarbeshi ki nuna damuwa da kulawarki a kansa" hajiya qarama tace da haseena wadda ke shirin shiga sashenta. Bata cewa uwar komai ba ta juya din da sassarta, ya qaguwa tayi da son ganin toufeeq din, tunda ya tafi ko sau daya bataji muryarsa ba bare ay zancan ganinsa. Tana dab da isa ta hangi labiba a tsaye a gurin,wani bacin rai ya taso mata,itafa ba labiba da suke takara tare ba,hatta da saahar din ta tsaneta. Ya gama karantar takun kowa a cikinsu, sai ya janye idanunsa cikin ransa yana raya kowacce zataci qaniyarta. A nutse ya bude motar ya sanyo qafafunsa waje. Cak kowacce ta tsaya daga inda take, kwarjininsa cikar haiba da kamalarsa yana dukan fuska da zuciyar kowaccensu. Hannu ya miga ma saahar dake zaune cikin motar, idanu suka hada ya sakar mata murmushin nan nasa me tsada,sai ta mayar masa da martani, ta miga masa nata hannun tana jin qaimi cikin zuicyarta,wani sashen na zuciyarta yana sake cika sosai da kishinsa. Tamkar wata da zara haka suka fito, sunyi want irin mugun kyau da matching da junansu, koda maqiyr idan ya gansu a lokacin sal sun burgeshi. Daga labiba har meenal kowacce sai data hadiye wani yawu mai tauri, a take dukka wani qwarin gwiwar da labiba ta debo ta tsiyaye ta kuma tarwatse a gurin, kallon sãahar kawai na farko taji ta raina kanta gaba daya,tako ina bata isa ta gwada kanta da ita ba, koda silin yatsanta guda daya tasan bata kamo ba,sãahar din tayi wata muguwar gogewar da ko ke diya mace sai ta burgeki bare d'a namiji,duk da wanna kuma idanuwanta sun gaza daukewa daga kallonsu. Yawun bakin meenal gaba daya ya dauke da wani irin mahaukacin kishin saahar, tabbas inda ace akwai bindiga yanxun a hannunta babu abinda zai hanata harbawa saitin zuciyar saahar, tako ina ita dimma tasan zati da cikar haiba nutsuwa da kamalar säahar ta zarta tata,saidai kuma bata jin ko kadan wannan Karan zatay giving up, ba zata sassauta ba wajen farautar toufeeq har sai taga abinda ya turewa buzu nadinsa,don haka ta tattara dukkan qwarin gwiwarta tayi taku biyu zuwa inda suke takawa,cikin fari da ido, lanqwasa harshe da yauqi tace "'Barka da dawowa yaa mohanmu..... "'Wayy!" Säahar ta datsin maganar da meenal ta debo tana lanqwashewa, abinda ya maida dukkan hankalin toufeeq kanta "Yaya? me ya faru?" Cikin wata muguwar shagwaba data shigeshi gaba daya cikin jini da julya tace "Qafafuna,na gaji,nidai ka daukeni" "Angama" ya furta yana nannade hannun tsadadden yadin jikinsa. A tausashe sannan a hankali ya tsugunna yasa hannunsa ya dagata cak ya fara takawa da ita zuwa sashensa idanunsa cikin nata yana tambayarta "Are u comfortable?" Kai ta jinjina masa sannan a sace ta dubi sashen da su labiba sukayi mutuwar tsaye,cikin sa'a suka hada idanu,ta aje musu wani kallo na baku isa ba sannan ta maida kanta saman qirjinsa ta kwantar a shagwabe. Dariya labiba ta qyaqyace da ita sanda taga haseena da tayi mugun shaqa,ta kuma gaza boye shaqar da tayi din ta hanyar binsu da kallo, duk da cewa sun bacewa ganinta "Ashe dai duka burga ce,ashe dai ba'a isa din ba,ashe duk kwana da tashin da akeyi gida daya duka suna ne,ah wai" labiban ta furta tana tura dauninta gaban goshi,duk kuwa da cewa ita dinma ta shaqi bacin rai har kusan fiye dana haseena. A mugun fusace haseena din ta waiwayo 'Ke, ki saurara malama, koda giwa ta fadi tafi qarfin wawa, ni ba sa'arki bace,don nafi qarfinki har abada" sosai labiba ta sanya dariya harda shewa "Mu gani a qasa mana,wai inji kare ana biki a gidansu yace mu gani a qasa,ashe duk wani cika baki da fankamar uwar taki na banza ne, tunda ta gaza mallaka miki mutum daya tal a rayuwarki,wannan ma ya isheku hasara da kaico, bayan kaicon da a wunin yau kafin faduwar rana yake shirin samunku, ku shirya zuwarma gagarumar FALLASA wadda zata cimma rayuwarku" daga wannan sai ta juya tana taku d'ai d'ai, cikin ranta tana jin FALLASAR da zata auku a yau din, tamkar mabudin nasara ne a garesu. _to maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta_ A bisa bigire daya suke takawa,saidai kowacce zuciyarta cike take da alwashi da kuma mugun tanadi ga ‘yar uwarta,wani irin kallo a sace wanda bakuna basu furta komai ba sai fatan cikan burika, a haka har suka iso mararrabar sassan guda biyu,dr jarma yay gaba. Daga Mansura har fauziyyar kowaccensu tsawa tayi "Ina miki barka da isowa qasarki ta gado,ina miki barka da isowa bigiren da zaki fahimci bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane,ina kuma yi miki jaje da kalar qaddarar da yau din tazo miki da shi, ina miki fatan samun juriya a bisa hakan" sai da gaban hajiya qarama. yadan fadi, amma kuma tayi gaggawar ture wannan daga ranta da tunaninta,don kuwa a kaf tarihinta bata taba yarda kalaman barazana sun tsoratata daga bakin abokin adawa ba. Jifanta tayi da murmushi duk da zuciyarta na cike da kokwanton yadda mansura ke magana kanta tsaye cike da qwarin gwiwa "Ke ya kamata ki riqe wadan nan kalaman kiyi bitarsu da kyau,domin a yau kadai zaki fahimci ni fauziyya nike sanyawa a auro a kuma saka sannan ayi kome a duk sanda naso hakan, baya ga wanna kuma..…... Tarantin nan da kike shirin taka gefansa, kina gab da gain asarar da bazaki iya qidanya adadinta ba" murmushin ta jefa mata Itama "Ni dake shege ka fasa" "Dan halak sai kallo" sai kowannensu ya juya yana nufar sashensa, saida dukkansu zukatansu cike suke da fargabar yagewar zaninsa a tsakiyar kasuwa,saboda gaba dayansu sunsan sunyi birniya me zurfi da kowa a cikinsu yasan da mummunar ajiyar dan uwansa,amma cikar da zukatansu sukayi da daukan fansa da samun cikar burin diyoyinsu ya sanya suke jin komai zasu iyayi, komai ta fanjama fanjam. *_turqashi, kuzo kuyi kallon dinkin gadar zare zai tsinke_* Da hanau gwara mannau inji hausawa * ,ku yimin uzuri,jiya dama ta bayar,yau kuma sal a hankali, na gode qwarai_* Zafafabiyar "HUGUMA* *TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 65 Zucivarta kamar zata fado take takawa zuwa bedroom din Dr jarma din. Hankalinta na tashi idan duk second daya da zai shude idan tayi tunanin ko dai fauziyya ta sanya Dr jarma ya dawo da shifa dakint? tunda dai kalamanta hakan suke nunawa yana shirin faruwa. Kai ta girgiza, indai hakanne har abada ba ) zata taba yadda ta zauna da shifa ba, ba zata taba aminta wata mace ta shigo mata gidanta ba gidan data ciwa burika masu yawa,take kuma sanya ran ita daya ce macen da zata yiwa dr jarma takaba ta kuma karba tumunin takabar ita daya. Fuskarsa cike da nishadi yake cire kayan jikinsa da zummar yin wanka,jya walwalar dake saman fuskarsa ya sake dasa mata matsananciyar fargaba "'Drya akayi na ganku tare da maji ne?, dama tare kukayi tafiyar?" Waiwayawa yayi ya dubeta yadda ta cake tana masa tambayar wadda tafi kama da titsiye. Kansa ya dan kawar yasan akwai dan rashin kyautatawa da yayi mata,a galla ya shaida mata koda ta waya ne zai maida aurensa "'Me kikeson ii mansura?" "Ka maida matarka ne?" Sake maida dubansa yayi a kanta "Me kike ci na baka na zuba?, ki barni na watsa ruwa mana, ba tun muna can kika gayan kin shirya mana liyafa tare ba?" Kai ta jinjina masa kawai • "Okay, bari na watsa ruwa na fito, saikiyi gogarin shaidawa kowa ya fito akan lokaci aci abincin tare. hakan dama va kamata lokaci lokaci a dinga yi, saboda vana kawo hadin kai da garin fahimtar juna" bata iya amsa masa ba har ya wuce zuwa bandakin,sai ta furzar da iska daga bakinta,ta dunqule hannunta ta daki dava tafin hannun nata, ta koma ta zauna ta kirayi daya daga cikin masu aikinta tace ta sake shaidawa kowa,amma sashen toufeeg a shaida musu ta waya. Ajiye wayar tayi gaba daya tana jin nutsuwa tana yin qaura daga gangar jikinta,duk yadda taso bawa kanta qwarin gwiwa da kwantarwa da kanta hankali abun ya faskara, sai ta bude wavarta ta hau shirya komai cikin shirin ko ta kwana koda bugatar hakan zata taso. Tun a hallway ya din bedrooms dinsu ya fara rage mata kayan [ikinta,yana tsaye daga bayanta yayin data dogara dukkan wani garfi nata a jikinsa,cikin wani irin slow motion suke takawa shida ita,sadarwar skin to skin din dake a tsakaninsu tana rura wutar dake zukatansu gaba daya. Ta dauka yana isa qofar bedroom dinsa zal bude, sai taga bai tsaya ba har dai dava isa gaban full length mirror din dake bangon garshe na hallway din. Tar surarta da tashi suka bayyana a jikin madubin, tsananin kunya ta sanyata juyowa da sauri ta bawa madubin baya tana boye kanta a qirjinsa. Wani galabaitaccen murmushi ya saki yana ci gaba da kallonta ta cikin madubin, yana jin yadda zuciyarsa ke sake laushi tana narkewa cikin soyayyarta. A nutse ya sanya lausasan tafukan hannunsa ya dago fuskarta yana kallon tsakiyar qwayar idanunta. Irin wanann kallon yana da bala'in tasiri cikin zukatan da jikkunansu su duka,musamman da suke kan irin wannan yanayin "'Biyan bashi zanyi yau din,i hope you're ready?" Wani lallausan murmushi da tasan vana tarwatsa duk wata nutsuwa tashi ta sakar masa,sanann tayi farrr da fararen idanunta da suka qara haske sosai,da zazzaqar muryarta tace dashi "Babies sun shirya sada zumunci da abbynsu... sassauta muryarta sosai "Nima ummien babies din a shire nake,i crave for you since "Shshshsh" ya furta yana murmushi hadi da dora yatsansa saman labbansa yana sakin murmushi "I know,i can read it ta can gasan wadan nan fitinannun idanuwan" tabe baki tayi kamar me shirin sanya masa kuka "You mean.....na zama fitinanniya fa?" Qaramar dariya ya saki "Ba ke bace ai nasan laifin babies ne" "Allah Allah nasan ni kake nufi" ta furta tana narke masa tare da dunqule hannunta ta daki qirjinsa. Hannu daya yasa ya dafe saitin zuciyarsa hadi da lumshe ido "Ya salam ya Allah, maji zata illatani, bayan ban fara komai akan sonta ba,zo muje ki gani,na tabbatar hallway din nan yayi mana kadan" sai ya dauketa ya wuce nutsatsen bedroom din nan nasa dake da wani irin tattausan yanayi dake garawa zukata da feelings na masoya armashi. Yadda a yau din ya susuce a kanta sai da abun ya bata mamaki ya kuma tsaye mata sosai a rai, don daga ita har shi din sun aminta da juna maqura,sai ya dinga jin kamar säahar din an sake sabunta masa ita ne,da ayar ta samu ta lallabashi ya shiga wanka itama ta wuce nata dakin don ta shiva,ranta da zuciyarta cike fal da mamakin sauyawarta,bata gajiya ko kadan da bugatuwa zuwa ga toufeeq din "Allah yasa kici gaba da tabbata a haka koda bayan kin bani ajiyata ne" furucin da ya fada mata kenan a dazun yana gangame da ita. Tsaf ta shirva cikin wani material me sulbi sosai cream color da adon brown flowers da wani avalli a jiki. Ta kusa mintuna ukun tana tsaye gaban madubi tana kallon kanta da kanta, bataga laifin toufeeq ba, dole ya sake haukacewa a kanta ya kuma sake manne mata, fuskarta ta aje wani kyau na musamman tayi mugu mugun yin fresh.Qaramin murmushi ta saki tana daukan wani siririn turarenta dake da wani sirrintaccen gamshi ta feshe jikinta da dashi sannan tasa wasu slippers masu taushi a gafarta da suka dace da kalar material din jikin nata. Har ta juya ta dakata,ta dawo da bava tana duban cikinta. Har yanzu a shafe yake ga idanun mutane saidai idan ta sanya English wears ko kuma ta dora hannun nata saman mararta shine take iya jin tasawarsa. Ko a yanzun saman mararta ta dora hannun nata, ta shafi cikin a hankali, iva tudun nasa da takeii kadai vana saukar mata da wani irin farinciki me tarin yawa,qauna mara misaltuwa da ita kanta batasan adadinta ba akan cikin. Yadda soyayyar mahaifinsu ke haukata a ranta, haka kullum rana takejin soyyayar 'yan tayin. Duk wannan abun kuma sai taga kamar toufeeq ya fita gaunarsu da nuna tsantsar kulawa. Kullum Allah shine da kullum sai yayi aqalla mintuna kusan hudu ko biyar kunnensa yana saman mararta wai yana gaisawa da biyunsa, hakanan kullum sai ya sanya tape ya auna tsaho da fadin cikin wai yaga sun qara girma?. Tun abun yana bata dariya harma ta riga data saba. "I love you and your daddy so much" "'Daddyn nasu shima yana masiliifar gaunar mamansu" taji an fada daga bayanta. Da hanzari ta juyo don bata tsammaci tsaiwarsa a gurin ba. Yana jingine da gofa hannuwansa goye a qirjinsa yana mata wani narkakken kallo. Sosai kunya ta kamata, batasan me yasa yakejin dadin yi mata labe yaji tace masa i love you ba, kunyar ta sanyata jan gefan mayafin boubou din tana sunne fuskarta a jiki. Dukka hannuwansa va bude mata yana dariya "Come-on babe bea, ba kalmar da yafi dadi a bakinki irin inji kince I LOVE YOU MY NUGGET the best name da nafiso bayan duk wani suna da za'a kirani da shi idan ka cire MUHAMMAD dina, taho taho" y fada yana sake ware mata hannuwansa. Iya takun data iss gareshi kawai sun tafi da imaninsa,sanann ya sanya tana isa gareshi ya bata hotties kisses ssman fuskarta wuyanta da goshinta,ya tsugunna sukayi hirarsu da yaransa kamar yadda yake fada sannan ya riqe hannunta suka nufi main parlor na gidan kamar yadda aka sanar masa. Kamar ma kowa su yake jira,don duk sun samu kowa cikin parlor din, maji na zaune gefe guda ita da nadeeya suna magana qasa qasa, fadeela na cinyar Dr jarma,hajiya qarama haseena na gefanta itama,hakama hajya mansura labiba na zaune daura da ita. Kallo daya zaka yiwa kowa dake wajen kasan zukata na cike da abubuwa masu tarin vawa da zukatan kadai aka barwa sani akan su. Sallamarsu ta maida hankula a kansu,zukatan maji dr nadeeya da fadeela cike da farinciki da alfaharin ganinsu. Yayin da mansura labiba da hajiya qarama abubuwan da suke zakatansu sun banbanta da na juna. Wani irin kallo na qurilla hajiya garama takebin säahar dashi, irin kallon da tunda suka je germany har suka dawo bata yi masa irinsa ba sai yau. Qirjinta yayi wani mugun bugawa sanda sahar din ke kaiwa gasa tana musu barka da warhaka. Idanunta ta maida ta kulle tana fadin ""Na shiga uku" saboda tudun data hanga daga gasan mararta "Yaushe tayi wani cikin har ya fito?, bayan a yanzun shine lokacin da zanyi kyakkyawan shirin cireta daga jarma family?, fita kuwa ta har abada? ba irin fitar da ameesha tayi ba tabar musu irin FADEELA?, ko dama qarya yakeyi mata toufeeq?, dama ba miscarriage tayi ba?" Wani mugun sarawa kanta yayi, har sai da takai hannunta da ya fara rawa ta dafe kanta tana sake kulle idanunta "Relax.....relax mana fauziyya‚u are a strong woman" ta gayawa kanta da kanta, saita bude idanunta cike da qwarin gwiwa tana furzar da iska me zafi daga bakinta. Kowa ya kama gurin zamansa,kamar yadda toufeed ke zaune kusa da säahar din, nadeeya da hajiya mansura ne suke serving, saidai shi din kuma ya kasa ya tsare. Bayajin zai iya barinta taci komai dake wajen, zuwa yanzu mutum uku ya yarda dasu akan säahar din. Maji cs ta farko sai nadeeya sai kuma baaba ramatu. "Me zakici ne surukata?" Hajiya qarama dake fidda shu'umin murmushi ta tambayi sahar idanunta yana tsakanin fuska da cikin säahar. Motsawa kadan säahar tayi, bagin matar yana sake mamaye zuciyarta,taso ace wannan tambayar tayi mata ita ne lokacin da babu mutanen da takejin nauyi da ganin qimarsu a wajen, tabbas da ta bata cikakkiyar amsar da zata isar da L sago, ba iya kanta kadai ba,har izuwa kunnuwan gadangarun 'yammatan dakeson shiga rayuwar toufeeq din nata. "Karki damu da abinda zataci,ke dai ki lura da abinda zai iya zuwa gabanki" toufeeq ya bata amsar da wani irin qwarin gwiwa hadi da wani tsattsauran kallo cikin idanunsa. A hankali ta janye idanunta daga kansa gabanta yana faduwa,iya kallon da toufeea yakeyi mata a yau ya dasa gaqgarfan zargi a ranta "Akwai abinda yake faruwa" ta bawa kanta amsa. "Tabbas akwai ayar tambaya,tsahon shekaru sama da ashirin ban taba gain irin wannan kallon daga idanun Muhammad ba" ta sake jaddadawa kanta tana recalling abubuwan da suke faffaru tsahon satittikan da sukayita wucewa. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 66 Maji kamar bata a wajen,saidai tana ankare da komai, dr jarma da hankalinsa duka yake akan majin da duk wani motsi nata,ya dan waiwaya sashenta "Shifa matsomin da wannan ruwan na gabanki na wanke hannuna" cokalin hannun hajiya mansura ne ya subuce ya fadi, ta watsa kallonta ga dr jarma. Alamu da dama suna mata nuni da yiwuwar faruwar was al'amura "Meye hadinka da tsohuwar matarka da zata baka ruwan wanke hannu?,duk da nayi kara da alkunyar ciyar da abincin da na girka da hannuna ba tare da nayi qorafi ba" "'Matarsa dai a karo na biyu ko?" Muryar hajiya qarama ta ratsa hargagin mansura. A gigice mansura ta waiwayo tana kallon fauziyya. Murmushin nan nata dake dauke da tarin ma'anoni ta jefeta dashi "Af, nayi hanzarin shaida miki maganar da ba'a bakina ya kamata a jita ba ko?, to tunda dai na riga na fada bari na garasa miki. "Ya isa fauziyya" Dr jarma ya dakatar da hajiya qarama a tsawace "Da dai ka barni na qarasa yaaya" ta sake fadi tana sakin garamar dariyar da zaka dauka cikin tarin zallar nishadi take "Da gaske ne abinda fauziyya take gayamin?" Hajiya mansura da tashi d'aya kamanninta suka juye saboda zallar tashin hankali ta furta "Samu guri ki zauna muyi magana,wanann zaman bana hayaniya bane" dr jarma ya fada cikin nutsuwa da tsare gida "Ban bugatar zama mahmud,amsa nake nema eh ko a'ah" ta fadi tana rige qugunta wutar bala'i da masifa tana ruruwa saman fuskarta. Toufeeq da kansa ke duqe,tunda hayaniyar ta fara tashi kansa yake a qasa yana son hadiye nasa bacin ran sal a sannan ya daga kai yana kallon mansura,cikin kakkausar murya yace "Malama ki zauna akace!!" Ya fada a dan tsawace da bacin rai, ita da hajiya garama din suna cikin sahun farko da a yanzun baisan me ya tsana kamarsu ba "Karka sake magana toufeeq, ba huruminka bane" mai tace dashi tana tsare gida. Motsawa yayi alamun zai mige yabar wajen, don bayajin zai iya jurewa kallon mansurar tana yiwa Dr haka "Koma ka zauna, matsala ce da ta shafi kowa da kowa" Dr jarma ya fadi, sannan ya mayar da dubansa ga mansura "Shifa matatace ta lalle uwar 'ya'yana,matar da duk duniya tayimin abinda ko.mahaifiyata iya abinda zata iya yimin kenan,wata gaddara da bansan meye silar faruwarta ba ta datse igiyar aurena da ita,na jima ina addu'a da bansan iya adadinta ba,a yanzun haka shifa na matsayin matata ta sunnah, an maida aurenmu a Algeria qarqashin jagorancin kawunta" "Tabbas!" Hajiya garama ta rufe da fadin haka duk da bata jin ko mansurar tana jin dacin da takeji a zuciyarta akan dawowar maji gargashin igiyar auren dr jarma din. Saidai a yanzun mansurar ce first target dinta, tanason ta nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane. "Mahmud saidai kuwa ka zaba,ko ni ko shifa wallahi tallahi!" Ta furta tana buga table din gabanta "'Maji kina gani fa!" Toufeeq ya fada yana yunqurin migewa cikin huci "Koma ka zauna Muhammad!" Ta sake daka masa tsawa. Da garfi ya koma ya zaune kan kujerar tasa. Säahar da ta tsorata da irin fushin da take gani kan fuskarsa ta laluba hannunsa cikin tafin hannunta. A hankali ya juyo ya zuba mata jajayen idanunsa, sai ta lumshe idanunta hadi da budesu ta kuma matse hannunsun guri guda, abinda ya kawo wani gwaggwaban gudun mawa,ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya can qasa yadda babu me jinsa yace “can't take it moon" "For maji's sake" ta maida masa a taqaice. "Bazan tsaya doguwar magana ko bata bakina wajen gaya miki na san wacace ke, nasan irin zaman da nayi dake dukka shekarun da muka kwashe ba,amma ina me shaida miki na bar miki dukka dukiyata da kika dinga diba da kadan da kadan kina tarawa….amma kuma ina me farincikin shaida miki,NA ZABI SHIFA, NA ZABI SHIFA,NA ZABI SHIFA, don haka na sakeki saki daya,na sakeki saki biyu....” "Dr!" Maji ta gwala kiran sunansa da garfi saboda ta fahimci me yake shirin qarasawa aikatawa,saidai kiran sunan nasa da tayi sam bai sakashi ya dakata ba sai daya kai inda yakeso yakai din "Na sakeki saki uku ni Mahmud jarma, ku shaida" tsaf labiba dake zaune saman daya daga cikin kujerun dining din ta sulale tayi zaman dirshan qasan marbles din dake gurin ta saki wani irin kukan tashin hankali. Cikin izza da tagama da madaukakin farinciki haseena dake daura da ita ta waiwaya tana kallonta,sai taja kujerarta gefe tana tabe baki "Su ungulu sai a shirya komawa gidan tsamiya ko?, abar masu abu da abunsu, banzar da akazo ci bata samu yadda akeso ba,sai a tashi aje gida". Maganganun haseenan sun sake jefa labiba cikin magurar tashin hankali, don me yasa mommyn zata bari har haka ta faru? me yasa zata janyo mata wanna babbar asarar?, gwara ita ta samu ta abinda ta samu,ta kuma tara abinda ta tara, amma ita fa?,ba toufeeq din, kuma bata tara komai ba. Kai tsaye mansura ta juyo tana aje kallonta ga hajiya qarama, ta san shaidanci da shu'umancinta,lallai ita fa qulla wanna abun, dawowar shifa da kuma sakin da dr jarma yayi mata a yanzun, saidai batasan cewa har kanta da kanta ta ballowa ruwan ba "Tabbas kin cika shu' uma,sannan na sake yarda ke kike aura masa mata ki kuma saketa a duk sanda kikaso kamar yadda kikayi igirari...... Mahmud" ta fadi tana waiwaya ga dr jarma. Yadda ta kira sunan nasa yaja hankalinsa "Duk cutar da nayi maka ba zata kama gafar wadda fauziyya tayi maka ba,duk wani ha'inci da na aikata maka baiyi rabin rabin wanda jininka tayi maka ba. Ha'inci cin amana da ha'intar gauna tana kasnacewa me saugi ne akan ace makusancinka ne yayi maka, yau zan fito maka da ainihin wacece fauziyya da fuskarta da baka sani ba" sai ta tsugunna qasan table din. Wata tsohuwar leda ta dauko da tasha qu|li ta fara kunceta. Kallon ledar kadai hajiya garama tayi hanakalinta yayi mugun tashi. Ashe!,har yanzu bata samu damar badda sahun wannan abun ba? ita kuwa ta yaya zata bari mansura tayi mata irin wannan tonon sililin a yau wanda yake dai dai da mutuwarta murus. A zabure. ta mige tana nuna mansura "Qaryarki tasha qarya mansura,dama ashe da gaskene shi matsiyaci idan ka daukoshi daga rana zuwa inuwa yana hucewa burinsa na gaba shine yaga ya tunkudaka wannan ranar?, to kin makaro,duk wani sharrinki don ki shiga soyayya da fahimtar juna dake tsakanina da yayana da yaransa baki isa ki shiga tsakanin wannan hadin da ubangiji ba" murmushi me ciwo mansura ta fidda tana dakatawa daga bude ledar "Ki bari na kammala fito da abinda ke ciki idan na gama nuna tawa shaidar kina iya musawa ko hajiya me gaskiya ) da amana?" . Koda Karen mahaukata ne ya cijeta ta yaya zata bari mansura ta kunce wannana ajiyar,sai ta maida dubanta ga dr mahmud wanda idanunsa yake a kansu yana kallonsu.. Kuka ta saki cikin salon da take amfani da shi a duk sanda takeson cimma wani buri nata akan yayan nata "Dama na sani akwai mutane da yawa a duniya da basason suga kulawa cikin idanunka a kaina, to matarka da na yiwa halacci ashe tana ciki, kada ka saurareta yaaya,wallahi tallahi kome zata gabatar maka garya ne" "Fauziyya!" Maji dake zaune tana karantar dukkan wani motsi na fauzivvan ta kirayi sunanta. Fitar sautin muryar maji da yadda ta kira sunan nata da wani irin amon sauti ya sakata waiwayowa ta kalleta "Ki nutsu kinji fauziyya,ita gaskiya fure take ai bata 'ya'ya, gaskiya bata bugatar rantsuwa ko ay mata ado don a gawatata a idanun mutane a fidda ainihin kamanninta,tafi buqatar a qyaleta da zahirin kalarta... ...banga abun tashin hankali ba akan leda kawai da ko budeta ba'a kai ga yi ba,ki dakata ta fadi duk abinda takeson ta fada din, ita gaskiya zatayi halinta da kanta" maganganun shifa sunyi dai dai da abinda Dr jarma yakeson fada,wanda tsabar mutuwar jiki ta hanashi furtasu. Haka kawai yaji jikinsa yayi wani mugun sanyi kamar babu laka a tare dashi. "'Fauziyya kenan" mansura ta fadi tana ware ledar cikin karsashi da qwarin gwiwa. Qulli biyu ne cikin ledar ta ajjiye qaramin ciki, sannan ta bude babbban. Wasu irin tarkace ne a ciki, wasu gananun tukwane da wasu tarin allurai da layoyi masu yawan gasken, sai ginin mutum mutumi guda biyu kowanne jilkinsa zagaye da allurar da layoyi da wasu gananun abubuwa kamar danyan nama yana wari wari. Da mugun hanzari har tanayin taga taga kamar zata fadi hajiya qarama ta mige tana duban mansura, ilahirin jikinta da bakinta suna rawa. A ina mansura ta tono wanann tsimammen sirrin da ya dauki shekaru kusan talatin a binne?. "Mansura!!!" Ta kirata da garfi, kiran da ya maido idanun kowa kanta. A take kuma kaicon yadda take qoqarin tonawa kanta a siri ya kamata,sai ta koma da baya ta zauna kafin irin da ta soma ji yana yawo da ita ya kwasheta ya zubar Ko kallon inda hajiya garama mansura batayi ba gaban maji da Dr jarma ta turasu tana dubansu "Wannan duka an shiryasu ne saboda ku,a raba tsakanin zucivarka da ta shifa,a raba tsakanin shifa da nadeeva Muhammad dake da gauna da qulafucin uwa a cire masa shifa daga zuciyarsa, sannan a mantar da shi uwarsa,saboda shi din namiji ne,yana da power taurarinsa tun a wancan shekarun sun haska,sun nuna kuma shi din rayuwarsa na cike da arzigi me yalwa da ya ninka na mahaifinsa, fauziyya kuma ta shirya ita daya zata mori wannan arziqin, daga nasa har na ubansa sai wanda taga dama" "Qarva kike mansura,garva ne wallahi " haiiya garama ta fada cikin hargagi tana nuna mansura da yatsa,duk da ciwon da kanta ya fara kamar zai rabe gida biyu. Murmushi mansura ta sake mata tana jin farincikin yadda fauziyya ta soma birkicewa tana fita daga saitinta,alamu kuma suna nuna dukka dabarunta sun fara qwace mata. "Saurin me kike fauziyya? idan duka kin musa wadan nan saboda daga ke sai malaminki kuka shirya shi,bakisan ina biye da kowanne taku naki ba,wannan ai baki isa ki garyatashi ba" ta fadi tana takawa dauke da qaramar ledar tana garasa budeta, sannan kanta tsaye ta isa ga tafkekiyar TV plasma din dake dining room din. A nutse ta jona komai, ta cire garamin memory card din ta soka shi a gefan tv din. Cikin qasa da second goma yayi loading ya hau,video clip guda daya ne akai, hajiya mansura ta daukj remote din tayi clicking akan video din. _TURK'ASHI_* Zafafabiyar "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI* Book 02 Page 67 • TURK'ASHI_* Tarrrr baby fadeela da a lokacin da kwanan watan dake a rubuce b'aro b'aro ya nuna tana da shekaru uku ne a duniya ta bayyana,sanye da wata pink gown wadda tsahonta yake iya qaurinta, an raba dogon sassalkan gashinta gida biyu an matseshi da pink din bands gananu masu kyau‚ba takalmi gafarta sai pink sock's me ‘yar teddy qananu a samanta. Tana tsave saman stair na can qarshe, bakin qofar da idan aka budeta zata sadaka da ainihin babban parlor zuwa bedroom din toufeeq. Bubbuga qofar takeyi a hankali tana faman kiran sunan ameesha "Mommy, Imommy yunwa nakeji, mummy kingi fitowa tun dazu,kizo ki bani abincin bacci zanyi mommy, mommy don Allah" daga yadda yarinyar ke magana tana goge hawayenta zai nuna maka ta jima tana bugun gofar, kuma tabbas har ta fara gajiya da bugawar. Zamewa tayi ta tsugunna bakin gofar dakin dai dai lokacin da video din ya dauko hoton hajiya qarama. Cikin sand'a da alamu na rashin gaskiya ta zame takalman gafarta ta ajjiye gasan stairs din, ta fara takawa cikin sanda da takatsantsan, ta yadda ko cikakken motsinta baka isa kaji ba. Bata tsaya ba har ta cimma fadeela wadda ta bawa stairs din baya, babu kuma ta yadda za'a yi taga tahowar wani don kamar ma ta fara gyangadi a wajen. Kamar qiftawar ido da budewarsa ta miga hannunta ta finciko gashin kan fadeela ta wancakalar da ita , abinda yayi sanadiyyar wata muguwar gangarowa da yarinyar ta farayi ba matakala bayan matakala ba,'ah bibbiyu bibbiyu ta dinga tsallakewa jikinta da kanta yana buguwa ta kowanne sashe, kama daga tiles din dake shimfide a wajen zuwa garfen jikin stairs din "Ab......mom....abbyyyy...." Sunan data furta kenan na qarshe ta qarsa gangarowa stair din garshe ji kake tassss! kanta ya bugu da marbles din. "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" sãahar ta furta da garfin amo cikin gigicewa tana kama fadeela gami da kauda fuskarta daga gain jinin dake malala saman kanta. Tsam fadeelan ta riqeta da gaske,ga mamakin säahar kuka yarinyar ta saki "Randa na fadin nan ko anty? tun daga ranar abby yace bani da lafiya,ashe fadowa nayi daga stairs" yarinyar dake lullube cikin jikin säahar ta fadi. Tuni Dr jarma ya mige tsaye yanajin jikinsa kamar an kwara masa tafasashen ruwan zafi, maji kuwa tafukan hannayenta ta sanya ta lullube fuskarta tana kiran sunayen Allah duk nau'in wanda yazo bakinta cikin gigita da bada amannar tabbas fauziyya ba mutum bace. Nadeeva gam ta rige maji tana wani irin kuka,tsoron haiiva garama yana mugun shigarta, tana jin kamar zata dauki wuga a yanzun nan ta sossoke cikin kowa a cikinsu. "Bagar annamimiya ni zaki shiryawa wannan sharrin?. "Shut up!, Ba sharri bane" toufeeq ya furta yana qogarin zaqulo nasa memory din ya jona musu da abinda suka gama gani yanzu. Doka wayar yayi da gasa saboda rawar da hannunsa yakeyi ya kuma samu ya cire memory din da gyar. Fusge wancan yayi ya watsar don ko ganin Ralarsa bayason yi ya saka na hannunsa. A hankali video din ya fara da nuna blank kafin fitowarta daga bedroom dinta cikin tsakiyar daren tai zaman irga tablet din. Wani dadi ya ratsa hajiya qarama,qasan ranta ta cika da fatan ya kasance komai yayi formatting ne. Tsulum kamar wadda aka jeho sai gata ta fito,wani annamimin gumi ya soma tsatstsafo mata ta kowacce kafa ta jikinta. Komai ya fara bayyana tiryan tiryan, tun daga nan har zuwa isarta dakin fadeela,musanyan magungunan da kalaman bakinta da sai da taji kamar ta hadiye kanta da kanta a lokacin _bagar matsiyaciya,kin kusa fita daga rayuwata,kin kusa barin gidan nan, gidan nan gidan meenal ne, toufeeq da abinda ya mallaka dama wanda ubansa ya mallaka duka na meenal ne da abinda zata haifa_ *Qarya ta gare bori ya kar boka* "Innalillahi wa inna laihi raji' un, allahumma la sahla illa ma ja'altuhu sahla,wa'anta taj' alal hazna iza shi'ita sahla" shine abinda Dr kawai yake fadi jikinsa na wani kakkarwa da mazari,ko ina na jikinsa yana rawa kai kace ciwon fargadiya yana shirin kamashi. Duka hankula sai sukayo kansa,hankalin maji 'yayi mummunan tashi, ta dafashi da hanzari, toufeea ya garaso da gaggawa yana yunqurin zaunar da shi. "Yaaya....don Allah yaaya!" Hajiya qarama dake gunjin kuka ta taso tana son isowa inda yake "Kina garasowa nan zan manta dake wacace karki kuskura ki garaso nan, kiyi gaggawar fita a wajen nan,idan ba haka ba na sakar miki karnuka su yagalgalamin namanki da ranki!munafuka azzaluma annamimiya" Toufeeq din ya furta wasu hawaye masu tsananin zafi da radadi suna zartowa a idanunsa. Idanuwan da sukayi wani mugun jaaa har baya iya ganin abinda ke gabansa sosai "Yaaya..... toufeeq...... "Kibar gurin nan fauziyya,bana qaunar na sake ganin fuskarki har abada" Dr jarma da yake fusgar numfashinsa da qyar ya fada yana dafe qirjinsa,ji yake kamar zuciyarsa tana shirin bugawa. Tunda uwarta ta haifeta bata taba ganin tashin hankali tozarta da abun kunya irin na yau ba,sanda take tafiya zuwa dakinta jiri ne yake angizata daga gaba zuwa baya. Meenal tana biye da ita itama cikin kukan,kukan nata da yake da nasaba da hango rasa toufeeq rashi na har abada. Yadda gaba daya parlor din ya rude ya birkice ya sanya dole maji ta gayyato juriya da dakiya irin ta uwa ta azawa zuciyarta da ruhinta, don dukkansu a yanzu suna bugatar wanda zai jagoranci tunaninsu ya kwantar musu da hankali "Dauko mota Muhammad mu kaishi asibiti, nadeeya kira baaba rabi tazo takai sãahar daki ta huta, ki cire damuwa daga ranki, jarrabawa ce mun ganta kuma mun cinyeta a yanzun in sha Allah alhamdulillah, Allah dai yayi nufin sai mun gani ne kawai ki cire damuwa saboda abinda yake jikinki" dai dai toufeea ya dawo a gaggauce, ya kama Dr jarma wanda yaketa ambaton sunan Allah sanoda vadda numfashinsa da girjinsa suka rige va fita dashi zuwa harabar gidan. Sai da maji taga baaba ramatu ta kama hannun sãahar sun wuce daki da ita,tace fadeela ma ta zauna gudun shiga tunani sannan suka wuce asibitin. Falon ya zamana babu kowa,hajiya qarama aneesa hajiya mansura da labiba sune suka rage. Wata shu'umar dariya mansura ta saki, ta hada hannuwanta dukka biyun ta tafasu da kyau, tayi taku biyu ta tsaya gaban hajiya garama "Tabbas abinda malam ya fada haka yake, faduwa guda biyun tawace da taki, nasara kuwa ta maji ce,a yau na tsinciki kaina banji takaici ko baqincikin yin nasarar wani ba..... Fauziyya kin dauka kai kadai ce kika iya shu'umanci? kin dauka ke daya aka yankewa tuggu cibiya a gabanki? kina tunanin zan zauna ne haka. sasakai kara zube ba tare da na tanadi mkaman gare dangi ba? bayan na san wacece ke?,ai duk makahon da kaii vace ayi wasan jifa to ya taka dutse ne.….na rasa mijina kin rasa dan uwanki!" "Kin tafka babbar asara mansura butulu" dariva ta kece da ita "Ashe? da kunya a idanunki har kina da bakin kiran wani butulu? ,kawai butulu sama dake? wadda taci amanar dan uwanta? taci amanar 'ya'yan dan uwanta? tunda kikaci amanar maji to tabbas ba wanda ba zaki iya butulcewa ba gwara ni.....kishiya ce kome nayi a kanta hada miji mukayi" "Ke da gamawa da duniya lafiya har abada!" Hajiya garama ta furta a birkice tana jin kamar qwaqwalwarta zata hautsine "Ke kuma idan aka leqa wuta ba'a ganki ba garwashin wuta ne ya rufeki fauziyya!" "Dalla malamai ku gara gaba,yanzun ba wata sauran alaqa tsakaninmu daku" haseena da duka wadan nan maganganun basa gabanta ta fadi, don abu daya ke damunta a yanzu,ta yaya zata samu toufeeq?. "'Me kike ci na baka na zuba meenal ya'aqoub aji?, awanni kadanne kuma suka rage muku a gidan nan yadda kuma ban samu toufeeq ba kema ke dashi saidai a hoto" labiba ta fadi tana jin sassaucin tashin hankalin data shiga a dazun, saboda tayi imanin ita da meenal dukkansu sun rasashi kenan. "Zo mu tafi mommy bakin alqalaminsu suma ya riga ya bushe musu" labiba ta fadi tana damgar hannun hajiya mansura suna ficewa daga falon. Dukkansu ita da labiban zucivar kowannensu cike take da tashin hankali, komai sunayi ne kawai saboda idanun haseena da hajiya garama,amma sunyi amanna watan fara sanin wahala a rayuwarsu ta kama. Kuka meenal takeyi sosai tana biye da hajiya garam cikin fushi da fusata da kuma tashin hankali, bata damu ko kadan da zubar hawayen idanun hajiya qarama din ba "'Ni duka bance kije ki aikata wannan abun ba,kinyi ne kawai saboda son ranki da biyan buqatarki,ni ba damuwa ta bane koma meye zai faru, kawai ni ki cikamin algawarin da kika daukarmin,ni toufeeq nakeso,na riga na tsarawa kaina da shi zanyi rayuwa" kalaman 'yar tata yayi mata tsauri da yawa, tana juyowa ta kwashe haseena din da mari "Ban taba sanin baki da imani ba sai yanzu, kome da ake tuhumata akai fiye da rabi na aikata shine saboda jin dadin rayuwarki da kuma inganta rayuwar taki amma baki ganib..." Kafin ta rufe bakinta siraran yatsun haseena masu azabar zafi sun samu lafiyayyen muhalli akan fuskar hajiya garaman. Wani mugun shock ne ya shigeta har fitsari yana ballewa a wandonta,da gyar ta tattaro yawun bakinta ta hada kalaman "Ni kika mara haseena ni uwarki da na dauki cikinki wata tara na haifeki?" "To sai meye? don kece kika haifeni ai ba kece kika halicceni ba,ga mari ga tsinka jaka? ga duka ga rashin biyan bugata?, to tunda ke sauna ce kin kasa aiwatar da komai ni zan samawa kaina farincikin da kika gaza bani din" saita kewayeta kamar zafa bangaji kafadarta ta wuce dakinta da gudu gudu. Sulalewa tayi ta zauna saman kujerar da tafi kusa da ita tana dafe da dukkam kuncinta guda biyu tana jinta kamar ba cikin duniya take ba. Tunda take a rayuwarta duk tashen gin jin maganarta taurin kai da* shaharar da tayi wajen iya garya da shirya makirci ko yayanta bata taba mari ba bare akai ga mahaifiya, sai gashi yau itace yarinyar data haifa,ta gwadawa gata fiye da kowa cikin duniya,taketa fadi tashin tara mata dukiyar da ko bayan ranta ba zata wulaganta ba,take ta yunqurin samar mata nagartaccen miji, yau itace ya shimfidawa fuskarta mari?. Qarar jan luggage dinta ya sanya hajiya qarama din daga kai. Ta shirya abinta kamar yadda tazo cikin gananun kaya. Da sauri ta janye qafafunta wanda banda hakan tsaf zata murjesu tabi ta kansu ta miqe tana kiran sunanta "Haseena baki da hankali ne? ina zaki haseena? wa kika sani?" Ta fada tana tarar gabanta cikin jin tsoron kada halayyarta ta tsananin fushi ta sanyata ta aikata abinda ba dai dai ba "Dalla matsa ki bani guri,ni yanzu baki da amfani a gurina, toufeeq shine rayuwata, kuma na rasashi, tunda kuma na rasa shi a shirye nake na rasa komai nawa" ta fada tana jifanta da wani wulaqantaccen kallo sannan ta gogi kafadarta tana wucewa. Tayi taga taga kamar zata fadi ta samu ta tsaya kan gafarta, ta bude baki zata sake gwada yunqurin tsaidata din sai sautin data sanyawa dukkan alert massages na bankunanta ya fara tashi a jejjere. Da sauri ta miga hannu saman dan table din data ajjiye wayar dazu kafin ta fita tana dubawa, mamaki yana cikata na shigowar massages din a jejjere babu qaqqautawa. "Na shiga uku......na lalace….meye haka?......kai jama'a wayyo Allah na ku kawomin agaji….Zasu yasheni.......zasu talautani…..wayyo Allah wai ba kowa ne a gidan" ta fada cikin budaddiyar murya tana kwasar hanya da mugun gudu tana fita daga sashenta. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI_ Book 02 Page 68 Dai dai lokacin da alert na qarshe ya shigo wayarta,wanda aka cire ragowar millin uku last amount da ya rage a bankinta, kuma qarshen abinda ta mallaka kenan duk duniya,don ta saida komai nata ta hade kudin cass cikin account dinta zata sake sabuwar order na dukkan shagunanta,har a ciki take sanya ran gyara da same bungasa plazas dinta da wuta tayi musu mugun ragargaza. Tsaiwa tayi cak a wajen,sai ta dafe kanta ta daga qafa da mugun gudu tana fitowa harabar gidan a birkice kamar wadda take da tabbacin barayin da sukayi mata aika aikar suna tsaye a qofar gidan. Saidar tana gara daga qafarta wata muguwar hajijiya ta debeta ta watsar da ita,sai gata tayi d'ai d'ai warwas a qasa. Amma hakan dai bai hanata miga hannu tana son yin kururuwa ba, kururuwar da babu damar fitarta daga bakinta saboda karkacewar da bakin nata yayi,sai wan! kakkauran yawu data fara zubarwa ta gefen bakin nata. Caaaa ma'aikatan gidan sukayo a kanta, sai suka rasa yadda zasuyi da ita,saboda sunga fitar masu gidan yanzu. Daga qarshe dai bayan kusan awa daya daya daga cikin masu aikinta tayi gundunbala ta shiga bedroom dinta ta dauko key din motarta. Acanne taci karo da kit na sarqoqin gold dinta rankacakaf data fitar dasu a dazun bayan dawowarsu da zummar zata saidasu saboda taji yadda kudinsu yayi daraja ta aikawa gawarta kudin dake dubai ta siya mata sabon design. Key din motar kawai ta miga musu ta wuce sashen masu aikin gidan ta hada kayanta zakara ya bata sa'a ta falle, cikin zuciyarta tana fadin "Allah ne yayi da rabona, muguwa kina samu amma ke kadai kike amfana,saidai mu mu qare ayi miki bauta" ( shawara a gareku masu ma'aikatan a gurin Sana'a ko kasuwanci ki cikin gidajenku de sauransu,sanda mutum yake zaune qarqashinka yake maka hidima,a duk sanda Allah ya buda maka,kaima kayi goqarin buda masa ku taru duka kuyiwa Allah godiya,wannan shine abinda zai dawwamar da soyayyarka a zuciyar ma'aikatan ka,da wata iriyar mana ta gaske da zaiyi wuya a hada baki dasu a cutar da kai, ko suna ji suna gani su bari a cuceka, Allah ya bamu ikon kyautatawa dukkan wanda muke tare dashi ameen summa ameen). Private hospital aka kaita kamar yadda sukasan duka iyalin gidan suna zuwa,babban asibiti ne da suke cazar kudi bana wasa ba,sanda aka isa asibitin da ita likitan da ya fara dubata ya tabbatar zaiyi wuya bata samu matsala ba,saboda jininta ya hau sosai, hakanan barin jikinta ya daina aiki, daya barin ma ya tabu sosai amfanin da zaiyi mata kadanne, duk wani abu dake daya sashenma totally ya daina amfani, kama daga idonta kunnenta hannu qafa da sauransu Sun tsaya anyi mata komai da komai ba don halinta da dabi' arta ba. Bayan komai ya kammala akayi total na kudin asibitin kwanciyar da zatayi da sauran bill na abubuwan da zata ci. Elyas na daya daga cikin wadanda suka tallafa aka kawota,don toufeeg din bai fita da kowa ba,daga shi sai maji din sai Dr suka wuce dashi asibitin. Bayan ya gama duba bili din wayarsa ya ciro yayi kiran toufeeq,cikin rusunawa yayi masa bayani "'Kana jina elyas?" "Eh sir" "Sisina daga abinda na mallaka da kuma abinda mahaifina ya mallaka ban amince ka cire ka biya komai ba,ku batta da su tana da gwarin qwiwar yiwa kanta komai,ka jini?" Kai ya gyada cike da biyayya "'Yes sir" sauke wayar yayi daga kunnensa yana furzar da huci daga bakinsa,shi kansa baisan wanne kalar hukunci ne va dace da ita ba. Zuwa magariba Dr jarma din ya koma normal, saidai sunce lallai dole sai ya kwana,saboda sunason jininsa da yahau ya dai daita kafin su sallameshi, basason ya tafi kuma ya dawo. "Bari na yiwa jibril magana maji ya maidaku gida ke da nadeeya,zan kwana a gurinsa in sha Allah" toufeea ya fada yana danna wayarsa. Murmushi maji din ta saki tana kallonsa "Kaji dan nema,waini zaka yiwa kaara? to ban yarda ba, kada kana tsaka da yimin jinya ka gudu ka barmin miji sai asuba ka dawo" nauyin maji ne ya kamashi sal ya fara shafar sumar kansa yana murmushi, ko ta fahimci tun dazun yaketa kiran number sãahar din dama bata daga ba? duka hankalinsa yana kanta tunda suka zo "Itama tana bugatar kulawarka Muhammad, ku tafi gida kai da nadeeya din,ka kula da matarka ni zan kula da milina" ta fadi tana maida dubanta kan dr jarma da idanunsa ke rufe kamar alamun yana bacci ne. Dan rusunawa toufeeg yayi cikin ban girma "Allah ya qara girma, Allah ya bashi lafiya" yayi musu sallama bayan ya tabbatar babu wani abu da zasu bugata har wayewar gari. Suna fita tana qoqarin dauko wayarta daga jaka taji an rigo hannunta, ta daga kanta a hankali sai taga Dr ) jarma ne yana daga kwancen, idanunsa da suka nuna jigatarsa da kuma gazawarsa tare da tarin nadama "'Na dauka bacci kakeyi ai ashe ka farka" ta fadi tana yunqurin migewa. Maidata yayi ya zaunar da hannunsa daya ya buda bakinsa da muryarsa ke fita da gyar yace "Ido na biyu shifa inajin kunyar hada nawa idanun ne da naki bansan me zance miki ba,bansan ta vadda zan nemi gafararki ba,bansan da wadanne kalamai zanyi amfani wajen neman afuwarki da yafiyarki ba" kanta tadan sadda gasa tana wasa sa hannun jakarta sannan tace "Tuntuni na yafe maka Dr tun a wancan shekarun don nasan muddin na gullaceka ko na yi maka mummunar addu'a rayuwar 'ya'yana na lalata, saidai kuma daga yau, kada ka sake sakaci da addu'a a rayuwarka,domin ita din garkuwa ce" "Bazan sake ba shifa,naga illar hakan iyakar ganina,wai 'yaruwata shifa.....uwa daya uba daya..." Sai ya kasa garasa fada. Da sauri ta matso gabansa "Ka daina tunawa don Allah abban Muhammad taka kalar qaddarar kenan, kuma ai yanzun komai ya wuce ) ko?" Ta fada cikin kalar tausasawar da bai taba gani daga idanun mansura ba. Da kalamai masu dadi ta kwantar masa da hankali har sai data tabbatar ya nutsu sannan ta mige "'Ina zaki?" "Zan hada maka wani abune ka saka a cikinka" kai ya girgiza "Ba yanzu ba, banajin cin komai,ki rufe qofar kawai kizo ki zauna kusa dani naji duminki shifa,inason na fanshe bashin shekara da shekarun da na dauka" murmushi ne ya qwace mata,cikin salon tsokana tace "Da wannan tsufar naka?,ai ka makaro" ido yadan fidda "Inii wa? idan kika cikamin baki da yawa ma tazarar haihuwarku keda surukarki zata kasnace ba yawa, nadeeya itama ta samu 'yan uwa" baki maji ta rufe da sauri tana dariya "Rufamin asiri" "Na rufa miki" ya amsa matan shima yana dariyar. A nutse yake takawa zuwa cikin gidan, har cikin ransa yana gara jin gidan ya qarasa fita gaba daya daga kansa. A cikin gidan al amura masu yawan gaske sun afku,wadanda sukayi silar rugujewar farincikinsa, komai na matsalolinsa a gidanne,a yanzun vanajin bashi da wani sauran bugatar ci gaba da zama a gidan,ya fita fitt daga ransa. A hankali ya ratsa falukan nasa ya fada hallway dinsu sannan kai tsave ya isa ga bedroom dinta. Murza handle din yayi ya bude sannan ya tura gofar ya shige. Sam dakin babu wadatar haske a ciki,amma kuma hakan bai hanashi gain komai dake dakin ba. Daga can saman abun sallah ya hangeta, sanye da wani baby pink hijab, fadeela na saman gadon a nannade, da alama tayi nisa a baccinta. Duka hannayensa ya zuba a aljihun wandonsa, ya jingina bayansa da bangon dakin yana kallonta,wani irin kallo da yakejin tamkar zuciyarsa tana narkewa saboda ita, A HEROIN…ta kawowa rayuwarsa haske me tarinyawa da bai zaci samunsa a nan kusa kaf cikin rayuwarsa ba. Jin bai garaso ba ya sanyata daga kanta a nutse ta bude bakinta a hankali ta langabar da kanta "Me kake kalla?‚ka qaraso" hannayensa ya sauke yana murmushi "Jarumar matata nake kalla, kinyi missing dina ne? ko na qaraso akwai labari?" Wani narkakken kallo ta watsa masa,tadan juya kanta kadan tana murmushi "Baka gajiya... "Shshshsh" ya fada sanda ya iso gabanta,ya tsugunna saman qafafunsa idanunsa cikin fararen qwayoyin idanunta " will never get enough of you moonbeam,you are the only home i want to stay for ever, kinsan wani abu?" Yayi mata tambayar kai tsaye. Fararen idanunta ta daga ta kalleshi,saita girgiza kanta tana jin zuciyarta da ruhinta dukka suna narkewa a kansa, tana jin wata iriyar soyayya me zafi da garfi tana fusgarta a kansa. A hankali ya zame va zauna sosai a gabanta kamar me zaman cin abinci,ya kama vatsantsa na tsakiya yana kallon tsakiyar qwayar idanunta,yanason ya aike mata sagon da gaske yadda kowacce gaba ta jikinta zata karba "Duk sanda nakejin kaina ya cika da tunanika kala daban daban my body is weak and my soul is aching....i find everything in your arms,you are my home....you are my peace SAHR" Idanunta ta lumshe qwarai "Ya salam! wannan wanne irin so ne haka me barazanar fasa zuciva?" Ta furta a hankali da salon magana cikin rad'a. Ji vayi kamar ya hadiyeta su zama abu guda shi da ita ko zasu fi samun saugi a cikin zukatansu. Sai kawai ya jawota a tausashe ya sanyata cikin jikinsa. Dan janyeta yayi da sauri yana duban fuskarta "Fever? me yasa zaki damu da yawa hakan akan lamarin matar data riga ta shude cikin rayuwarmu?, muddin wani ,abu ya faru dake tabbas sai ta d'and'ana kudarta bayan wadda zata dandana din, ta gama cutatar mana da ahalinmu har abada in sha Allah " hannunsa ta riqe sosai tana kallonsa "Cool down hottie, am safe fa,nayi bacci ne da yawa sai ya sanya jikina yayi dumi sosai, but am fine fa" ta fada a shagwabe,iska ya furzar daga bakinsa "Alright,ta tsira" ya furta a hankali. Zafafabiyar "HUGUMA* •TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 69 Washegari ta zame jikinta daga nashi ta fita a duvet din ta barshi vana bacci ta shiga kitchen. Breakfast me kyau ta shirya musu gaba daya,harda wanda za'a kaiwa dr asibiti. Ta gama tsaf tana goge waien taji takunsa a hankali da qamshinsa me sanyin nan,ta waiwaya a nutse tana dubansa. Shima ita yake kalla da tattausan kallo ya garaso a hankali yana duban warmer's din data shirya. Da idanu ya tambayeta, saita saki murmushi tana dora yatsantsa saman lips dinta alamun yayi shuru. Hannu yasa ya fincikota jikinsa,ya riqe qugunta da kyau suna yiwa juna kallon kallo "Kin karya doka,kika kwantar dani ina bacci kika taso kina aiki, waye kika tambaya?" A nutse ta miga hannunta zuwa sumar dake kwance baqiqqirin qasan habarsa tana dan wasa da ita idanunta cikin nashi tana sakar masa wani kallo "A yimin afuwa hottie......but hidimar iyaye ba'a sanya wajen yinta" garamin murmushi ya saka yana jin qaunarta cikin ransa, darajarta da kimarta suna sake qaruwa, sai ya sake matso da ita jikinsa sosai yayi kissing nata a tausashe "Zanyi wanka sai mu fita dasu jibril na miga masa" langabe masa kai tayi a shagwabe "'Nifa?, zanje fa" hannu yasa ya lakace mata hanci "Duk sanda kike min magana kamar haka,sai na dinga ji kamar na tsayar da lokaci ya daina tafiya nayita kallonki kamar haka" hannunta ta sanya ta zagaye shi duk da bata iya ratsashi ba,rungumeshi tayi tana dora kanta saman girjinsa "Am all yours thank you for loving me you have Brightened up my life with your beautiful spirit and caring heart" kansa ya kwantar tsakiyar lallausan gashinta dake hargitse yana lumshe idanu, har cikin zuciyarsa yana tasirin saukar kalamanta,a hankali yace "I only regret one thing in our marriage... .. Zuciyarta tadan buga kadan,sai ta zame kanta a hankali ta dagashi tana kallonsa da fararen idanunta da suka bayyana fargaba Wata lallausar dariya ya saki, ya sunkuceta gaba daya ya azata saman kitchen cabinet, hannayensa ya zura ta gasan rigar baccinta,ya soma tafiya dasu a hankali cikin wani salo na tafiyat tsutsa, bai tsaya dasu ko ina ba sai da yakai tsakiyar bayan nata, ya sake matsowa da fuskarsa sosai, hucin numfashinsa yana sauka saman fuskarta tata "One thing i regret in our marriage... that i haven't met ¿ you sooner" murmushi ne ya qwace mata, sai ta karyar da kanta gefe,tsoro da fargabar da ya dasa mata a lafazinsa na farko ya zagwanye. Binta yayi da kallo yana jin gaba daya tana tayar da tsigar jikinsa,wani mahaukacin kyau murmushi yakeyi mata,inda da hali tabbas da ya hana mata yin murmushi a ko ina "Kinsan me?" Ya fada a hankali yana matso da bakinsa saitin kunnuwanta,abinda ya sanya tsigat jikinta zubawa sosai, taji yarrrr har tsakiyar kanta, kafin tayi controlling kan nata ya fara sauke mata kalaman da suka fara rikitata "I've tasted your lips in my dreams,and when i woke up, knew for sure what i wanted for breakfast" numfashinta taja da kyau jin kamar zai subuce mata, idanunta a lumshe, tana kunyar budesu yaga abinda ya cikasu "I need a big, hot steaming cup of you this morning....kin bani d....." Bai qarasa ba ya tsinci bakinsa dumu dumu cikin nata tana aika masa da salon kiss din da yafiso,bai wani tsaya bata lokaci ko daga qafa ba yayi mata kyakkyawar tarba suka soma rikita juna. Basu fahimci me suka aikata ba saida komai ya kammala,suka kalli juna cikin matsananciyar kunya murya qasa qasa tace dashi "A kitchen?" Girarsa duka biyun ya daga mata yana fidda murmushin da yake tabashi har can qasan zuciyarsa,saboda wani irin farinciki data bashi "And whe enjoyed it" sai suka saki siririyar dariya a tare. Hannu ya miga mata ya kuma sauketa a hankali daga saman cabinet din sannan ya rigeta,a nutse suke takawa zuwa bedroom din shi da ita, ya hada musu ruwan wanka bai tsaya shawara da ita ba ya sunkuceta sai bandakin. Suna gaban madubi yana busar mata da gashinta,wata sassanyar hira suke a madubin ta cikin qwayar idanuwansu ba tare da baki ya furta komai ba. Dan garamin tsaki yaja gain yadda aketa neman izinin shigowa hallway din nasu ta garamar na'uarar dake magale a bedrooms dinsu. Cumb din hannunsa ya anivya zaro abayarsa ya zura yana fadin "'Ina zuwa" ya juya a nutse ya fita. Murmushi ta saki tana satar kallonsa har ya fice din,ta maida idanunta ta kulle tana jin yadda soyayyarsa keyin yadda taga dama a zuciyarta yadda take kassara kowacce gaba ta jikinta. Wani irin sassanyan mutum ne da ya iya cusa zazzafar qaunarsa a zuciyar iyalinsa. Adadin yadda mu'amalar aure ta hadasu,adadin yadda yake sake ratsa zuciyarta da wata irin zazzafar soyayya,yasan yadda ake tafiyar da mace over and over, batasan yadda bakinta zai iya fasaltawa ba. Nadeeya ya gani a tsaye sai ya jefa mata harara cikin salon tuhuma da kuma tsare gida "Am sorry yaaya‚police ne suke nemanka" "Shine zakizo kiyita disturbing mutane?" Ya fada hankali kwance "Yi haquri" ta sake fada. Sai a lokacin yaga kamar akwai alamun tashin hankali kan fuskarta "Are you okay?" Kai ta gyada tana hadiye yawu da ayar,sai ya kewayeta kawai yana ficewa ta bio bayansa "Kibi ta daya qofan ki koma cikin gida" yace mata ganin akwai maza da vawa a wajen harda ma'aikatan gidan. Cikin nutsuwa da kamewarsa ya garasa gurin. Dukkansu sukayi saluting nasa saboda fuskar da basu zata ba suka gani. Babbansun ya matso ya miga masa hannnu sukayi musaba "'Sir......na shiga tantama da kokwanto, da gaske a nan din meenal ya'agoub aji take?" "Meenal?" Ya maimaita sunan cikin tantama "Oh,right eh nan ne" ya fadi bayan kuma ya tuna wace me sunan. Juyawa yayi kadan ya kalli yaransa sai ya karba wata takarda daga hannunsu ya migawa toufeeq yana cewa "Am sorru to inform you tayi commiting suicide,ta kashe kanta" "Subhanallah, subhanallah" toufeeq din ya furta yana maimaitawa tare da karbar takardar yana duba tabbacin gwaji ne na mutuwarta da kuma shaidar kashe kanta tayi din. "Zamuje tare ku sanya hannu sai mu baku gawarta" "To babu damuwa, bari na sanarwa da family na" "Zamuyi gaba sir,sai ka samemu a Murtala Muhammad specialist hospital" "Ba damuwa" waiwayawa yayi ya kira libril yace ya fiddo mota,ya juya cikin gidan da sassarfa Sassansu nadeeya ya wuce yana sallama ya samu fadeela zaune tana cin indomie, gefe ga cup data cika da madara, cartoon take kalla a mbc 3. Da mamaki yadan bita da kallo,wasa wasa ta kama abinci sosai tunda akayi aikin fiye da wanda takeci lokacin säahar. Murmushi ya wadata kan fuskarta,ta ture plate din tana migewa hadi da fadin "Good morning daddy" "'Bazan amsa ba, gaisuwarki tazo late" kai ta langabe "But daddy, banason zuwa na tada ku a bacci fa,nasan anty N a gajiye take sosai,tun kafin ayimin aiki bata bacci, kullum addu'a take kwana tana yimin, inason tayi bacci sosai yanzu don ta haifa min ganne masu garfi da zasu dinga taremin fada" a bisa dole murmushi ya kubce masa,yasan wanna sharrin surutun nadeeya ne, har ya fesa mata kenan, ita kuma bilhaqqi qanne takeso shi yasa take kiyayewa "Good girl" ya fada yana saluting nata da hannunsa. Sake gaidashi tayi ya amsa, ya tambayi nadeeya da baaba ramatu tace "Suna kitchen,abby ka duba abincin da suke bani don sunga anty N bata kusa" ta fada tana nuna masa abincin da baki. Murmushi ya sake subuce masa,gaba daya yarinyar kamar an sake bude bakinta ne da komai nata "'Ayyah,zamu kai gara wajen AUNTY N" "Eh dama na fada,nayi missing abincinta sosai, please daddy yau tayi mana dinner mana?" Kanta ya shafa "Nima navi missing abincinta angel, amma sai ta warke sosai zata dafa mana muci ko?" "Ni ko bata dafa min bama, indai zata kawomin qanne na 1 mu dinga wasa shikenan" dariya ta bashi duk da yanayin zucivarsa babu dadi amma sai da ya sake murmusawa "'In sha Allah, kiyita mata addu'a yadda tayi miki kema" "Zanyi daddy,i promise" "That's good my angel,yanzu jeki kiramin su" da gudu ta cilla tayi kitchen din cike da farinciki, tana wassafa yadda zata kula da nata gannen itama, zata yita bawa 'yan class dinsu labarin qannenta itama yadda kowa yake bata labarin nasa,dama ita kadaice bata da. Rudewa dukkansu sukayi, nadeeva na hawaye baaba ramatu tana salati "Relax please, banason SAHR taji yanzu saboda yanayin da take ciki, please take care with her" ya qarashe maganar yana kallon nadeeyan, saboda yasan itace sarkin raki. Kai ta jinjina ya juya yana fita daga sashen. Batasan me yake faruwa ba,taga dai ya shirya a gaggauce,yayi kissing hannunta yana cewa "Zanje na dawo,ki kwanta ki sake hutawa kafin anima na sake tara miki wata gajiyar,yanzun bana bugatar kiyi komai saidai ki bani kulawa, idan da hali ma bacci nakeso kiyi" kafada ta maqale a shagwabe "Kada ki damu,i will handle it with care and softness,it would not be harmful". Haka ya fita ya barta da tarin tunaninsa a kanta,murmushi kuma fal fuskarta. Ta gaji da zaman,don haka sai ta shirya ta gyara sashen tsaf sannan ta sake gyara jikinta ta fito,don tana sin ganin fadde dinta, tana kewarta. Hankalin maji yayi masifar tashi da jin labarin mutuwar haseena, ba kuma wai mutuwar ce abun tashin hankalin ba,hanyar da tabi wajen salwantar da rayuwarta. "Ka shaidawa mamanta ne?" Maji ta tambayi toufeeq "I think tana asibiti, nidai na gama nawa gawar tana asibiti maji". waiwayawa maji tayi ta dubi Dr jarma da aka gama rubutawa sallama "Abba,haqqij yi mata sutura yana wuyanku,saidai bansan ta yadda za'a gayawa fauziyya rasuwar ba tunda bata da lafiya itama" "Dole ta sani ai,ko don ta roqawa 'yarta gafara ko?" Ya fada yana sauka daga saman gadon hadi da duakan wayarsa. Toufeeq sajjad dr har da maji suka isa asibitin da hajiya qarama ke jinyar. "Dama muna shirin neman 'van uwanta mu sallameta ne,saboda babu me jinyarta, abinda ya hana mu bata sallama ma ba'a biyamu bill dinmu dake kanta ba" wata nurse ta fada cikin girmamawa sanda taga dr mahmud hadi da toufeeq,wanda kusan ba boyayyu bane kusan kowa yasan fuskarsu. "Sannan sir,kamar akwai abinda yake shirin taba qwaqwalwarta,akwai magana da yawa da takeson fada ma amma kuma ba'a iya jin abinda take fada sosai,a shawarce a fara ganin likitan qwaqwalwa kafin abin yayi nisa". Shikam toufeeq zame jikinsa yay yabar wajen,don baya jin sisinsa zai iya sanyawa wajen neman lafiyarta. Zafafabiyar "HUGUMA* •_TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 70 A haka aka kinkimeta sukayo gida da ita, duk da Dr jarma vaso kafewa akan ba za'a koma da ita cikinsu ba "Abba yayi gaskiya maji, ki barta kawai" toufeea ya fada cikin I don't care manner. Dubansu tayi duka su biyun "Inajin babu wani hukunci da kuka isa kuyi mata kamar wannan da Allah yayi mata,ba lafiya babu dukiya diyar da takevin fadi tashin tara komai da mallakar komai saboda ita ta kashe kanta da kanta, banda Allah wa ya isa ya hukuntata haka?, saboda haka ku barta taji da nata, kuci gaba da fatan ku bar sararin duniya lafiya,kada Allah ya jarabceku da son zukatanku har takai ku aikata abinda ta aikata din" wannan maganar ta sanyaya musu jiki dukkansu saidai har yanzu TOUFEEQ bayason koda kallon fuskarta,gashi ita din ta nace da kallonsa bakinta dake zubda miyau yanata motsi, da alama akwai maganganun da take fadi amma ba'a iya jin ma me take cewar. Abinda yayi gudu kusan shi ya faru,bayan isarsu gidan gain gawar haseena ya sanya hajiya garama tayita kwarara ihu,ihun da iya shi kadai ke fita ake iya jinsa, amma muddin magana zatayi komai baya fita. Wanann shi ya daga hankalin sãahar sosai, uwa uba mutuwar data tabbata haseenan tayi,ya sake saka mata tsoron Allah da kuma tsoron duniya, da gaske budurwar wawa ce, kuma babu mayaudariyar aba irin duniyar yanxun nan zata daura aure da kai,yanzun nan zata sakeka,waccae shekarar iwar haka hajiya qarama din nata tsara yadda wannan shekarar zata kasance mata cike da cikar burikanta da haskowa kanta tarin nasarori da kuma ci gaban rayuwa,amma a ayanzun sai gata a kanannade cikin keken guragu, ba gafa ba hannu babu baki,ba lafiyar ma dukanta,babu dukiya ba miji babu diya,lallai ba shakka babu abinda yafi aikata alkhairi dadi a rayuwa,KOWA YAYI NA GARI KANSA kamar yadda bahaushe yake fada, kuma hakan take. Ganin tana neman birkice masa sai va dauketa gaba daya ya kaita bristol ya kama royal suit kamar yadda ga saba sukayi zamansu a can. Katafaren gidan da yake kan ginawa ya tayar da qarasa ginin,cikin. sati guda komai ya kammala. Babu abinda suka dauke daga wancan tsohon gidan sai suturar jikinsu. Ana ya goben zasu tare ya kaita gida yace ta kwana wajen maama "Zaki zama full house wife, idan kika shiga MY KINGDOM ban miki alqawarin fita ko yaushe ba,ki kula da ni ki kula da abinda zaki haifa min for the rest of our lives shine burina". Ranar da zasu tare din dr iarma na zaune a parlor dinsa suna yin dinner tare maji na serving nasu ya kalleshi "'Diyarka kadai zaka dauka nima dauke tawa diyar zanyi" Dr jarma yace da toufeeq. Kansa ya daga yana duban maji ko zata shiga maganar sai yaga ta fuske, da suka hada ido sai ta kauda kai "Ai gaskiya ya gaya maka,ka sakata a gaba ba batun aure bayan ta gama isa munzali har tana shirin wucewa aurar da ita zamuyi muma" "'Kodai kunason ku shaqata ne maji?" Ya fada qasa qasa yadda Dr bazaiji ba. Spoon din hannunta ta jefa masa tana cewa "'Qaniyarka,me yasa ka maidani kakarka ne?" Dariya ya saki yana kaucewa "Afwa ni ba wani abu nake nufi bafa". "Bar dan nema, ka dauka tsufa mutuwa ce?" Dariyar da yake rigewa ya saki yana hada hannunsa guri daya "Ayimin afuwa,na tuba". Har qasan zuciyarsa yakejin rayuwarsa ta sauya, yana mugun jin dadi idan yazo yaga maji da Dr a tare guri guda suna hidimtawa juna da sunan miji da mata _(kowanne yaro a duniya bashi da burin da ya wuce wannan, dukkan yaran da uwayensu ke wani gida suna auren wani tabbas don basu da yadda zasuyi ne amma inda ace son ransu ne ko gaddara ta basu damar rubuta abinda zai wanzu a rayuwarsa,da zasu rubuta tabbatuwar iyayensu guri guda, babu abin alfahari irin ka tashi kaga mahaifiyarka tayi rayuwa kuma ta rasu cikin dakin auren mahaifinka, saidai idan ba yadda ka iya da yadda Allah ya tsara maka qaddararaka, yan uwana mata,mu qara haquri akan wanda muke dashi kan zamanmu gidan mazajenmu, MAZA)MATA a duk sanda rayuka suka baci, muka yanke shawarar rabuwa da junanmu,mu dinga saka tunanin makomar 'ya'yanmu akan gaba kafin komai,Allah ya zaunar damu lafiya ya gara mana haguri da mazajenmu, suma Allah ya qara musu haquri da juriyar zama damu)_ Sai data shiga gidan ta tabbatar gidan yaci sunansa MT JARMA KINGDOM,wani irin fasali da tsarin ginin gidan turawa akayi, kowanne sashe na gidan idan ka kalla zakasan cewa lallai da gaske gidan na masoya ne, an kumayi tanadin wanzar. da soyayya me dimbin yawa a gidan,da rayuwa me cike da ma'ana da sanyayar da zukata. Wata ravuwa da ko a mafarki dukkansu basu taba zaton akwaita a duniyar ma'aurata ba suka shiga shimfidawa cikin gidan, dukkansu kowa yasan irin bacin rai baqinciki da karayar zuciyar da ya samu,wanann ya qara musu qaimi wajen kula da juna matuqa da gaske. TOUFEEQ wani irin gold ne a cikin duhu,wanda sai me sa'a ce qwarai zata takashi. Tun asali namiji ne daya amsa sunan NAMIJI bawai muna maza ba, idan nace NAMIJI ba ina nufin a halitta kawai ba,a'ah, irin mazan da sukayi qaranci a yanzun, wanda yake buda hannayensa ya kuma bude kafadunsa don ya tallafe dukkan nauyi da bugatar iyalinsa,ya bata lokacinsa a kansu,ya nuna musu zallar madarar qauna da kulawa,yayi gyara cikin hikima da iya sarrafa harshe idan anyi laifi ya kuma bada uzuri me nisan gaske a garesu. Ya yarda da maganar annabi da yake fadin mu din an haliccemu daga gashin haqargari na, ko ayi haquri damu aji dadi damu a haka a karkacen da muke, ko kuma ace sai an migar damu, miqar damu kuma yana nufin karya mu,karyamu shine rabuwa damu. Gefan sãahar kuwa ko daya ciki bata bari va hanata bashi dukka wata kulawa data kamata ba,gasa da wata guda ta gama fahimtar halayya da dukka dabi'unsa wanda batakai ga fahimta din ba. Tayi kuka tayi kuka a sujjada har batasan iya adadi ba bayan data fahimci musayar alkhairin da ubangiji yayi mata,tayi sadaka me tarin yawa dukka tana godewa Allah da bai wofantar da wahalarta ba yayi mata kyakkyawar sakayyar da a nata ganin bata cancanci haka ba, girman rahama jin gai da kuma tausayin bayinsa ne yasa ya mallaka mata toufeeq din. Kamar yadda yake a tsarinta tun can baya,yanzun ma bata wani yarda ta dauki me aiki ba,tanason samun ladan gidanta da hannunta. Daga harabar gida garden na gida da sauran hidimomin gida akwai ma'aikatan da sukeyi acan waie ta cikin gida kuma baba ramatu suka taho da ita,' yar amanarsu,itake gyaran dakuna da bangaran säahar din yayin da säahar din ke rige da ragamar kula da hatta da cup din ruwan da toufeeq zai sha bata dorawa kowa ba. Yayi mitar ta dinga zama tana hutawa shi ya yafe amma tace sammm, saidai idan ya dawo ko yana gida shike tayata su kammala komai tare. Dalili na biyu da yasa bata dauka me aiki ba,tana ganin a yanzun fadeela ta fara tasawa,shekara takwas tana sanvata fara kovar wasu abubuwan, batason gata da dukiyar mahaifinta ya sanya ta tashi a SANGARTACCIYAR MACE. Yarinyar ita kanta qaunar ace vi abu kaza takevi.don haka ta taso da wani irin qwazo, idan ka ganta tare da sãahar baka isa duk qwaqwarka kace ba ita ta haifeta ba. Cikin hukuncin Allah cikinta ke girma cikin goshin lafiya,tun a sannan yaso ya kwashe iyalansa subar gasar saboda harkokin business dinsa amma maji tace bata varda ba girma takeyi vanzun tana da bugatar rayuwa cikin ahalinta wanda abaya bata samu wanna damar ba, uwa uba ma bata yarda ya daukar mata yarinya da 'yan jikokinta ba jirgi yana gantali dasu. Yadda tayi lafazin son zama cikin iyalin nata ya taba zuciyarsa qwarai, don haka ya haqura shima ya tattara tafiyar ya watsar, duk da yasan zamansa guri daya a nigeria bazaiyiwu ba,saboda yabar kasuwancinsa a wasu qasashen, don ma bashi da haufi ya hadu da directors 'yan amana,sannan kuma kusan komai dashi akeyi ta na'ura, koda meeting ne dashi akeyi ta conference call. *****Wani irin gawataccen daki ne da aka yiwa tsari 2) me kyau da wasu irin books shield na glass da wani irin garfe me haske da daukan idanu. An gawata dakin da nau'in kuieru biyu, sofas masu taushi da kuma lounge chairs da suka dace da paint curtains da carfet na dakin. Takardu ne masu tarin yawa a gabansa da yaketa signing tare da karanta rubutun jikin was daga ciki. Kana ganinsa zakasan he was so busy hankalinsa kuma yayi nisa sosai. A hankali aka turo qofar dakin,säahar ta bayyana cikin wasu silk nightgown farare tas in and top,gashinta me tsaho da sheqi yana daure a siririn band da baka ko rya ganinsa saboda cikar da gashin ya qarayi. Ta aje wani irin kyau idan ka dauke tulelen cikinta da take tallafe dashi saboda nauyin da yayi matan, fuskarta a tsuke take sosai, babu alamun walwala ko kadan a tattare da ita. Sam bai ankara da shigowarta ba sai sheshsheqar kukanta ya ji. Fatali yayi da takardun cinvarsa va mige da sauri yana dubanta,sai kuma ya fara takowa zuwa inda taja ta toge fuskarsa ciks da damuwa "Ya salam, ya isa cutie tell me me kuma ya faru?" Sake fashe masa tayi da kuka,abinda ya sake rikitashi gaba daya,ya kamo hannunta ya rige sosai cikin nasa ya fara janta ciki a tausashe amma saita cake "Ka sakeni tunda yanzun baka sona,har suna ma ka canzamin,saboda tsabar baka sona yanzu kake tsokanata da wani cutie,bayan fuskata duka ta kumbura, kyauna dama kakeso ba ni ba,yanzu kuma na zama mummuna ka daina yayi na" matugar juriya kadai yayi bai fashe da dariya ba, saboda yanzun nan cibi zai zama qari. Tunda cikinta ya fara nauyi ta zama mafadaciya,komai akayi mata ba'a kyauta mata ba,ba'ayi mata dai dai ba,ga dan banzan tsarguwa, ko kallonta ya cikayi sai tace muninta yake kalla "Wallahi kinji Allah kenan, inda zaki zauna a haka zanso hakan bayan kyan da kika qara har tacen wajen ma ko?, ba'a magana" kunyarta har yau tana nan, maganar tasa ta sanyata dauke kanta murmushi na shirin kubcemata, amma tsabar qwarewa a rigima saita fuske "Ban yarda ba, inda hakanne ai ba zaka barni ina jiranka ba,ni kadai almost one hour?" Wannan karon dai sai da dariyar ta qwace masa,yasa hannu ya juyo da fuskarta yana cewa "A'ah…ayimin afuwa,ashe duka wannan fushin abun ake nema?,aikam aiki dai ya gare mun samu babban aiki" ya fadi yana jin dadi qasan ransa. Shi kam ya daga mata gafa ne saboda cikin kwanaki ukun kamar yaga bata jin dadi sosai, tun ranar data dawo daga sunan afifa wadda ta haifa baby giri dinta qatuwa wadda taci sunan SHIFA(MAJI), suna kiranta da AHLAM, shi dai wannan ciki •) ya biyashi dari bisa dari. Ko taku daya bai bari ta garasa ba ya dauki abarsa ya wuce da ita fadarsa, yana tafe yana tsokanarta "You gain weight moonbeam" "Kaine ka jawomin" ta fada tana mintsininsa a tsakiyar qirji, tasan yana tsokanarta ne don yasan batason yace tayi nauyi. Yana alfahari da ita gwarai ta wannan fannin, duk hanyoyin faranta rai ta sansu. Idanunsa a lumshe yana tina irin farinciki da gamsuwar da take bashi yaji tadan tureshi kadan tana guna guni,kunne ya saka da kyau "He acts like he's the smallest thing in the world but he's freaking huge" dariva ce me garamin sauti ta subuce masa,ya daga fuskanshi yana kallon tata "Eheenn,wanann grumbling din bashi da ma'ana,kin fada ne don ki rama nace kin qara nauyi, after all ma sai da kika gama kwashe dadin?, kwadayayya?" Kukan kissa ta sakar masa tana dan kai masa duka, shi kuma ya bita da gwalo yana boye kansa cikin boobs dinta. Sai data gaji ta barshi jin tayi shuru sai yakai hannunsa ya shafi gefan fuskarta "What happened?" "Am hungry" ta fadi cikin salon ban tausayi. Tashi yayi sosai yadda zai iya ganin fuskarta,da gaske ta bashi tausayi, tana wahala da cikin sosal,bai sani ba ko haka kowacce mace keyi?, ameesha dai baiga bakan daga gareta ba "But you just eat. "Need something sweet,am craving" dariya ta bashi,sai yasa yatsusa yadan rufe rabin fuskarsa yana zuba mata ido "Uhunnn" ta fadi tana kallonsa itama. Da gaske ya fuskanci yau rigimar ce a kanta, don ledar data matsa yayi mata siyayya ma gata a yashe a gasa, da kanta tavi list din komai amma bataci komai din a ciki ba. Baison rigimar tayi tsaho, don haka yayi wuf ya tashi yana dagata "Go bath" "Noooo hottie" "Dole indai kinason maqulashe". Kumatunsa ta riqe da hannunta daya tana jaa "Having someone who can handle all your moods is such a blessing" hannun ya sunkuya yayi kissing yana murmushi. Zafafabiyar "HUGUMA* _TABARMAR KASHI* Book 02 Page 71 Tare suka shirya shi da ita, ta saka doguwar rigar abaya wanda yanzun sune suturarta saboda girman cikinta,shi kuma ya Sanya kaftan abaya sassauga suka fice. "Ina muka nufa?" "Pizza zanci" ta fada tana tande baki. Dole ta bashi dariya sosai "Wadan nan babies,wanne irin kwadayayya suka maida ke?" "Ask them" ta fada kawai tana nuna masa tsinin cikinta wayarta na hannunta tana qoqarin kunnata. Gurin saida pizza me kyau tsafta da inganci va kaita cikin nasarawa GRA "A nan fa zamuci" ta fada tana neman gurin zama "Oh god" ya fada a hankali, mamaki yana sake kasheki, da gaske ake cewa dole ka sake yin karatu na musamman akan mace idan tana da juna biyu, wawayen maza sai suyita cusgunawa matansu a irin wanan yanayin su dauka kome iskanci ke sawa suyi. Tunda yake da ita bai-taba gani ta zauna cin abinci cikin mutane da yawa bama bare waje sai yanzu. Hakanan yaja tasa kujerar shima ya ) zauna,ya jira waitress ya bata order. Dukan pizza din ya tura mata,yana kallon yadda take ci hannu baka hannu qwarya ..Hmmm. ...i love you" "Baby iam finished" "Alright" ya fadi yana miqewa "Moha…...i wanna discuss something with you please mana" ta fadi tana narke murya tare da tara hawaye a idanunta. Tare suka waiwaya suka kalleta shi da sãahar din, kasa ci gaba da kallonta tayi saboda wani irin kallo da taga tana jifan toufeeq din dashi, ta dauke kanta gefe tana gogarin hadiye wani mugun kishi da ya taso mata, bata taba zaton tana da kishi irin wannan ba sai yanzu. Mamakin zallar garfin hali ko gegashewar zuciya zaice irin ta ameesha ke kai kawo a ran toufeeq, bai taba zaton har gaban abada zata iya tararsa da zancan ban haguri bama bare batun ya koma sonta har akai ga zancan ta koma tana amsa sunan MATARSA. ransa yaji wani wani irin baci, duk sansa ya kalli fuskarta sai va tuna zunubinta,sai yaga komai muraran shimfide saman fuskarta muraran kamar a lokacin kunnuwanta suke jive masa abinda yaji din. Karo na biyu säahar ta gaza jurar kallon da tayi imani har yanzu ameesha na jinfan toufeeq din nata dashi,sai ta waiyawa tana mata wani qasgantaccen kallo "Da kamun kai da cikakkiyar nutsuwa akasan diya mace, bin d'a namiji ba nata bane, ki tagaita kallonki a kansa wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa he's mine ever and ever" Kalaman sun taba ameesha sosai, dole ta waiwayo ta zubawa säahar idanu,kallon fuskar säahar din taketa gudun yi din batasan me yasa a duk sanda ta kalleta ba sai taji kamar ita nata ajin baiki ba, duk sanda ta dubeta sai taji kamar har abada toufeeq bazai iva sake kallon kowacce diya mace yaji ta burgeshi ba, duk sanda ta kalleta tana jin cewa tsananin rabo da kuma tausayi ya mallaka mata toufeeq a baya,duk sanda ta kalli qualities din da sãahar din ta hada sai taji kamar ta rasa toufeeq har abada,mafi munin tunin da batason tunashi wanann ne kuma ya sanya taqi giving up,wata yudararriyar zuciyar tana gaya maya cewa ZAKIYI NASARA,SHI ME TAUSAYI NE. Taku biyu yayi ya kamota cikin jikinsa qasan ransa yanajin farinciki yana ratsashi, har yanzun classy säahar din nan tasa tana nan babu abinda ya canzata,me tsananin kamun kai da jin takaicin yadda mata da yawa suka zama was marasa aji da sanin ciwon kansu "Yes‚iam your's,lam all yours,let's go" ya fadi yana dauka mata wayarta tana jingine a jikinsa suna takawa a nutse. Zallar kishin da ya gani cikin idanunta bai taba ganin irinsa ba kaman yau,mota ya bude mata ta shiga,ya kunna mata Ac ya kuma daura mata seatbelt ya dage dukkan glasses din "Ina zuwa, kada ki fito" ya fada yana rufe mata qofofin sannnan ya juya yana barin wajen. Tanason tace masa ina zaije? yazo kawai su tafi amma ta kasa,minti daya biyu har biyar shuru, take zucivarta ta fara raya mata qila ma ya shanya ne kawai vana wajen tsohuwar matarsa suna soyewa. Wannan tunanin ya kumbura zuciyarta,sai kawai ta fashe da kuka,take mararta tayi wani mugun motsawa da matsanancin civo. Ransa fes yake dawowa ga motar,ya tabbatar yau vau kawo garshen case din ameesha,yayi imani daga rana irin ta yau ba zata sake marmarin hada hanya da shi ba indai da zuciya a qirjinta. Zasu biya su dauko fadeela da yanzun maji keson qwaceta itama, tuntuni yakeson ta dawo gida säahar ke hanashi daukota "Zaka iya kallon idon maji kace kazo daukar 'yarka?" "B wani madam, kema fa nasan kaara kawai kikey" murmushi kadai takeyi bata taba yarda ta amsashi ba. Yana bude motar sautin kukanta ya sauka a kunnensa "Subhanallah" ya fadi da sauri yana dagota saboda vadda ta zauna din ya tabbatar ta takure da yawa *Ka daina tabani, marata kamar zata tsinke,babu dadi, ka koma wajen tsohuwar matarka ka gyaleni naii da ciwona" bai sake ce mata komai ba sai kawai ya tayar da motar, cikin wani mugun speed ya fice da motar daga harabar asibitin. Kafin sukai asibitin ciwon ya sake tsananta. Luckily suka tarar da Dr raheema na shirin fita daga duty, dubawar farko taga haihuwa ce, kuma gadan gadan tazo don takai 4cm. Ya rude gaba daya saboda yadda yaga tana juyi a tana riqe komai da qarfinta na gaske sai ya daga masa hankali. Ya rasa waye zaima fara kira?,sai kawai ya kira maji. Hankalinta yadan daga, saboda burinta a duniya na garshe taga tulin jikoki daga jikin diyoyinta guda biyu,tunda ita Allah bai gaddareta da samun tarin 'ya'ya masu yawa ba, ta daure zuciyarta cikin nutsuwa tace "Ma sha Allah, Allah ya raba lafiya,Kun dauko kayan haihuwar ne?" "Daga gurin pizza nagudar ta tashi" "Ashsha wanne irin sakarci ne haka Muhammad? ka dinga yawo ya yarinyar mutane da tsohon ciki?,waye yace maka ana fita anyhow da tsohon ciki?" Kai kawai ya girgizawa,maji ba zata fahimta,yanzun inda bai fito da ita ba da yanzun tana gida suna dambarwa "Ka yiwa baaba ramatu magana,gani nan isowa nima" katse wayar yayi kawai ya kira baaba ramatu din. Maama maji ta kira, amma saboda kara irin tata,duk kuwa da cewa säahar din auta ce, autar ma da ake fatan ganin abinda zata haifa amma cikin alkunya tace "Haba maji, kina gurin ai ba sai nazo ba" sosai maii keiin dadin yadda dr girema da maama ke bata girma da damqa mata säahar halak malak, saidai duk da haka ta roqi tazo din a haka suka rabu. Cikin abinda bai wuce mintuna talatin ba sai gasu a asibitin. Maji, anty farheen, anty sumaira, raihanatu wadda tazo musu hutu ne(cousin din adam da su dr girema suka turata karatu,bayan dawowarta sun laluba ainihin dangin mahaifinta sun maidata hannunsu, sun kuma yi mata kaykkyawan rigo,sun barwa momee itane dama saboda ta dage zata rigeta da amana, suka barta suna ganin kamar 'yar 'yaruwarta ce ba zata cutar da ita ba yanzun haka shirin bikinta akeyi) sai fadeela data kasa ta tsare itakam vau zatayi 'yan ganne. Kwatsam saiga afifa ita dake da danyen jego ta saka sajjad din a gaba sai da suka taho. Sosai maji ta dinga fada,tace ya dauketa su koma amma ya bawa majin haquri, tayi algawarin bestie dinta tana sauka zasu koma,tunda ance takai kusan 7cm ma. Yadda ta marairaice yasa ta bawa maji tausayi,sai ta qyaleta kawai suka zauna kowa yana fatan samun labari me dadi. Oga toufeeq kuwa basusan ina ya shiga bama,don basu sake ganin fuskarsa ba ma. • Zafafabiyar "HUGUMA* •TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 72 Awa daya da wasu mintuna daya daga cikin nurses din dake labour room din suka fito. "Hajiya d'iyarku ta sauka, amma bazan fadi abinda aka samu ba sai an bani goron albishir" ta fada tana murmushi Caaa sukayo mata,har abun ya bata dariya yadda taga suna zumudi. Tun kafin maji taji abinda aka samu ta balle jakarta ta fidda rafas na 'yan 100 sabbi kar ta migawa nurse din "Sauka lafiyar ma da kikace tayi ya wadatar,ga goron albishir dinki" fuskarta ce ta fadada sosai da fara'a tana juya kudin,kafin ta sake cewa komai afifa ta bude tata iakar ta ciro 'van dari biyar biyar ta damqa mata "Kun samu 'yan samari mazaje" nurse din tayi saurin fada tana rige kudin cikin farincikin tagomashin da ta samu a yau din. Baaba ramatu ce ta rangada guda cikin tsantsar farinciki "'Ma sha Allah,alhamdulillah" ta rufe da fadin hakan. Cikin ganganin lokaci gurin ya kaure da hayaniyar farinciki. Sai sannan aka fara cigiyar toufeeq. Murmushi.Sajjad ya saki "Oga fa inajin yana masallaci, bari na duboshi" ya fadi yana miqewa ya fice daga gurin. Sanda sajjad din ya shigo yana zaman tahiya na garshe. Ya zauna daga gefansa har ya sallame, cikin fargaba ya waiwayo yana dubansa, amma murmushin da ya gani saman fuskar sajjad din ya sassauta tsoronsa "'Yallabai anata qiyamullaili ko? sai kazo to ta babies sun iso” "Really?" Ya fada yana fidda ido "Ahaf, kai dai ka tanadi goron albishir dina" ya fada yana migewa. Ai kafin sajjad yakai bakin qofa har ya riskeshi ya ma wuceshi. Cikin wata irin sassarfa yake takawa,wani farinciki da karsashi suna ratsashi. Duka basu a veranda din, sai hayaniyar su da yake jiyowa daga dakin hutu. A nurse ya bude gofar dakin, tashin farko idanunsa suka sauka kan fuskarta. Tana zaune sosai abinta saman gadon tana kurbar tea me zafi da kauri, sam ba zakace itace tasha wannan gwagwarmayar ba. Wani irin sassanyan farinciki ne yake ratsa kowacce gaba ta jikinta, tun daga ainihin zuciyarta har zuwa kan fuskarta. A sace take kallon yaran, tana tasbihu ga ubangijin da ya maidata vara biyun data barar bayan ya maida mata su sai ya sauya musu da nagartaccen uba na gwarai,wanda zasuyi alfahari da fitowa ta tsatsonsa. Komai na duniya idan ubangiji yayi akwai hikima a ciki, haka siddan baya hukunta komai ba tare da dalili ba. A sannan taji babu dadi matuga game da rasa cikinta har taji kamar duk duniya ita daya ke cikin qunci da takurar zuciya,ashe duka ubangiji ya hukunta hakan ne saboda tanadin sauyi mafi alkhairin da yayi mata. Qamshinsa shine ya fara janye hankalinta,duk da jama'ar dake dakin amma hakan bai hanata shanshano shi ba. Daga kai tayi, idanunsu suka gauraya da na juna,sai ya lumshe mata nasa idanun yana sakar mata wani tattausan murmushi gami da hada hannunsa yay! mata jiniina. Kai ta sunkuyar tana jin nauyinsa data tuna abinda ya faru awannin dazu,sai shima ya kau da kan nashi ya fara takowa cikin dakin bakinsa dauke da sallama. Hankali kuma sai yayo kansa,kowa yana qoqarin masa barka yana amshewa yau dai duk yadda yakai ga turbune fuska lafiyayyen murmushin nan nasa yaqi boyuwa,a haka har ya qarasa gaban gadonta. Kuiera nadeeya ta bashi, sai ya jawota gaban gadon ya dora gafarsa kawai akai, fili yake da bugata su bashi,saboda kyakkyawar runguma ce yake gain tafi dacewa da ita. Idanunsa cikin nata yana jin kamar zasu narke su zama abu guda. Cikin hikimar manya maji da baaba ramatu suka mige zasu fice, abinda ya sanya nadeeya fadeela anty farheen da anty samreen suma bin bayansu. Afifa ce dake cikin babban mayafi tana baiwa baby nono ita da sajjad basu fita din ba. A gefansu nadeeya ta jere yaran tana cewa "Maji din ta fita ai, saiki sake ki qare wa kayanki kallo antyN" ta fadi cikin dariyar tokana tana yin gofa da sauri gudun kada toufeeq din yakai masga. Hannunsa ya mige ya rige tafin hannunta cikin nashi yana ci gaba da yi mata wannan tattausan kallon "Yanzu Madam kishi kadai dama ya isa tayar da naquda har a haihu?" Ya fadi cikin salon tsokana kadan. Kai ta langabe tana kallonsa tana kuma satar kallon afifa,ta tabbatar idan afifa taji ta shiga uku da tsokana. Murmushi ya sake mata yana kanne mata ido d'aya. "Idan nace sannunki Allah yayi miki albarka batayi kadan ba?" Kai ta gyada cikin murmushi tana kallonsa itama "Ida nace na gode qwarai, Allah ya sanya mahaifanki cikin aljanna madaukakiya shima baiyi kadan ba?" Nan ma kai ta jinjina tana murmushi zuciyarta cike fal da mahaukaciyar soyayyarsa,sai ta motsa bakinta a hankali itama "Dukkan wadannan kalmomi naka masu tarin tsada da daraja ne" "Kamar vadda kike da tsada da darajar da bansan adadinta ba a idanuna, bude idanunki mu kalli tsarabar da kika kawomin a tare" ya fadi yana miga hannunsa cikin takatsantsan da kulawa ya soma bude fuskokin varan "Yes!, ma sha Allah, Allah banyi wahalar banza ba" ya fadi kansa tsaye yana ma mantawa dasu sajjad dake dakin. Da sauri saahar ta rufe bakinta saboda kunya,sai sajjad din ya tattara towel din ahlam yana cewa "Oya let's go, muje ki garasa bata ko cikin mota ne" ai da gudun tsiya afifan ta rungume diyarta suna ficewa kada ayi barin zance a gabanta "Ai da kunyi zamanku" toufeeq ya fadiwa sajjad cikin gatse sai sajjad din ya gyalgyale da dariya baiko waiwayo ba "Bestienkin nan da sajjad original 'yan sanya ido ne" yayi maganar sanda ya Sanya hannu yana gogarin daukar babyn ya zauna a gurin "Ko yaushe gana fadi min muna basu mamaki, basu taba tsammanin soyayya zatayi mana mummunan kamu har haka ba" "Sai gashi tayi mana kamu me kyau harda result" ya furta yana sake bude fuskar dayan baby din, suna nannade cikin wasu lausasan shawl farare gal masu ratsin blue a jiki Har wani lumshe ido yakeyi sanda yake kallon fuskar varan "Na yarda ni din jarumi ne, duka vara na ahalina suke daukowa,kiyi haquri ina miki fatan nasara a gaba" kukan shagwaba ta sakar masa, sai ya saki dariya sosai kaman ba MUHAMMAD TAUFEEQ JARMA ba "Eh, next time ina expecting baby girls twins, zan tayaki addu'ar samun masu kama dake, don nima ina kwadayin* nayita kallon kyakkyawar fuskar nan ta cika kowacce kusurwa ta gida na" sai ya sunkuya a tausashe yayi U kissing dinsu su duka sannan ya juya kunnuwansu yayi musu khuduba “Muhammad da Mahmud" ya fadi yana kallonta. Farinciki ne sosar ya ratsata, tabbas taji dadin wannan zabin nasa,dama tun asali sunaye ne masu asali "Allah ya raya dr girema da dr jarma" ta furta a hankali Ameen,let me hug you please ko zan samu sassaucin abinda nakeli na farinciki a zuciyata" ba musu ta bude masa hannayenta,yayi mata kyakkyawar runguma yana sauke ajiyar zuciya idanunsa akan yaran. Awanni shida kacal aka rubuta mata sallama cikin aminci da goshin lafiya. Tunda yaji maji na zancan tafiya da ita ta kula da ita ya kasa ya tsare. Koda aka rubuta sallamar sai daya kwashesu ya kaisu motarsa sannan ya gaya musu batun sallamar, kafin maji ta ankara tuni motarsa ta dauki hanyar gidansa, don ko kadan bazai iva jumurin rashinsu a kusa ba. Yanzunne yakejin kansa a cikakken magidanci,wanda ya hada dukkan wata falala da farinciki na rayuwa. Hakanan maji ta gama salatinta ta haqura "Muhammad ya maidani kakarsa Allah da gaske" haka tayiya mita tana fada. Nadeeya na gefe tana dariya "Maji, shifa yaa moha har yanzun farin shiga ne,sai yanzu yasan meye dadin family ki bar masa matarsa da yaransa" "Allah baiko isa ba, dole na gyara diyata, idan yaso su garata,amma dai yara shima yasan bashi kadai ke dasu ba" "Ah lallai maji akwai kallo kenan,nan gaba kwashesu zakiyi" "Zasu haifa wasu in sha Allah" ta fadi, don har ga Allah a son ranta ma su koma gidanta da zama. Wani irin alheri albarka da farinjini yaran sukazo dashi,yadda gidan yake cika kullum saika dauka suna akeyi kullum. Saahar sai yanzu ta sake amanna da gasken gaske 'ya'ya rahama ne,da gaske haihuwa wata falala da baiwa ce daga ubangiji,wani irin budi da alkhairi ita kanta take gani tako ina. Gadan gadan ake shirya I katafaren suna, duk wani taro na biki da basuyi ba toufeeg ya shirya fansheshi a ranar sunan,ya tsara walima ta musamman shi da abokansa, haka bangaren mata da zasuyi nasu cikin yalwatacciyar harabar gidan. Zafafabiyar "HUGUMA* *_TABARMAR KASHI* Book 02 Page 73 Qarfe takwas na dare ta fito daga wanka,wanka ne sosai na jego akeyi mata da dalbejiya,jego takeyi na gaske wanda aka sani a qasar hausa,qanwar maama da maji suka tsaya kan hakan, tuwo kunun gyada wankan darbejiya da gasashen nama bata wasa dashi. Yaran duka na nannade cikin was kayan babies masu taushi da daukan idanu 'yan qasan turkey,gaba daya ubansu ya maidasu kamar shi, kullum shigar fararen kayan babies suke,komai nasu fari qal sai ratsin blue wani lokaci. Afifa da nadeeya ne cikin bedroom din nata, fararen hannuwan nan nata da gafarta sunsha jan lallen suna har bayan hannunta,wani irin dan ubansun lalle kamar ka daye shi daga fatarta, kanta ma yasha gyara na musamman sai gyallin da gamshi yake fiddawa,ta cika ta sake yin dam ta zama 'yar duma duma,don da gasken gaske take gyaran kanta. Tana gogarin shirya kanta nadeeya tace "Kada na manta na shiga uku,yaa moha ya kira yace ki sameshi a sassansa, kada ki manta ki tafi masa da Asad(Muhammad) da as'ad(Mahmud)" amsa mata tayi da to,sannan ta waiwaya a nutse ta fara gyara jikinta. Cikin minti talatin kacal ta fito cikin lallausan material baby pink color da kalae sea blue a jikinsa,tayi sassanyan kyan nan nata da ya cakude da kyan jego,tayi fresh sosai, jikinta sai qamshin turarenta yake fitarwa. Baki afifa ta saki tana kallonta sanda ta dauki asad da as'ad "Anya kuwa? ,kada fa kije ki ballowa kanki ruwa" ta fadi tana dubanta. "Ruwa wanne iri?" Gyara zamanta afifa tayi "To don Allah kina jego inake ina buga irin wannan kwalliyar?" Harara säahar ta sakar mata "Kefa kin cika sharri, har yanzu bakisan an girma ba? ina kikaga nayi kwalliya a nan?" Tabo nadeeya daketa danne danne a wayaa afifa tayi "Sister nadiya tayani gani, don Allah ko ke bata dauki idanunki ba bare me gida?" Kame kanta nadeeya tayi tana danne dariyarta "Anty afifa,na rabaki da shiga sha'anin yaa mohaa da ,anty N,wallahi lamarin yafi qarfina, kame kaina nakeyi kafin naji ya moha ya kirani da munafuka" saita mayar da kanta kan wayar ta tana murmushi qasa qasa "Kanku akeii" säahar ta fada tana rungume yaran ta fice. dasu "Su sãahar dadi miji" afifa ta fadi cikin dan daga muryar duk dai cikin salon tsokana. A tausashe tayi sallama sassan nasa. Ya daga kansa daga zaunen da yake, sai ya ajjiye duk abinda yakeyi cikin lallausan murmushinsa ya taso yana takowa zuwa gareta idanunshi a kansu. Sanye da wasu pyjama ruwan sararin samaniya. Har ya qarasa gareta idanunsa suna karakaina a kanta,yana jin wata qaunar ahalin nasa tana gewayeshi. Hannu ya miga ya shafi gefan fuskarta cikin murmushi idanunsa cikin nata,sai ya miqa hannu yana karbar asad "Barka da zuwa giwa ta" ya furta cike da wani irin launin soyyaya da ya haifar da murmushi me qayatarwa saman fuskarta "Barka kadai aljanna ta" itama ta maida masa tana juya qwayar idanunta a kansa. A nutse ya juya yana shiga ciki vana fadin "Bari nayi hanzarin matsawa, those beautiful eyes.. Sai bai garasa ba ya saki murmushin da sai da ya bata dariya. Da d'aya da d'aya ya kwantar da asad da as'ad,a nutse ya waiwayo yana kallonta, har yanzu wannan murmushin bai bace a fuskarsa ba. Hannunsa ya sanya ya riqe nata hannun yana murzawa da vatsuntsa a hankali, idanunsa na biye da kowanne zane na jan lallen hannunta da yayi masifar daukar hankalinsa "This henna..." Shuru ya sakeyi yana cije lip's dinsa. Sai kuma ya daga kansa yana kallonta "It's been a long day,i need one of those tight hug" zame hannuwanta tayi, taja baya a nutse, ta buda masa dukkan hannuwanta. A hankali ya sake matsowa gabanta,ya buda shima masa hannayen ya cusasu ta bayanta ya shige jikinta sosai yana kwantar da kansa saman kafadarta ita kuma ta maida hannuwan nata ta lullubeshi tsam. Duk da bata iya ratsashi ba amma wani irin nutsuwa yakeji tana saukar masa,yayi imani da gaske ne babu abinda yakai mace ta gari bayar da nutsuwa da kwanciyar hankalin mazaje. "Your touch and your kisses are my weakness" ya furta dai dai saitin kunnenta, abinda ya sanya tsigar jikinta tashi. Ta sani yayi missing kiss ne,saboda tasan yana daya daga cikin abinda yakeso yake kuma rage masa zafi. Dan ja baya tayi kadan,abinda ya basu damar ganin fuskar juna sosai "Please stop being cute,it makes me want cuddle with you forever" ya garasa fada yana cije lip's dinsa. Hannu tasa ta dan ja kumatunsa tana murmushi "I can't taste my lips, could you do it for me?" Rigota yayi sosai cikin jikinsa vana murmushi "Thanks for this beautiful opportunity" bai sake qara koda second biyu ba ya hade bakunansu waje daya. Hungrily yake kissing nata in and out na bakinta,yanaji cikin jikinsa yayi kewarta sosai. Duk yadda yaji vanason ya wuce ga'ida amma dole ya yiwa kansa birki saboda yasan yanayin da take ciki,ya maida jikinsa ga bango yana maida numfashi, kusan minti biyar sannan ya budesu a hankali. Hannu ya miga mata "Zo ki gani" ya fada da dakusashiyar murya. A nutse ta tako ta iso gareshi,sai yaja hannunta a nutse suka zauna saman lallausan carfet din dake zagaye da tsakiyar dakin. Wata kyakkyawar jaka ya jawo ya bude,ya fara ciro abubuwan da suke ciki. Set ne na gold dan kunne sarga da abun hannu da zobe, muqullin sabuwar dalleliyar mota qirar BMW,sai wasu takardu dake buge da sunanta a sama. Duka ya tattara ya miga mata "'Bansan da wanne abu zan saka miki ba,bansan meye zan mallaka miki da zai tabbatar da godiyata da jin dadina akan abubuwan da kika yiwa rayuwata ba, inda ana bayar da aljanna tun a duniya lallai da na jima da mallaka miki ita,na baki wannan ne don na nuna kadan daga cikin jin dadin abinda kikayimin,bawai don na biyaki ba" gasa tayi da kanta tana jin wani sassanyan abu yana ratsata tana duban takardun dake gabanta. A duniya babu abinda yafi tsarkin zuciya dadi a lokacin da adam yake dukkan qoqarinsa don gain ya rabata da abinda ta mallaka da guminta qwanjinta da dukka nemanta.....sai-gashi Allah ya aiko mata da wanda ya sadaukar mata da dukiyarsa saboda farincikinta, cikin girmamawa da ) mutuntawa. Adam ya kwashe takardun filayenta sai gashi yau an mallaka mata estate guda, ta mallakawa adam bangles dinta don tsantsar sadaukarwa da soyayya da zuciyar daya.....ya ha'inceta akan hakan,sai gashi yau ta mallaki sarga bangle's da zobba da tasan cewa kudinsu ya ninka abinda ta sadaukarwa da adam. Adam yaso tattare kudadenta ya gudu,sai gashi ta mallaki motar da ta ninka ninkin baninkin abinda ta tara din,me zata cewa ubangiji banda addu'ar qwarai?, tabi toufeeq tsananin biyayya kamar yadda d'a zaibi uwarsa?. Hawayen da take zubarwa yaja hankalinsa,ya jawota jikinsa sosai vana shafa bayanta a hankali "Kada kice komai,all i want is to stay with me forever" gangameshi tayi tana matse ragowar hawayen idanunta tana jin wata qauna me zafi tana Huda qirjinta,a duniya a yanzu batajin akwai wata rayuwa tata da zata iya yiwuwa babu toufeeq. Zafafabiyar *HUGU MA* _TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 74 *_BAYAN SHEKARU UKU_* A nutse take takawa cikin mansion house din mallakin DR MAHMUD JARMA wanda ko ina kai kawo ne na jama'a,kaikawon da duba daya zai tabbatar maka da hidima akeyi, hidima irin ta biki. A nutse MAAMIN SÄAHAR ke takawa cikin dogom corridor din dake qunshe da kebantattun dakin baccin maji,gurin da amintattunta kadai ke ratsashi, kamar saahar nadeeya da afifa da a yanzun ta zama kamar diyar cikinta. Dakakkiyar shadda 'yar mali ce a jikinta Onion color da yarfin baqi da kima off white, dinkin tea boubou wadda yayi matuqar tafiya da tsari da qirar jikinta. MRS MUHAMMAD TOUFEEQ JARMA, KHADIJA MUHAMMAD GIREMA, babbar mace hakima da Allah ya huwacewa baiwa masu tarin yawa. Tana sabe da Mahmud as'ad dake sanye da wata suit ta yara me azabar kyau da daukan idanu,kyakkyawan fine boy wanda kamanninsa ke sake bayyana da babansa shi da dan uwar tagwaitakarsa,kamar toufeeq yayi kaki ya ajiye,bacci yakeyi lakadan a kafadarta,duk da yadda yaketa doki da zakwadin tafiya dinner din SISTER NADEEYA kamar yadda suma suka tashi suna kiranta. Wani irin sabo sukayi qwarai da ita,suna daukarta babbar abokiyarsu da suke mugun sakewa da ita. Cikin shekara ukun kacal khadija Muhammad girema ta sauya gaba daya,ta zama wata hakimar mace da idan ka kalleta sai ka sake son ka sake dubanta a karo na biyu,iya 'ya'ya mata kawai kishin kyau da ajin da take dashi sukeyi. Wannan ya sanya Muhammad toufeeq kishinta sosai da son killaceta hadi da kaffa kaffa da ita,domin ita din rayuwarsa ce kuma mahadin ruhinsa. Daya daga cikin gofofin ta murda ta bude ta shiga bakinta dauke da sallama. Qamshi da sanyin na 'urar sanyaya daki ne abu na farko da zai fara buso maka. Maji wadda ke a zaune saman carfet din dakin ta amsa. Tana sanye da wata light army green super Holland ta ainihi,fararen hannayenta da qafafunta sun sha jan lalle, ainihin qabilarta da dangantakarta da jinin labarabawa ya fita zammm,gashinta da har yanzu bai surka da furfura ba ya fito ta qasan dankwalin atamfarta. 'A'ah yayar amarya baki tafi ba dama?" Maji ta tambayeta tana miqa hannu zata karbi as'ad. Bata jin nauyin yaran ko kadan,duk da cewa jikin kakansu sukayo Dr jarma,suna da qiba madaidaiciya da cikar zati "Ban tafi ba maji,na dai tsaya naga tafiyar kowa" * "Kedai sannunki, Allah ubangiji yayi miki albarka" "Ameen ya Allah maji" ta amsa a sanyaye tana qogarin fidda murmushi. Sai data gyara zaman as'ad a jikin maji sannan ta mige ta gyara wuyan rigarta,ta miqa hannu tana daukan mayafinta mahadin kayan jikinta ta yafa "Zamu wuce maji" "Ke da waye zaku tafi?" "Yusuf ne zai kaini a motata" "To Allah ya tsare saikun dawo". Ta amsa da amin tana juyawa maji din kuma ta bita da kallo. Har takai bakin gofa maji ta kirata,sai ta dawo ta samu gabanta ta zauna "'Amma me yake damunki maami?" Shuru tayi tambayar maji tana taba zuciyarta,a sanyaye tace "Ba komai" shuru itama majin ta danvi, ta sani dole ko tsakanin harshe da haqori ma ana sabawa bare miji da mata. To amma tsahon shekarun aurensun nan, ko sau daya daga ita har toufeeq din babu wanda ya taba kawo mata qarar dan uwansa, batason ta cika zurafaf tambaya don tasan a yadda halaye da dab'un sãahar din suke na zurfin ciki ba zata gaya mata komai ba,bata dai jin dadin yadda take gain damuwa saman fuskarta, tun daga shekaran jiya da suka taho biki gidan kawo yau "Shikenan, Allah ya rufa asiri, amma ki rage sanyawa ranki damuwa ko don abinda yake jikinki" daga kai säahar tayi da sauri tana duban maji kamar me neman garin bayani. Maji din tasan hakan zata faru saita dauke kai, alamu sun nuna mata sãahar din batasan da zaman cikin ba,shi yasa tayi mata jirwaye mai kama da wanka. "Tashi kije, Allah ya tsare, ko ba'a tashi ba ki sanya yusuf din ya dawo dake kinsan halin Muhammad" "'In sha Allah" ta fada tana migewa. Gidan duk an yoye an tafi dinner din nadeeya da mijinta Nader,a hankali maganar maji take dawo mata a kai "Abinda yake jikina kuma?,maji na nufin wani cikinne dani?" Ta yiwa kanta tambayar dai dai sanda ta iso gaban motarta. Yusuf dan qanwar maji ne da sukazo biki daga Algeria, matashin saurayi ne da duka duka bai wuce shekara goma sha tara ba,amma yana da hankali sosai kirki da kuma son jama'a. Yana matugar son asad da as'ad,duk sanda yazo Nigeria baya rabo da yaran. Hannunta ta sanya ta shafi cikin nata tana mamakin ace juna biyu ne da ita, kuma har ana iya gani amma ita bata ankara ba?. Shuru ta sakeyi tana wani tunani, kwanakin nan tana danjin motsi a mararta,amma saboda ba cikin nutsuwarta take sosai ba bata ma baiwa ranta komai ba. "Yaaya another half zaiji?" Ta yiwa kanta tambayar,sal kuma wani abu ya ratsa zuciyarta. Wanne toufeeq din?, toufeeq din da suke tafka rigima yau kusan sati guda kenan?, ko zuwanta bikinma ta taho ne da yawun maii kawai. Kanta ta kwantar tana dubam fuskar wayarta,tunda suka taho din ko sau daya bai nemeta ko ya kirata ba,yaransa ma a wayar fadeela suke gaisawa kamar baya qasar, bayan kuma yana nan "Qila ma yana can suna waya da Hamdiyya" zuciyarta ta raya mata. Ido ta runtse tana jin zafin iya tuna hakan da tayi,cikin ranta tana kiran sunayen Allah hadi da tuna maganganun da ya furta mata ranar da zata taho "Kije abinki, ban hanaki ba, kome kikayi dai daine,tunda kin gama da zuciyata,kin kuma san soyayyar da nake miki,amma wallahi na gama yarda mace tayi amfani da soyayyar da nake mata ta wahalar da rayuwata, akwai masu sona dake da yawan gaske, zan qara aure na ne, kema kiyi abinda duk kikeso" hawaye ya sauko mata tasa gefan mayafinta ta daukeshi, ashe duk abinda akewa rigimar ma yana tare da ita su duka basu sani ba. Sanda suka isa guri ya dauki harama sosai, tace yusuf ya riqe key din motar zata kirashi idan ta tashi tafiya,saita wuce ciki. Batasan ya akayi ba tana shiga MC ya kama sunanta lokacin da aka kira ango da amarya,kwata kwata batayi niyyar hawa wajen ba,amma saboda ba yadda zatayi ta mige ta bude jakarta ta fidda rafas guda biyu na dubu daddaya sabbi qal a mige suna daukan idanu. Liqi sosai takewa nadeeya da nadir,me ya cika gurin da kambamata da kiran sunanta saboda ganin yadda take barin kudi,farinciki da qaunar säahar ya sake lullube nadiya. Cikin sabgar bikin tun daga kamawarta har zuwa yau da za'a gargare säahar din ita ta zame mata uwa kuma babbar yaaya. Riqota taji anyi ta baya,ta waiwaya kadan sai taga fadeela "Abby yana motarki yana kiranki" mamaki yadan kamata ta kauda wannan ta migawa fadeela sauran kudin tace ta liga musu,ta soma sauka daga step din a nutse, idanuwa suka sake yawa a kanta MC ya fara kwarara sagon godiya wanda har ya fita daga hall din bai daina zubata ba. Dukka hannayensa biyu ya saka yana dafe steering motar yana lumshe idanunsa hadi da furzar da iska me zafi a bakinsa. Har cikin tsakiyar zuciyarsa yakejin suya da zafin yadda bakin wani qato ke kiran sunan säahar din yana maimaitawa kamar shi va rada mata sunan, sosai yakejin zafi a zuciyarsa,yana cewa ya hanata zuwa gurin dinner din?, bama ta nadeeya ba, kowacce dinner idan ba tare suke ba, saboda shi kadai yasan abinda yake gani, Allah ya mata ajiyar wani irin kyau me sanyi da daukan hankali,irin kyan dake iya zamewa fitina ga mazaje idan ba'a hadu da mace mai kamun kai da miji mai kula ba. Shi kansa kullum ta Allah ya sake ganinta yake kamar wata sabuwa a idanunsa. Hana jan qofar ta bude, saita sake budeta sosai tana matsawa gaba zata shiga. Fes ya bude idanunsa da suka canza launi a kanta vana kallonta "Kata'i" ya samu kansa da furtawa,wani bacin rai yana sake lullubeshi saboda mahaukacin kyan da tayi,abu daya ya hana zuciyarsa gazawa,shigarta ta boye halittun jikinta sosai,saidai yau din tayi masa mahaukacin kyan da sai daya dauki mintuna yana dubanta kafin ya janye idonsa ya maida gaban motar yana jin kamar ya fashe da kukan takaici. Me yasa ya biye mata sukayi fada har ta samu damar yin tafiye tafiyenta ita kadai?. Fuskarta ta hade tsam kafin ta shiga motar bakinta dauke da sallama,har yanzu tana jin zafin cewa zai qara auren da yace zaiyi. Maida murfin tayi ta rufe,bai waiwayo ba vace "Waye ya baki izinin zuwa nan?" "Maji ce" ta amsa masa kai tsaye tana jin zuciyarta tana mata zafi itama "Mugullin motar ma itace tace ki bawa wani gardin ya kawoki?" Waiwayawa tayi da hanzari "Yusuf dinne gardi?" Ta jefa masa tambayar tana ) dubansa, shima juyowa yayi yana dubanta "(dan ba gardi bane mene?" Abinda ta gani a idonsa ya sanyata janye dubanta daga kansa ba tare da tace komai ba "Soyayyarki da nake miki ce ta Sanya kika fara rainani ko?" Yayi mata tambayar da zafi zafinsa yana jiran amsarta. "Wannan kwallivar da kika fita da ita wani gazami yana kiran sunanki ta mic shima duka maji dince tace kiyi?" Ya sake jefa mata tambayar. Gaba daya taji ta diririce da tarin tambayoyinsa, ta rasa wacce amsar zata bashi,sai kawai ta fashe masa da kuka "Ba aurenka zakayi ba?, kaje kayi,nima ka barni nayi rayuwata,dama ai ba sona kakeyi ba" "Ni dake waye baison wani? 3yrs amma ana zancan haihuwa kina dojewa,kije ki zauna abunki zan dauko wadda zata yita haifamin yara, kuma zakisan da gaske nake" daga haka ya tayar da motar ya fusgeta cikin bacin rai suka haura kwalta. Sai da yayi dai dai akan titi sannan ya sassauta gudun saboda yadda kukanta vake kassara jiki da zuciyarsa,amma ko akan fuska yaqi ya nuna hakan,bayaso ya bata wata qofa da zata gane lagonsa. Har taci kukanta ta godewa Allah basu isa gida ba,bata fahimci yawo kadai suka dinga yi saman titi ba sai bayan da taga sun qara goma a hanyar kafin su dauki hanyar gida. Sanda suka isa gidan ita ta fara fita a motar,sai bayan mintuna kusan goma ya rufe motar ya wuce ciki shima. Dakinta ta wuce abinta,ta fidda kayan jikinta ta fada wanka tana ajiyar zuciyar kuka. Karo na farko data fara kuka hankalinsa bai tashi ba bai kuma saurareta ba,abinda yayi matuqar sanyaya mata jiki kenan. Koda ta gama wankan tsaye tayi gaban madubin bandakin daure da towel tana kallon kanta, idanunta ta sauke akan cikinta,kamar yasan shi take kalla wani motsi mai garfi ya ratsa ta qasan mararta. Hannu ta saka ta dafe marar tana furta "'Subhana man khalaqal Janeen fil arham" wani hawaye yana cika mata idanu. Karkiyi missing last page Zafafabiyar "HUGUMA” •TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 75 Tasbihi ta dinga yi ga ubangiji cikin ranta,komai na rayuwa yana da iyaka,hakanan duk abinda bawa yaga bai samu ba lokacinsa ne baiyi ba. Cikin mutuwar iiki ta shirya ta haye gado, idanunta a rufe zuciyarta har yanzu babu dadi. Sunayen Allah ta dinga ambata a hankali, har wani bacci me nauyi yayi awon gaba da ita: Tunda suka shiga gidan ya wuce sassansa ya kasa nutsuwa cikin ransa,duk shirinsa zuwa kwanciyarsa kukanta ke masa amsa kuwwa a kunnensa, saidai duk da haka baiso ta gane lagonsa, da haka ya dake ya gama shirinsa. Har va kwanta ya dinga juyi,sam bacci ya gauracewa idanunsa, kusan minti arba'in yana a haka. Migewa yayi ya kunna wutar dakin ya sanya slippers dinsa ya dauki wayarsa ya fito. A nutse ya isa sassanta hancinsa na shagar wannan daddadan gamshin da yake mugun tasiri, qamshin da bai taba jin makamancin sa a wani waje ba sai a sassanta sai kuma jikinta,qamshi ne na musamman da gurinta kawai yakejin irinsa Shuru har ya isa gofar bedroom dinta, cikin jikinsa ya dinga jin kewar yaransa, da yanzun suna zaune a nan yana fama da rigimaru da fadace fadacensu. Dim light ne kawai a dakin, ya saki gofar ya taka zuwa ciki. Daga gaban gadon ya tsaya,ya sanya hannu ya kunna side drawer lamp sai ya rage haskenta kadan ya jawo stool ya zauna gaban gadon. Fes fuskarta ta bayyana cikin dan garamin hasken fitilar, innocent face din nan da yaga zallar kishinsa muraran a kwance a samanta, tuna hakan kadai ya sanya murmushi ya subuce masa,sai ya miga hannu ya shafi gefan fuskarta yana jin tausayinta kadan kadan yana ratsashi, ko yaushe qara kyau takeyi,sam shekarunta basa wani nunawa, idan kaga sa'ad da as'ad ba zaka ce itace ta haifesu ba sam. Ya kusa awa guda zaune a wajen kafin ya miqe, a nutse ya gyara mata duvet dinta ya mayar mata da lallausan gashin ta baya ya kashe fitilar bayan yayi kissing dinta ya fito. Yana matuqar son kasancewa cikin ilkinta a daren da ya fara busa wani yanayi na sanyi sanyi,amma kuma yana son ya zama taayayyen namiji,wanda so baya rufe masa idanu ya hanashi aiwatar da abinda ya dace. Yana shirin komawa ya kwanta kiran maji ya shigo masa waya,ya zauna sosai sannan ya daga wayar "Tare kuka fita da maami?" Kansa yadan shafa, säahar na vawan sakashi sauka a layi a cikin idanun maji "Eh muna gida" "Allah ya tashemu lafiya" ta fada a taqaice, don idan da sabo ta riga ta saba,musamman da ya zamana wannan zuwan da tayi din shi ba haka yaso ba,yafiso kullum tazo ne ta koma. "Zakuci ganiyarku tunda kuka bar yaran nan sun dawo din kenan" ta fadi a hankali. Hilma (wata cousin dinta)ta tabe baki "Wai nikam maji ko kishi yaronki bakyayi?, duka yarinyar nan ta gama juya masa tunani? ba zuwa ne na farko ba,duk zuwan da nakeyi abinda na karanta kamar yarinyar nan ta gama dashi, ya zama kamar wani bita zai zai, ya sanya ayiya ajiye miki yara suna yawo, ya maidata kamar alihunsa ke kina zaune?" Wayar ta saka tana duban hilma baki bude "Kinsan akan waye kike magana? to säahar ko kamata nayi tana zubawa moha maganin mallaka a abinci saidai na tayata juyawa,saboda nayi imanin ba mallakar da zata cutar da shi zatayi masa ba,babu suruka irin tawa kaf zamanin nan saidai tsakanin rabo don Allah karki sake magana makamancin haka akanta, inda kinsan me ta yiwa rayuwarmu mu duka da baki fadi haka ba" sanyi jikin hilma yayi, bata kuma sake cewa komai ba taja bakinta tayi shuru. Washegari jikinta babu qwari ta tashi, amma a daddafe ta shirya masa sassaugan breakfast ta koma daki ta kwanta. Sanda ya gama shirinsa na zuwa gidan maji,saboda a ranar nadeeya zasu wuce qatar da mijinta,ya bude breakfast din,sai baici komai ba ya hada ruwan tea ya sha ya fice,duk da zuciyarsa tanata otsa masa da son ganinta. Itama bata jima ba bacci ya dauketa, koda ta tashi farkawa garfe dava na saura, mamakin kalar baccin da tayi ya kamata,ta shiga toilet ta wanke bakinta ta dawo tayi nata breakfast din tayi sallar azahar,duka sai wata kasalar ta sake rufeta, ko awa daya bata rufa ba wani baccin ya sake daukarta. Stil ba ita ta tashi ba sai shida saura,a gurguje tayi la'asar tana istigfari,ta kalli agogo taba rayawa a ranta sauran mintuna kadan jirginsu nadeeya ya tashi. Taso qwarai tayi ma nadeeya din rakiya, saboda ita din ganwar miji ce ta gari qwarai da gaske, wadda samun irinta a wannan lokacin sai an tona. Samun kanta tavi da kunna wayarta da tun jiva da zata kwanta ta kasheta,batason ma ta barta a kunne don ta tabbatar za'a yita kiranta ne ana daga mata hankali, yadda kuma taga yanayin toufeeq din kuma tayi imanin babu wani maganar ya barta fita a yau din. Kamar jira akeyi kira kuwa ya shigo, nadeeya dince, muryarta can qasa ta daga "Jikinne maami?" "Alhamdulillah sister nadeeya da sauqi ai,ya taro?" Raunana muryar nadeeya din tayi sosai "Taro ya tashi maami, zamu wuce,ki yafemin... ." Sai kuka ya qwacewa nadeeyar. Sosai zuciyar säahar ta raunana, itama muryarta na rawa amma lallashinta takeyi,daga gefe taji shigowar muryarsa "Kiyi kuka ki sakata kuka? wanne irin shirme ne wannan?" Sai kuma taji wayar ta katse. Kanta ta saka a gefan gado,sai kuka sosai ya I gwace mata,kukan da take tasan bawai na nadeeya kadaj bane,wani raunin zuciya kawai takeji cikin girjinta,can deep inside her sabaninsu da toufeeq yana kassarata amma kuma taqi bawa zuciyarta amanna akan hakanne. Ta jima a haka kafin tayi controlling kanta,ta miqe tana ninke abun sallarta, saita tsaya kalion kanta gaba madubi. "Anya zata iya jurewa?" Ta tambayi kanta. Sai ta koma da baya ta zauna. A hankali ta fara tuna asalin faruwar matsalaryawan kiransa da yarinyar da batasan ko wacece ba takeyi,tun tana kau da kai har ta magantu. Dariya sosai ya dinga yi kafin yayi mata bayani "Ni ban santa ba, infact ma ban taba daga kiranta ba bare naji muryarta,ina dake bani da buqatar kowacce diya mace a duniya,so ki kwantar da hankalinki, a yanzun bana ganesu gaba daya". Hankalinta ya kwanta a lokacin, tunda tayi imanin baya magana biyu kamar yadda qarya ba dabi'arsa bace. Ranar da ya rage saura kwana biyu bikin nadeeya,tana ta zagaye zagayen yadda zata gaya masa zasu tafi gobe, zasu kwana har sai an kammala biki, tunda tasan bayaso,bayan ya shigo sun gama welcoming nashi ya wuce wanka,ta bishi ta fidda masa pyjama din da zai sanya cikin sabbin pyjamas din data siya masa da kudinta. Tana zaune saman sofa kira ya dinga shigowa wayarsa,tun bata tsargu ba har ta tsargu, sai tasa hannu ta dauki wayar "Soulmate" shine abinda taji an fada. Kalmar ta daketa sosai iya duka,amma sai tayi controlling kanta ta maida wayar ta ajjiye. Daure da towel ya fito a gugunsa, jilkinsa sharkaf da lema data jige gargasa da sumar qirjinsa. Tana gaba madubi,ya risketa ya kama qugunta ya hade da nasa,ya dora kansa saman kafadarta yana kallon fuskarta ta dikin madubi "Inason baby girl me irin fuskar nan sosai, yaushe zaki harama?" Sai taga kamar gatse yakeyi mata,don haka ta zame jikinta tana cewa "Ni da haihuwa ba yanzu ba" sak yayi yana duban fuskarta sai kuma ya basar yaci gaba da qoqarin shirya kansa. Rashin tankawarsa sai zuciyarta ta yunquro,shaidan ya dinga raya mata kamar akwai abinda ya taka shi yasa bai damu ba don tace haihuwa ba yanzu ba. Fita tayi tabar masa dakin, kafin ma yazo kwanciya ita ta gama shirya yara suna dakinsu tazo ta shirya itama tayi kwanciyarta. Mutum ne shi bai matugar bawa dan adam uzuri qwarai da gaske don haka koda ya sameta a kwance sai shima ya shirya yabi bayanta. Sanda va fara aike mata da sagonni sai ta tankwabe saqonsa,daga qarshe ma ta miqe tana sauka daga kan gadon, mafi munin abinda shi kuma yafi tsana kenan kaf rayuwarshi "Mun zama second hand fa,a bari amarya tazo,gobe idan Allah ya kaimu zamu wuce gidan maji,sai kafijin dadin sakewarka da yin waya da soulmate din taka® shuru yayi ya zuba mata ido yana kallonta,duk maganganun da takeyi kuma taqi bari su hada idanu,sai kawai ya miqe ya dauki abinda zai dauka ya canza daki. A daren ya dinga qoqarin cooling down kansa da kansa,har zuwa wayewar gari yana shirin fita sai gata, ta sake shaida masa zasu wuce fa gidan maji "Ba da vawuna ba" abinda ya fadi mata kenan ya fice. Yana office maji ta kirashi, ta kuma bashi umarnin ya dauko mata sãahar din da yara ya kawo mata su. Bai tambayi ba'asi bai kuma musanta mata ba,ya katse duk abinda yakeyi ya koma gida ya daukosu kamar yadda maji ta fadi, saidai abinda ya fara daga mata hankali da taji yana waya,salon wayar da bata gamsu ba,saidai kuma bata gane da mace ne ko da namiji yake wayar ba. "Zamu tafi" tace dashi tana dubansa sanda ya saukesun,jikinta yana danyin sanyi. Maganganun da ya gaya matan sune suka tsaya mata a rai matuqa Ajiyar zuciya ta sauke tana jin ranta duka babu dadi "Astagfirullah" ta fada qasa qasa, tana hango rashin kyautatawar muraran. Knocking din baaba ramatu taji,sai ta bata izinin shigowa "Sau uku ina kewayowa amma banji mitsinki ba,gashi dare yayi kuma ba'a dafa komai ba duk da tagwaye basa nan" dan murmushi ta saji,tana jin dadin kulawar da baaba ramatu ke basu "Yanzu zan fito baaba, tare zamu sbiga kitchen din, a cire nama a freezer danye a zuba masa ruwan zafi" "To shikenan, saikin fito" tace da ita. Gefan sofa ta koma ta zauna,ta jawo hula ta sakawa kanta,sannan ta miqe tsam tayi kitchen. Duk da dare ya soma kawo kai, amma haka ta zage a nutse ta shirya masa dinner sassauqa amma ta musamman tare da taimakon baaba ramatu. Har ta gama bataji shigowarsa ba, itama hakan yayi mata dai dai, ta kammale komai ta barwa baba ramatu gyaran wajen. Sai data gamsasa gidan da dukka nau'in turarukan da tasan yana so sannan ta wuce bedroom dinsa. Kintsashi shima tayi,bai wani hargitse ba duk da kwana biyu kenan Bata nan ta sanyayashi da turaren da ta tanadeshi ne kawai saboda bedroom dinsa sannan ta wuce nata dakin. Kayan jikinta ta cire ta fada toilet, ta zuba man wanke gashi sosai ta wanke sumarta sannan tayi wanka ta fito. Tanata sage sage tana gogarin busar da kanta a gaban madubi tana kuma duba agogo, qarfe tara saura na dare, cikin ranta tana mamakin me ya tsayar dashi har kawo wannan lokacin bai qaraso gida ba. Har ta ajiye Drayer din zata fara taje kanta taji an turo gofar da sauri lokaci guda ana kiran sunanta. A nutse ta waiwaya,asad ne da as'ad sai kuma fadeela biye dasu. Kamar yadda suka saba, kowa rige rigen isowa gareta yakeyi, murmushi ya qwace mata tana dubansu. A rayuwarta kaf tanason wannan moment din,tana jin babu wata uwa data kaita a duniya. Murmushin ta yayi dai dai da kallon bakin qofar dakin da tayi. Zafafabiyar "HUGUMA* •TABARMAR KASHI_* Book 02 Page 76 Yana tsaye bakin gofar dakin sanye da trouser da shirt charcoal color da yayi matuqar haska fatarsa. Idanunsa a tsaye carr a kanta,yadda sumar kanta ta bazu a sassan fuskarta da farar lalalusar fatar jikinta sai ya zama kamar wani ado ne a gareta, fuskarta tayi fayau tayi kyau sosal. Shi ya fara dauke idanunsa,ya juya a hankali da zummar barin gurin, zuciyarta sai ta karye "Sannu da zuwa" ta fada da karyayyar muryarta,bai amsa ba yaci gaba da takawa yana barin wajen. Sosai zuciyarta ta sake karyewa,banda yaran dake mararin ganinta ba zata iya ci gaba da tsaiwa bata bishi ba. Duk irin tsauri da zafin zuciyarsa zata iya cewa bata taba ganin fushi haka da I don't care manner haka a tattare dashi ba. A daddafe ta zauna ta biyewa shirmensu da hirarrakinsu,sannan ta samu ta tattarawa baaba ramatu sunata cewa "Gobe zamu koma maii tace a hada mana kayanmu" "Allah ya kaimu" tace da as'ad yafi kowa dokin komawar. Cikin nutsuwa ta bude gaba daya closet dinta, idanunta akan kayanta daya bayan daya. Tsaida kallonta tayi akan was kaya,murmushi ya kubce mata, tana iya tuna ranar data sanya masa kayan, cak ya dagata sama ya juyata sosai,babu inda baiyi kissing a jikinta ba kafin labari ya sha banbam. Tsaf ta shirya cikin kayan, ta tsaya sosai gaba madubi ta yiwa gashinta wani irin gyara me tafiya da hankali,sannan ta fesheshi da sassanyan hair mist. Kayan abincin ta kwashe ta mayar sassansa, bata sameshi a falo ba, tayi imanin yana cikin toilet yana wanka,abinda bai taba faruwa a tsakaninsu ba kenan. Kusan ko yaushe wankansu tare sukeyi,koda tayi nata wankan idan ya dawo sal ya batashi,wani irin mutum ne da tara vaara basa hanashi baje kolin soyayyarsa, baya tsufa da soyayva hakanan idanu basa hanashi nunawa matarsa qauna da kulawa. Ta godewa Allah da va bata maji a matsayin suruka,mace me fahimta wadda al'adarta tasha banban data bahaushe, tayi imanin banda hakan da tuni ta fara ganun canjin fuska saboda kukawa gauna da tattali da yake nuna mata. Tana da kawaici qwarai da gaske, a kullum bata gajiya da sake iadda masa girman amanarta dake wuyansa. Kafin ya fito ta gama kai kawonta tsakanin sassanta da na yaran,ta tabbatar ta sallamesu, kiwa yayi shirin kwanciya dukbda weekend ne goben sannan ta wuce sashen nasa. A nutse ta bude bedroom dinsa, har yanzu still yana toilet, saboda tana iya jin qarar saukar ruwa. Zare hijabin jikinta tayi ta aje saman sofa. Dakin takebi da kallo _r a nutse,ko na kwana daya ta masa daga dakin sai taji tayi kewarsa,tana mamakin vadda ameesha ta iva rabuwa da toufeeq,yana da shiga rai ya kuma hada dukkan wasu. qualities na miji na gari. Matsawa gaban dressing table dinsa tayi tana gyara turarukan da ya zube akai,gefe kuma qaramar jakar ce me kyau dauke da tambarin company din da yayi siyayyar. Daya daga cikin kwalaben ta daga, favourite turarenta ne, siyo mata yayi kenan?, ta tambayi kanta,duk da yana fushi da ita amma hakan bai sanya ya manta ko ya wofantar da duk abinda ya shafeta ba "Shi din na musamman ne" zuciyarta ta gaya mata hakan "Good men still exist one of them is mine" ta fada a fili hadi da lumshe idonta tana rungume turaren a qirjinta. Baivi zaton ganinta ba sanda ya bude gofar amma maganar da ta furta gasa gada ta shiga kunnensa,can gasan zuciyarsa wani abu me sanyi ya saukar masa, baqin gashinta me qyalli idanunsa suka fara sauka a kai sannan a hankali suka sauka zuwa gadon bayanta da fiye da rabinsa yake a bude fara tas din fatarta ta dace da launin bagar rigar jikinta. Ta cikin madubin take satar kallonsa,tsayyayen jikin dake gine da wasu muraddun muscles, tashin farko taji kewarsa ta cikata. Wani irin mutum ne shi mai •r tsayawa a zuciya a kowacce tarayya zakayi dashi. Cikin sa'a ya lura da satar kallonsa da takeyi ta gasan ido duk da ta fara fusgar hankalinsa amma sai ya dauke idanunsa daga kanta 'yan miskilancin suka motsa. Qaramin towel ya saka yana goge ruwan sumarsa data jikinsa,sumar kansa mai santsi da laushi duk ta cakude,yaja stool ya zauna gaban dressing table din daura da ita har yanzun kuma bai dubi sashenta ba. lya maqura haqurinta ya gaza,ta ajjiye kwalbar turaren hannunta, ta taka a hankali ta zagaya bayansa. Qaramin towel din hannun nasa ta rige da kyau,suka hada ido ta cikin madubin, saita dage masa dukka girarta biyun. Bugawa zuciyarsa ta danyi yana jin wani abu yana bin sassan jikinsa,ya lumshe kyawawan idanunsa yana sakar mata towel din salin alin, ita kuma ta zare towel din a hankali ta dorashi saman sumar tasa. Cikin wani irin salo ta soma nutsa yatsun hannunta cikin sumar tasa,a hankali ta soma yamutsata cikin wani irin yanayi da ya tilasta masa rufe idanunsa ruf yana jin duk wani motsi na zara zaran yatsun nata har cikin kwanyarsa. "i feel bad for making you sad am sorry for making you loose your temper, sorry for being rude and hurting you with my words,i promise not to repeat it ever" idanunsa 5° ya lumshe yana jin zagin kalamanta. Tana da baiwar iya kalami mai sanyaya zuciya da cire duk wani fushi da bacin rai duk da shi dama bawai har vanzun vana fushi da ita bane,a'ah,he want to teach her lesson. Ci gaba tayi da yamusa gashin nasa tana kuma tayar da kowacce tsiga ta jikinsa. Ganin yayi shuru bai amsata ba sai ta dan bubbuga qafa a shagwabe "Kace wani abu pleaaaaaaaassssseee.i can go to any extent to make it up to you,am sorry from the bottom of my heart,please better half..... forgive me manaaaa,) miss your sweet voice, your hug and your smile,sorry for hurting you" still har yanzu ya kasa bude idanunsa,duk da zuciyarsa kamar zata fito daga qirjinsa yakeji wani wata irin soyayya me motsa zukata,tare da tsananin shauginta da yakeji, muryarta kadai na neman rikitashi. A nutse ya bude idanun nasa ya watsasu a kanta "Ba wani, baki sona,bakin sadaukarwa da wata ni ba?" Kuka ta sake ta sake masa tana bubbuga qafafunta a gasa tamkar qaramar yarinya, abinda ya bawa boobs dinta damar motsawa qwarai yadda zata samu damar jan hankalinsa sosai. Burinta ya cika,don gaba daya kasa motsawa yayi daga inda yake zaunen, sosai take masa shagwaba tana tsaye daga gabansa,shi kuma ya lalace a kallonta yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da sauri da sauri. A nutse ya miqe yana gyara zaman towel dinsa a qugunsa,sannu a hankali yake takowa a nutse saiji tayi ya sakata cikin jikinsa,ya rungumeta tsam ta baya. Kusan lokaci guda kowannensu ya saki ajiyar zuciva ya dora tattausan tafin hannunsa saman ruwan cikinta ya fara yawo da su yana shafa fatar saman cikin wani yanayi yana ratsashi. Hannu daya ya saka yayi gefe da gashinta sake fake va barbazu a bayan nata. Cikin wani irin yanayi dake nuna zallar shaugi da yadda qauna ke kassafa jiki jini da bargo ya dora labbansa saman wuyanta, abinda ya sanyata daukewar wuta sama numfashinta na wasu daqiqu kafin ya dawo dai dai "No matter what happens you will always remain my biggest priority" ya furta mata da wani sirrintaccen sauti da ita kadai ta isa ta jishi. ) "No bodv above mistake,you are a wife material na sani, sometimes i look at you and i wonder How i got to be so damn Lucky" sosai kanta ya fasu,sai fa dinga jin duk duniya babu macen data dace da miii irinta" "I will make up for all the days i ruined baby" itama ta maida masa cikin yanayi na rad'a hadi da sakar masa dumin numfashin bakinta. Zafafabiyar TABARMAR K'ASHI HUGUMA BOOK 02 PAGE 77 END Wani numfashi ya aje mata da ya ratsata har cikin kunnenta,sai ya sake mannata sosai da jikinsa ya mayar mata shima cikin rada " melt when you call me baby" "And i like when you call me yours" ganqameta yay cikin jikinsa kamar zai maidata su hade su zama abu guda "You are mine and only mine, all rights reserved" ido ta lumshe zuciyarta na dandana zaqin kalamansa,tanaji kamar ta sanya hannu ta fiddo zuciyar tata ta miqa masa "Mohhhh" ta kirashi da wani sirrintaccen suna da ita daya ke kiransa da shi a irin wanann yanayin "SAHR" ya amsa mata shima ilkinsa na amsa sagon da take aika masa dashi a fakaice ta sautin murvarta da tsaiwarta cikin jikinsa "I really want to kiss you,and not just on the lips" kaman an fusgeshi da lantarki yaji, sai ya sake qangameta da kyau kafin ya saketa, yaja baya sosai yana bude hannuwansa gaba daya kamar wanda yake jira ayi hugging nasa sanann yace "Kiss me moonbeam,kiss me iya yadda kikeso, I don't care if it's 5minutes or a whole night,i am always ready to cheer you up,no matter the time place or situation" •cikin wani irin taku me janye hankali ta garaso gabansa,ta Sanya hannunta ta rige gefe da gefan fuskarsa,sanann tayi dage don ta samu isa ga bakinsa saboda ya fita tsaho "No...wait" ya fadi da sauri, hannunta ya riqe da kyau ya dagata ya dorata saman qafafunsa, ta tsaya sosai a kansu,ya tallafo qugunta ta baya yadda ba zata fadi ba tsaiwar kuma zatayi mata dadi "Thank you" ta fada tana hade fuskokinsu guri guda. Yadda take sauke masa salon kisses kala kala ya sake narkar da zuciyarsa cikin gaunarta,tun suna a tsaye a hankali har tsaiwar ta gagaresu suka zube saman gado. "I Know you want me but I want you to tell me" ya fada numfashin yana fusgarsa, ko ina na jikinsa yana rawa "I want you,i need you...." ta fada itama lafuzzan suna rarrabe mata saboda bugun da zuciyarta keyi da qarfi sosai. Daga nan ya kasa ci gaba da bata dama,ya fara maida mata zazzafan martani, wanda shi yayi jagorancin kaisu wata duniva me nisa wadda daga shi sai ita suke iya fahimtarta. Tsahon rabin awa kafin komai ya daidaita,jinsa shuru baice komai ba sai saukar numfashinsa me dumi a fatar ilkinta ya sanyata motsawa,da sauri yace "Shshshis..... don't move,when i am holding you,the whole world makes sense" sake gyara mata kwanciya yayi sosai a jikinsa,dumin jikkunansu yana ratsa kowannensu "Ki qaramin lokaci,inason wanann yanayin,i prefer silent conversation,ones our bodies speak and our hearts listen" birkota kanta da kanta tayi fa juyo tana fuskantarsa,saita shige cikin jikin nasa sosai ta kwantar da kan nata a qirjinsa tana lumshe ido hade da murmushi. Wannan ya bata damar jin qamshinsa sosai,ta zuqi numfashi tanajin dadin qamshin kamar yau ta fara ji. Yatsantsa daya ta saka tana wasa da gargasar qirjinsa "Mohhh" ta sake kiransa a nutse "Am all ears" "Am jealous" wani qaramin kyakkyawan miskilin murmushi ne ya qwace masa "Yes i know" "Ehhnnn?" Ta fadi tana buqatar qarin bayani, zamewa yayi a hankali yana boye fuskarsa tsakiyar qirjinta "Am sorry NUGGET,na fada ne kawai saboda nayi tsokana,saboda kada ki tafi, but bazan sake cewa zan kawo wata ba gidan nan, banyi alqawarin bazanyi ba, amma banayi da sha'awa bana kuma fata har abada" "I can't bare to loose you" "Zamu zama a tare har abada" kalmominsa sun wanke mata rai fes sai ta sake narkewa a ilkinsa. Migewa yayi da hanzari "Gate up nugget" ya furta yana qogarin dagata tana dariya qasa gasa hadi da sake narke masa. ******Washegari** Tana farkawa hayaniyarsu da kakacinsu ne ya isketa har kan gadonta, muryar toufeeq asad da as'ad sai fadeela. Kai ta girgiza a hankali tana sakin murmushi, qarfi da yaji sun maida abby din nasu magananne wani lokaci ita dinma ko da ta gudu ta barsu sai sun zagulo ta Wayarta ta daga ta kalla tana murmushi, babu arziqin da ya wuce wannan a rayuwa,samun lafiyayyen family me cike da farinciki da qaunar juna,ga arizigi da wadatar rayuwa. "Ikon Allah" ya furta a hankali, saboda kwanan wata yana nunawa yau hajiya qarama ta cika kwanaki arba'in da rasuwa. Wayarta ta ajjiye tana sauka daga gadon tana ji a ranta ya kamata suyi mata sadaka na kwanan arba'in din. Toilet ta wuce kai tsaye don ta tabbatar gidanta a gyare yake fes sannan breakfast ma ya kammala, abinda kawai zatayi gyaran bedrooms dinsu. Cikin mintuna qalilan ta gyare bedrooms din nasu. Wani kyakkyawan zama sukeyi wanda zaka samu Muhammad toufeeg jarma kamar bashi ba cikin gidansa. Yana iya zagewa su gyara duk part din da suka kwana a ciki fadeela na tayashi. Säahar takan jima tana mamaki har wataran yace "Komai isa dukiya da taqamarka a wajen matarka holoqo ne kai, sannan komai izzarka da jin ka isa kai din ba kowa bane idan bakayi koyi da fiyayyen halitta ba,yace mafi alkhairinku shine mafi alkhairinku ga iyalinsa,shin bazan so na kasance mafi alkhairi ba nima don ranar gobe na shiga jerin sahun mutanen da prophet Muhammad S A W zaiyi alfahari dasu ba?" A ranar har qwalla sai da tayi. Kwata kwata idan ka kwantanta rayuwar ADAN da TOUFEEQ misalin rayuwar matacce ne da rayayye. Takan rasa da wanne irin kalmomi zata godewa Allah da bata shi da yayi. Tana shiryawa bayan ta fito daga wankan tana tuna jinyar hajiya qarama, har ta mutu bakinta yanason fadin wasu maganganu amma kuma Allah bai bata iko ba,saboda ba'a ji ba'a kuma gane abinda take fada, saidai duk sanda taga wani abu da ya shafi dr ko toufeeq tayita kallonsa tana hawaye, idan taga su asad kuwa tayita son kama hannuwansu kenan. "Allah yasa muyi kaykkyawan qarshe" säahar ta fadi tana warware sabuwar lafayarta 'yar borno me tsananin kyau da tsada. Haka kawai yau tayi sha'awar yi masa kwallivarta da safe,tsaf ta nade jikinta da ita,ta kuma lullube gashinta me tsaho da santsi wanda ta zubo dashi gaba ya rufe rabin goshinta ta zagaya dashi vabi ta bavan kunnenta ta kuma daureshi da babban ribbon. Best perfumes nashi ta yayyafawa jikinta sannan ta dauki wayarta ta fito. Idanunta na akan wayarta, bata lura da shi ba saida sukayi clashing. Dukkansu sukaja baya suna kallon juna, babu abinda yazo zukatansu sai rayuwarsu a MT JARMA GLOBAL COMPANY. Baya yaja ya harde hannayensa a qirjinsa yana mata wani azababben kallo from head to toe,ba abinda yake masa yawo a kai sai sanda take irin dressing din nan,ganinta na farko da ya farayi a mt jarma a matsayin president dinsa. "Wanne irin mutum ne kai mara kirki mara iya mu'amala? wanda baisan kima da martabar dan adam ba? me yasa dukkan zancanka kudi? me yasa kake hangen kudi sune gaba da komai?" Ta fada tana tsuke fuska tamkar a lokacin abun yake faruwa. Takowa yayi a hankali yana sauke dogayen yatsun qafarsa saman Tallausan carfet din hallway din. Gabanta ya iso ya sulale yana sauke dukka gwiwoyinsa a gasa hadi da hade tafukan hannayensa guri daya ya kawosu saitin bakinsa "Am sorry mr president, am arrogant, ki yafemin" kai ta dauke gefe "Nooo, you are fired" dariya ta qwace masa ya mige da sauri ya dagata cak yana dariya "Baki isa ki koreni ba, zan karba kora daga kowanne guri a fadin dunivar nan amma banda daga nan wajen" ya fadi yana nuna saitin zuciyarta da yatsarsa. Dariya itama sosai ta qwace mata tana sake rigeshi "Nasha wahala qwarai da gaske don duk sanda kikazo da shigar laffayar nan haka kawai sai naji zuciyata tana zafi, kuma gashi kullum ina sake qoqarin tabbatarwa kaina komai bai hadamu ba,coz na tsorata da na kasa jin haushi da tsanarki a zuciyata kamar yadda nakeji ta sauran dukka mata at once....... shigar na masifar yi miki kyau da qara miki kwarjini,zaki iya tuna ranar da na kori jamal?" Kai ta gyada don ta tuna "Kamashi nayi yana hirar kyan da kikeyi da laffaya,sannan kina boye dirinki ne a ciki, ranar kwana nayi da zazzabi, kamar zan mutu haka naji, but ban gane so bane, rabon dai sai na sha wahala kafin na sameki" murmushi ta saki tana jin dadin labarin, uwa uba kuma tana a jikinsa ne yana takawa da ita zuwa parlor "For the first time na hadu da macen da kudi kyau ko matsayi basa gabanta,na hadu da mace me sadaukarwa irin sadaukarwar nan me tsada sadaukarwar da za'a yi maka ita a boye ba tare daka sani ba,ta warware min tunani na na dukka mata mayun kudi ne,zasu iyayin komai saboda kudi,ta dauki dukiyarta tayimin hidimar da kudi bai isa ya biyata ko ya siyeta ba.....sanda kikacemin zakiyi aure ne ba zaki dawo kici gaba da kula da fadeela ba.....kinsan saura kadan zucivata ta fashe? sanda kikace kin amince zaki aureni kinsan yaya naji?" Kai ta girgiza,sai ya kada kai kawai yana murmushi, don baisan yadda zaiyi mata bayani ba "Baki da wayo da gaske na yarda, baki taba tunanin me yasa naqi yarda muyi yarjejeniya cikin aurenmu ba?" "Gayamin please, don ka yaudareni da gaske fa abby" dariyar da ita daya ke samun irinta ya saki "Ban aurenki don mu rabu ba,koda banason mace bazan aureta don mu rabu ba,hakanan malamai sun tabbatar duk auren da aka daurashi bisa wani sharadi ki yarjejeniya to wannan auren BATACCE NE" "You are the real definition of deciever" "Na yarda indai a kanki ne" "Abby......yara fa, saukeni" ta fada da sauri gain sun kai qarshen hallway din suna gab da shiga parlor, ga kuma muryar yaran tana jiyowa "Ai madam tuhumarki nakeyi fa" ido ta fiddo "Dame?" Sauketa yayi ta tsaya cak da qafafunta, idanunsa cikin nata yace "Jiya naji wani gagarumin sauyi,ina suspecting ban ruwana yayi kyau‚na jefa kyakkyawar qwallo a raga" kunya taso kamata amma saita waske "Bansan wannan zancan ba" "Ki rantse" ya fada yana takowa zai risketa,a yadda taga yana kallonta tsaf zai iya cewa zaisha mintinta,don haka da sauri tace "Na rantse ina kyautata zaton haka ne" tsintarsa tayi kawai yayi sujoodush shukr, koda ya dago hawaye ne cikin idanunsa "Ya rabb, baiwar da ka yimin na gode,ya Allah kasan inason baiwar nan taka, Allah kaci gaba da yiwa rayuwarta dama rayuwar duk abinda zata haifa albarka" r jikinta ya qara sanyi, zuciyarta na qara cika da soyayyarsa. He's strong man, amma akanta a nan weakness nashi yake,dole ne tayi duk me yiwuwa wajen kyautata masa shi da mahaifiyarsa,ta kuma kula da tarbiyyar yaransa,wannan shine abu daya da zata saka masa dashi. Ita ta taka ta dagashi, ta riqe hannuwansa tana duban idanunsa "'Duk kalmar da zanyi amfani da ita wajen maka godiya sai naga tayi kadan" murmushi ya saki yana dora yatsansa kan lebanta "Kici gaba da kasancewa dani har garshen rayuwarmu" "'Nayi alqawari" kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai muryoyinsu asad ya fara dososu "Anima zamu fita mu maidawa maji su as'ad,daganan zamuje Sr raheema ta dubamin lafiyan baby girl dina" dariya ya bata sosai "Baby girl kuma?" "Yes in sha Allah, twins baby girls" "Maami zata haifa?" Muryar as'ad ta shigo da tambayar. Harara sãahar ta jefa masa,sai ya dan tsaya ya Rama kunnensa duka biyun yana kebe baki "Am sorry bazan sake ba maami, amma inason baby girls don Allah maami ki siyo mana a kasuwa,ni banason Teddie's din nan‚masu magana nakeso" dariya ya basu gaba dayansu, har fadeela data bivosu zata kamasu ta maidasu parlor "Ka fara shirin zuwa suna hanya in sha Allah" toufeeq ya fada yana kama kumatunsa qaunar yaran da suke debo tsananin kama dashi tana sake mamayeshi kwatankwacin yadda yake qaunar mahaifiyarsu maami sãahar. . Tammat Alhamdulillahi rabbil Aalamin_ -*Dukkan yabo godiya da jinjina sun tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da aminci su tabbata ga shugabanmu annabi muhammad* *ina miga matuqar godiya da jinjina ga dukkan kafatanin masoyana,wadanda basa gajiya da bibiyar labarina, basa gajiya da bibiyar gamayyar marubutan zafafa biyar, Allah ya qara dangon gauna da soyayya yasa wanna tarayya tamu ta zame mana silar alkhairi da samun tsira* "Mun gode* "Mun gode* * _zafafabiyar na godiya_* *Haqiqa SAI DA KU* AARO _ina fatan sagon da nakeson isarwa va isa kurakuren dake cikin wanann rubutu Allah ya yafe mana,ya taramu a ladan_ • "Bazan rufe ba tare da na ambaceku ba jama'ar ZAUREN TABARMAR QASHI,na gode qwarai da hadin kanku* _sai mun sake haduwa a littafi na gaba idan me duka ya bamu aron rai lafiya da kuma dama_ _subhanakallahumma wani hamdika,ashahadu an la'ilaha illa anta,astgafiruka wa' atubu ilaika_ Downloaded From https://tknovels.com.ng